*_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖0️⃣1️⃣ .......Ƙaddarorin rayuwa tamkar TASWIRA ce dake zane a takardar lissafin rayuwar kowanne ɗan adam, duk yanda ka so gogesu ko san kauce musu ba lallai ne ka samu makaman yaƙin ba balle GARKUWAR kare kanka daga isowarsu gareka ko mai gajartar tsahon shekaru ko yawaitarsu. A wasu lokutan mukanyi kuka ne da hawaye, sai dai kukan ZUCIYA shine mafi ciwo da ɗacin kuka da yafi kassara rayuwarmu da nasarorinmu a ɓoye ko a zahirance da bama iya mantawa. Dan a wasu lokutan har tambarin tabon da zamu iya ringa tunawa a lokaci bayan lokacin yake bar mana.     A farkon haihuwar mu iyayenmu sune GARKUWARMU, dan sukan sadaukar da komai nasu ne domin lulluɓe RAYUWARMU da dukkan fatansu. Sukan rainemu da shauƙi da yaƙini har zuwa girmanmu. Hakan yake saka SOYAYYAR su bata taɓa iya goguwa a ZUKATANMU, sannan takan banbanta da irin kowacce soyayya da zata biyo bayanta. Koda hukuntamu sukai mukaji zafi mukai kuka wannan soyayyar tasu bata taɓa canja kanta a ZUKATANMU saboda su ɗin sune dai ɗaya tamkar da dubu a dukkan abubuwan dake zagaye damu na NASARA ko akasinta.        A lokacin da girmanmu ke ƙara yawaita sai TSUFA ya riskesu. Mu kuma ƘURUCIYA ta baibayemu. Sai dai me daga lokacin daka iya tantance ma'anar FARI da ƁAKI a yau ɗinka da gobenka littafin ƘADDARARKA kuma ya fara kenan da manyan zanukan layukan dake bayyana JARABAWOYINKA. Gwagwarmaya ta zama ƙawa ko abokin RAYUWARKA. Yaƙin ba yana farawa da gwagwarmayar RAYUWAR DUNIYAR kawai bane ba. Harda ta neman LAHIRA da zaɓama kai makoma ƙyaƙyƙyawa ko akasinta. Domin kuwa fara rayuwar girman na farawa ne da daidaiton mizanin ayyukan samun LADANKA da kuma ZUNUBI duk a bayyane kuma a rubuce ga wanda ya HALICCEKA. Iyayenmu kan gama gwagwarmayar ƙuruciyarmu, sannan su koma ta girmanmu babu gajiyawa saboda su ɗin na dabanne a cikin daban a garemu.       A lissafin fara fahimtar kanka da tabbatar da WANENE kai, da wahala kaga babu armashin soyayyar ƙuruciya da takanyi kutse a ƙaddararka. Ba soyayyar bace ba kawai abar kallo ko zama daban a gareka ko wanda ke tare da rayuwarka. A yaya SOYAYYAR ta FARA? Ko ta ƙare? Ko ta kasance? Ko ta cigaba da wanzuwa? Itace madubin dubawarka ko masu juriyar bibiyar labarinka.      ★ Ƴammata ne uku sanye cikin kayan hidimar ƙasa. Tsaye suke a bakin titi kowacce hannunta riƙe da hannun trolling alamar abin hawa suke jira. Dan suna ma ta ƙoƙarin tsaida napep amma mafi yawanci sai kaga akwai wani a ciki ta yanda bazai isa su ukun duk su shiga ciki ba. Cikin ɗan damuwa da ƙosawa ta tsakkiyarsu da bata da yawan fara'ar fuska ta ɗaga kai tana kallon sararin samaniya dake haɗa hadari. Ko kaɗan bata fatan ruwan nan ya taɓa ta. Dan hakan baya zama mai sauƙi a gareta shiyyasa tafi kowa damuwa da samun abin hawan nasu, daɗin daɗawa tafiyarsu mai nisa ce. Dan kuwa jihar Kaduna suka nufa.        Fara tasowar iskar hadarin ta sata duban ƴan uwan nata idanunta na cika da ƙwalla. Sai dai kafin ta samu damar cewa wani abu wata jar mota tai parking a gabansu. Su duka idanu suka zubama motar, sai dai buɗewa da fitowar matashin saurayin dake ciki ya saka biyu a cikinsu sakin murmushi da mamaki. Yayinda ta tsakkiyar sun nan dai ta sake haɗe ƙyaƙyƙyawar fuskarta tana mai kauda kanta gefe. Shi kam saurayin nan gaba ɗaya hankalinsa na kanta. Ya ƙaraso gabansu dai-dai saitinta ya tsaya tare da faɗin, “Yanzu duk saurin da nake sai da kika nema guje min?”.      Fuska ta sake haɗewa tana ɗan matsawa baya. Kansa ya ɗan sosa yana mai sakin murmushi. Hankalinsa ya maida ga sauran biyu cikin jifansu da harar wasa ya ce, “Amana batace dai haka ba friends. Kamar ni ina daku amma a so haɗa kai da ku a gudu min”.      Dariya suka ɗanyi a lokaci ɗaya. Ta gefen damarsa mai ɗan jiki kaɗan ta bashi amsa da, “Ina ai bazamu taɓa yarda hakan ta kasance ba. Ko an gudu maka mu zamu kawoka har wajen ɓuyar RK. Amma ai mana afuwa mutuniyar taka ce ta addabemu da tafiyar sassafen nan. Kasan jiya ko barcin kirki batai ba saboda farin cikin zata koma gida taga Ammie”.            “Ko dai tana farin cikin zata gudu daga Jos ta bar ɗan nacinta ba?”. Ya faɗa idonsa a kan budurwar tsakkiyar dai. Da sauri ta gefen haggunta ta amshe da “Haba RK kaima kasan ba haka bane sam”.      “Humm Aneesa dama ai baƙya son laifinta ke tuni na fahimci haka. Duk ta inda aka ɓullo sai kin kareta. Ni dai yanzu ku shiga mota muje kunga ruwa na shirin sakkowa karya jiƙa min sarauniyata”. Kafin wani cikinsu ya bashi amsa a hankali ta fara jan akwatinta domin barin wajen. Saurin riƙo akwatin yay, hakan ya sata tsayawa cak batare da ta juyo ba. Zai yi magana Aneesa tai saurin girgiza masa kai tare da amsar akwatin. Babu musu ya sakar mata yaja da baya.     Akwatin tai ƙoƙarin ƙara ja Aneesa ta sake riƙewa. Hakan ya sata juyowa a fusace zatai magana a zatonta shine sai taga Aneesa. Idanunta tai wani irin lumshewa da cizar gefen lips ɗin ta irin na takaicin nan kawai. Hakan ya saka Aneesa sakin murmushi dan tasan ta gama ƙurewa a fusata. “Kiyi haƙuri dan ALLAH” ta faɗa da sauri, bata jira amsarta ba ta cigaba da faɗin, “Kiyi haƙuri mu bisa _Maanal_, kalla garin nan ki gani hadari ne da akoda yaushe za'a iya fara ruwa. Kinfi kowa sannin illar da hakan yake miki. Kema kin san iyakarsa yace zai kaimu tasha ne kawai. Daga yau ne fa an rabu shike nan kuma. Dan ALLAH kada ki bari kuyi irin wannan rabuwar da shi. RK bai cancanci hakan daga gareki ba. Ko bazaki taɓa amince masa ba kada ki munana masa a yau ɗin nan da zamu rabu. Yanda baki wulaƙantasa ba a baya yanzu karki aikata. A rabu lafiya daga haka kuma bashi ke nan ba tunda ko lambarki dai yanzu bai da ita ballema kice zai cigaba da takura miki, ba kuma sanin gidanku yay ba idan kika cire sunan gari”.       A hankali ta buɗe idanunta da suka gama kaɗawa, ga hawaye sun cika su zubowa kawai ya rage. Lips ɗinta ta buɗe zatai magana ruwa yay wani irin kecewa lokaci guda. Gaba ɗaya ta rikice. Har bata ma san Aneesa taja hannunta ta tura cikin motar ba itama ta shiga. Sai da taji babu saukar ruwan a kanta sai ƙararsa sannan ta farga ta ɗago kanta data cusa cikin ƙafafunta da sauri. Waigowar da zatai suka haɗa ido da RK daya wani zuba mata ido kamar zai cinyeta. Nata ta janye da sauri tana mai juyawa ta kalla ƙawayen nata. Da sauri Zeezah ta nuna Aneesa alamar babu ruwanta itace. Aneesar ma saita marairaice mata fuska alamar kartace komai dan ALLAH. Harara ta sakar mata tare da ɗauke kanta, sai kawai ta juya tana goge fuskarta da ruwa ya fara taɓawa da handkhachief.....      Tunda motar ta fara tafiya babu wanda yay magana. Ga ruwa ana kwararawa kamar da bakin ƙwarya. Tuni wasu motocin ma sun koma gefen titin sun tsaya. Ganin sunzo sun wuce tasha yasa Zeezah yinƙurin yin magana. Da sauri RK dake kallonsu ta mirror yay mata alamar roƙon tai shiru. Haɗiye maganar tayi tana murmushi, sai kuma ta ɗan dubi Maanal da kanta ke sunkuye novel a hannunta alamar karatu takeyi, shiyyasa bata san wainar da ake toyawa ba ma.        Shima dai RK ya raba hankalinsa biyu ne. Rabi ga tuƙi rabi a kallonta. Maanal ƙyaƙyawar yarinya ce kuma nutsatstsiya. Za'a iya kiranta tsaka tsaki a tsaho, a wani gurin kuwa ma wasu kai tsaye zasu kirata doguwar duk da ba shalleliya bace, sannan bata da wani jikin kirki. A duk wanda ya santa musamman a tsukun shekarun nan zai iya sakata a jerin miskilayen mutane. Bata da yawan magana, hakama bata da fara'a ko yawan walwala sam. Dan da wahala kaga murmushi ma a fuskar Maanal balle akai ga dariya. Akoda yaushe fuskarta ciɗin-ciɗin take. Hatta da magana ma sai taso take yinta. In har ba wani abu take mai muhimmanci ba to akoda yaushe zaka samu novel a hannunta tana karantawa. Hakan na nufin ita ɗin mayyar karance-karance ce. Dan zamu iya cewa ma yawan karance-karance nata ne yasa koda yaushe zaka samu idanunta da eyeglasses fari tas da mutane da yawa basa iya ɓoye mata cewar yana mata matuƙar ƙyau. Itama kanta tasan yana mata ƙyawun, dan takai tun ma tana sakashi domin karatu, har ya zame mata jiki akoda yaushe zaka ganshi tare da ita in har ba barci take ba ko wani abinda ba'a buƙatarsa. Sai dai kuma abinda kowa bai sani ba wani dalili ne daban ya ɗabi'antata da yawan daka gilashin akoda yaushe bawai dan karance-karance kawai ba, duk da a ɓangaren karatun ma yana bata gudummawa matuƙa........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ _________________ Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki _______________ 🅿️➖0️⃣2️⃣ .......Ganin tafiyar taƙi ƙarewa yasata kai hannu ta ɗan gyara eyeglasses ɗin tare da ɗagowa ta kalla titi, har yanzu ruwa ake zulawa, sai dai hakan bai hanata fahimtar har sun fara barin gari Jos ba. Da mamaki a karo na farko ta dubi RK da tunda ta ɗago ya kama kansa daga satar kallonta da yake yi. Kamar zatai magana sai kuma ta kauda kanta. Sake maidawa tayi ga book ɗin, sai dai ba karatun take ba tayi shiru ne kawai tana juya maganar da take son fitarwa. Sai da ta mula dan kanta sannan a hankali cikin sassanyar muryarta da take matuƙar zama mafi girman rowa ga masu son ji irinsu RK ta furta. “Bayan waccan tashar akwai wata ne a gaba naga mun wuce?”.         Har cikin tsakkiyar kai yaji gajeren zancen nata. Sai da ya wani lumshe idanunsa ya fuɗe tare da sakin murmushi sannan ya bata amsa da, “Bazan iya saukeki a ko'ina cikin ruwan nan ba kiyi haƙuri sai a Abuja”.       Ɗagowa tai kamar zata kallesa sai kuma ta fasa. Sake maida kanta tai ga buk ɗin kawai tana ɗan cizar gefen lips ɗinta. Murmushi ya ɗan saki shima dan ya fahimci wannan cizar lips ɗin nata takan yisa a duk sanda takai ƙarshen takaicin da har ta rasa abin cewa.      “Kiyi haƙuri Please”.   Ya sake faɗa a hankali. Bata tanka masa ba, sai ma sake maida kanta tai a karatun kawai. Shima sai yay gum da bakinsa ya maida hankalinsa gasu Zezaa tunda dai ya samu da alama ta haƙuran. Tanata karatunta suna hirarsu. Yawan sakkota a hirar tasu da dariyar da suke ya fara gundurarta, sai kawai ta manna Bluetooth a kunnenta ta ajiye book ɗin ta lumshe idanunta. A haka barci ya kwasheta tana sauraren karatun Alkur'ani data sanya daga bakin Gwani Abdullahi Zaria. Har suna gab da shigowa garin Abuja ruwan akeyi, har kuma lokacin Maanal barci take sosai dan sam batai isashen barci jiya ba. Addu'a yay tayi da fatan subar Abuja bata farka ba. Dan yasan zata iya tuburewa akan ya ajiyesu anan ɗin, aiko addu'ar tasa bata amsu ba. Dan sun wuce zuba kaɗan kuwa ta farka. Agogo ta fara kalla sannan ta juya tana kallon su Zezaah.      “Muna ina ne yanzu?”..   Ɗan kallon juna sukayi, sai Zezaah tai tsulum tace, “Mun fita a Abuja”.         Da mamaki Maanal dake kallon titi ta ce, “Mun fita fa? Wannan ba hanyar suleja bace? Ko nan ba madalla bane?”. Yanda ta ƙare maganar tana kallon RK ya sashi ɗan sosa goshinsa yana furzar da iska. Sai kuma ya jinjina mata kai ganin ta wani tsaresa da idanunta dake matuƙar firgita masa lissafi. Kanta ta ɗauke tana faɗin, “To Alhamdullah sai ka sauke mu a dikko kawai ai zamu samu motar Kaduna a wajen”.        Sosai fuskarsa ta nuna damuwa. A marairaice ya ce, “Haba miya rage Baby, tunda mukazo nan can ma bazai gagara ba. Kiyi haƙuri mu ƙarasa, ina Abuja ina Kaduna”.      Yanda yake mata magana kamar zai yi kuka yasa haushi ya sake kamata. Mutumin nan sam baya ganewa, ta rasa mi kuma zata masa ya gane ɗin. Duk yanda taso hanasa kaisu kadunar hakan bai yiwu ba. Dole tana ji tana gani ya ɗauki hanya. Hankalinta ta sake maidawa akan novel ɗinta ta sharesa. Sai su Zeezah ne keta hirarsu da shi. Yanzun ma ko sun sakkota bata tankawa. Suna isowa Kawo tace ita anan zata sauka. Yi yay kamar bai jita ba. Cikin ɓacin rai ta juya tana kallon su Neesa. Cikin jin haushi, duk da muryar tata na fita ne da sanyinta da nutsuwa ta furta, “Malamai kusa ya saukeni anan tunda naga da sawarku yake komai”.            Kafimma su bata amsa RK yay saurin faɗin, “Sorry Baby babu ruwansu. Ni dai fatana sai na direki har ƙofar gida dan ALLAH”.    Yanzu kam harara ta zuba masa. Ya wani lumshe idanu da buɗewa a lokaci guda ya saukesu a kanta. Da tasan ta'asar da harar nan ke masa data tausaya masa ta bari. Ganin dai zata kife da shi yay ƴar gyaran murya yana wani marairaice fuska. “Please ki tausaya min hararar nan illa take min”. Ya faɗa a wani irin hankali kamar mai raɗa har yana ƙoƙarin ɗan matso ta. Janye jikinta tai ta lafe a murfin tana rumtse ido da ƙarfi. Daga haka bata sake magana ba. Su Neesa ne suka shiga nuna masa hanya har anguwarsu Maanal ɗin data kasance cikin manyan anguwannin da kadunawa ke ji da su (Ina da tambaya?, wai Kaduna akwai anguwanni masu ƙyau dan ALLAH ko sai sun zo Kanon mu suke gani kawai😂🥱🤪🤪. 🏃🏃🏃Bari na ware kafin ƴan Kaduna su maidani awara yau ɗin nan kun san bazazzage ba sauƙi🤣😘). Dai-dai ƙofar wani katafaren farin gate da akaima ado da golden suka tsaya. Ya wani sauke ajiyar zuciya yana kallon gidan da ƙyau. Eh lallai ashe itama ƴar masu kuɗi ce. Dan gidan nan kam dai ya kai a kirashi gida.....         Fitar Maanal a motar ta sashi saurin katsewar tunanin sa. Shima da sauri ya buɗe ya fita. Dai-dai tana ƙoƙarin buɗe booth. Shine yay saurin sakko mata da akwatin ta. Ya juya da nufin sauke nasu Neesa taja kayanta. Su Aneesa da suka gama fahimtar mi take shirin yi duk suka fito. Magana Zezaah tai yunƙurin mata tai mata wani kallo na babu ruwanki da ni taja akwatinta tai gaba. Sai da tai ɗan taku uku zuwa huɗu ta juyo ta kalla RK daya zama kamar gunki a tsaye. Idanunta dake cikin gilashi ta ɗan lumshe ta buɗe a kansa. “Mun gode da ƙoƙarinka. ALLAH yabar zuminci. Amma zan baka haƙuri dan ALLAH karka cigaba da wahalar da kanka, kamar yanda na faɗa maka gaskiya tun a farko itace dai har yanzu. ALLAH ya haɗamu da alkairinsa a yafi juna”..      Kafin yay wani yunƙuri harta shige gida. Ƙoƙarin binta yay da hanzari mai gadi dake tsaye daga ciki ya babbake ko'ina ya hanashi. Dole ya dakata yana mai kai hannu ya ɗan dafe goshinsa da furzar da iska mai nauyi...........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖0️⃣3️⃣ ______________ Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki _______________ ........“Kayi haƙuri dan ALLAH RK”. Aneesa ta dawo da RK dake bin maigadi da kallo idanunsa sun kaɗa sosai. Iska ya ɗan sake furzarwa batare daya daina kallon maigadi ɗin ba. Sai kuma yay murmushi da gyara tsaiwarsa hannayensa duka biyu a cikin aljihu. Kansa ya ɗan girgiza tare da juyo da dubansa yana kallon Aneesar fuskarsa da murmushin dake bayyana damuwarsa. “Baku min laifin komai ba Aneesa. Haka itama banji haushinta ba sam. Sai dai bazan iya rabuwa da ita ba kamar yanda take buƙata. Da gaske ina son ƙawarku matuƙar so da ban taɓama wata mace ba da sunan soyayya ta aure. In dai zan jure waccan shekara gudar data shuɗe mizai hana na iya jure wannan balle yau dana san gidansu. Zan cigaba da farauta nasan watarana zan dace in sha ALLAH”      Zezaah da ranta yakai ƙololuwar ɓaci ta ce, “Humm amma RK kasan dai Maanal da kafiya. Wlhy duk abinda tace bazatai ba bafa zatayin ba. Ya kamata kaima ka gane hakan tunda dai kagani. Shekara ɗaya cur ana abu ɗaya amma komai bai canja ba. Taya yanzu kake tunanin zata canja da kuke nesa da juna?”.          “Nabar komai a hannun UBANGIJI, shine mai sarrafa zuciyoyi a yanda yaso ai Zulfah, ina ji a raina zata canja”. RK ya bata amsa yana haɗiye damuwarsa. Aneesa ce tai ɗan murmushi, har cikin ranta tausayinsa take ji. Murya ta kwantar cike da son kwantar masa da hankali ta ce, “In sha ALLAHU kam tunda ka dogara da ALLAH zakaci riba. In dai Maanal matarka ce kuwa sai ka aura, itama nasan ba tana yin komai danta wulaƙantaka bane, akwai dai wani dalili, saboda duk wanda yasan Maanal sani na gaskiya yasan bata da wulaƙanci, na nesa da itane kawai ke mata kallon girman kai amma sam ba haka bane ba wlhy”.      “Nima shaida ne Aneesa, shiyyasa nake mata uziri”.     “Nagode sosai daka fahimci haka RK. Bari muje mu ƙarasa gida muma, mun gode sosai da ƙoƙarin ka, ALLAH yabar zuminci ya saka da alkairi. Mun tasoka tun daga Jos”.       Murmushi ya saki mai sanyi. Sai kuma ya girgiza kansa tare da shafa kwantaccen sajensa ya ce, “Babu damuwa. Dama Abuja zanzo ai. Ku ba nan anguwar kuke ba kenan?.”          “Eh anguwannin duk daban-dabanne”. Zeezah ta bashi amsa.     “Oh to ku muje na kaiku ai har gida kuma. Kunga idan na tashi dawowa saina tattaroku dan ƴar darun nan tawa al'amarin ta sai da ku a kusa”.     Dariya sukayi gaba ɗaya. Babu musu suka koma motar yaja suka bar anguwar. A gidan su Zezaah duk suka ce ya saukesu. Dan basu da nisa da Aneesa da ƙafa ma zata ƙarasa. Su Zeezah dai ba masu kuɗi bane ba. Amma akwai rufin asirin ALLAH. Da alama ƴar darun tasa ta fisu komai dai kam. Godiya suka masa da sake bashi haƙuri. Ya tabbatar musu babu komai sai ya dawo dubasu zuwa weekend. Zai kuma kirasu a waya in sha ALLAH. Daga haka yaja motarsa ya wuce...        ★★★★★      A hankali ta jingina da jikin gate ɗin ƙwalla na cika mata ido. Dauriya kawai takeyi, amma tausayi RK ke bata matuƙa. Ta jima da fahimtar irin ɗunbin soyayyar da yake mata a cikin idanunsa. Sai dai tasan bazata iya bashi abinda yake buƙatar ba. Kota bashi ma zata cutar da shi ne kawai dan bazai taɓa samunta yanda yake huƙata ba. Dan zuciyarta ta jima da mutuwa. Mutuwa irin wadda mushenta ma baida daɗin kallo. A zahiri take Maanal, amma a zuciya tuni ta mutu, ta mutu babu ita a wannan rayuwar... RK na tuna mata abubuwa da yawa a rayuwarta da sam bata son tunawa, shiyyasa akoda yaushe take yakicesa a jikinta ta ƙarfin tsiya. Amma shi ya kasa fahimtar akwai wani ciwo ne a zuciyarta da ya jima da raunata ta ta yanda babu wani ɗa namiji da zai sake morarta.....      Raff-raff!! Sautin tafi da dariya ya sata dawowa hayyacinta. Hannu ta kai ta share guntun hawayenta kafin ta kai dubanta ga mai dariyar da basai an mata ƙarin bayani ba tasan Huznah ce. Ita ɗince kuwa. Ƙyaƙyƙyawar budurwa fara doguwa san kowa ƙin wanda bai samu ba. Zata girmeta a shekaru, girma ma bana wasa ba dan Huznah zata iya zama kusan sa'ar babbar yayarsu duk da dai ita yayar tasu zata iya girmarta....             “Agola kafi ɗan masu gida. Wato iskanci yayi lagwada har ba'a so dawowa gida ba kenan?”. Huznah ta faɗa tana watsa mata kallon wulaƙanci.      Idan gate ɗin da ke kusa da su ta motsa to Maanal ta tanka. Dan kuwa daga kallo ɗayan nan bata sake dubar ko sashen da Huznah take ba taja akwatinta tai gaba cikin tafiyarta mai sanyi da tarin nutsuwar da kowa ke ɗauka iyayi da yanga ce. Sai dai kuma hakan a gareta normal ne. Dan tun ma tana tashen rashin jinta tafiyarta mai sanyi ce.      Ba ƙaramin takaici rashin tankawar ya saka Huznah ba. Cikin haushi ta lailayo ashariya ta maka ma Maanal. Sai dai yanzun ma bata samu amsa ba, Maanal ɗin kuma bata waiwayo ta dubeta ba harta shige ɗaya daga cikin ɓangarorin gidan. Domin ɓangare har biyar ne a gidan ciff kasancewar matan mai gidan uku ne. Sai sashensa, sai kuma na samarin yaransa. Ƴammatan dai kowacce tana sashen uwarta ne....                Shigowarta sashen nasu da abinda ta taras ya wanke mata gaba ɗaya damuwarta. Dan kuwa taci karo da ƴan uwanta biyu da yaransu duka sunzo gidan domin dawowar tata kawai. Ai tuni ta watsar da damuwar RK data Huznah suka rungume juna. Sosai suke matuƙar ƙaunar junansu ta yanda idan ka gansu kai kanka sai sun matuƙar burgeka.            “Amma Didi kikace min ke bazaki wani zo tarbata ba”.      Dariya wadda ta kira da Didin tayi tana mai dungure mata kai da faɗin, “Naƙi zuwa babarki ta ƙulaceni Auta”.       A tare suka kwashe da dariya, dai-dai nan wata dattijuwar mata cikin kwalliya ta fito daga wani lungu mai nuni da hanyar kitchen ne dan hannunta riƙe yake da wani ɗan bowl. Tuni Maanal ta saki yayunta ta nufi matar da sauri ta wani daka tsalle ta rungumeta. Dariya yayunta da yaransu suka sanya. Yayinda matar ke faɗin, “Oh ya ALLAHU jama'a sai yaushe Maanal zata girma ne? Yanzu idan kika karyani fa?”.        Cike da shagwaɓa, tare da sake shigewa jikin matar ta ce, “Ni dai bazan taɓa girma ba Ammie. Nayi kewarki fiye da kowa da komai. I really miss you Ammie na”.             Ƙaramar dariya Ammien ta saki mai ƙayatarwa, tare da sake rungume ɗiyar tata a jikinta tana mai sumbatar kanta da faɗin, “Nima nayi kewarki sosai Maanal. Congratulations my Auta, yau dai finally an gama boko.”       “Kai Ammie dama ana gama boko?”. Ta faɗa cikin dariya mai ƙayatarwa da mutane da yawa basu san tana yi ba. Itama Ammien dai dariyar ta sake yi, sai kuma ta ɗagota tana mai ƙare mata kallo da ƙyau. “Auta duk kin sake rame min, kina lafiya kuwa?”.             Kanta ta kwantar a jikin hannun Ammien data riƙe, sai kuma ta amsa da, “Lafiya Lau nake Ammie. Kewarki ce kawai ta hanani sukuni”.     “Oh wai kin damu mutane da kewar Ammie kawai. Kina nufin mu bakiyi kewarmu ba ne Auta?”.          “To Sarkin kishi, ALLAH Ammie ban taɓa ganin mai kishinki sama da Didi Amal ba. Kijifa dan ALLAH, nayi kewarki itama dole sai nayi kewarta?”.    Jefota da filo Amal tayi, da sauri ta kauce tana murmushi. Yayinda Didi Shahidah da Ammie da yaransu ke musu dariya..........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_**_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖0️⃣4️⃣ ______________ Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ________________ .......Bayan an natsa da murnar dawowar tata da gaishe-gaishe Ammie tace ta wuce ta gaida mutanen gidan. Fuska ta ɓata kamar zatai kuka, sai kuma ta shiga roƙon Ammien akan dan ALLAH ta barta taje tai wanka ta canja kayanta tukunna. Ammie zata ƙi su Amal suka tayata roƙonta. Dole ta barta taje ta fara wankan sannan, yayinda su kuma suka cigaba da aikin shirya abinci dan dama girki suke sanda ta shigo.       Ɗakin da yake mallakinta ta shiga, an gyarashi tsaf ga ƙamshi mai daɗi na turaren da take matuƙar so na tashi a cikinsa. Sosai ɗakin ya haɗu, sai dai haɗuwar tasa baisa ta taɓa jin daɗin zaman gidan ba. Kawai dai tana zaune ne saboda mahaifiyarta na'a cikin gidan ne. Duk kuma inda Ammie take rayuwa koda a dokar daji ne itama zata zauna ta rayu saboda a duniya bata haɗa komai da soyayyar da takema mahaifiyarta ba. Ita ɗin dabance a zuciyarta. Idan tace daban tana nufin daban a cikin dukan daban. (ALLAH ka gafartama iyayenmu, wanda suke raye ka bamu ikon ƙyautata musu😭🙏).      Jacket ɗinta ta fara cirewa, tare da ƙurama rigar ido tana mai sakin murmushi. Finally yau ta gama sarvese, duk da Ammie tace boko ta ƙare, itafa a gareta yanzu ne aka saka ɗanba, sai dai Ammie tayi haƙuri amma sai taga ƙarshen biro in har ana ganinsa. Sanin yaran can zasu iya shigowa su fara addabarta yasa taƙarasa zame kayan nata da sauri-sauri ta ciri towol daga Waldrop ɗinta fari tas ta ɗaura. Bayin ta nufa dan tasan duk abinda zata iya buƙata Ammie ta saka mata shi kasancewar ta jima bata gida. Dan watanni biyar kenan bata zo ko weekend ba. Tunma data wuce sarvese sau ɗaya tazo gida, ɓacin ran data gumtsa a zuwan yasa tai alƙawarin ƙin sake zuwa har sai ta kammala. Alhamdullah kuma gashi sai da ta kammala ɗin.          Wanka tayi na gaske. Dan sai da ta tabbatar ko'ina na jikinta ya mata yanda take so sannan ta fito tana raɓar ruwa da ƙamshin shower gel ɗin ta mai shegen daɗi daya gauraya da na sabulunta da turaren wanka. Maanal tasan sirrin gyaran jiki da kula da jikin ma. Dan yarinya ce ƴar ƙwalisa akwai son gayu. Damma ba Maanal ɗin da bace data taso da shegen son kwalliya kamar ƴar aljanun. Tana tsaka da shafa mai Amal ta shigo. Cike da tsokana ta ƙaraso gareta tana faɗin, “Uhm kaga ƴar ƙwalisar gidanmu Autar Ammie. Irin wannan ƙamshi haka kamar zaki tashi gari”.        Murmushi mai sanyi Maanal ta saki da ɗan girgiza kanta tana ajiye man hannunta data matsa. Wanda ta matsa ɗin ta fara shafawa a fuska tana faɗin, “ALLAH Didi sai kisa a rataye mutum a tsakiyar kasuwa. Daddyn su Safnah na haƙuri dake gaskiya. Yanzu mine abin wani ƙwalisa anan daga shafa mai dai sai wanka. Ni ko fauda bazan shafaba ma”.            “A'a wlhy dole ki shafa. Zakije gaida waɗan can ƴan tsirkun ai sai kin cakare. Dama ga ɗan mutuminki yazo garin, dan muna shigowa da shi na fara cin karo a harabar gidan nan ɗazun”.     Cak Manaal ta dakata daga shafa man da take zuciyarta na wani irin motsawa da ƙarfi, a take fara'ar fuskarta ta ɓace ɓat. Sai kuma ta fara haɗiyar numfashi da sauri-sauri. Fahimtar hakan ya saka Amal wayancewa da faɗin, “Amma ban sani ba ko shirin komawa yake a lokacin dan da akwati na gansa ma fa. Fitinanniyar uwarsa a tare da shi ko rakkiya tai masa oho musu”.             A hankali Manaal ta saki numfashin data ɗan riƙe a maƙoshinta. Sai kuma ta cigaba da shafa manta da kauda zancen ta hanyar faɗin, “Ina dai fatan kin soyo min fara ta Didi?”.     “Harma da su Alewar madara Munaya ta matsa nai miki”.         “Oh my sweet daughter ɗina, Shiyasa nake son yarinyar nan. She is my bestie”.      “Uhm kudai kuka sani. Ni tashi ki shirya ke ake jira aci abinci. Kin san yau akwai hira duk an haɗu”.     Murmushi tayi cike da jin daɗi, dan tafi kowa son irin wannan haɗuwar tasu. Takanji kamar su dawwama a haka tare gaba ɗaya kamar yanda suke da can. A gurguje ta shirya cikin doguwar rigar Abaya milk color da ɗan kwalliyar coffee kaɗan a jiki. Ta saka turarrukanta masu sauƙin ƙarfi. Suna ƙoƙarin fitowa Shahidah ta shigo ɗakin, dariya suka sanya mata dan sun tuna baya. In dai kaga Shahidah tai irin wannan shigowar fuska a ƙwaɓe to abinci aka ajiye zasu fara ci sukuma suka maƙale a ɗaki hira, ita kuma sam bata da jimirin yunwa musamman idan ta dawo daga makaranta ta kwaso rana. Sai ta shigo cikin haushi tana faɗin (“ALLAH idan baku fitoba zanci nawa ne”).        Baki suka haɗa wajen furta (“ALLAH idan baku fitoba zanci nawa ne”). Ai ba shiri Shahidah ta sanya dariya da musu daƙƙuwa. Daga haka suka rankaya suka fito inda Ammie ke zaune a tsakkiyar falon da ƴan jikokinta zagaye da ita. Dan a anan aka shirya abincin yanda za'aji daɗin ci fiye da saman table.      Manaal na zama yaran duk suka matso kusa da ita kowa na faɗin tare da ita shi dai zai ci. Ganin abin zai zama rigima ta miƙe tana faɗin, “Kunga ku jira ku gani”. Kitchen ta shiga sai gata da babban faranti ta ɗakko, ganin haka Ammie tace, “To ai kawai zuba gaba ɗaya anan Auta sai muci duka baki ɗaya”..      Cike da farin ciki suka ci suka ƙoshi, damma Ammie ta hana surutu. Bayan sun kammala babbar yarinyar Didi Shahidah mai suna Barru ta gyara wajen tsaf sauran yaran na tayata. Maanal ya gyara zama da tunanin Ammie ta manta da batun zuwa gaida mutanen gida sai Ammien ta harareta da faɗin, “Oya tashi kije gaida mutane”.        Fuska Maanal ta ƙwaɓe sai dai babu yanda zatai dole ta miƙe. Hannun ƴar gaban goshinta Munaya ta kama suka wuce tare. ALLAH badan Ammie ba babu inda zataje. Da sashen Hajiya Yaya ta fara. Hajiya Yaya itace uwargida a wannan gida na Alhaji Usman Chalawa. Tanada yara bakwai tare dashi. Babban shine kaɗai namiji sauran duk mata ne. Macece mai son mulki da ƙyamar talaka. Dan mahaifinta kamar ma shine silar arziƙin mijin nasu shiyyasa take jin komai na gidan ta isa da shi kuma dole a bita har shi kansa mai gidan ma. Sai dai kasancewar shi ɗin tsayayyen namiji ne a gidansa yasa wani abun bata da power a kansa, dan in ma ta nuna ƙarfa-ƙarfar yakan saurin taka mata birki. Kasancewar ta mace ta farko a gidan part ɗinta yafi na kowa girma da tsaruwa, sai dai hakan ba yana nufin na sauran matan ma bai haɗu bane. A'a a komai dai natan yana sama dana kowa kasancewar ita ta fara tarewa a cikinsa.     Sai da Maanal ta dana door bell har sau biyu kafin ta tura ƙofar falon da sallama duk da tasan ba sallai a jita ba kasancewarsa ƙaton gaske ne. Ilai kuwa babu wanda ya amsa mata sallamar duk da kuwa kusan duk yaran na falon harma da ita kanta Hajiya Yayan. Sai dai kasancewar ta danna door bell kafin shigowar yasa duk suka maido hankalinsu ga ƙofar dan son ganin mai shigowar. Suna yin tozali da Maanal wasu a cikinsu suka kauda kawunansu cikin jan tsaki. Yayinda Hajiya yaya ta zubama Manaal ɗin idanu tamkar zata cinyeta da su. Sai Autar Hajiya Yayan da zata iya zama sa'ar Manaal ɗin mai suna Amrah ce tai murmushi tare da miƙewa cike da farin ciki tana faɗin, “Oyoyo mutanen Jos sauka haka babu notis”.     Murmushi Manaal ɗin tai mata, yayinda ita kuma ta rungumeta. A dai-dai nan idon Manaal ɗin ya kai ga ƙaton dining table dake gefensu kaɗan. Sosai zuciyarta ta motsa sakamakon saukar ƙwayoyin idanunta akan wanda ke zaune a wajen shima ya zubo ma inda take idanunsa masu kaifi.........✍️        ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖0️⃣5️⃣ ______________ Aslm barkanmu da wannan lokaci Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka Mallaka Maganin sanyi Maganin cire tumbiMaganin farin jini Maganin matsiMaganin mata Maganin sa ni’ima da dandano Dulka Amare Set na gyran jiki Set na amarya Tabaje tsumin Gomba Xuma kiba ta hips and Brest Magungunan gyran Brest Magungunan Karin hips Maganin sliming Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291 Idan maganin mata kikeso akwai Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻 Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k🥭 Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500 Garin bata gaban kishiya 500 Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500 Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500 Za a bakisu akan 3800 Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k 🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki ________________ ......Da sauri ta kauda idanun nata tamkar bata ganshi ba. Sai ma cikin wayancewa ta ɗago Amrah tana faɗin, “Wai haka kika ƙara lukucewa matar nan?”.     Dariya Amarhn tayi da kai mata mintsini a gefen hannunta itama tana faɗin, “Ke dai zauna nan kamar za'a hureki. Ni kin san bana wasa da cikina”.     Murmushi kawai Manaal ɗin tayi batare data bata amsa ba. Hakan yasa Amrah jan hannun Munaya tana mata wasa. Da wannan damar Maanal ta ƙarasa cikin falon sosai. Cike da girmamawa ta kai duƙe duk da kallon wulaƙancin da Hajiya Yaya ke mata da sauran yaran ta shiga gaidata a mutunce. A yatsine ta amsa mata sau ɗaya ta ɗauke kanta. Hakan ya ƙona ran Maanal matuƙa amma sai ta daure, fuskarta da ɗan murmushi ta maida ga sauran yaran ta shiga gaishesu dan duk sun girmeta. Babu wanda ya amsa mata sai ma tsoki da wasu suka ja mata. Dai-dai nan saurayin nan dake zaune a dining ya miƙe zai fita a falon yana kai waya kunnensa alamar zaiyi magana.        “Ina kuma zakaje Yazeed?”.    Uwar ta ƙatse masa hanzari da ƴar tsawa-tsawa. Cikin dakiyarsa ya juyo da hannu yay mata nuni da waya zaiyi, batare da ya jira sake cewarta ba ya fice abinsa.          “Hummm! Wai shi mai wayo fa Mamma”.     Ɗaya daga cikin ƴammatan ta faɗa fuska a kumbure. Kafin wani ya bata amsa Maanal taja hannun Munaya suka fice suma. Duk rakata sukai da harara, sai kuma wadda tai maganar ta miƙe zumbur tana faɗin, “Ina zuwa bari na muku leƙen asiri. Dan nasan ko rantsuwa zanyi babu kaffara dan ita Yaya ya fita a falon nan babu wata waya da zai amsa”.         “ALLAH nima na fahimci haka Nanah, dan tunda ta shigo ya dakata da cin abincin ma sai wani binta da kallo yake. Kinga muje”.      A hasale Hajiya Yaya ta furta, “Aiko da naci ubansa a gidan nan yau. Tunda na rabashi da yarinyar nan na kuma haramta masa alaƙa da koda inuwarta ma balle ita. Amma kuje ku ganar min yana ina”.      Ai kafin ma uwar ta rufe baki sun fice da sauri har su uku. A dai-dai fitowar tasu kuma Manaal ke shigewa sashen Hajiya Basariyya. Hajiya Basariyya itace mace ta biyu a gidan. Itama dai ɗin ba kanwar lasa bace ba. Dan ba mutuncin ne da ita ba. Sai dai ita akwai banbanci tsakaninta da Hajiya Yaya. Dan a zahiri baka isa fahimtar ita ɗin wacece ba saboda macece mai fuska biyu. A zahiri akwai faran-faran da jama'a da son nuna ita ɗin ta ALLAH ce. Shiyyasa mutane da yawa sai ta gama musu illa suke farga da ita ɗin wacece. Macijin sari ka noƙe ce ita ta bugawa a jarida. Yaranta biyar itama a gidan kuma duk mata, dan ita bata da namiji ko ɗaya. Huznah da Maanal ta fara haɗuwa sanda ta dawo itace ƴarta ta farko. Itama ɗin dai family nata akwai kuɗi, dan Yayanta daya riƙeta hamshaƙin mai arziƙi ne. Kuma babban aminin Alhaji Usman Chalawa ne, suna huɗɗar kasuwanci sosai da har wasu ma ke ganin dukiyarsu a cuɗe take da juna. Shiyyasa itama bata yarda Hajiya Yaya ta ɗaga mata hanci ta ɓangaren dukiya dan kar ce tasan kar. Kowa najinsa a wani shege. Komawa su Nanah sukai nasu sashen cikin taɓe bakuna. Dan Manaal na ƙoƙarin shiga sashen Hajiya Basariyya shi kuma yayansu nama ficewa a gidan da motarsa.        Tun ma kafin su ƙaraso Hajiya Yaya data cika tai tab ta fara jeho musu tambaya cikin huci dan macece mai ƙiba sosai. Irin ƙibar nan bata wasa ba. Dan ko daga nesa ka hango ta kasan ALLAH yayi manyan mata a wajen nan. Zaune duk suka zube cikin takaicin rashin samo abinda za'aci mutuncin Maanal da uwarta yau a gidan. Nanah tace, “Mamma yama fita a mota. Ita kuma ta wuce sashen Momyn Suhana”.     Cikin ƙwafa da takaicin itama bata samu yanda take so ɗin ba ta ce, “Ya taimaki kansa. Dan wlhy da yau har shegiyar uwartata sai sun bar gidan nan. Kai na tsani mutanen nan a rayuwata”.      “Ai bake kaɗai ba Mamma”. Cewar ƴarta ta biyu mai tana huci. Auren nata ne ya mutu kusan shekara uku kenan tana gidan. Dama ita kawai ta aurar, rana ɗaya akai bikinsu da su Shahidah yayun Maanal. Sauran kuma ALLAH bai kawo ba, ko muce ruwan ido da jiran ƴaƴan masu hannu da manda irinsu ya hanasu auruwa. Burin kowannensu da ma uwarsu shine suyi auren ƙwarya tabi ƙwarya.. Buɗe shafin zagin su Manaal sukai a falon kamar sun tare musu numfashi, sai Amrah ce keta ɓata fuska dan ita bata son hakan. Ita birgeta ma Ammien take a rayuwarta mace mai dattako da sanin ya kamata. Babu ruwanta da duk abinda iyayen nasu keyi a gidan sabgar gabanta takeyi kawai da ƴaƴanta. Ko su duk abinsu bazasu taɓa cewa ga randa Ammien taima wani abu mara daɗi ba, amma tasa miyasa basa sonta da yaranta?...      A ɓangaren Maanal can ma door bell ta fara dannawa kafin ta shiga. Shima dai sashen Hajiya Basariyya da suke kira da Momyn Suhana ya matuƙar haɗuwa. Girmansa kuma ɗaya dana Ammie. Ita dai bata falon sai su Huznah da ƙannenta dake cin dafaffen gyaɗa suna hira. Duk sun zubar da kohon a saman lallausan carpet ɗin tsakkiya ko'a jikinsu. Dan sun san mai-aiki ce zata gyara basu ba. Har zata juya batare data musu magana ba sai ga Hajiya Basariyya ɗin ta fito daga kitchen riƙe da kofi tana waya fuskarta da murmushi.      “A'a ƴan Jos an dawo kenan?”. Ta faɗa cikin katse hanzarin Maanal kamar tuni ƴarta Huznah bata kawo mata labarin dawowar Maanal ɗin ba tun ɗazun. Juyowa Maanal ɗin tayi fuskarta kadaran kadahan ta ɗan kalla Hajiya Basariyya ɗin da nata fuskan ke ɗauke da murmushi mai ƙayatarwa, sai dai acan ƙasan zuciyarta wani irin maƙoƙon tsanar Maanal ɗin ne ke mata kaikawo. Risinawa Manaal tai tana gaisheta. Nan ma ta amsa cike da fara'a tana nuna ma Maanal ɗin kujera da faɗin, “Haba sai kace wata baƙuwa zauna mana Maanal ga ƴan uwanki nan na bikin cin gyaɗa ka kuci. Da fatan dai kun dawo lafiya? Kuma komai ya kammala?”.       Kai kawai Maanal ɗin ta jinjina mata kanta a ƙasa, sai dai yanzu da ɗan gajeren murmushi a fuskarta. Ganin bata zauna ɗin ba Hajiya Basariyyar ta sake nuna mata kujera. Kai ta girgiza mata da kama hannun Munaya ta ce, “A'a Momy mun gode dama munzo gaisheki ne kawai”.         “Masha ALLAH aiko ina godiya. Sai dai ni bana cin miƙe gaskiya azo mini hira dai. Suma su Shahidah ki faɗa musu ina godiya sun barni da jira. Tun ɗazun har abinci nasa akayi dasu ga gyaɗa da aka dafa amma shiru kake ji”.     “Zan faɗa musu in sha ALLAH Momy”. Maanal ta faɗa cikin muryarta mai zurfi da nutsuwa. Daga haka ta kama hannun Munaya tana mata sallama. Da harara duk suka bita har Hajiya Basariyyar. Sai da ta gama ficewar harda turo ƙofar Huznah taja tsoki da faɗin, “Ni wlhy Momy ina mamakinki, kiyita wani musu magana mai daɗi. Shegu sunzo sun gaje mana gida baka isa kai magana ba Daddy ya kama faɗin yayansa ne suma na halak. Ko ina suka zama ƴaƴan nasa agololi. Ni ko wanda ma yakema kallon ƴaƴan nasa ƙilama da cikinsu tazo.”      “Hummm”.   Kawai Hajiya Basariyya ta faɗa tana kaiwa zaune batare data kula maganar Huznah ɗin ba. Hakan ya sake bama yaran haushi suka cigaba da zagin Maanal dan kamar ma sunfi tsanarta fiye da sauran ƴaƴan Ammien. Duk da kuwa sunƙi jinin Hameed ma da Waleed da Ammien ta haifa a gidan suke matsayin uba ɗaya dasu. Balle da Daddyn ke tsananin nuna musu soyayya. Dan yanzu haka ma yana tare dasu ƙasar Amurika yin hutu. Duk da dai yace taro zaije ya tafi da su. Amma babu wani taro kawai yaje dasu ne dan hutawa na sati har biyu...       Rai ɓace Manaal ta koma sashensu. Sai dai yanda bata gayama kowa abinda ya faru ba babu wanda ya tambayeta. Sai ma zama tai suka fara hirarsu. Babu jimawa kuma Daddy ya kira Ammie ta video call. Daga nan suka gaisa da shi ya bama Hameed da Waleed da Ammien ta haifa a gidan. Ƙanensu kenan guda biyu. Yarane matasa da zasu iya kai shekara sha biyar da sha uku. Suma duk kamanin Ammie suka biyo kamar su Maanal ɗin. Sai dai su farare ne sun kwaso hasken fatar Alhaji Usman Chalawa sosai kasancewarsa farin mutum tas..        Suna cikin hira da ƙannen nasu ne babu zato akai knocking ƙofar falon. Kafin wani yay magana a cikinsu mai knocking ɗin har ya shigo. A take Maanal ta shanye fara'ar fuskarta da maganar da take da Waleed ko nace faɗa irin na sako duk da kuwa ta girmesa sosai. Kauda kanta tai da jan mayafin abayarta daya zame ta rufe gashinta da ƙyau, yayinda su Amaal ke masa barka da shigowa. Shiko yana amsawa da ɗan murmushi hankalinsa akan yaransu dake gaishesa duk da sai da ya gama ƙarema Maanal kallo a kai-akaice.      Gaban Ammie da hankalinta itama ke kansa tana ɗan murmushi ya ƙaraso. Cike da girmamawar da yake bata ya rissina yana gaisheta. Da kulawa take amsawa itama, kafin ta ɗora da faɗin, “Baka wuce Abujan ba kenan?”.           “Eh Ammie fasawa nai saboda wanda zanje wajensa yace yana Lagos sai gobe zai dawo. Nima kawai sai na bari sai goben na tafi dan bana son naje naita zaman jiransa ina kuma da abinda zan ɗanyi anan ɗin”.       “To ALLAH yayi jagora. Yay muku albarka, ya kuma saka muku hannu a dukan al'amuranku”.      “Amin ya rabbi Ammie Nagode sosai”. Ya faɗa cike da jin daɗi yana maida hankalinsa kan Maanal dake ƙoƙarin tashi tabar falon. Kansa tsaye ya furta, “Ke ƴar hidimar ƙasa yaushe kika dawo?”........✍️         Hummm yanzu fa aka fara shimfiɗar bama wasan ba. Mi kuke tsammani. Yazeed, ga kuma RK. Ga Maanal da bama musan alƙiblarta ba. Shin wai mi aka AJIYE A DUHUN nan ne? Ya dai kamata a haska mana mu gani ko zamu tayasu lalube🏃🏃🏃🏃🏃. Maza garzayo cikin tawagar littafan zafafa biyar da zasu zo muku da sabon salo na musamman in sha ALLAHU. Kowanne da salonsa da kuma takunsa. Mi kuke jira, ai sai kawai kuzo ayi tafiyar nan daku karku bari sai wasu sun baku labari.😘😘😘👌 A fa dun inda ZAFAFAN suke ZAFAFAN ne🫣😘😘👍🏻 ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖0️⃣6️⃣ ALBISHIRINKU 💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃 Idan kinada burin samun babban jari🤝 ko siyan wata babbar kadara irinsu gida mota ko gold fili ko Gona ko canja kayan daki ko kinada yanmata kinaso kisaimusu kayan aure ko canja rayuwarki daga tunanin yauda kullum xuwa lissafin dollars 💰daga Kwance 💃 Uhmmm garzayo kiyi rijista da 52U kiyi aiki kisha mamaki acikin shekarar nan rayuwarki xata canja ta dalilin yin rijista da $21 kacal😱 Yar uwa kisani cewa a kullum muna fuskantar tashin hankali idan akace mana darajar dala tatashi😫 Kullum naira da muke kashewa darajarta Kara faduwa takeyi😩 Tsadar rayuwa kowa yanxu fama yake da wnn tashin kayan😰 Mezai Hana kuxo mu runtuma muyi harkar dollars din kawai sbd yazamana ko ina muna nan 🤗 52U harkar dollars ce Mai sauki ga samu 52U alkhairi ce rijista kawai xakayi da $21/35k bayan haka baasaka kudi a 52U kuma 52U babu level level kawai rijista ne akeyi da kudi ba platforms bane ❌ Networking ne💯 Yanxu mu yan 52U idan akace mana dala tatashi murna mukeyi ba bakincikiba sbd inkanada dala kacanjashi naira ninkuwa yakeyi💃 Kaya kullum farashinsa tashi yakeyi Baya saukowa muna rokon Allah yahoremana abin saya don ga tsada gashi babu isheshshen kudin saya akwai kura wllh😂 Amma Inda kudin abin bazaimaka wahalaba😅 52U idan kayi rijista xata Baka jarin loan a dashboard Dinka Wanda kullum zaidinga juyuwa 💰 Kubiyoni domin Jin cikekken labarin 52U don koda kudinka saida rabonka abin na yan baiwane 52U ba platforms bane networking ne kuje kuyi bincike kafin kuyimin magana 08031507345 ___________ ______________ ........Idanu Manaal ta ɗan rumtse kamar zatai wucewarta sai kuma ta dakata saboda hararar da Ammie ta watsa mata, cikin sanyinta ta furta, “Yau ne Yaya, ina yini”.        Batare daya amsa ba ya sake furta, “Ai da yake ke baƙya zumunci ko a waya sai kinso ake jinki. ALLAH ya sanya albarka to”.      Kasancewar ta fara tafiya a taƙaice ta amsa masa da Amin. Ganin da gaske barin falon zatai kuma harga ALLAH dan ita yazo ya dakatar da ita da sake faɗin, “Zoki bani abinda kuka girka anan ɗin naci”.      Cak Maanal ta sake tsayawa zuciyarta na wani kalan harbawa da sauri-sauri, sai kuma ta yunƙura zata cigaba da tafiya ranta na wani kalar jin zafinsa da mamakin rainin hankalinsa. Ba abinci suka samu yana ci a sashensu ba? Shine dan guntun kutsugu zaizo nan kuma yace a bashi abinci......      “Wai nikam ba dake ake magana ba halan?”.   Ammie ta katse mata hanzari cikin kaushin murya. Jitai kamar zata saki ihu, sai dai babu yanda ta iya dole ta furta, “Ammie nafa amsa“ daga haka ta nufi kitchen a maimakon hanyar bedroom ɗinta. Abincin ta zubo mata tana faman ƙannan magana a ranta. Itafa wlhy da tasan ma yana gidan bazata dawo ba. Kuma ko yanzu idan taji zai jima a KD ɗinne gara tabi Didi Shahidah Abuja har sai ya tafi ta dawo kawai. Da wannan tunanin ta dawo da abincin. Tana ƙoƙarin nufo falon ya miƙe yana faɗin, “Bani anan”.       Kallon dining ɗin daya nufa tayi, sai kuma ta kalla Ammie kamar zata saki kuka. Ganin Ammien ta ɗauke kanta ta maida dubanta gasu Didi Amaal. Da baki Amaal tai mata nuni da Ammie. Hawayen da suka cika mata ido kawai ta haɗiye kafin ta taka a hankali ta ƙarasa inda yake zaune yana jiranta. Tray ɗin ta ajiye a gabansa. Tana niyyar barin wajen ya dakatar da ita da faɗin, “Dawo ki zauna”.      Yanda yay maganar babu wani wasa kuma a gadarance ya sake kunna zuciyarsa. Sai dai kuma babu yanda zatayi dole ta koma ta zauna dan tun fil azal shi baya wasa dasu. Sannan kaf ɗin gidan nan babu wanda zai ce baya tsoron Yaya Yazeed. Mutum ne bamai yawan shiga sabgar kowa ba, amma baya ɗaukar raini. Abincin ya ɗan fara ci a nutsensa yana lumshe ido, sai da yay kusan lauma uku ya ɗago yaɗan kalleta. Fuskarsa babu wani walwala ko alamar wasa ya furta, “Abincin Ammie dabanne a gidan nan Manaal. ALLAH dai yasa ki gadota iya girki dan ina son abinci sosai. Idan ko kina wasa da koya ki ƙara dagewa sosai kinji”.         “Hummm” ta faɗa kawai batare da tace komai ba. Manyan idanunsa ya ɗan zuba mata yana ɗan sake tsuke fuska. “Miye wani hummm. Kin san fa bana son halayyar nan naki ai ko? Tom zamu fara ai kenan. Dama baki son ina fushi dake bane. Tunda nai tafiyar nan baki taɓa nemana a waya ba why?”.       Rasama mizata ce dashi tayi, tsahon lokaci bata tanka ba har sai da ya sake tsareta da kaifafan idanunsa sannan ta motsa lips ɗinta da ƙyar ta amsa masa da “Ai ban san da wane layi zan sameka ba”.        “Hummm dama ba niyyar kiran nawa kike da shi ba. Ni wannan halin miskilancin naki ban san yaya zan kwashe da shi ba Maanal. Amma ba komai zanyi maganinki ai. Yanzu ke miya samu naki layin da ban samunki kwana biyu, ko blocking ɗina kikayi?”.       Nan ma ta jima bata amsashi ba. Kafin ta nisa da ƙyar ta amsa masa a taƙaice. “Matsala ya samu, mizaisa nayi blocking ɗinka”.          “Sai kuma kika gagara zuwa ki gyara ko?”.    Shiru tai ta ƙi bashi amsa. Shima sai ya bar zancen dan yasan ɓacin rai kawai zai ƙarama kansa. Abincinsa ya cigaba da ci, sai da yana gab da gamawa ne yake sake kallonta da faɗin, “Lokaci fa yayi da zaki cireni a gidan gandun nan. Dan kasa isasshen barcin daren nan da nake ya fara isata haka nan Manaal”.       “Kamar ya?”.   Ta faɗa cikin ƙosawa da mamaki kuma, sai dai muryarta acan ƙasan maƙoshi da kuma sanyi. Idanunsa da suka ƙanƙance lokaci guda ya ɗan lumshe mata ya sake buɗewa. Sai kuma ya wani maidasu ƙasa-ƙasa tare da muryarsa ya furta, “Saboda ina buƙatarki a gefena. A tsakanin nan a matse nake da buƙatarki a kusa dani. Dan haka zanma Daddy magana a tada zancen aurenmu tunda kin kammala karatu harda sarvese ai nayi ƙoƙari sosai”.       Wani irin mugun bugawa ƙirjin Maanal ya shigayi. Yayinda jikinta ke wani tsuma. Cikin rawar murya da sake bayyanar rauninta ta ce, “Yaya Yazeed Please ka ƙara min lokaci mana, ka......”        Spoon ɗin hannunsa ya ajiye cikin tsatstsareta da idanunsa da suka hanata cigaba da maganar tata. “Manaal lokaci kuma? Miyyasa baƙya tausayina. Kin san shekarata nawa kuwa a duniya? 35 fa nake ƙoƙarin cikawa. Kin san kuwa nakai maƙurar ƙurewa da buƙatar abokiyar rayuwa ko? A wancan karon kince kina son kammala karatu, nayi miki wannan alfarmar, kika kammala kika sake roƙon haɗa masters naki na sake kauda kaina saboda Dadday, yanzu harda su sarvese duk bance komai ba amma ki sake cewa na baki lokaci. Ko kina son sai an samu matsala na far miki a cikin gidan nan ne saboda halin da nake ciki?”.       Zuciyarta ce ta sake harbawa da sauri, duk da kuwa bawani fahimtar zantukan nasa take ba kasancewar hankalinta ya gama rabuwa biyu. Shima ganin tunaninta na neman yin nisa da shi ya kira sunanta murya a ƙasan maƙoshi. Ajiyar zuciyar dawowa cikin hayyaci tayi, sai kuma takai hannu ta goge ƴar ƙwallar dake neman gangaro mata. Cikin rawar muryar kuka ta ce, “Yaya Yazeed!”.       Idanunsa kawai ya zuba mata batare daya amsa ba. Dan shima dai miskilin ne kamar yanda ake zaginta akan natan. Sai dai ita ɗin ta takashi ta shanye. Dan shi yakanyi magana a inda yaso idan yaso hakan. Ganin taƙi cigaba da magana ya ce, “Ke nake saurare.”         Maganar take son yi sai kuma ta kasa, sai faman wasa take da dogayen yatsunta masu ɗauke da farce masu haske dan babu ɗigon lalli a jikinsu duk da kuwa ita ma'abociyar sonshi ce. Nuni ya mata alamar ita yake saurare. Itama saita ɗaga masa kanta tana ƙoƙarin shanye abinda ke mata kaikawo ta cigaba da faɗin, “Mamma!. Ya kamata ka....”       “Maanal Please, kema kin san an wuce da wannan matsalar tuni, Mamma tsakaninta da Daddy ne bada mu ba. Mizai sa ki ɗauka ki saka hakan a tsakkiyar rayuwarmu. So please indai ba so kike ki sake jana a ƙasa ba kuma bayan na baya ki bani haɗin kai. Ina buƙatar abokiyar halitatta Maanal. Ina cikin takura matuƙa akan hakan kada kisa na cutu”.           Idanunta ta rumtse da ƙarfi, kalamansa na mata wani kalar kuɗa a zuciya da ƙirji. Yayinda ta wani gefe suke maimaita kansu a sigar ƙaddararta ta ƙuruciya. Rawa jikinta ke neman farayi saboda abinda ke neman jijjigo gyanbon ƙasan ziciyarta da kowa ke tunanin ya jima da warkewa. Kamar wanda ke karantarta ya ce, “Okay na baki dama kije kiyi shawara dama duk wanda kike ganin zakiyi. Kafin nan dai kafin Daddy ya dawo ki tsaida min zance ɗaya. Idan ba haka ba sai dai kiji batun saka rana. Zuwa anjima ina son ganinki a garden, ki zo min da layin naki dakeda matsala zan saka a dubashi”. Ya ƙare maganar yana miƙewa abinsa. Har yay sallama dasu Ammie ya fice a sashen Maanal na zaune kamar gunki da aka dasa don tarihi a dining area ɗin ta kasa tasowa. Saima wata irin zufa ce data cika mata gaban goshi. Yayinda hawaye ke ambaliya a saman ƙyaƙyawar fuskarta. Amaal da dama tun ɗazun hankalinta ke kanta ce ta ƙaraso wajen da sauri. Kamota tai cikin rawar jiki tana tambayarta mike faruwa? Maimakon amsa sai ta faɗa jikinta kawai ta rungumeta tsam ta saki wani sirrin kuka mai ban tausayi. Rikicewa Amaal ɗin tayi, hakama Didi Shahidah tuni ta taso ta nufosu. Ammie ce dai kallo ɗaya ta musu ta kauda kanta gefe, dan ta ɗaura ɗammarar itama bazatai sanya a wannan karon akan Maanal ɗin ba. Ta gaji da zamanta haka gara ai auren nan ko hakan zaisa ta manta da baya. Tana jiyo yanda ƴan uwanta ke sake jera mara tambayoyi a rikice batabi takansu ba tama tashi tabar falon zuwa bedroom ɗin ta. Bakin gado takai zaune tare da fara sarrafa wayarta, sai kuma ta kaita kunne alamar kira tayi. Babu kuwa jimawa aka ɗaga daga can, bayan sun gaisa da tambayar juna iyali ta fara magana kamar haka.          “Nene na kiraki ne akan ƴar gidanki, yau dai ta dawo an kammala service”. Ta ɗan yi shiru alamar saurare. Sai kuma tai murmushi da cigaba da faɗin, “Shine ma dalilin kiran naki Nene. Dan anyi sa'a shima Yazeed ɗin yana gida yazo wani aiki kuma zai jima kamar yanda ya sanar min. To sai nake ganin hakan damace da za'ayi kawai a huta. Dan nagaji da wannan ɗage-ɗagen saka ranar auren nasu shi kuma Baban nasu na biye mata. Gara ayi a huta, idan taga abin bawasa bane tama ƙarasa nutsuwa. Saboda na fahimci Maanal fa bazata taɓa kasancewa a yanda ake buƙata ba a haka gaskiya. Amma shi idan suka je can zai san ta yanda zai ƙarasa mantar da ita komai dan yaron nada hankali da nutsuwa. Banga abinda Yazeed bai mallaka ba da mace bazatai alfahari da shi ba ako'ina matsayin miji”. Nan ma tai shiri tana saurare. Ta jima kafin ta amsa da, “Ni abun sake bani tsoro yake. Yanzu haka bakiga yanda ta dawo a fige ba wannan karon kamar kazar fakat. Al'amarin Maanal na tayar min da hankali Nene wlhy”. Ta ƙare maganar muryarta na rawa.      “Hakane Nene ina kan yimata iya ƙoƙari na. Dan ko sadakar nan wlhy kusan don itane bana iya jinkirtawa. Amma dai a aiko mata da ruwan addu'ar ma sai ta cigaba da sha. ALLAH ya kawo iyakar komai ya kuma bama yaron nan ƙwarin gwiwar kwantar mata da hankali ta sake manta komai”.      In sha ALLAHU Nene bana jin Yazeed. Yarone mai addini da sanin yakamata tamkar mahaifinsa. Dan sam baida halin mahaifiyarsa, baya kuma biyema al'amarinta kamar ba daga jikinta ma ya fito ba.”        “To Amin ya rabbi sai kin shigo ɗin ma ƙarasa”. Daga haka sukai sallama.      ★★“Auta dan ALLAH kibar kukan nan haka. Wlhy yana ɗaga mana hankali. Ki mana bayanin mike faruwa ne? Ko wani abu yace dake mara daɗi?”.     Kanta ta shiga girgiza musu tare da share hawayenta. Sai kuma ta tashi daga kwanciyar datai a jikin Didi Shahidah ta koma ta jingina da fuskar gadonta. “Didi dan ALLAH ku taimakeni, wlhy bana son auren nan bana buƙatarsa dan bazan taɓa yin aure ba wannan alƙawarine da naima kaina. Amma su Ammie da Yaya Yazeed sun kasa fahimtata. Wlhy kosun matsa nayi auren nan GANGAR JIKINA kawai zai aura, sannan bazan taɓa biyayya irin ta aure ba a gareshi, bama shi ba ga kowanne ɗa namiji. Didi miyyasa bazai fahimta bane, Maanal ta jima da mutuwa babu ita a wannan DUNIYAR ta mutane. Duk gangar jikin dake rayuwa da matacciyar zuciya bashi da wani amfanin rayuwa. Amma sun kasa fahimta, sun kasa min uziri, dan ALLAH ku ku fahimtar dasu maybe zasufi saurin yarda daku idan ni basa gane yarena. Koku fahimtar da Yaya Yazeed shi maybe ya fisu gane illar yin AJIYA A DUHU da yayi, cigaba da matsawarsa kuma zai zama ƙonewar komai daga hasken fitilar da yake ƙoƙarin haskawa don lalubo abinda ma babu shi koda a cikin duhun....”         “Maanal Please...” Didi Shahidah ta faɗa tana kamota jikinta ta sake rungumewa. Itama cikin murya da lallashi ta ce, “Please ki kwantar da hankalinki mana. Kin san ba wani lafiyace ta isheki ba. Ciwonki baya buƙatar irin waɗannan abubuwan kinfi kowa sani. Maanal iyayenmu suna son taimakon rayuwarki ne ba cuta miki ba. Sannan Yazeed babu abinda ya rasa daga zama cikakken Namiji. Yana kuma matuƙar kaunarki, duk da boren mahaifiyarsa akan al'amarinku bai taɓa canjawa ba. Miyyasa bazakiyi haƙuri ki manta da komai ba ki amshi wannan ƙaddarar?......”      “Saboda ƙaddara tana tafiya ne da rayuwa Didi, ni kuma na riga na jima da Mutuwa, mi zaiyi da gawa? Mi zai yi da gangar jikin da babu zuciya? Mi zaiyi da wadda labarinta ya jima da rubutuwa da ƙarewa? Tuni fa Maanal ta gama mutuwa, na mutu! ni tamkar hawace Didi..”         “Keba gawa bace Maanal, ya kamata ki fahimci bafa komai a rayuwa kake samu hundred percent ba, dole sai kayi haƙuri da wani abun sannan kake mallakar wani. Please ki amshi ƙaddararki a karon na biyu, nasan zaki ji daɗin zama da Yaya Yazeed wlhy mutumin kirki ne, tunda kin san dai babu yanda za'ai a barki haka babu aure. Kuma Yazeed ya dace dake matuƙa”.     “Didi ban musa miki kirkinsa ba ko nagartarsa ko cancantarsa. Duk abinda kuke hange min nasan fiye da haka gareshi, sai dai bana buƙatar kowanne namiji a rayuwata gaba ɗaya ku fahimta mana dan ALLAH”..........✍️    _Tofa, mace kuwa zai yiwu tace bata buƙatar namiji a cikin rayuwarta?????. Shin jama'a mike damun Maanal ne haka?????🏃🏃🏃🏃🏃._ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖0️⃣7️⃣ .......Hawaye ne suka cika idon Amaal, yayinda Shahidah ke ƙoƙarin shanye nata itama. Tausayin ƴar uwar tasu na ƙara cika musu zuciya. Dai-dai nan Ammie ta shigo, kallo ɗaya tai musu su duka ta kauda kanta. Sai kuma tai gyaran murya. A tare duk suka kalleta, Maanal ta share hawayenta da ƙoƙarin kaiwa kwance, amma sai Ammie ta riƙota tana kaiwa zaune kusa da ita da faɗin, “Auta wai yaushe zaki bar shagwaɓa ne?”.        Baki Maanal ta tura gaba da yin narai-narai da idanu zata sake sakin sabon kukan Ammien tai mata hararar wasa. “Kina sakin min kuka zan zaneki ne tas a ɗakin nan”.     A tare suka kwashe da dariya, dan yanda Ammie tai maganar sai ya tuna musu baya. Kai Maanal ta zuba fitina a rayuwarta, ga tsoron dukan masifa. Dan duk rashin mutuncin da zata zuba da Ammie tace zata zaneta take nutsuwa. Ammie data ji daɗin ganin damuwar tasu ta kau sai ta cigaba da jansu da hira. Idan ka gansu abin sha'awa kamar wata babbar yayarsu can ba mahaifiyarsu ba. Dan Ammie an mata aure da ƙarancin shekaru ne, kuma ALLAH ya bata haihuwan da wuri, shiyyasa idan baka sani ba sai ka ma ɗauka ba itace ta haifi su Shahidah ba, dan za'afi ganin Maanal a ƴar farinta kamar. Kamar wasa suka sha hira sosai sai da aka kira Magrib Ammie ta fita. Babu wanda ya sake tada batun auren Maanal ɗin har dare. Sun idar da salla Shahidah da Amaal suka shiga kitchen, yayinda Maanal ta nufi ɗakin Ammie dan tana son tambayarta gobe in sha ALLAHU da wuri zata fita gyaran jiki. Ta samu Ammie akan abin salla tana waya da mijinta, dan haka ta haye gadonta ta kwanta tana saurarenta. Sun jima kafin suyi sallama ta juyo ga Autar tata tana tambayar, “Mi kuma ya faru ƴar shagwaɓar Ammie?”.      Murmushi Maanal ɗin tayi, cikin yanayinta na miskilaye da shagwaɓa ta ce, “Ammie ina son naje gyaran jiki gobe in ALLAH ya kaimu, ban sani ba ko kina da kuɗi. Jibafa yanda jikina duk ya bushe ga kaina sai ƙaiƙayi yake mun”.           “Uhm ko bani da kuɗi auta ai dole na nemosu, ke idan fitinar gyaran jikin nan naki ya tashi ai duk fatarata baƙya raga min”.      Sosai Maanal takema zancen Ammien murmushi. Yayinda Ammien ke kallonta cike da jin daɗi, idan taganta cikin farin ciki haka daɗi take ji, sai ta dinga ganin asalin Maanal ɗinta ta baya sarkin rikici da kwaramniya, amma yanzu duk ta zama sanyi-sanyi ga miskilanci, sam bata son sabon yanayin nata na wannan shekarun, sai dai babu yanda zatai tana mata addu'a. Katse mata murmushin tai da faɗin, “Ke duba wayar nan taki tun ɗazun take haske alamar kira”. Amsa Maanal tayi da faɗin, “Inaga Zezaa ce ko Anees....” sai kuma ta kasa ƙarasawa saboda ganin number mai kiran, dan ko saving batai ba, amma nacinsa yasa tuni ta haddace lambarsa a kanta. Fuska ta ɗan tsuke, har zata maida wayar ta ajiye sai kuma ta dakata, dan tasan shegen nacinsa ba lallai ya barta ba idan bata ɗaga ɗin ba. Inda Ammie take ta ɗan kalla, ganin hankalinta baya kanta ta ɗaga tana mai kai wayar kunnenta. Can ƙasan maƙoshi cikin muryar nan tata mai zurfi da rashin sakewa tai sallama. Tana jiyo sautin ajiyar zuciyar RK da ga can, dan haka ta taɓe baki kawai.          “Baby duk kin saka hankalina tashi. Ai da nace idan nayi kira dubu baki amsa ba komai dare zan sake kamo hanyar Kaduna ne”.      “Hummm” kawai tace a taƙaice tana ɗan satar kallon Ammie. Ganin ita take kallo yanzu sai ta ɗan sake ɓata fuska. Yayinda kunenta ke sauraren RK dake magana cikin kulawa da tambayarta ta samu gida lafiya. Cikin sake maida muryarta ƙasa sosai ta ce, “Alhamdullah ina yin abune”.           Ɗan jimm yay na damuwa da nuna ƙosawa da shi da tai, koda yake yau an samu cigaba ma ta ɗaga wayar ai. Dan haka yay guntun murmushi da har tana iya jin sautinsa tare da furta, “Okay bari na barki. Amma Please anjima na kira to?”. Da sauri ta ce, “Uhm-uhmm”.      “Why?”. Ya tambaya kamar zai yi mata kuka. Banza ta masa. Dan ta matuƙar gajiya da shi. Sake haɗa ido da sukai da Ammie ya sata yanke wayar tama kasheta gaba ɗaya tana wani sake tsuke fuska. Shifa wannan mutumin ta kula sai ta masa fatattakar karan mahaukaciya zai ƙyale rayuwarta ta huta shima yaje ya hutama ransa. Bai san yanda tai matuƙar tsanar maza bane a duniyarta ta yanzu daya kama kansa tuni. Amma ba komai, tunda yanzu tabar garinsu tana da damar da zata buga masa warning na ƙarshen ƙarshe da kakkaɓesa daga jikinta gaba ɗaya, yama barta taji da matsalar gabanta...      “Tunanin mi kuma kika tafi?”.   Ammie tai maganar tana taɓata. Ajiyar zuciya ta sauke da ɗan laɓe lips ɗinta tana kaiwa zaune kusa da Ammien. Kwantar da kanta tayi a kafaɗarta tare da rungumota. Cikin son kauda wancan yanayin ta ce, “Ammie yau tare da ke zanyi barci nayi kewarki”.         Murmushi Ammie tai da kai hannu ta shafa ƙyaƙyƙyawar fuskarta. “Nima nayi kewarki Auta. Amma babu yanda zanyi tunda wataran ma inaji ina gani gidan miji zaki wuce ki barni”.       Tsam ta miƙe batare data ce komai ba ta ɗauki wayarta ta fice. Da kallo kawai Ammie ta bita. Wani irin tausayinta da ƙaunarta na sake ratsa mata zuciya. Miƙewar tai itama ta fito. A kitchen ta samesu su dukansu har Manaal ɗin. Ta ɗan duba abinda suke dafawar ta fita ta barsu. Yanzun ma a tare sukaci abincin daren bayan sun kammala. Suna tsaka da ci sai ga Yazeed ya shigo sashen. Duk gaisheshi sukai bayan shima ya gaida Ammie, yayinda Maanal tai kamar bata gansa ba tanata wasa da spoon a cikin abincin. Shiko hankalinsa duk yana kanta, duk da dai magana suke da Ammie wadda su Maanal ɗin basa jin mi yake faɗa mata. Bai wani jima ba yay musu sai da safe ya fita. Wata ƴar ajiyar zuciya Maanal ta sauke a hankali. Babu wanda yay mata magana sai ma Ammie data shiga musu bayanin da Yazeed ɗin ya mata. Ashe zasuje Zaria ne gobe idan ALLAH ya kaimu ita da shi halartar wani ɗaurin auren ƴar abokin maigidan. Sunyi addu'ar ALLAH ya sanya alkairi su duka. Sai kuma ta ɗora da faɗin Maanal ɗin ta shirya sai ta mata rakkiya ita da Amrah dan shi Yazeed ɗin zai rigasu tafiya ne da abokinsa. Ɓata fuska tayi zatai magana Ammie tai mata daƙƙuwa. “Sai fa kinje daddawar gida da bata son fita”.        “Nifa Ammie ba cewa zan bazanje ba. Amma gyaran jikina fa?”.     “Ki tashi da wuri ayo miki, tunda sai sha biyu ma zamu wuce in sha ALLAHU ”.    Badan taso ba dai ta amsa da to, dan taji Yazeed shima zai je. Sai dai sauƙinta tafiyan nasu ba ɗaya bane...      Kamar yanda ta faɗa a ɗakin Ammie tai kwanciyarta manne da ita kamar za'a ƙwace mata ita ko wata ƴar goye can. Dan da Ammien ta tashi sallar dare ma da ƙyar ta ɓangare ta a jikinta. Bata kuma jima da fara sallar ba itama Maanal ɗin ta tashi tayo alwala. Haka take itama akwai yawan ibada kamar Ammien, dan ko sanda take tashen rashin jinta dama Maanal akwai son addini, tun bata kai girma ba zatace zatai azumin litinin da Alhamis, ko an hanata kuma sai tayi sai dai ta kaisa a galabaice. Kusan ƙarfe uku da rabi barci ya fara rinjayar idonta, addu'a tayi ta koma saman gadon ta kwanta tabar Ammie anan.....       Koda suka idar da sallar asubahi ma sake hayewa gadon tayi tai kwanciyarta, dan barcine sosai a idonta, sai kuma jikinta dake mata kamar babu daɗi. Da ƙyar Ammie ta tasheta wajen ƙarfe takwas akan ta tashi ta shirya taje gyaran jikin nan, idan ba hakaba sai dai ta bari sai gobe idan ALLAH ya kaimu dan babu fashi da ita za'aje Zaria. Dole ta tashi badan taso ba ta kimtsa. A falo ta samu ƴan uwanta suna hira da karyawa, saboda saurin da take gaishesu kawai tayi ta haɗa shayi a wani gora mai ƙyau na ƴan gayu ta wuce tana faɗa musu saita dawo.     Tsokanarta suka shiga yi akan ko gayyata ma babu. Ta fice tana faɗa musu susha zamansu baza'a cinyema Ammie kuɗin account ɗinta ba. Idan kuma suna da kuɗi su taho. Babu kowa a harabar gidan sai masu gadi su biyu da mai bayin fulawoyi daketa yi, da alama sauran ma'aikatan duk sun kammala nasu aiki sun wuce. Dan dama mai sharan tsakar gida ne da mai wanki. Kamar yanda ta saba cikin girmamawa ta gaidasu, suka amsa mata da kulawa da tambayarta gajiyar tafiya. Koda ta fito tana kallon titin da fatan samun napep da wuri dan gidan nasu a bakin titi yake sai kawai idonta akan Yaya Yazeed dake tsaye jikin motarsa yana waya, sai dai shima idonsa a kanta. Sai da gabanta ya faɗi, amma sai ta dake tana ambaton sunan ALLAH. Tafiya ta farayi a ƙafa tana mai fatan zuwan napep yanzu, sai dai ko taku goma batai ba taji horn a bayanta. Sosai ta rumtse idanunta tare da cije lips, sai kuma ta sake ɗaga ƙafa zata cigaba da tafiyarta ya ɗan sha gabanta da motar tare da sauke glass ɗin. Cikin gizagonsa da tsare gida ya furta, “Wai nikam yaushe raini yay ƙarfi tsakanina da ke haka Maanal?”.         Fuska ta ɗan sake tsukewa da juyowa ta kallesa. “Toni Yaya minai maka na raini?”.       Cikin tsareta da kaifafan idanunsa ya ce, “Oh bama ki sani ba ko? Zan gyara miki zama ne. Ina zaki je da wannan safiyan haka?”.     (Kama gyaran tsaiwa ba zama ba) ta faɗa a ziciyarta. A fili kam sai ta amsa masa da, “Nan zanje kusa wankin kai”.          “Okay, bismillah shigo na ajiyeki”.     Baki ta buɗe zatai magana ya harareta. Dole ta shiga hankalinta dan tasan halinsa shi baya son wargi. Zagayawa tai ta ɗayan side ɗin da har ya buɗe mata, haka ta shiga tana ƙunƙuni cikin ranta. Jan motar yay suka cigaba da tafiya yana wani shegen tuƙi a hankali kamar baya so, zatai magana wayarsa ta shiga ƙara alamar kira. Ɗaga wayar yay ya saka a hansfree tare da yin sallama. Daga can aka amsa masa da faɗin, “Oga kayi haƙuri ka jini shiru jiya da nace zan kira”.         Amsa masa yay da, “Eh ai harna shaƙa ma. Dan yanzu kamar ma bazan ɗaga kiranka ba dai na daure na ɗaga ɗin. Kasan ni bana son wasa da abu mai muhimmanci Hashim”.     “Na sani oga kayi haƙuri. Wlhy ina gaya maka sai kusan 2 na samu ganawa da AA ɗin. Shima mintuna ashirin ya yarda zai ganni da ƙyar da taimakon yaron nan nasa da nake gaya maka cousen ɗina ne”.          “Mtsoww! Mutumin nan fa na lura ɗan wulaƙanci ne Hashim. Kodan yaga muna buƙatar kayan nan yake ta garamu haka ne? Shi ana tattalin customers shi yana yanƙwana mutane”.      “Tom oga sai dai haƙuri, sai dai kuma ni yanda na fahimcesa kamar ba wulaƙanci bane ba. Yariga da yayi ƙarfine sosai. Dan wlhy manyan ƙasashen Larabawa nan yake huɗɗa dasu sosai. Kai harma turawan tako'ina kayansu shiga sukeyi. Gashi abin mamaki yaro ne ƙarami dan indai bakuyi shekaru dai-dai ba to kai zakama iya girmarsa wlhy. Amma yana da wayo da ban mamaki. Yanzu dai na taƙaice maka batu ya bamu damar haɗuwar da shi a cikin Companyn *_MAWAAD_* ɗin. Ya kuma tabbatar min da in dai mukabi ƙa'idar komai daya dace zamu dinga samun kayan nasu fiyema da yanda muke buƙata”.      Ajiyar zuciya ya sauke mai ƙarfi da faɗin, “Alhamdulillahi Hashim naji daɗin wannan labari. Kaga an gama da wannan matsalar kenan. Nasan Daddy ma zaiji daɗi sosai abu kusan shekara munata fama”.            “Wlhy kuwa oga ai dole ai farin ciki. Yanzu dai na tura maka komai ta email sai ka duba”.     “Okay ba damuwa zamuyi magana”. Daga haka ya yanke kiran tare da juyowa yana kallon Maanal da duk ke sauraren wayar tasu amma a zahiri hankalinta nakan wayarta tana duba saƙon da RK ya tura mata.          “Madam!”.      Ya faɗa a hankali cikin katseta. Jitai kamar ya dakar mata zuciya da guduma. Amma sai ta daure ta amsa da faɗin, “Kai yaya minene kuma wata Madam?”.      Ɗan dubanta yay yana murmushi mai ƙayatarwa, sai kuma ya maida hankalinsa ga titin yana faɗin, “Ai Madam ɗin ce. Kwana nawa ya rage kuma Manaal. Ke yanzu a yanda muken nan bakiji inama ace mu ɗin ma'aurata bane?”.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖0️⃣8️⃣ ______________ Assalamu alaikum Ina Neman mutane 20 dazasuyi register da company 52u a karkashin link Dina akan $21 wato 35k a kudin mu na Nigeria account din zaibude a cikin 5-6 weeks idan account din yabude nikuma nayi alkawarin zanbiya mutum 20 dinnan salary 10k kowani mutum na tsawon wata 5 kunga riba biyu kenan kuka samu ga ribar kudin ku yadawo harda riba ga account din kun na 52u zanbude a wata na shida sai kudin ga kwasa duk kudin ku duk wata 💃🏽💃🏽💃🏽mai ra,ayi yamin magana https://chat.whatsapp.com/K0ECLn6O3WS1fnfCggOeu5 08083531881 ______________ .......Shirun da tai na kusan minti biyu batare data amsashi ba ya sashi ɗan kallonta. Kanta tai saurin kaudawa tana mai ƙoƙarin haɗiye ɗacin daya mamayeta. Shima sai ya ɗauke kansa bai sake magana ba. Babu jimawa suka iso gaban gidan da take zuwa gyaran jikin, wanda yasani ne tuni saboda yanda take ma'abociyar zuwa gidan kusan duk ƙarshen wata. Jikinta har tsuma yake nason ta fita a motar, dan bata so ya sake mata wata magana amma sai taji motar a ɓame alamar ya saka luck. Dole ta ɗan dakata tana rumtse idanunta. Sai kuma ta juyo ta dubesa, ganin shima ita yake kallo ta maida kan ta duƙar. Murmushin ya sake saki kaɗan da ɗauke idanunsa a kanta cikin son basar da yanayin ke bashi a jikinsa. “Ki tayani murna?”.     Batare data sake kallonsa ba ciki-ciki ta ce, “Tami?”.         “Akan albishir ɗin da akai min yanzu a waya. Mutumin nan kusan shekara guda kenan muna son haɗa Bussines dashi amma ko ganinsa ya gagara a gareni. Amma yau kinji har zan samu ganinsa, nasan Daddy zaiji daɗi akan hakan shima matuƙa”.    Karo na farko tai ɗan murmushi. Sai kuma ta ce, “ALLAH ya tabbatar da alkairi a haɗuwar taku to”.        “Amin ya rabbi dear. Ammafa nasha wahala sosai. Mutumin ya riga yayi nisa ne matuƙa saboda yanda yake huɗɗa da manyan mutane na wajen ƙasar nan dama cikin gida Nigeria. Nasan dai bazaki rasa jin Mawaad ba”.             “Ina dai ganin sunan Companyn a jikin buhunan shinkafa, ban sani ba ko sune ko kuma da banbanci”.      “Yes sune. Dan yana harkar noma yanzu matuƙa a ƙasar nan. Kuma Kinga wannan harkar ma bai wani jima da farata ba. Amma da yake ALLAH ALLAH ne cikin ƙanƙanin lokaci nan ma yayi zarra.”          “ALLAH sarki”. Kawai Maanal tace dan bataga ma'anar bata wannan labari ba ita kam da dam bata da alaƙa da shi. Cikin marairaicewa ta ce, “Yaya bara naje kada na makara Ammie tace zamu rakata anguwa”.      Amsa mata yay da “Okay bari na barki ki wuce. Inata baki labarin abinda bai shafeki ba, haka nake buƙatar rayuwata Manaal, wato iyalinna su dinga sanin komaina dan su kasance masu min addu'a. Dan haka sai ki shirya, dan zaki dinga raba farinciki da mijinki hakama akasinsa idan ya gitta” ya ƙare maganar yana miƙa mata atm card ɗinsa. Kanta ta girgiza masa da sauri. “A'a yaya ga Ammie ta bani nata zanyi amfani da shi. Hararta ya ɗan yi da zare atm ɗin Ammien ya ajiye mata nasa a cinyarta. “Kiyi amfani da na mijinki, dan nike da hakkin hakan ba Ammie ba. Idan kin kammala ki kirani dan ba nisa zanyi ba”.      Yanda ya tsatstsareta da ido yasa ta kasa magana. Dole ta buɗe motar ta fita dan shi in baiso wasa ba dole kaji shakkarsa. Bai bar wajen ba har saida yaga ta shige. Ajiyar zuciya ya sauke a hankali da jingina jikinsa da kujera yana mai lumshe idanunsa. Ya jima a hakan dan yaci kusan mintuna biyar kafin ya tada motar yabar wajen yana mai danne abinda ke tsikarar zuciyarsa game da ita.....       ★★★     Yanda Maanal ta samu tarba a ciki zai tabbatar maka akwai shaƙuwa da sanayya sosai tsakaninta da mai gyaran. Dan duk miskilancintan nan sai murmushi take da ɗan maidama mai gyaran hiranta dan tana mata tambaya ne akan Jos. Basu wani jima ba aka fara gyaran saboda tun jiya ta sanar mata. Kafin tazo ta haɗa komai. Gyara sosai jikinta ya sha. Ga turarruka kamar wata amarya. Hatta kanta da ƙafafunta zuwa farce an musu ƙal. Haka Maanal take akwai son gyara jiki, ƴar gayuce sosai da son kwalliya, sai dai yanzu yanayi yasata ɓarar da kwalliyar gefe gyaran jikinta da tsafta ne dai tana nan da abinta akoda yaushe. Sun gama a ƙurarren lokaci, dan har Ammie na kiranta a waya ma. A gurguje ta bata ta cire kuɗin aikinta tare da amso kayan ƙamshin data haɗa mata suka fito zata mata rakkiya. Turus taja ta tsaya da ganin motar Yaya Yazeed a ƙofar gidan, kafin ma ta samu abin faɗa ya buɗe mata gefensa alamar ta shigo. Ganin fuskarsa babu wasa sam yasa batai magana ba ta shiga kawai. Sallama sukai da mai gyaran bayan ta gaida shi ya amsa mata ciki-ciki yaja motar suka wuce. Shiru motar har sun ɗan yi nisa a tafiyar cikin ƙarfin hali ta ce, “Yaya dama baka wuceba ne?”.        “Mi kika gani?”.    Ya faɗa cikin wata irin kasalliyar murya data bata mamaki. Gashi yaƙi kallonta sam a yanzu. Itama sai kawai ta ce, “Ba komai”.       Bai sake magana ba, itama tai shiru har suka iso gida. Sai da ya gama parking ta miƙa masa atm ɗin tana godiya. Kansa kawai ya ɗaga mata batare daya kalleta ba ko tankawa yanzu ma. Itama sai kawai ta buɗe motar tai ficewarta. Da Hajiya Yaya dake daga can ƙofar sashensu da wata baƙuwa suka haɗa ido, ganin irin kallon da suke mata yasa duk ta tsargu, amma sai ta dake ta nufesu badan taso ba, sai dan mahaifiyarta ta mata tarbiyya na girmama duk wanda ke gaba da ita. Sannan kodan Yaya Yazeed dake iya ƙoƙarin sa na girmama Ammie zata iya shanye komai daga mahaifiyarsa itama.       “Tofa, kice agola kafi ɗan masu gida an dawo kenan?”.     Matar da suke tare da Hajiya Yayan ta faɗa cikin yamutse fuska idonta akan Maanal dai-dai tana isowa inda suke. Wani harbawa zuciyarta tayi har tsakkiyar kanta. Ba wai yau ne karo na farko da aka fara kiranta da sunan AGOLA gidan ba, amma har yanzu ta gagara sabawa. A duk sanda aka kirata da shi kuma tana jin matuƙar ɗaci da zafi a ranta. Har takanyi yunkurin son barin gidan, sai dai yinƙurin nata baya zuwa ko'ina take komawa tai laƙwas saboda wasu dalilai. Hawayen da suka cika mata idanu ta haɗiye, tare da dai-daita kanta sannan ta ɗan risina fuskarta da murmushi ta ce, “Barka da gida Mamma. Aunty ina yini”.         Kafin Hajiya Yaya ta amsa wadda ta kira da aunty ɗin ta sauri ta cafe zancen cikin masifa, “Oh kaji wani ɗan iskan gaisuwa wai barka da gida sai kace wasu sa'oinki?”.      Cikin sake hasala Hajiya Yaya ta ce, “Kinga da yawa ai, idan batai iyayi ba ai bata cika jinin Asiya ba, Amma wai a haka Alhaji ke neman ƙaƙabama jinina ita”.      “Humm kar kiga laifinsa wlhy Yaya, tunda uwarta ta shanyesa kina ganin shima Yazeed ɗin zasu barsa ne. Balle suna ganinsa shine gidan da uban gaba ɗaya”. ta faɗa tana mai ballama Maanal wata shegiyar harara.     Tsamm Maanal ta miƙe kafin Hajiya Yaya ta bama ƙanwar tata amsa. Cikin ɗan sassarfa tabar wajen tana mai jin ɗaci da ciwo sosai a zuciyarta game da cin mutuncinsu ga Ammien ta. Tarasa mi Ammie ta tsare musu a gidan da su duka basa ƙaunarta...         Shikam Yazeed tana fita ya kife kansa a saman steering yana mai cije bakinsa da masifar ƙarfi. Kai bazai yiwu ba, dolene ya zigirgiɗi Daddy azo ayita ta ƙare a bashi matarsa. Dan gaskiya yana cikin tashin hankali, da yasan ma abinda gyaran jikin nan zai zame masa yanzun nan daya hana yarinyar nan yinsa ko kuma yaƙi komawa ɗakkota. Ɗan buga glass ɗin saitinsa da akai da ɗan ƙarfi ya sashi ɗagowa. Sai da ya ɗan saisaita kansa kafin ya sauke glass ɗin. Da Hajiya Yaya yaci karo, ai da sauri ya janye idanunsa da sukai wani irin kaɗawar da duk mai hankali idan ya kallesa zai fahimci halin da yake ciki. Ita kanta Hajiya Yayan sai da taji wani iri a ranta, amma ta dake cikin masifa ta ce, “Yazeed miye haɗinka da waccan yarinyar? A ina ka ɗakkota?”.       Ɗan gyaran muryarsa data koma can ƙasa yayi, kafin ya furta, “Mamma anan ƙofar gida ne mai napep ya ajiyeta shine nace ta shigo na ƙaraso ciki da ita. Wani abu ne ya faru?”.         Wata hararar bana son rainin wayo ta balla masa. Kafin cikin masifarta ta furta, “Yazeed! Yazeed wlhy ka kiyayen, ni zaka maida sakarai ko....”      “No Mamma ba hak....” Hannu ta ɗaga masa cikin tsawa, “Bana son ji, ka sameni ciki yanzun nan”. Tana gama faɗa ta juya ta bar wajen. Iska mai kauri ya furzar daga bakinsa tare da sake maida kansa jikin steering yana mai lumshe idanunsa. Yafi mintuna biyar a haka sannan ya buɗe motar ya fita yana mai saka glass a idanunsa domin ɓoye abinda ke cikinsu. A falo ya sami mahaifiyar tasa da ƴar uwarta. Cikin girmamawa ya gaida innar tasa dake wani binsa da kallon ƙurilla kamar mai son gano halin da yake a ciki batare data amsa masa gaisuwarsa ba ta ce, “Yazeed! Anya kuwa kana son nemawa mahaifiyarka mutunci damu ƴan uwanta a gidan nan. Wai kai bazaka bar batun yarinyar nan ba ne shin ko yaya kake nufi?”.       Sai da ya ɗan haɗiye abinda ke masa yawo a maƙoshi sannan ya furta, “Aunty Please mun wuce maganar nan fa tuni. Dan ALLAH a barta kawai”.      “Anƙi a bari ɗin dan ubanka. Yazeed ni dai kake son cigaba da tozartawa ko? Ni dai mahaifiyarka dana sha baƙar wahalar rainon ciki ka da naƙudar haihuwarka da shayar da kai. Asiya dai ta fini muhimmanci a wajenka ko? Shike nan kaje kayi duk abinda kake ganin dai-dai ne agareka. Amma ka sani ko mutuwa nayi kurwata bazata barka zaman aure da yarinyar can ba. Dan na riga na maka mata kamar yanda na faɗa maka. Garama ka shirya tun kafin takaimu da bakanta a cikin gidan nan. Amma bari shi Alhajin dake ɗaure maka ƙugu ya dawo gidan ina dai-dai dashi wlhy”.      Kasa iya furta komai Yazeed yayi, sai wani irin haɗiyar zuciya yake acan ƙasan ransa dan mutum ne mai zuciyar tsiya dama. Haka suka cigaba da masa masifa bai iya sake cemusu komai ba har sai da ALLAH ya taimakesa Daddy yay kiran wayarsa sannan ya tashi ya fita domin amsawa. Daga haka bai koma wajen su ba ya gudu sashensa dan ya shirya gashi har yana neman makara....     ________   A ɓangaren Manaal bata sanarma Ammie komai ba. Sai ma ƴan uwanta ne da suka zagayeta suna yaba irin ƙyawun da gyaran yay mata. Daga haka Ammie ta korata dan ta shirya kada su makara. Saboda tasanta da nauyin shiri. Aiko bata kammala shirin ba sai da Ammie tai mata tsiya-tsiya. Faɗan Ammien yasa ta fito ɗauko da ɗan box ɗin da take ajiye kayan ƴan kunne da makamantansu ciki a hannu tana neman agogon da zata saka da zobe. Su Amal ne dake musu dariya suka amsa suna duba mata. Dai-dai fitowar Ammie tana faɗin, “K muje ai ba dole sai kinsa wani agogo can ba bana son shiririta”.        Jin hakan ya sata miƙewa dan tasan kaɗan daga aikin Ammien ta maketa ma saboda bata ƙaunar jira, da sauri Shahidah da takamo hannunta ta ɗaura mata wanda ta zaro kalar silba kawai ta shiga ɗaura mata batare da su duka sun maida hankali akansa ba. Daga haka suka fice hannunta riƙe da ƴar bag ɗinta sai gwangwanin maltina data ɗauka saboda yunwan da take ji kasancewar bawani break ɗin kirki tayi ba ta fita gyaran jikin, yanzu kuma Ammie tace bazata zauna cin abinci ba aiba itace ta hanata ci ɗazun ba sai dai ta bari idan sunje gidan bikin taci. Itako tasan bazata taɓa iyawa ba cin abinci a gidan biki koda na wanda ta sani ne balle wannan, duk da kamar gidane can ɗin ma saboda alaƙar dake tsakanin mai gidan da uban amaryar mai matuƙar ƙarfi ce, ta wani gefen ma za'a iya cewa akwai zuminci. Koda yake su sai dai suyi kara saboda Ammie kawai amatsayinsu na ƴaƴanta...........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖0️⃣9️⃣ ______________ Lady's collection and more Zumar kiba Zumar breast Zumar hips Zumar infection Zumar sliming Zumar sabon budurci Back to virgin Abayas Atamfa Less Hijabs Supplements Kitchen items and more Muna maraba da masu siyan Daya ko 08169307477 Address bayan gidan drugs katsina State. Kayanmu nada inganci da zasu birge mai saye fiye da yanda yake zato. Maza ku garzayo kada ayi babu ku. _______________ .........Tunda suka fito ya zuba mata ido daga inda yake tsaye jikin mota. Itakam sam bata lura da shi ba tana ta  ƙoƙarin gyara kayan data zubo a handbag ɗinta dataƙi rufuwa. Sai da suka iso gab da shi ta tsinkayi muryarsa yana gaida Ammie. Yayinda Amrah ta taɓota itama tana gaida Ammien. Ɗagowa tai ta dubi Amrah ɗin, suka sakarma juna murmushi, harta maida kanta sai kuma ta ɗan ɗago dan sai yanzu hankalinta ya kai garesa sosai. A take ta shanye murmushin saman fuskarta ziciyarta na takurewa waje ɗaya a ƙirjinta. Tabbas da tasan tafiyar nan tare zata kasance musu ALLAH duk yanda zatai da sai tayi ta zame kanta a masu yinta. Amma yanzu babu yanda ta iya dole ta dake. Ganin su Ammie sun shige itama ta fara ƙoƙarin shiga kusa da su amma sai Amrah tai saurin rufe murfin tana faɗin, “Kije wajen Yaya mana gashi can ya buɗe miki”.       Tsaye tai kawai tama gagara cewa komai, koda ta saci kallon Ammie sai taga ta ɗan harareta, dole ta shiga kusa da shi ɗin tana faman sauke ajiyar zuciya. Ɗan karkatowa yay inda take kaɗan kamar zai ɗauka abu a ƙasan ƙafafunsu. Cikin raɗa ya furta, “You look so good dear”. Kasa cemasa komai tayi, sai ma takurewa data ɗanyi jikin kujerar, yayinda shi kuma ya ɗaga yana gyara zamansa tamkar bashi yay maganar ba dan fuskarsa sam babu wani walwalan kirki.       Sun fara tafiya shiru motar babu mai magana. Sai da suna gab da barin titin anguwar gaba ɗaya kamar ance ta kalla hannunta idanunta suka sauka akan agogon da Didi Shahidah ta ɗaura mata. Ba ƙaramin bugawa ƙirjinta yay ba har kana iya ganin yanda maƙoshinta ke kaiwa da komawa a wuyanta. Ta ƙurama agogon ido wani abu mai shegen nauyi na sake saukar mata a dukkan illahirin jikinta. Bata masan wani ƙarfi yazo mata ba tasa ɗayan hannunta ta fincike agogon, kamar zatai wurgi da shi waje sai kuma ta daure ta ɓalle bag ɗinta ta jefashi ciki batare data zuge zip ɗin ba ta maida kanta ta nannaɗe cikin ƙafafunta data ɗage gaba ɗaya zuwa saman kujerar. A take wasu hawaye masu zafin gaske da raɗaɗi suka fara zirara mata. Yanda tayi ɗin sai sukai tunanin ko barci take, musamman Ammie da tasan bawani barcin kirki ta samu ba a safiyar yau dama daren. Shima Yazeed daya ɗauka barcin tayi sai kawai ya farama Ammie hira. A haka har suka iso Zaria kasancewar tafiyar ba wata mai yawa bace ba. Da yake Yazeed yasan hanya basu wani sha wahala ba nan ma suka iso. Sun sami anguwar kanta da mutane sosai balle ƙofar gidan daya kasance masha ALLAH dan har Ammie na faɗin, “Anya Yazeed zamu iya keta mutanen nan zuwa cikin gidan kuwa?”.      Amsa ya bata da faɗin, “Ammie zaku iya shiyyasa ma nai parking tanan ganin yafi ƙarancin mutane. Zan bidaku ta baya ne akwai wata ƙofa dana sani Uncle na amfani da ita nasan zata kasance buɗe yau kodan baƙinsa”.         Cikin gamsuwa Ammie ta ce, “To Alhamdullah hakan ma yayi”.   Sun firfito yayinda a kallo ɗaya Ammie ta fahimci Manaal tayi kuka duk da gilashin dake a idonta. Sai dai ta fassara kukan nata da zaman gaba da aka sakata yi ne dole. Dan haka ta watsar da ita tama haɗe fuska. A wannan yanayin suka shiga gidan ta inda Yazeed ɗin ya faɗa. Aiko sai suka samu sauƙi jama'a anan sai falon Uncle ɗin ne ma da mutane dan akwai takalma kusan ƙafa bakwai a wajen masu ƙyau. Wucewarsu sukai zuwa cikin gida dan itama Ammien ba wannan ne zuwanta na farko ba. Hakama Amrah. Maanal ce dai bata taɓa zuwa ba dama sai yau ɗin. Amma ta ɗan san yaran gidan saboda suna zuwa can gidan nasu lokaci-lokaci...     ★----------- Babu jimawa da shigewar su Maanal tawagar ango da abokansa suka iso ƙofar gidan. Cikin tsari da nutsuwa tarin motocinsu suka layantu dai-dai inda Yaya Yazeed yay parking motarsa. Firfitowa duk suka shiga yi, kowa ka kalla shar da shi cikin dakakken yadi mai shegen ƙyau da tsada, wasu kuma shaddoji. Sai shima ango dake sanye da shadda fara ƙal tanata maiƙo da ɗaukar idanu. Sun gama firfitowa sai motar dake kusa data Yazeed ce kawai wanda ke ciki baida alamar fitowar, sai da angon ya juya yana ɗan kalle-kalle da faɗin, “Wai Uncle fa?”.         Duk motar suka kalla. Kafin wani a cikin abokan yace, “Bai kai ga fitowa ba kamar ma suna magana ne da Uncle Nass”.      “Oh ai fa an haɗu. Ni dai suyi su fito kar a fara neman waliyyai aga duk basa kusa. Bara ma na taɓa su Uncle Fawzan suma”.    Dariya abokan nasa suka sanya masa da shaƙiyanci. Yayinda yay gefe yana dariya. Wanda dai ya ambata da Uncles basu fito a motar ba sai kusan bayan mintuna talatin, suma ɗin dai ba tsoffi bane, matasane da shekarunsu ya haura talatin kaɗan, ɗaya ma zai iya girman ɗayan. Wanda bai kai shekarun ba dake sanye cikin yadi milk ne ya fito ta sashen da motar Yazeed take. Ɗan jingina yay da motar yana amsa waya kansa a sunkuye ta yanda ko fuskarsa ba'a wani gani da ƙyau. Yaci fin mintuna biyu a haka kafin ya katse wayar yana mai kai wa duƙe ya ɗauki abinda idonsa ya sauka a kai tun fitowarsa dake yashe a ƙasa. Agogo ne silver na mata mai ƙyau sosai, juyawa yay ya kalla motar daya jingina batare da yayima agogon wani kallon tsaf ba. Har ya kai hannu zai aza agogon saman motar da tunanin maybe masu motar ne suka yadda sai kuma ya fasa. Tunanin ajiyewa yay a hannunsa dan maybe su haɗu da masu motar sai ya basu, kada ya ajiye kuma wani ya ɗauka dan a ɗan kallon fisha da yay ma agogon ya fahimci mai daraja ne da za'a iya sayensa da kuɗi masu yawa. Motar da suka fito ya buɗe ya jefa agogon sit ɗin mai zaman banza daya zauna dan ɗayan ne yayo driving ɗin.  Daga haka ya juya abinsa kawai....     ______________★    Duk da yawan taron jama'a bai hana ai musu tarba ta musamman ba da girmamawa da mutuntawa. Dan can ƙuryar ɗakin amaryar gidan aka kaisu tare da musu sauka ta musamman da abinci da kayan ciye-ciye irin na biki. Sai nan nan Hajiya Majdiya keyi da Ammie dan tuntuni take son su jone su zama ƙawaye Ammien ce dai bata maida hankali ba. Ita kuma ba komai yasa hakan ba sai sanin uwargidanta jone suke da Hajiya Yaya 5&6, ko bikin nan ma dan na yarinyar matar tsakkiya ce shiyyasa Hajiya Yayan bata zo ba saboda suna matuƙar adawa da juna. Ita kuma aminiyar Hajiya Basariyya ce dan ita tun sassafe ma tana nan Zaria ɗin da duka yaranta kuma kwana zasuyi dan har Abuja inda za'akai amarya zasuje ma.         Ƙorafin da take tayi yasa Ammie bama su Maanal umarnin cin abincin. Amrah ce ta zuba ma Ammie sannan ta zuba musu. Maanal na cewa ta ƙoshi Hajiya Majdiya tace, “Haba ɗiyata kada kimin haka mana, idan kuma baƙya sonshi na canjo miki wani ko na dafo miki yanzun nan”.      Da sauri ta ɗauki spoon ta saka cikin abincin, hakan ya saka Amra kwashewa da dariya. Sunci abincin Ammie da Hajiya Majdiya na hira sai ga wata budurwar yarinya ta shigo ɗakin. Zasu iya zama sa'anni dasu Maanal, tayi ƙyau cikin lass da nake ƙyautata zaton ankonsu kenan dan ƴammata da yawa na dashi a wajen bikin. Tafawa suka ɗan yi da Amrah alamar sun san juna sosai sai kuma ta ɗan zunguri Maanal cike da tsokana ta furta, “Kurman Ammie”. Hararta Maanal ta ɗan yi duk da ba wani sabo sukai ba gaskiya, dan ko gidan sukaje iyakar Maanal ɗin da su gaisuwa ne. Cikin dariyar da suke ta gaida Ammie, yayinda Amrah ke faɗin, “Amma fa sunan nan ya dace da ita sosai, Najwa kin iya saka suna ALLAH”.      Dariya Ammie da Hajiya Majdiya suka sake yi. Nan dai suka cigaba da tsokanar Maanal ita da Amrahn. Bayan sun tsagaita ta dubi Maman nata tana faɗin, “Ummy Uncle Rafeeq fa ya iso”.        “Oh Masha ALLAH har ya ƙaraso, da'alama gudun nashi na tsiya yayi kenan. Yana ina?”.       “Na kaisa ƙaramin falonki wai yunwa yake ji, sai yaci abinci zai fita wajen ɗaurin aure”.    Ƴar dariya tai da faɗin, “Acici kenan mala'ikun tauna. Ga key dama na haɗa masa abincin ai. Idan kin ɗauka ki rufe min kitchen ɗin, sai ya gama sai nazo mu gaisa”.        Amsa tai tana miƙewa, sai kuma ta kalli su Amrah, “Ku taso muje kunzo kun ƙunshe a nan. Amrah karfa ki bari Maanal ta koya miki halinta”.        Da sauri Amra ta ce, “Da naga takaina. Maanal fa ko maijego bazata faɗa mata zaman ɗaki ba, magana kuwa yakan iya sati batayi da kowa ba”.      Hararar su Maanal tayi batare data motsa ba ko yin magana. Ganin haka suka fahimci bazanje ba. Dan haka Najma tai saurin kai ƙararta wajen Ammie. “Ammie kinga wai bazata ba”.    Kallon Maanal Ammie tayi dole ta miƙe badan taso ba suka fita. Kitchen ɗin ta shiga ta ɗauka basket ɗin da aka shirya kayan abincin sanan suka bi wani ƙofa, roƙonsu take akan suje kai amarya Abuja dan ALLAH. Yayinda Amrah ke bata amsa da basuzo da wasu kaya ba. Dai-dai zasu shiga take cewa baga nata kayan ba tasan zasu musu ai, kokuma idan zasu wuce Abujan su tsaya kd ɗin su ɗauki kayan. Shigarsu tasa babu wanda ya bata amsa. Falone ƙarami amma yayi ƙyau sosai cikin tsari.       “I'm sorry Uncle na barka kana jira”. Ta faɗa dai-dai tana ƙarasawa gaban mutumin dake zaune ya ɗan juya ma ƙofa baya ta yanda basa ganin fuskarsa da ƙyau. Juyowa yay ya kallo ta inda suke cikin sigar harara, sai idanunsa cikin na Maanal. Cak kuwa ta tsaya kamar wadda aka buge mata ƙafafu da sanda, hakama numfashinta sai da yay rawa. Shima ɗin da wani kalar mamaki ya zuba mata idanunsa har yana ɗan warosu waje na kasa ɓoye mamaki. Sai yanda yay ɗin ya saka su Amrah kallon Maanal ɗin suma cike da tambayoyi.         Lips ɗinsa ne suka ɗan motsa a hankali ya faɗi abinda ita da su duk basu ji ba. Yayinda Najma ta furta, “Uncle ko ka sansu ne?”.    Maimakon amsa mata sai ya saki wani ƙayataccen murmushi kawai da kai hannu ya ɗan shafo sajensa siriri yana lumshe idanu da kauda kansa gefe. Itama Maanal janye nata idanun tayi a hankali daga garesa, sai kuma ta juya da nufin fita. Najma ce ta riƙota da sauri tana faɗin, “Kimma isa madam. Dawo ku gaisa. Ai mu wannan abin farin ciki ne agaremu Uncle Rafeeq da budurwa a yau”.      Da sauri Maanal ta harareta da faɗin, “Aka faɗa miki”.         “Basai an faɗa mana ba komai ya bayyana kansa ko Amrah?”. Tai maganar da kallon Amrah da jikinta duk yay sanyi. Murmushin yaƙe ta mata da faɗin, “Ai kam dai gara mu sani”. Maanal zatayi magana suka ja hannunta suka ƙarasa cikin falon dole badan taso ba. Zama sukayi ita da Amrah, yayinda Najma ta duƙa gabansa tana haɗa masa abincin. Shiko ya zuba ma Maanal ido ko ƙyaftawa baiyi. Ita kuma data ɗago taga ita ɗin yake kallo sai ta ɗan hararesa, shi kuma ya sakar mata murmushi. A haka Amrah ta gaishesa. Ya amsa mata cike da basarwa kafin ya maida dubansa ga Najma, cikin sigar tambaya yay mata nuni da Maanal. Juyawa tai ta kalleta itama da ƴar dariya a fuskarta ta ce, Ƙawayena ne kuma ƴan uwana.”       “Uhm yayi ƙyau” ya faɗa yana maido kallonsa kan Maanal dai. Hakan yasa cikin dauriya da sake tsuke fuska ta ce masa “Ina yini”.      Kansa tsaye ya amsa da, “Ya gajiyar tafiya? Da ƙin amsa min waya?”.           Jitai kamar ta ja abu ta wulwula masa bisa kai amma dai ta daure kodan su Najma, batare data kallesa ba ta ce, “Hummm”.       Shima Humm ɗin ya faɗa yana ɗaukar spoon ya fara cin abincinsa.      “Oh oh mukam an sakamu a duhu, Uncle Please ka mana bayani”.     “To uwar gulma anƙi ɗin. Ga ƙofa maza kama gabanki idan na gama zan nemoki. Auntyn ma kice ta hutar da kanta ma gaisa bayan an ɗaura auren”.           “Oyooooo!! Korarmu ma ake, kinga Amrah taso mu ware to”. Tai maganar tana kama hannun Amrah suka nufi ƙofa. Miƙewa itama Maanal tayi dan bazata yarda a barsu su biyu ba, sai taga shima ya miƙe idanunsa a kanta kamar zai cinyenta da su.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖🔟 ______________ Abubuwan da nake saidawa Atamfofi Laces Shadda Materials Takalma Jakunkuna Mayafai Trolley Sarka da dan kunne Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries ____________ ........Fuska ta ɓata sosai kafin ta kallesa babu wasa. “Kasan fa bana son irin haka ko?”.         Kansa ya ɗan rausayar gefe yana murmushi da raba idanunsa a kanta. Cikin raɗa-raɗa ya ce, “Sam ban sani ba sai dai yanzu da kika faɗa min”.    Harararsa ta sake yi zata raɓasa ta wuce yay saurin shan gabanta yana ƙara faɗaɗa murmushinsa. “ALLAH idan kika ce sai kin fita tare zamu fita ne, kuma duk inda kika shiga sai na biki a gidan nan kin dai sani”.       Ɗagowa tai da mamaki ta kallesa, “Ka bini fa?”.      “Yes gwada kuma ki gani, kin dai sai ni nafi mayen ƙarfe ai garama ki koma ki zauna kawai”.      Kanta kawai ta ɗan girgiza, a zuciyata tana faɗin (Kai guy ɗin nan bala'i ne). A fili kam sai kawai ta koma ta zauna a kujerar dake kusa da ƙofar dama anan ta tashi. Ajiyar zuciya ya sauke shima tare da komawa ya zauna a inda ya tashi. Sai da ya ɗiba abincin zai kai baki sannan ya ɗago ya kalleta. “Bismillah”. Kanta ta girgiza masa kawai batace komai ba. Shima sai bai damu ba ya cigaba da faɗin, “Ina su Aneesa?”.         “Gida”.      Ta faɗa a taƙaice. Kansa ya jinjina kawai shima. Sai kuma falon yay ɗan shiru, a can ƙasan zuciyarsa wani irin farin cikine ke ɗawainiya da shi. Har dai ya kasa dannewa sai da ya furta, “Ashe ma ni a gida nake farauta amma naita wahalar da kaina. Ya kuke da su Najma?”.        Ɗagowa tayi na ɗan kallesa, ganin shima ita yake kallo sai ta maida kanta ga wayata kawai.      “Humm zama da miskilin mutum dai sai haƙuri, shike nan tunda bazaki sanar min ba. In tai wari naji. Ni bara na faɗa miki nawa alaƙan da su to. Mahaifiyarta Yaya tace uwa ɗaya uba ɗaya. Nine autan ɗakinsu, shiyyasa kikaji Najma na kirana Uncle”.          Har cikin rai sai da taji tashin hankalin alaƙar tasu. Amma sai ta dake a taƙaice ta ce, “Masha ALLAH”.   Murmushi yayi da ɗan girgiza kansa. Dai-dai nan Hajiya Majdiya tayi sallama. Amsawa yay yana mai maida dubansa ga ƙofar tare da bata izinin shigowa. Koda ta shigo idonta a kansu, fuskarta kuma ƙawace da murmushi. “Auta na kasa haƙuri ne ALLAH, yanzu Najma taje mana da wani daddaɗan labari”.       “Kai wannan yarinya da gulma take aunty”.     Cikin dariya Hajiya Majdiya ta ce, “Aini gulmar tata ta biyani. Kai idan hakan ta kasance zanyi matuƙar farin ciki Rafeeq. Kaga tuwona maina kenan, ALLAH ya tabbatar da alkairi dai”.          Ko kunya Babu ya amsa da, “Amin aunty. Sai kita tayani addu'a dan gimbiyar har yanzu taƙi bani babban fili koda na zuwa gidane a sanni. Kuma shekara ɗaya kenan muna tare”.       “Kai haba shekara ɗaya fa? Wai kodai dama itace kake faɗa mana ni da Aunty Babba kwanaki wadda kuka haɗu a jos?”.      “Tabbas itace aunty”.    “Ikon ALLAH, ni ashema abu a kusa dani yake haka. Karka wani damu kanka Maanal yarinyar kirki ce kamar yanda kake mutumin kirki. Na tabbatar itama zata soka”.            Ko kunya babu ya kalli Maanal yana wani ɗage gira da faɗin, “Wai haka?”.      Da sauri ta ɗauke kanta zuciyata na wani irin gudu da sauri-sauri. Yayinda take jin wani irin takaicinsa na yanda ya ɗaureta gaba ɗaya a wajen matar da take matuƙar ganin girma da kimarta. (Ya ilahi, RK kuwa nada hankali?) Ta ayyana a zuciyarta tana jin kamar ta saki kuka. Ita sai ma taji tausayin Hajiya Majdiya ɗin yanda taketa farin ciki kamar ma ance an aura masa Maanal ɗin.....             Bayan ficewarta ta kallesa da idanunta da suka kaɗa dan masifar dake cin ranta. Sai dai tana motsa baki zatayi magana ya mike yana dariya. “Koma mi kike son faɗa haɗiye abinki ni na tafi wajen ɗaurin aure, ALLAH yasa muma azo namu nan kusa”. Yay ficewarsa yana kashe min ido ɗaya ga dariyar rainin wayo yana yi. Yana fita baifi da mintuna biyu ba, kafin Maanal ta gama tattaro abinda ya dunƙule mata nunfashi Najma da Amra suka dawo. Rungumeta Najma tai tana farin ciki wai zata zama matar Uncle ɗinta. Surutanta take amma ita Maanal sam bata wani fahimtar komai....      _____________★         “Wai nikam lafiya duk kin zama wata sukuku ko duk gajiyar bikin ce haka Auta?”.     Didi Shahidah ce mai maganar tana zama kusa da Manaal dake kwance a doguwar kujera idanunta a lumshe. Tunda suka shigo gidan ta zube a wajen tana bitar abinda ya faru a Zaria. Ƙaramin murmushi ta sakar ma ƴar uwar tata. Sai kuma ta yunƙura ta tashi zaune sosai. “Babu komai Didi. Kawai na kwanta ne dai”.     Murmushi Didin tai mata, sai kuma ta kai hannu ta ɗan shafi fuskarta. “Auta gyaran jikin nan na amsarki sosai. Idan kika yosa duk sai ki canja kamar wata amarya dake”.         Da sauri Maanal ta ɓata fuska. Zatai magana aka buga ƙofar falon da ƙarfi har duk sai da suka razana. Hajiya Yaya ce sai yaranta biyu biye da ita. Cikin hargagi da masifa ta shiga ƙwala kiran ainahin sunan Ammie. Duk miƙewa sukayi, dan yanda take a birkice zakasan babu lafiya. Ita kanta Ammie da sauri ta fito ɗankwalinta a hannu.       “Ya salam Hajiya miya faru?”. Ammien ta faɗa tana ƙarasowa cikin falon da sassarfa.    “Oh tambayata ma kike miya faru? Wai Asiya nikam kodai ke kika haifar min Yazeed a gidan nan ne?”.         A hankali Ammie ta sauke ajiyar zuciya tana mai girgiza kanta. Sai kuma a nutsenta ta bata amsa da “Hajiya kiyi hakuri ban san akanmi kike magana ba. Yazeed ai kowa yasan kece kika haifesa”.       “To kuwa tunda kin san ni na haifi abina ki fitar min sabgar yaro. Dan wlhy idan ma kina mafarki ne ki farka. Ki kuma je ki sanarma bokanki anan anfi ƙarfinki anfi ƙarfin tsafinsa. Alhajin dai da kika iya mallaka har kika aura kinci nasara, wataran kuma ruwa zai ƙarema ɗan kada shima. Amma Yazeed har gaban abada bazai auri wannan ƴar taki ba, wancan ya samu ya gudu da ƙyar ko nace uwarsa ta miƙe tsaye a kanku shine ni za'a ƙaƙudubar min yaro da tsafi da asiri a haɗashi da sauran ciwo. Kuma wlhy daga yau sai yau, kika sake ɗaukar min yaro ya kaiki anguwa duk abinda nai miki kece kika jashi a gidan nan, mayyar mata kawai.......”       “Haba Mamma nafa miki bayani Daddy ne yace muje ba laifin Ammie bane ba”. Yazeed daya shigo falon ya katseta cikin sarƙewar murya. Kansa ta juya da masifa kamar zata cinyesa. Harda faɗin idan har bai rabu da Maanal ba ALLAH sai ta ɗaga masa mama. Sai kuma ta juyo ga Ammien ta cigaba da mata zagi na rashin mutunci da gori. Gaba ɗaya rayukansu Shahidah sun gama ɓaci, yayinda Amal ta kasa haƙuri ta yunƙura zata tanka mata Ammie ta hanata. Dole tai shiru. Da gudu Maanal tabar falon kuka mai ƙarfi na ƙwace mata. Hakan yasa Amal bin bayanta itama zuciyarta kamar zata kama da wuta. Sam bata so Ammie ta hanata ba. Amma koba yau ba ta ɗauki alwashin sai ta gogema matar nan abinda ke kanta. Haba wanna abin ya isa haka mana. Tasara miyyasa mutanen nan basu da adalci sam, kowa dai Ammiensu kowa Amminsu sai kace itace kaɗai kishiyarsu. Taga dai suma kishiyoyin juna ne, amma basa fitinar juna sai Ammie, shin sai yaushe ne Ammiensu zataji daɗin rayuwar aurenta?. A gidan mahaifinsu bata zauna lafiya ba, fitinar miji data uwar miji, aka dawo ta kishiya har sai da ta bar musu gidan, yanzu kuma anan ta kishiyoyi har biyu....       Sosai Hajiya Yaya ta diga jidali da tujara wa Ammie kamar ta samu ɗiyarta. Ammien kuma bata tanka ba bata bar ƴaƴanta sun tanka ba. Hakan kuma shine mafi mata ciwo, kai su duka su wannan shirun da Ammien ke musu akoda yaushe na ƙona musu zuciya da ruhinsu. So da yawa suna mata abu dan ta tanka amma sai ta basar. Da ƙyar Yazeed ya lallaɓata ta fita. Suka bar Ammie da su Manaal cikin matsanancin ɓacin rai. Ga Ammie ta hana kowa maganar har dare sashen nasu babu daɗi. Hakan yasa duk suka kwanta da wuri. Sai can cikin dare Maanal ta bar ɗakinsu da ayanzu yake nata ita kaɗai sai idan sauran ƴan uwan nata sunzo gidan ne ta koma na Ammien. Ta sameta tana salla, dan haka itama ta fasa kwanciyar tayo alwala tabi sahunta. Sai da sukai sallar asubahi suka ɗan sake kwanciya Maanal ɗin dai nata daurewa dan bata jin daɗi......   ____________     “Wai Auta bazaki tashi a barcin nan naki ba haka nan. Jibafa lokaci ko kari bakiyi ba, ga ƴan uwanki na jiranki ki rakasu gidan mai gyaran jiki. Suna fara damunki kuma nasan zaki manta da yunwar cikinki ne ku tafi”.           Kaɗan Maanal ta buɗe idanunta ta ɗan kalla Ammie mai maganar ta maida ta lumshe tare da sake naɗe jikinta waje guda. A yanayin mai barci da yanayin muryarta mai zurfi ta amsa da, “Ammie bana jin daɗi”. Da sauri Ammie ta ajiye abinda ke hannunta ta nufeta. Zama tai a bakin gadon tare da janye duvet ɗin da take a ciki ta ɗaura hannunta a goshinta, da sauri ta janye ta maida a wuyanta. “Ya salam, Manaal kinga tashi muje asibiti jikinki zafi, amma bayan kinyi sallar asubahi ne ma zazzaɓin nan dai?”.        Hannun Ammien ta riƙo ta rungume a ƙirjinta. Cikin rauni ta furta, “Ammie abinne zai zo, ga kuma ƙirjina yamin nauyi, kwana biyu kenan kullum da safe nake zazzaɓin, shekaran jiya ma da muka taho banda lafiya”.      Sosai rauni da damuwa suka bayyana a fuskar Ammie. Muryarta har rawa yake wajen furta, “Yaushe ya dawo yimiki kuma Maanal?”.          “Ammie duka watannin nan da banzo gida ba yanayi. Na ƙarshen nan kwanana uku a hospital ma, hakkin ma ji nake kamar zai dawo”.     “Ya arrahaman. Amma a watannin nan idan na tambaye ki kuma kita cewa babu damuwa. Haka kika dinga shiga cikin halin nan Manaal amma kina ɓoye min? Shiyyasa tunda naga duk kin sake figewa nasan kin ɓoyemin abubuwa ne. Nikam wannan ciwon naki na tayarmin da hankali, dan ALLAH Maanal ki cirema ranki duk wani abu, itafa rayuwa ɗaya ce, sannan bawa baya kasancewa a cikinta sai da jarabawa dama. Bakiga na haƙura nima na manta komai ba, hakama ƴan uwanki?”. “ALLAH Ammie babu abinda na sakama raina, kune kuke ganin kamar har yanzu ina riƙe da abubuwa, amma sam ba haka bane ba. Nifa musulma ce, kuma nasan minene rayuwa da ƙaddara. Ki cigaba da min addu'a kawai Ammie”. “In sha ALLAHU koda yaushe cikin yi muku nake. Kuma Alhamdullah da sauyin rayuwa da UBANGIJI ya bamu mai tazara sosai, idan mukai dubi da baya. Tashi kiyi wanka naima bana maigadi magana ko zamuje wajen mai maganin nan tunda nasa anji daɗinsa”.            “Amma Ammie shima kuma gashi ya dawo ai”.     “Duk da haka Manaal, ai kin samu ban iska tunda an samu sassaucin wahalar nan da kike sha kusan na shekaru bakwai”.          Kanta ta ɗan jinjina cike da damuwa. Dan ita kanta ciwon nan na ɗaga hankalinta, ga shi kusan duk sanda zatai period sai abun ya ƙwaɓe mata da ciwon mara da take fama da shi shima, dan kamar ciwon maran yana zama sanadin tada ciwon zuciyar ne sakamakon tuno mata da abubuwan da suka faru baya da hakan keyi a duk irin lokacin. Har rama take farayi idan akace maka lokacin nan ya matso mata. Dan ita kaɗai tasan irin kalar azabar da take sha a rayuwarta. Duk yanda zata misalta ba lallai a fahimta ba. Shiyyasa idan akace mata haihuwa nada ciwo sai taita mamaki da ganin anya zata kai azabar da take sha a ciwon mara idan zatai period. Itafa nata ma dabanne dana duk wanda ta taɓa sani, ƴan uwanta ma duk sunayin ciwon idan zasuyi prioud ɗin, amma bai kai ko rabin nata ba. Kuma sunayin aure duk suka daina. Ammie tace ita suka gado, dan itama tasha fama har sai da ta haihu sannan. To ita abin nata ya zama biyu ne, ga ciwon zuciya kuma, shiyyasa hankalin kowa ke matuƙar tashi a duk sanda irin haka ya taso musamman akan ita Manaal da nata yafi tsauri.      Ammie da kanta ta taimaka mata har zuwa bayi bayan ta haɗa mata ruwan zafi. Haka ta daure tayo wankan ta fito sai kuma rawar sanyi. Kasa zaman shafa mai ma tayi ta haye gadon ta sake ƙudundunewa. Dai-dai nan Amaal da Shahidah da Ammie tai kira a waya ta sanar musu suma Baba maigadi magana akan maganin Maanal ɗin dan ɗan uwansa ne ke bata suka shigo ɗakin. Su kansu su Shahidahn duk fuskokinsu sun nuna damuwa. Ƙarasawa sukayi inda Manaal ɗin ke ƙudundune suna mata sannu. Sai kuma Shahidah ta juya ta fita tana faɗin bari na amso maganin dan kamar sallamar Baba maigadin. Ilai kuwa shine, dan babu jimawa ta dawo da magani a gora. Da taimakon Ammie suka bama Maanal ɗin saboda rashin sonta da magani. Tana gama sha kuwa sai amai, dama haka yake mata, sosai tayi aman har ta basu tausayi. Haka suka taimaka mata suka gyara mata jiki ta sake yo wanka ta canja kaya ta koma ta kwanta. Cikin amincin UBANGIJI sai kuma barci mai nauyi sosai yay awan gaba da ita. Ajiyar zuciya suka dinga saki a tare, saboda in sha ALLAHU suna ganin kuma shike nan.      Barci kuwa tayi sosai, dan bata farka ba sai bayan azhar. Alhamdullah taji daɗin jikin, ta samu ta sake yin wanka Ammie da kanta ta bata abinci, sai da taci sosai dan Ammien nata lallaɓata ga kuma waya da sukai da Nene zata zo gobe in ALLAH ya kaimu ya sake sakata jin daɗi saboda matuƙar son Nene da take a rayuwarta. Ga kuma ƴan uwanta zagaye da ita. Hakkanne ya sake ƙarfafata zuwa bayan la'asar tace suje ta rakasu gidan mai gyaran jikin zata iya. Koda sukace a'a sai Ammie tace suje ai fitar zata saka ta sake jin ƙarfin jikinta ta kuma warware. Da wannan shawarar sukai amfani suka tafi........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖1️⃣1️⃣ ______________ Abubuwan da nake saidawa Atamfofi Laces Shadda Materials Takalma Jakunkuna Mayafai Trolley Sarka da dan kunne Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries _________ .........Fitarsu babu jimawa ashe masifar Hajiya Yaya ta jiya bata ƙare ba. Dan yau yinin nan guda bata gidan, sai yanzu zuwa yamma sai gata ita da ƙanwarta da suke kira Aunty Sabuwa a gida da yaranta ƴammata guda biyu. Nan fa wata sabuwar fitinar ta tashi dan har sashen Ammie suka sameta wai sun sake zuwa mata gargaɗi ita da Maanal akan Yazeed. Yayinda aka nuna ƙaramar ƴar Aunty Sabuwar wai itace Yazeed zai aura dan haka sai Maanal da Ammie su maida maitarsu a kansa. Ba ƙaramin zafi kalaman sukaima Ammie ba. Ga shi lokacin su Manaal ma basa gidan taje raka su Shahidah gidan mai gyaran jikin da za'ai musu. A yanzun kam kasa daurewa Ammie tai ta yayyaɓa musu magana. Fuskarta kuma ɗauke da murmushin da yake ƙona zuciyarsu ta kalli Sabuwa mai kora bayanin..      “ALLAH sarki ai mu wannan abin farin cikinmu ne Sabuwa. Ina kuma taya Yazeed murna da fatan alkairi dan ko bai auri Maanal ba har gobe ɗa yake a gareni tunda ina auren mahaifinsa. Daga ke har Yaya kuma ku daina ɗagama kanku hankali akan Maanal, dan ita dama sam bata buƙatar wannan haɗin, ta karɓa ne kawai dan maida alkairi da hallaci. Har miye abin kace nace da ɓacin rai akan abinda ALLAH ne maiyi kawai. Wani rabon zafi ne da shi musamman ma na aure, idan aka tsananta sai ya kawar da rayuwa kuma ayi abinda ba'a son a bayan ran masu adawar”.       “Oh kina nufin zaki kawar damu kenan ki aurama Yazeed ƴar ki?”.     Hajiya Yaya da kalaman Ammie suka shige ta ta faɗa a hargitse. Murmushin Ammie ta sake yi da faɗin, “Rayuwa da mutuwa ai na ALLAH ne kawai Hajiya. Ina fargar da kune dan ikon ALLAH yafi gaban wasa, ku daina matsawa da yawa dan ALLAH”.        Wannan fa kalamai na Ammie sune suka sake tunzura wutar wannan harmutsi. Dan takai har Hajiya Yaya na iƙirarin maka Ammie a kotu wai tace zata kashe su ta aurama Yazeed ƴarta. Haka ta kira maigidan tana zazzaga masifa. Ta gama ta fice zuwa gidansu ita da ƴar uwarta suka sanar da mahaifinsu. Lokacin da su Manaal suka dawo gidan sun tadda komai a hargitse matuƙa. Ga su Hajiya Basariyya ƴan biki sun dawo daga Abuja ita da yaranta. Aiko ta shiga tai kane-kane tana ƙarama wutar fetur a bayan fage. A yau kam Maanal data jima da mutuwa mai rashin ragi ga duk wanda ya taɓata sai gata ta dawo. Wani irin ɓacin rai ya rufe idanunta. Cikin razananniyar tsawa ta ce, “Kai haba ya isa haka mana. Nace ya isa!! Ya isa!!!. Wai shi Yazeed ɗin anyisa da gold ne ko diamond ko tagulla ko azurfa ne? Ko na taɓa ce muku dama ina son aurensa ne? Gashi nan ku tambayesa ko sau ɗaya nata amsa masa ina son sa? Shin Yazeed na taɓa cewa ina sonka? Ka faɗa musu mana ko zasu kama kawunansu. Ni nan da kuke ganina bama Yazeed ba kowanne namiji bana buƙata, domin Manaal ta jima da amincewa zata rayu a matsayinta na MACE kawai batare da kowanne NAMIJI ba takowanne fanni. Kun taɓa ganin wanda ya mutu yana son kasancewa da rayayye? Mi matacce zaiyi da rayayye? Ko shi rayayyen mi zaiyi da matacce?. Dan haka idan kunso ku aurama Yazeed mata huɗu a rana ɗaya ko duka matan duniya shine zaku birgeni ko kanku dan ALLAH, damuwarku ce wannan. Ku daina fakewa da maganar Yazeed kuna cin zarafin Ammien mu, idan ba haka ba wlhy wlhy zakuga ainahin Maanal kuwa. Dan kaf ɗinku sai kunsha matuƙar mamaki ba tsoro yasa ake ƙyaleku ba girmama kaine da darajar shi Yazeed ɗin da Daddy. Saboda ina girmama waɗan nan mutanen guda biyu a cikin TARIHINA. Zan iya ce muku sune suka saka zuciyata banbanta sunan MAZA daga jam'in da nai musu. Amma tunda kunce ku baku san kawaici ba kumuje zuwa daga yau a gidan nan ni daku ɗan halak ka fasa. Na fiku iy.....”       “Manaal!!”.   Ammie ta faɗa cikin tsawa tana ƙoƙarin riƙota. Kanta ta shiga girgizawa sai kuma ta fashe da kuka mai ban tausayi tana cigaba da faɗin, “Ammie ki barni na gaji, nagaji haka nan Ammie. Mi mukayima rayuwa ne? Mi muka tare musu ne? Mi mukayi musu da zafi haka da kowa ke son ganin ya wulaƙanta rayuwarmu, na taɓa ce musu bazan rayuwu ba sai da wani NAMIJI ne Ammie?. Basa tunanin kafin su ina dake ba! Basa tunanin ba dole bane sai mace ta rayu da namiji zata amsa sunan mace? Basa tunanin na haƙura da wanda ma yay sanadin kawoni wannan duniyar bisa izinin UBANGIJI balle su, su ɗin nan da ba komai ba a rayuwata. Su ɗin nan da zan iya canjawa da ire-irensu a duk lokacin da naso. A tunaninsu dole-dole sai da sune zan RAYU?! Ko babu su zan rayu Ammie, zan rayu dake kaɗai da ƴan uwana kun isheni, kun wadatar dani a wannan rayuwar, bana buƙatar kowanne namiji, suje, suje ban buƙatarsu.....” kuka ya sarƙe ta sai tari. Ɓull!!! Ɓull!! Jini ya dinga ambulowa ta bakinta ta hanci.        Wani irin firgitaccen kukan tashin hankali Ammie ta saki jikinta dake riƙe dana Maanal na rawa. Tuni Shahidah, Manaal da Yazeed sun yo kansu a ɗari. Su kansu su Hajiya Yaya da tawagarta da sauran jama'ar gidan al'amarin ya matuƙar firgitasu. Dan a wai-wai suke jin Maanal nada matsalar ciwo mai haɗari, amma basu taɓa ganinta a ciwon ba, kai zasu ma iya rantsuwa basu taɓa ganin ana aman jini ba sai yau musamman wannan da takeyi ta baki ta hanci.        Kowa ya rikice an rasa mai cewa a tafi asibiti. Sai baba maigadi ne daya iso wajen a hargitse yake faɗin asibiti ya kamata a tafi. Da wannan magana tashi suka zabura gaba ɗaya. Cak Yazeed ya ɗauki Maanal daketa aman jini ya nufi hanyar gate a maimakon motocin gidan saboda tsabar yanda ya rikice. Shahidah, Amal, Ammie suka take masa baya sai Amara da itama ta zabura ta bisu tana kuka. Fitowar Yazeed dai-dai da isowar RK ƙofar gidan, dan haka a cikin rikicewa Amal ta buɗe motar RK ɗin kawai tana cema Yazeed ɗin ya shiga batare data tantance motar waye ba itama. Shima bai wani tantance komai ba ya saka Maanal a ciki, da sauri itama Ammie ta shiga ta rungumeta tana kuka da faɗin, “Haba Maanal ya zaki mun haka, dan ALLAH kiyi haƙuri kada ki tafi ki barmu mu muna sonki, muna tsananin ƙaunar Maanal. Muna buƙatar ki a duniyar mu Maanal...”     Wannan furuci na Ammie shi ya zaburar da RK da ya tsaya yana kallon ikon ALLAH, sai kuma lokacin ya gane Ammie da Amra dake kuka. Duk da halin da Maanal ke ciki itama bai gagara ganeta ɗin ba. Ai da wani irin tashin hankali ya tada motar, Yazeed ya shiga kusa da shi suka bar anguwar. Napep Amal da Shahidah da Amrah suka tare suma suka bi bayansu....       Yazeed ne ya faɗa masa asibitin da zasu je, inda Maanal ke ganin likita kenan. Asibitin kuɗin ne, kasancewar kafin su isa ma Yazeed ya kira abokin nasa doctor Nazeer ya sanar masa zuwansu suna isowa suka samu nurses har huɗu da Doctor Nazeer ɗin kansa na jiransu a waje. Da ƙyar aka iya ɓanɓare Manaal daga jikin Ammie. A kallo ɗaya idan kai mata zakai tunanin bazata sake rayuwa ba. Dan yanda take yunƙurowa ƙirjinta na ɗagawa tana aman jinin kaɗai ke nuna akwai sauran numfashi a tare da ita. A haka dai aka shiga da ita ciki kowa a kiɗime. Dai-dai nan suma su Shahidah da suka biyosu a napep suka iso...        Abu kamar wasa sai ga ƙaramar magana ta zama babba. Dan yanda doctors ke shiga da fita ɗakin da aka shiga da Maanal basa ko sauraren kowa zai tabbatar maka al'amarin yayi tsamari da yawa. Dan har zuwa goman dare babu wani bayani mai daɗi. Zuwa sannan Nene ta iso, (Nene ƙanwar mahaifiyar Ammie ce da yanzu take kallo kamar mahaifiya. Zamu iya cewa ma ta sandinta Ammie da ƴaƴanta suka zo cikin Kaduna. Ita a anguwar dosa take, ita da zuri'arta. Dan itama yaranta huɗu duk maza a yanzu haka duk suna da aure da ƴaƴansu suma, sai ɗaya ce kawai mace itama dai tayi aure).       Har wannan lokacin RK na asibitin, hasalima tuni ya shige cikin likitocin da shi ake bama Maanal taimako kasancewarsa shima ƙwararren likita masani a fannoni da dama daya shafi aikin. I'd card ɗinsa kawai ya nunama Doctor Nazeer ya amince masa shiga cikinsu aka rufu kan Maanal. Haka shina Yazeed tsaye yake da ƙafafunsa. Duk abinda akace ana buƙata kafin wani dogon lokaci zakaga ya kawosa. Sai su Ammie suka kasance ƴan addu'a da share hawaye. Daga can gidan dai babu wanda ya biyo bayansu, sai dai Yazeed ya kira mahaifinsu ya sanar masa. Ya kuma tabbatar masa a yau ɗin nan zai baro inda yake zuwa Nigeria. Domin shima hankalinsa yay matuƙar tashi bana wasa ba. Koda yasa Yazeed ya haɗashi da Ammie kasa magana tayi sai kuka data fashe masa da shi kawai. Sai hakan ya sake birkita masa lissafi gaba ɗaya babu shiri ya fara neman ticket ta online......       ___________   Alhaji Usman Chalawa bai iso ba sai washe gari wajen misalin ƙarfe ɗaya na rana. Babu wanda yasan da dawowar tasa a cikin matansa, dan hatta ita ma Ammien bai sanar mata ba. Sai Yazeed kawai ya sani. Shi kuma tashin hankali ya mantar da shi sanar ma kowa sai da Daddyn ya tura masa saƙon yazo ya ɗaukesu sun kusa sauka sannan ya tuna. Ya bar asibitin ne dai-dai lokacin RK na bada shawarar yima Maanal transfer zuwa Abuja. Dan gaskiya jikin nata sam babu daɗi. Su kansu likitocin sun fara karaya, RK ɗin ne ma ke ƙarfafasu duk da shima gwiyawunsa a sare suke yana dakewane kawai da ƙarfafa kansa...       Kai tsaye asibiti Yazeed yayo dasu Daddyn. Rungume Ammie su Waleed sukayi, yayinda take kallon mijin nata cikin karaya idanunta cike da ƙwalla. Cike da kulawa ya girgiza mata kansa alamar kar tai kuka. Sai kawai tai ƙasa da kanta tana mai rungume Hameed da Waleed sosai a jikinta. Idanun nasa ya ɗauke cike da damuwa ya maida kan su Shahidah dake gaishesa. Ya amsa musu da kulawa yana tambayarsu mai jiki. Maimakon amsa sai suka fara hawaye suma. Jiyay gaba ɗaya zuciyarsa ta ƙara karaya, da ƙyar ya iya gaishe da Nene, sannan ya wuce office ɗin doctor inda suke meeting shi da su RK. Doctor ne yay ma RK bayanin matsayin Daddy a wajen Maanal duk da tare da Yazeed suka shigo, dan RK bai ɓoyema doctor alaƙarsa da Maanal ɗin ba. Cikin girmamawa RK ya rissina ya gaishe da Daddyn. Nan ma doctor ya sanarma Daddy RK likita ne, ya kuma masa bayanin shawaran da suke akai yanzu haka game da maida Manaal ɗin Abuja. Babu wani musu Daddy ya yarda, tare da ƙarfafasu cewar ayi komai yanda ya kamata ama bar ɓata lokaci, bari yaje ya bincika ko akwai jirgi mai wucewa yanzu sai su wuce a ciki zaifi mota sauri....      Hakan kuwa akayi, dan zuwa la'asar an gama shirya Maanal zuwa tashar jirgin ƙasa. Zasuyi gaba harda Nene da su Shahidah. Ammie kuma sai zuwa gobe in ALLAH ya kaimu da safe zasu bisu ita da Daddy kamar yanda ya buƙata.         Suna isowa Abuja ambulance ce tazo ta ɗauki Maanal dan tuni RK ya gama booking komai. Shi da Yazeed ne suka bi ambulance ɗin, yayinda mijin Shahidah da yazo shima ya ɗauki su Shahidah ɗin da Nene da Amal. Yaran duk suna Kaduna sai gobe idan ALLAH ya kaimu Ammie zata taho da su nan. KK HOSPITAL asibiti ne mai tsanani ƙyau da kowa ya sani a cikin Abuja. Suna da ƙwararrun likitoci da suka san aikinsu ƙwarai da gaske. Suna ƙoƙari matuka wajen bama mara lafiya kulawa yanda ya kamata, ga sauƙin kashe kuɗi dan talaka da mai arziƙi duk zasu iya biya. Babu wani ɓata lokaci cike da kulawa aka shiga da Maanal, yanda ake girmama RK a asibitin yasa suka fahimci eh lallai yana da wani matsayi babba a wajen.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖1️⃣2️⃣ ______________ Abubuwan da nake saidawa Atamfofi Laces Shadda Materials Takalma Jakunkuna Mayafai Trolley Sarka da dan kunne Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries __________ .......Yau kwanakin Maanal biyu a KK HOSPITAL. Zamu iya cewa Alhamdullahi abubuwa sun fara dai-daita, duk da dai har zuwa yau ba'a barin kowa shiga inda take sai doctors kawai. Tun a jiya su Ammie suka iso suma ita da Daddy. Tsabar munafunci na Hajiya Basariyya sai ta ce zata biyosu taga jikin Maanal ɗin. Dan a waccan ranar da Daddy ya dawo tunda ya koma gida ya rufesu da faɗa ita da Hajiya Yaya akan ƙin zuwansu asibiti, sai dai faɗan nasa yafi tsamari akan Hajiya Yaya data zama itace sanadin komai, dan yama sanar mata ya haramtawa Sabuwa zuwa masa gida, idan kuma tai gigin zuwa ALLAH sai ya saka jami'an tsaro sun kamata. Itama kuma ta jira hukuncinsa bayan Maanal ta warke dan yanzu baida lokacinta. Tofa wannan abu da Hajiya Basariyya dake laɓe taji yasa ta dawo ta lallaɓa Daddyn ta bashi haƙuri akan nata laifin daya faɗa naƙin zuwa asibiti kawai, ta kumaji duk halin da ake ciki akan maida Maanal Abuja shine ta maƙale itama zata bisu. Ammie bata san da batun ba sai da suka fito zasu wuce taga Hajiya Basariyyan. Sosai ta sake jinjina makircin matar a ranta, dan ta jima da gane wacece Basariyya, sai dai bata taɓa nuna mata ba ta barta da halinta. A lokacin ma murmushi kawai tai batace komai ba, hakan kuma sai ya ƙonama Hajiya Basariyyan rai, ta rasa wacece Ammie, ta rasa ta inda zata kamo lagon matar, ta rasa ta inda zata shiga jikinta kamar yanda take shiga jikin Hajiya Yaya tasan sirrinta. Amma ba komai, idan tasan wata ai bata san wata ba.      Anan Abujan itama ta kwana dan Daddyn nada gida anan ɗin dan yana harkar sayen gidaje da sayarwa ne. Kasancewar komai akwai a gidan yasa sauka kawai sukai anan ɗin. A yanzu ma haka tana a asibitin tare da su. A ɗakin da aka kwantar da Maanal ɗin ɗakine na musamman kamar palor da bedroom, dan haka duk suna a palor ɗin zaune itama Maanal na daga ciki babu mai shiga sai dai su leƙata ta jikin ƙofar glass ɗin. Shahidah da Amal suka iso ɗauke da abinci, bayan duk sun gaishesu suna ƙoƙarin zama Daddy da RK suka shigo ɗakin sai wani ba'indiyen likita da shine akan case ɗin Manaal ɗin ma. Gaishe da Daddy su Shahidah sukayi, sannan suka gaisa da su RK da suma suke gaida su Ammie. Su RK na ƙoƙarin barin wajen kamar daga sama sai Hajiya Basariyya cewa tai, “Nikam likitan nan kamar na sanka”. Yanda tai maganar idonta akan RK ya sakashi fahimtar da shi take, kallonta ya ɗan yi sai kuma ya rissinar da kansa tunda bai san matsayinta ba a garesu ya ce, “Mommy zata iya yiwuwa. Sai dai ban san a ina kika sanni ba”.     Batare data damu da kallon harara da Daddy ke mata ba ta ce, “A zaria gidan Alhaji Saminu Ashafa”.      Cikin jinjina kai RK ya bata amsa da, “Ni ƙanin amaryarsa ne Majdiya”.    Kafin Hajiya Basariyya ta samu yin magana Ammie da Daddy suka dubeshi. Abinda ya faru a ranar da sukaje ɗaurin aure gidan Alhaji Saminun ya shiga dawo mata a rai. In dai batai kuskuren fahimta ba shine yaron da Hajiya Majdiya ke mata bayanin yana son Maanal kenan. Wani irin sanyi taji a ranta, dan koba komai ita dai yaron ya shiga ranta a lokaci guda, sannan ta samu karɓuwar addu'ar ta akan al'amarin Maanal ɗin da Yazeed tunda ga raba gardama yazo.. Shikam Daddy murmushi yayi cike da nuna mamaki ya ce, “Ikon ALLAH ashe ma kai ɗin na gida ne doctor. Ai nasan Hajiya Majdiya kuwa sosai saboda Alhaji Saminu aminine kuma ɗan uwana ta fanin mahaifiya, zan iya cemaka ma neman auren Majdiya da komai dani akayisa”.       Wani ɗan karen daɗi ne ya ratsa RK har cikin maƙwallaton zuciya. Sai yake jin gaba ɗaya matsakarsa ma shi ta ƙare kenan. Nan take ya ƙara sakewa da Daddy. A karo na farko Daddy ya shiga ɗakin da Maanal ke kwance shi da Ammie da Nene kawai. Sosai tausayin Maanal ya ƙara mamayesu, dan Ammie kasa daurewa tayi sai da tai kuka. Duk wanda yaga Maanal ɗin sai yayi matuƙar tausaya mata. Numfashi ma sai da taimakon na'urori take yinsa. Duk ta sake figewa. Sun mata addu'a suka fito aka bar Nene kawai dan doctor ya buƙaci a ɗan goge mata jiki a canja mata kayan jikinta. Da ance Ammie tayi amma ta nuna bazata iya ba. Sai dai Nene tayi. Tsaf Nene ta gogema Manaal jiki aka canja mata kaya. Doctor da RK suka shigo, hakan yasa Nene fita ta basu waje dan suyi aikinsu. Ta tarar da Hajiya Basariyya cike fam da takaici, wai tana fushine ita ba'ace ta shiga ta duba Maanal ba, shine taima Daddy ƙorafi akan hakan.  Shi kuma yaƙi tanka mata shine ta cika tai fam. Ita dai Ammie haƙuri ta bata, yayinda su Amal ke mamakin abinda Hajiya Basariyyan tayi. Ita kanta Nene abin ya bata mamaki, dan bataga abin wani ƙorafi ba a wajen tunda gasu Shahidah suma ba'a barsu sun ganta ba. Ita kanta dan Ammie tace bazata iya gogema Maanal ɗin jiki bane aka barta ta shigan. A haka Yazeed da yaje Kaduna ya dawo ya samesu, tare da duk yaran gidan yake tafe, amma abin mamaki yau ɗin ma Hajiya Yaya bata zo ba....       Da mamaki Amrah ke kallon RK, har dai ta kasa haƙuri sai da tayi magana. Murmushi yay mata da tambayarta ya gajiyar biki. Hakan data faru tsakanin Amrah da RK sai ya tsayama Yazeed a zuciya har sai da ya kira Amrah ɗin gefe ya binciketa. Kanta tsaye ta sanar masa abinda ta sani. Yayi mamaki ƙwarai da gaske. Haba no wonder yake mamakin yanda RK ɗin ke tsaye very serious akan case ɗin Manaal ɗin. Ya jima yana son haɗa al'amarin a ransa amma ya gaza samun makama, tunda shi dai sun fitone kawai suka samu motar RK ɗin a ƙofar gida, daga wannan taimakon kuma na kawosu asibiti baiyi tunanin cigaba da ganinsa ba amma sai yaga ya tsaya tsayin daka komai anayi da shi, yayi tunanin kawai tausayi da taimakone sai da aka dawo Abujar nan ya ɗan fara zargi a ransa sai kuma dai yay saurin kaudawa tunda bashi da tabbas musamman ganin RK ɗin matsayin likita shima. Ashe kuwa hakanne.        A ranar su Amrah suka koma Kaduna harda Hajiya Basariyya data wuce bisa tirsasawar Daddy dan kuwa badan taso ba, taso ace sai taga kwal uwar daka. Ta zata da Daddyn zasu tafi sai yace mata shi yana nan har sai yaga yanda hali yayi akan jikin Maanal ɗin. Hakan ya masifar ƙona mata rai, dan ta kalla abunne a sigar rainin hankali irin na maza kawai. A ganinta Daddyn nason holewa da Ammie ne a wannan ƙayataccen gida shine ya fake da ciwon agola. Ita Ammie tsaf ta fahimci manufar Hajiya Basariyya ɗin, amma sai ta basar kawai tama dinga ƙarfafa Daddy ɗin akan yaje suma suna da hakki a kansa, tunda dai Maanal ɗin tana samun dukkan kulawa anan ɗin gasu kuma ga Yazeed shi yaje ya huta gashi ya dawo daga tafiya. Sam Daddy ƙin saurararta yayi, daga ƙarshe ma ya fara fushi da ita dole tai shiru ta zuba masa ido kawai su Hajiya Basariyyan suka wuce...       A ɓangaren Yazeed kuwa ya fara janye jikinsa daga RK. Tun RK ɗin bai fara fahimta ba har ya fahimta. Dan sai wani isa ma Yazeed ke nuna masa akan Maanal ɗin yanzu da gadara. Mamaki hakan ya bama RK, dan shi a zatonsa Yazeed da Maanal uwa ɗaya uba suke ko uba ɗaya dan yana ɗan tantamar Ammie ta isa haihuwar kamar Yazeed ɗin. Bai daiyi magana ba yabar abin a ransa dan ganin iya gudun ruwan Yazeed ɗin. Ana cikin wannan dambarwa a tsakaninsu Hajiya Majdiya yayarsa tazo duba Maanal ita da yaranta tun daga Zaria. Dan shine ya kirata yake sanar mata, aiko baiwar ALLAH sai gata tazo. Ammie tayi mamakin hakan kasancewar batai waya da Hajiya Majdiya ɗin ba akan hakan. Sai Hajiya Majdiyan ke sanar mata, “Sirikinki ne ya kirani yake sanar min ai.”     Murmushi Ammie tai da faɗin, “Haba nayi mamaki fa, sai kuma hankalina bai kawo nan ɗin ba. Ai babu abinda zamuce da Rafeeq sai fatan alkairi. ALLAH yay masa albarka”.         “Amin ya rabbi. Yaya jikin nata yanzu? Dan naga hankalinsa a tashe yake matuƙa yau har cewa yay na nema masa masu saukar Alkur'ani yana son ai mata”.     Ajiyar zuciya Ammie ta sauke. Zuciyarta na sake jin nutsuwa da RK ɗin. “ALLAH sarki, ALLAH ya saka masa da alkairi. To Alhamdullahi zamu ce. Sai dai har yanzu bata san wanda ke kanta ba. Amma dai suna tabbatar mana bugun zuciyarta na dai-daita zuwa yanzu. Kowane lokaci kuma zata iya farfaɗowa cikin hayyacinta.”        “ALLAH ya bata lafiya, yasa ya zama kaffara. Abin tausayi yarinya ƙarama haka da wannan irin babban ciwo mai haɗarin gaske, ALLAH ka bamu ikon cinye jarabawoyinmu. Shiyyasa gata nan sanyi-sanyi ko kuzarin kirki bata da shi. Ban taɓa sanin tana da wannan lalurarba ai da tuni na haɗaku da Rafeeq ɗin dan aikinsa ne. Yanzu haka reshen wannan asibitin suka buɗe acan garin jos shine yaje can da kansa yake riƙe da asibitin kusan shekara ɗaya kenan, anan ne ma ALLAH ya haɗasa da ita”.         Murmushi Ammie tayi tare da jera addu'a ma RK ɗin. Ganin yanda Ammie ta ɗauki zancen da muhimmanci Hajiya Majdiya ta cigaba dama ɗan uwanta campaign wajen Ammie. Yinin gaba ɗaya suna a tare sai bayan Magrib RK ya ɗaukesu ya maida can gidan babbar yayarsu dake nan Abujan zasu kwana anan dan sai gobe idan ALLAH ya kaimu zasu koma Zaria. Sosai Ammie taji daɗin kasancewa da Hajiya Majdiya a wannan rana. Dan zaman ya sake tasirantar da abinda take ji a zuciyarta game da RK da Maanal idan har ALLAH ya tashi kafaɗunta. Bata ɓoyema Nene da su Shahidah ba akan alaƙar Dr Rafeeq ɗin da Maanal. Suma sai abin yay musu daɗi matuƙa, dan suna ganin idan har ALLAH ya baiwa Maanal lafiya wannan itace hanya mafi sauƙi da maganar Yazeed zata janye cikin sauƙi batare da sun ɓata ran Daddy ba kamar yanda duk suke gudu. Dan gwara dai a haƙura da batun Yazeed ɗin nan haka nan tunda dama ita wadda ake dan ita bawai tana sonsa bane. Abu na biyu sudai a haka yanayin Dr RK ya musu hundred percent, dan mutum ne mai sauƙin kai ga girmama na gaba da shi, ga yanda yake ɗawainiya dasu a asibitin nan cike da mutuntawa ma abin a soshi ne. Shi kansa Daddyn sun fahimci RK ɗin ya shiga ransa. Sai dai babbar matsalar sun san ga Yazeed za'a sameta kam. Dan kowa yasan Yazeed na matuƙar son Maanal wannan a bayyane yake. Sannan shi kansa mutumin kirki ne, dan yana da nagartattun halaye masu yawan gaske daya gada ga Daddy, tako ina Yazeed ya cancanci zama mijin Maanal kodan halaccinsa garesu, dan hatta Daddy ya sansu ne a dalilin Yazeed. Sannan kodan Daddy a bama Yazeed auren Maanal, mahaifiyarsa ce kawai matsalar gaskiya, dan Hajiya Yaya sam ba kanwar lasa bace. Bata da kirki ko misƙala zarratin, kanta kawai ta sani, kuma tabbas zata iya aikata komai akan wannan auren kamar yanda take shan faɗa idan har akayisa. ALLAH dai ya bama Maanal ɗin lafiya, zasu cigaba da tayata addu'ar zaɓin alkairi dan duk MAZAJE biyun nan sun matuƙar cancanta da aurenta...       ★ A mota Hajiya Majdiya ke bama RK labarin hirarrakinsu da Ammie, babu abinda yake sai murmushi da ƙara jin ƙaunar ƴar uwar tasa. Sai da ta gama bashi labari tsaf sannan ya jeho mata tambayar abinda ke cimasa zuciya..     “Humm Aunty Alhamdullah na samu karɓuwa wajen Ammie da ƴan uwan Maanal, sai dai ba duka ba”.     “Kamar ya ba duka ba miye matsalar to?”.         “Yazeed Aunty, Yazeed shine matsalar kuma na fahimci yana da ƙarfin faɗa aji akan ƴan uwan nasa. Da farko dai ni da shi normal gaskiya. Amma kwana biyun nan ban san miyyasa ba ko ya fahimci alaƙata da Maanal ɗin sai naga yana jajja baya dani, sannan yana min gadara da al'amarin Maanal ɗin. Dan ma baida yanda zaiyi ne kasancewata ɗaya daga cikin likitocinta shiyyasa. Har abin ya fara bani mamaki dan kamar wani mai kishi da ni. Sai dai nasan ba hakan bane tunda mizai sakashi yin kishi akan wadda suke Uba ɗaya ne ko uwa ɗaya ma ban sani ba”. Ya ƙare maganar cikin damuwa sosai.         Fuskar Hajiya Majdiya cike da damuwa itama ta furta, “To kodai Yazeed ma son Maanal yake?”.     “What?!!!”..   RK ya faɗa a ɗan razane yana taka birki da sauri.........✍️ 🤣Sai ka ɓarar daku malam Rafeequ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖1️⃣3️⃣ ______________ Abubuwan da nake saidawa Atamfofi Laces Shadda Materials Takalma Jakunkuna Mayafai Trolley Sarka da dan kunne Oil perfumes Numbers 08034469681 08135142610 Handles Instagram @ummu_mahnoor_luxuries TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries Facebook ummu_mahnoor_luxuries ______________ ........“Kamar ya sonta Aunty? Wace magana kike haka? Ba mahaifinsu ɗaya ba?”.       “Ba mahaifinsu ɗaya ba Rafeeq. Dan Alhaji Usman bashi ne ya haifi Maanal ba ita da yan uwanta biyu mata. Ƙannen Maanal maza biyu da kake gani Waleed da Hameed sune ƴaƴan dake tsakaninsa da Hajiya Asiya. Kaga ko zata iya kasancewa Yazeed son Maanal yake yi shiyyasa. Kuma kamar yanda ka faɗa ya fahimci kana sonta ne a yanzu shiyyasa ya canja maka. Amma ka bari zan bincika komai in sha ALLAHU”.        Wata irin zufa ce ta gauraye illahirin jikin RK. Idanunsa har sun kaɗa na damuwa. Yana ganin ya fara bin hanyar nasara ashe akwai sabuwar ƙura a tafiyar, dan tabbas indai har Yazeed son Maanal yake da wahala shi ya samu. Ammie dai bazataƙi ɗan mijinta ba, haka shima Alhaji Usman ɗin bazai ƙi ɗansa ba, ita kanta Maanal ɗin bashi da tabbacin bata son Yazeed ɗin ma a.....        “Kaga ka kwantar da hankalinka fa, in sha ALLAHU komai zai kasance cikin sauƙi. Ba nace zaka iya samun Maanal bane cikin sauƙi, ban kuma ce bazaka iya samunta ba tunda komai na ALLAH ne. Dan haɗin Yazeed da Maanal zai yi matuƙar wahala saboda nasan wacece mahaifiyar Yazeed. Hajiya Sadiyya da wahala ta amince da wannan haɗin musamman yanda nasan tayi bala'in tsanar Hajiya Asiya. Dan haka kada ka karaya da izinin ALLAH nasara tamu ce, kai dai kawai ka cigaba da neman soyayyar yarinyar shine babban makami a hannunka bayan goyon bayan Hajiya Asiya a yanzu”.      Nannauyar ajiyar zuciya ya sauke. Sai kuma ya zari handkhachief ya goge zufar goshinsa. “Hakane kam Aunty, ina jin tsorone kawai kar ya kasance itama Maanal ɗin tana sonshi, wannan kam kinga bazan iya jayayya da kowa ba tunda itace mai zaman auren.”          “Eh tabbas kam, amma nidai ban taɓa jin akwai wata alaƙar soyayya a tsakaninsu ɗin ba gaskiya. Tunda da akwai na faɗa maka mahaifiyar Yazeed sai a hankali ce, da sam bazata bari a zauna lafiya ba. Amma yanzu ma inda wata shawara, ka samu lokaci ka shigo Zaria wajen Abbansu Najma. Ka masa bayani a matsayin kana son ya maka iso wajen Alhaji Usman ɗin akan maganar mana, ni kuma kafin kazo zan sake bincikawar kamar yanda nayi maka alƙawari”.        Ajiyar zuciya mai haɗe da ƙayataccen murmushi RK ya saki, sai kuma ya kama hannun ƴar uwar tasa ta sumbata yana faɗin, “ALLAH ya saki a aljanna Aunty na mai share kuka na”.     Dariya tayi tana mai kai masa ɗan rankwashi a kai, hakan ne ya sakashi shima yin dariyar sannan ya tada motar suka cigaba da tafiya......        ✨✨✨✨✨✨✨    Alhamdullah wannan zuri'a suna cikin farin cikin farfaɗowar Maanal a yau, duk da ba'a barsu sun ganta ba har zuwa yanzu saboda likita dake tare da ita hakan bai hana bayyanar murmushi a fuskokinsu ba. Sai da su Dr Ranjet suka gama mata dukkan abinda ya dace kafin su ka buƙaci Nene dake goge mata jiki kullum ta shiga ta goge matan. Shahidah da Amal kuma sukai shirin komawa gida haɗo mata abincin da Doctor yace zata iya ci. Bayan kammalawar Nene Daddy da Ammie ne suka fara shiga. Tana kwance fayau da ita saboda ramar da tayi na ciwo. Gaba ɗaya na'urorin da aka sanya mata a kwanakin da suka gabata an janyesu, sai igiyar daketa jikin hancinta kawai. Jin ƙamshin turaren Daddy kusa da ita sosai ya sakata buɗe idanunta da suka ɗan kumburo, daga cikinsu sun ɗan yi ja sun kuma ƙara girma. Daga shi har Ammie dake tsaye ta zubama idanun, sai kuma a hankali ta saki murmushi mai sanyi tare da miƙa musu hannunta. Ammie dake murmushi tana hawaye ce ta kama hannun tana kaiwa zaune bakin gadon kusa da ita. Yayin da shi kuma Daddy ya ɗan duƙo ya shafa kanta yana murmushi shima, kafin yakai zaune a kujerar gaban gadon.         “Sannu kinji Daughter. ALLAH ya baki lafiya yasa kaffara ne”.     Kanta ta ɗan jinjina tana sakin murmushi, sai kuma ta motsa lips ɗinta a hankali ta furta, “Amin Daddy nagode”.     Murmushi ya sake mata, tausayin yarinyar da ƙaunarta na sake gauraye zuciyarsa. Maanal ta maida kallonta ga Ammie dake sharar hawaye. Nan ma a hankali ta ce, “Ammie ki daina kuka na samu lafiya fa”. Kai Ammie ta shiga jinjina mata tana share hawayen da sakin ƴar dariya. “Na daina Maanal kinji, ALLAH ya ƙara miki lafiya da nisan kwana. ALLAH yasa kaffara ne, ALLAH ya rabaki da wannan ciwo gaba ɗaya”.        “Amin Ammie nagode. Ina su Didi fa?”.      “Sunje gida yimiki abinci yanzu zakiga sun dawo. Ko kina son cin wani abune a kirasu su yi miki?”.     Ɗan shiru tayi alamar tunani, sai kuma ta kalla Daddy dake ta kallonsu yana murmushi, itama ɗan murmushin ta masa sannan ta sake maida dubanta ga Ammien. “Ammie sumin faten dankali, sai kunun gyaɗa”      “To shike nan bari na kirasu karsu taho”.    Kai Maanal ta jinjina mata, yayinda Ammie ke ƙoƙarin kiran su Amal. Dai-dai nan Yazeed ya shigo ɗakin da sallama Waleed riƙe da hannunsa, sai Hameed biye da su. Daddy ne ya amsa masa. Yayinda ita kuma ta zuba musu raunannun idanunta. Da sauri Hameed da Waleed sukayo inda take cike da farin cikin ganin idanunta a buɗe. Hannunta duk suka kama suka riƙe suna kaiwa durƙushe daga ƙasa ta yanda fuskokinsu zasu daidaita da tata.       “Alhamdullahi Didi ta samu lafiya”. Cewar Hameed yana sake ƙanƙame hannunta. Shima Waleed cike da ɗoki ya furta, “ALLAH mun gode maka yau muna cikin farin ciki Daddy Didi ta buɗe ido”.      Ƙaramar dariya Daddy yayi da faɗin, “Alhamdullahi” shima. Maanal cikin magana a hankali tace, “Ƴan turai kamarku daban”. Dariya duk suka ƙyalƙyale da shi. Itama saita maida kallonta ga Yazeed dake tsaye kawai yana kallonsu fuskarsa ƙawace da murmushin farin ciki. Kallon da take masa ya sashi ƙarasa ƙarasowa gaban gadon sosai. Sai kawai ta lumshe nata idanun a hankali ta kuma sake buɗewa duk a lokaci guda.           “Alhamdullahi. Sannu Maanal ALLAH ya ƙara lafiya yasa kaffarane kinji”.        Murmushi ta sakar masa a karo na farko, murya can ƙasa ta ce, “Amin Yaya nagode”.     Amsa mata yay cike da farin ciki, jiyake tamkar ya rungumeta a jikinsa sai dai babu damar hakan. Balle ma ga Ammie a wajen ga Daddy. Suna a hakan dai kuma sai ga RK. Tunda ya shigo idanunsa akan Maanal ɗin ne shima, itama dai shi ɗin take kallo da ɗunbin mamaki. Yayinda zuciyarta ke raya mata (shi wannan duk inda naje sai ya bini ne shin?) Rashin mai bata amsa yasata janye idanunta a zahiri daga kansa. Shima sai dai janye nasan yayi tare da ƙarasowa ya gaida Daddy da Ammie cike da girmamawa. Maanal ta sake shan mamakin ganin yanda duka amsa masa da kulawa da alamar sanayya sosai kuma. Dubansa ya maida a kanta yana mai ɗan kashe mata ido, hakanne ya sakata yimasa ƙaramar harara. Murmushi ya saki mai faɗi da ƙoƙarin ɗaukar file ɗinta dake a drower ɗin gefen gadon yana faɗin, “Gawa taƙi rami yaya jikin?”.      Dariya Daddy da su Waleed sukayi, yayinda Ammie tai ɗan murmushi kawai. Yazeed kam fuska ya sake tamkewa kamar bai san minene dariya ba. Yayinda Maanal ta ɗan tsuke fuska itama tana hararar RK ɗin yanzu ma. Yi yay kamar bai ganta ba ya miƙama Yazeed hannu cike da shaƙiyanci yana faɗin, “Babban Yaya barka ƙanwa ta miƙe. ALLAH ya ƙara lafiya yasa kaffara ne ya kiyaye gaba”.      Rasa abinyi Yazeed yayi, sai mamakin RK ɗin ke sake mamaye masa zuciya. Wani gefe kuma na tunanin RK fa bawai yasan ainahin alaƙarsa da Maanal bane, dan kuwa kallon yayanta uba ɗaya yake masa kenan. Daurewa yay ya ɗan sake fuska ganin Daddy na kallonsu ya bashi hannun shima suka gaisa yana amsawa da, “Amin doctor muna godiya, kuma kunyi ƙoƙari ai sai fatan alkairi a gareku”.        “Doctor!”.    Manaal ta faɗa a hankali cikin suɓutar baki idonta akan RK. Kafin ma RK yay wani yunƙurin bata amsa Waleed yabata amsar da “Eh mana Aunty shine likitanki tare da Dr Ranjet. Kuma yana da kirki kullum sai yaje damu yawo ya saya mana abubuwa, yana kuma cemana mu dinga miki addu'a a dallarmu ALLAH ya baki lafiya ko warke gaba ɗaya ki daina wannan ciwon ”.      Sake dai kallon RK ɗin Maanal tayi kawai, zuciyarta na wani irin motsawa a ƙirjinta da sauri-sauri kamar ma ciwon nason dawowa sabone komi. Ganin kallon da Ammie ke mata ta sata lumshe idanu kawai tai shiru dan ita kam bata kuma san abin faɗaba bayan hakan. Ɓoyayyen murmushi kawai RK yayi yana cigaba da dudduba abinda ya kamata, sai kuma ya fara mata tambayoyi a hankali. Dole ta buɗe idanunta a kansa dan yanda yake magana can ƙasa-ƙasa tsigar jikinta har tashi take. Kasa amsa masa ko ɗaya tayi da baki, sai jinjina masa kai kawai da girgizawa. Wani irin kishi ne ya turniƙe Yazeed, dan shi mutum ne mai kishi sosai. Rai a ɓace ya ɗan duƙo shima gareta murya can ƙasan maƙoshi ya furta, “Kina son cin wani abu Miss?”.      Idanunta ta ɗan maida garesa, “Yaya su Didi na zuwa da abinci ai”. Ta faɗa a hankali dan muryan baya fita sosai. Cikin jinjina mata kansa ya ce, “Na sani, ko ɗan fruit haka baƙya so? Ko wani abu bayan abincin?”.      “Zanci apple to, amma green”.    “An gama Baby”. Ya faɗa cikin raɗa ta yanda ita kaɗai taji sai RK dake kusa da su sosai. Saurin kauda kanta tayi, sai kuma ta kalla sashen da Ammie da Daddy suke. Ganin hankalinsu na kan su Waleed yasa ta sauke ajiyar zuciya. RK ta ɗan kalla, sai taga shima yay wani kicin-kicin da fuska yanata rubutu a file ɗin ta. Tana ƙoƙarin janyewa ya ɗago nasa idanun sai caraf a nata. Wani miskilin murmushi ya sakar mata tare da sake duƙowa kusa da ita gab, cikin raɗar shima ya furta, “Apple yana cikin abinda bazaki ci ba a yanzu wife to be, dan haka kada ki ma wahalar da Yayanmu”. Ya ƙare maganar da kashe mata ido ɗaya sai kuma ya kalla Yazeed ya sakar masa wani ɗan iskan murmushin rainin hankali.         (Nikam mike damun waɗan nan?) Maanal ta faɗa a zuciyarta dan tama rasa yanda zata masalta al'amarin nasu. Tana fama da kanta sunzo sun sakata tsakkiya da shirmensu ya ilahil alamin. Shigowar su Shahidah ne ya taimaketa. Cike da farin ciki sukazo suka rungumeta suna hawayen daɗin ganinta. Itama farin cikin take ji a ranta matuƙa. Nanfa suka shiga nan nan da ita. Sai kawai Daddy da Ammie suka fita tare da su Waleed. Dan ba'aso suyi yawa a ɗakin sam. A hakan ma dan RK najin nauyinsu shiyyasa baiyi magana ba. Ganin Yazeed bashi da niyyar fita a ɗakin RK ya dubesa cikin danne kishinsa ya furta, “Yauwa babban yaya inama son magana da kai. Dan akwai alluran da za'a mata zuwa 6pm naga kamar babu shi anan ya ƙare, ko zaka samo mana shi a pharmacy please?”. Yayi maganar ne idanunsa a kan takardun hannunsa yana kuma ɗan tafiya, dan haka baka isa gane ainahinsa ba kai tsaye. Bin bayansa Yazeed ɗin yayi batare da yace komai ba. Maanal ta bisu da kallo ƙasa-ƙasa.      Da taimakon yayun nata biyu ta ɗan ci abincin, nurse ɗin dake kula da magungunan ta ta shigo ta bata. Babu wani jimawa barci mai nauyi yay awon gaba da ita. Dama haka doctors ɗin suke buƙata ta dinga barci isashe dan zuciyarta da brain ɗinta su samu nutsuwa.........✍️ _🥱Team RK & Team Yazeed ina miƙo gaisuwar ban girma😌👌._     ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖1️⃣4️⃣ .......A ɓangaren Yazeed da RK kam suna fita Yazeed ya tsaya cak. Kallonsa RK ya juyo yanayi, sai kuma ya saki lalataccen murmushi yana dawowa da baya inda Yazeed ɗin yake. “A'a babban Yaya yaka tsaya kuma? Ya kamata muje ko”.      Murya a sarƙe Yazeed ya amsa masa da, “Rubuta sunan alluran ka bani anan. Sannan ka daina wani kirana Babban yaya dan ban san alaƙar data maidani yayanka ba”.       Hannu RK ya kai ya shafo bayan ƙeyarsa yana murmushi irin na ƴan duniya shi a dole irin yaji kunyar nan. “Haba bazan iya kiranka da sunanka ba gaskiya. Ko a bayan ma kafin na fahimci kai Yayan Maanal ne yasa nake kira. Yanzu kam dana sani sam bazan iya hakan ba”.       “Ni ba yayan Maanal bane kawai mijin da zata aura ne”. Yazeed ya faɗa a gadarance. Wani irin mugun dukan zuciyar RK furucin yayi, amma sai ya dake cike da basarwa ya furta, “Irin wannan wasan ai saika saka zuciyata ta buga babban yaya, kona ɗauka baka son aura min ita ne. Please mubar zancen haka ga sunan allurar”.     Yana miƙa masa ƴar takardar da yay rubutun yabar wajen da sauri dan baya buƙatar sake jin wani furuci daga Yazeed ɗin bayan wanda yaji. Shifa wlhy san Maanal yake. Kuma baya jin zai iya barma Yazeed ɗin koma mi za'ayi. Sai dai suyi yaƙi mai rabo ya ɗauka. Babu ruwansa da ƙarfin alaƙarsu kowa ya iya allonsa kawai ya warke. Da wani irin kallo Yazeed ya bisa kawai batare da ya sake cewa komai ba shima yabar wajen... _________★      Ganin jikin Maanal Alhamdullah Ammie ta matsama Yazeed komawa kan saboginsa. Shima Daddy ta damesa da roƙon ya koma Kaduna kada su shiga hakkin sauran matansa. Yazeed dai ya jitane kawai. Dan ya ƙudura a ransa bafa zai tafi ya bar Maanal a hannun wannan kuren likitan ba RK. Dan haka ƙafarsa ƙafarta idan ta samu lafiya. Shi kam Daddy sai da sukai ƴar rigima sannan ya yarda zai wuce Kaduna ɗin, amma kuma dole sai tare da ita, yace nan da kwana biyu ta dawo ta sake dubata tunda dai ga Nene gasu Shahidah. Ita dai Ammie tace hakan yafi mata duk da bata so hakan ba, dan tana son kasancewa da Maanal ɗin itama amma babu yanda ta iya haka ta haƙura suka tafi bisa shawarar Nene dan itama tafi son yaje ga sauran matansa kar abin ya zama wani daban kuma. Yazeed dai ya nuna mata akwai aikin da yake anan ɗin dan gobe ma zaiyi zama da masu Companyn Mawaad ne.. Wucewar Daddy da Ammie kamar ya buɗema Yazeed da RK wani filin TAKUN SAƘA ne, dan kuwa kowa ya riƙe wuta yana baje kolin hajarsa. Yayinda ita kuma take nuna bama ta fahimci inda suka dosa ba su duka. Tun suna abin a kaikaice har ya fara bayyana kansa sosai, dan takai da Yazeed ya shigo duba Maanal tsalam zakaga RK a ɗakin ya shigo kamar wanda aka jeho. A wajen su Amal taji duk yanda akai aka kawota Abuja. Nan ta fahimci RK yaje gidansu ne sai ya kasance a dai-dai lokacin da take a halin taimako. Hakan ya kwaranye mata mamakin ganin nasa anan. Sai dai kasancewarsa likita bai bar bata mamaki ba. Dan har sukai zamansu a Jos suka gama bai taɓa nuna musu ga aikinsa ba. Kai ita tama sha yin gulmarsa da jifansa da kalmar mara aikinyi, sannan a tunaninta shi ɗin ɗan Jos ɗin ne ma ai.       Yau Nene ta ɗan tashi da ciwon kai, dan haka ta wuce gida dan ta ɗan huta. Dama itace ke kwana da ita anan, da safe zuwa goma sai ta wuce gida idan su Amaal sun zo, sukuma suke yini da ita anan har sai dare idan Nenen ta dawo sukuma sai su wuce. Daga Nene har Amal suna a gidan Shahidah ne yanzu, dan bayan wucewar su Ammie sai itama Nene ta koma can gudun karta zauna ita kaɗai anan ɗin duk da ma ƙarfin zaman nata a asibitin ne dai. Bayan wucewarta Maanal ta tashi a barci, da taimakon Nurse tai wanka, kafin ta fito an gyara ɗakin, tana ƙoƙarin zama a bakin gado take tambayar Nurse ɗin, “Nene fa?”.        Amsa ta bata da, “Doctor Rafeeq ya kaita gida ta huta kanta na ciwo”.     Shiru kawai Maanal tayi, mamakin RK na sake kasheta, gaba ɗaya fa yabi ya kanainaye mata ƴan uwa kowa ya sanshi. Yanzu haka kullum Waleed da Hameed na manne da shi har sai da suka wuce aka samu lafiya. Haka idan su Didi sunzo zaizo ya zauna wai yazo gaishesu duk hararar da take masa baya ma nuna ya gani. Itako yaya zatai da wannan bawan ALLAH. Babu ma abinda ke damunta sai zaman marina da suke tsakaninsa da Yaya Yazeed, hatta gaisuwa sama-sama sukeyinta yanzu ma ta rasa mike damun kawunansu haka.... Shigowarsa ɗakin shi da Doctor Ranjet ya katse mata tunaninta, da sauri taja hulanta ta saka tana ɓata fuska. Ɗauke kai RK yay kamar bai ganta ba yama hau duba magungunanta. Shi dai Dr Ranjet matsowa yay kusa da ita yana tsokanarta, haka yake mata dan shi mutum ne mai wasa sosai. Dole ta daure ta ɗan masa murmushi dan turancinsa na sata nishaɗi, kullum gaya mata yake ita ɗin mai sa'a ce. Ruhunta nada tauri sosai, saboda da wahala kaga mai irin matsalarta ya shiga irin yanayin data shiga kuma ya tashi ya cigaba da rayuwa, dan shi kansa a randa aka kawota asibitin baimayi tunanin zata kai washe gari a raye ba. Dai-dai Dr Ranjet na ƙoƙarin mata wata allura da kullum a irin wannan lokacin ake mata RK ya ƙaraso wajen. Kujera yaja ya zauna yana mai zuba mata ido dan sai ɓata fuska take tana kallon allurar. Amma tana juyowa suka haɗa ido da shi sai ta ɗaure fuska ta fiske abinta. Kansa ya kauda kawai yana murmushi baice komai ba. Allurar akai mata, ana gamawa ta kwanta saboda jiri take sakata. Idonta a rufe har fin mintuna biyar Doctor yay mata sauran abinda ya rage har ya fice da kusan mintuna biyar sannan ta iya buɗe idanunta da suka kaɗa sosai. A kansa ta saukesu, sai kuma ta janye da sauri ganin shima ita yake kallo.        “Nifa bana son haka, azo a tasa mutum gaba ai haramunne ma wannan”.      Murmushi ya saki mai faɗi yana mai janye idanun nasa daga gareta. Sai kuma ya furzar da huci kaɗan a hankali ya furta, “To amin afuwa sarauniya. Sonki ne kawai ke neman zubar dani amma ke kina ɗaukar komai wasa”.        Shiru ta masa bata tanka ba. Shima sai ya bar zancen ya kama wani daban. “Ni kam banga Zizaah da Aneesa ba, ko basu san baki da lafiya bane?”.     Kansa ta jinjina masa alamar eh.   “A gaskiya ya kamata su sani. In sha ALLAHU anjima zan kirasu na sanar musu kuwa”.        “Ni dai ban saka ba”.    Idanu ya ɗan waro waje. “Saboda mi?”.      “Ba saboda komai ba, kawai dan mutum na ciwo sai anta talla da shi. Yanzu miyyasa ka kai Nene gida ma?”.      “Saboda taje ta huta. Ba su Didi na zuwa ba”.    Hararsa ta ɗan yi, kafin tace, “To idan kuma ina buƙatar wani abu fa kafin su suzo?”.       “Ba gani ba sai ki sakani nai miki. Ai shiyyasa nazo nan na zauna a madadin Nenen. Faɗi mi kike buƙata gimbiyar Rafeeq?”.      Baki ta buɗe zatai magana tsulum sai ga sallamar Yazeed. Kafin ma su gama amsashi ya riga ya shigo. Kallon kallo sukaima juna shi da RK ɗin sai kuma kowa ya janye cike da basarwa. Takowa yazeed ɗin ya ƙarasa yi ta ɗayan side ɗin. Saboda neman magana sai ya zauna a bakin gadon kusa da ƙafafun Maanal. A hankali ta matsar da ƙafafun nata dake cikin bargo, dan RK ya wani zubama ƙafafun nata ido kamar mai kallon television duk da a lulluɓe suke a bargon. Cikin dauriya ta gaida Yazeed. Ya amsa mata idanunsa kafe a kanta....        “Yaya jikin naki?”.    “Na samu sauƙi Yaya. Ya aiki?”. “Alhamdullahi. Tunda kin samu sauƙi sai sallama kenan ko?”.       Maimakon amsa saita sakar masa ɗan murmushin yaƙe kawai. Abinda ke hannunsa ya miƙa mata. “Ga abinda kikace kina so, shine maimakon ki sanar min kika kama faɗama su Shahidah ko? Bana gaya miki duk abinda kike buƙata yanzu ki sanar min ba. Domin nine da hakkin yimiki shi ai, kwana nawa ya rage mana zama ma'aurata”.         Kanta kawai ta jinjina masa da faɗin, “Nagode”. Yayinda RK ya saki wani ɗan iskan murmushi yana sake yin balance a kujerar. Sai kuma ya wani laɓe baki yana kauda kansa. Duk Yazeed na lure da shi, dama kuma yayi furucin domin shi ne.    “Ina Nene?”. “Taje gida bata jin daɗi”. “Ayya ALLAH ya bata lafiya. Ai tana ƙoƙari ma ga jikin girma. Su su Shahidah fa?”.      “Basu ƙaraso ba, suna hanya dai sukace”.    “Okay yayi”. Ya faɗa yana zaro wayarsa da ake kira. Ɗagawa yay tare da kaiwa kunne, sai kuma ya miƙe saboda masifar da Mamma ke masa daga can, dan har ita Maanal ɗin taji furucinta na farko ma. Sassanyar ajiyar zuciya Maanal ta sauke ƙasa-ƙasa dai-dai Yazeed ɗin na fita. Hakan yasa RK tuntsurewa da wata dariyar wulaƙanci. Kallonta ta maida garesa cikin mamaki. Shiko ya wani ɗage mata gira cike da neman rigima ya ce, “Amma dai kina matuƙar tsoron wannan yayan naki fa. Irin wannan sauke ajiyar zuciya haka”.      Ƙin kulashi Maanal tayi, sai dai maimaita kalmar tsoron daya ambata tanama Yazeed ɗin take a zuciyarta. Shima bai sake cewa komai ba ya kawo hannu zai ɗauki abinda Yazeed ɗin ya bata tai saurin ɗaukewa tana ɓata fuska.      “Wai kai idan baka shiga rayuwar mutum ba da abinda ba'a sakaka ba baka jin daɗi ne halan?”.      “Oh haka kike fassarani ashe?”.    “Hummm”. Kawai tai shiru. A ransa yace miskilatu kenan. Magana fal cikinta amma bata son yi. A fili kam zaiyi magana sai ga Yazeed ya dawo. Bai fasa ba ya cigaba da faɗin, “Birthday na ya kusa mi zaki bani as gift?”.         “Humm”.   Maanal ɗin ta faɗa idonta akan Yazeed daya iso gaban RK ɗin rai a ɓace. Shi kuma yayi kamar bai gansa ba. Cikin fusata ya ce, “Malam ina son magana da kai”.    Sai lokacin RK ya dubesa. Sai kuma ya nuna kansa cike da rainin wayo wai shi? A kausashe Yazeed ya ce, “Eh”.        “Okay to Bismillah ai gani. You are free zaka iya maganarka kawai”.     “Ba'a nan ba”.    Yanda yay maganar a fusace ya saka Maanal dake saurarensu kallon Yazeed ɗin a karo na farko. Sai kuma ta kalla RK dake wani shegen murmushi baida alamar motsawa balle aje ga batun tashin. A hasale Yazeed ya sake buɗe baki zaiyi magana Shahidah da Amaal sai mijin Shahidah ɗin sukai sallama. Dole ya haɗiye maganar yana mai furzar da huci, sai kuma ya juya suka fara gaisawa da mijin Shahidah. Shima RK miƙewa yay yana amsa gaisuwar su Amal, kafin ya juya ga mijin Shahidah ɗin shima suka fara gaisawa. Daga haka ya fice a ɗakin. Hankalin Manaal naga su Amal Yazeed shima ya sulale ya fita, sai da ta ɗago da nufin yin magana dashi kawai taga wayam. Waige-waige ta fara cikin mamaki, cikin tsokana Mijin Shahidah ya ce, “Oh in dai samarinki ne ai sun fice auta”.      Fuska ta ƙwaɓe kamar zatai kuka ta ce, “Kai Uncle Sadeeq”.    Dariya suka sanya mata su duka....         ★★★ Sam RK bai san Yazeed na bin bayansa ba. Dan hankalinsa ma nakan wayarsa fuskarsa da murmushi saboda saƙon da yake karantawa. Jin ansha gabansa ya tsaya cak tare da ɗagowa. Kallon ido cikin ido sukaima juna shi da Yazeed ɗin kaikace zakuna ne jirace da juna a filin daga.      “Doctor ina son maka gargaɗin farko da ƙarshe akan yarinyar nan”.        “Saboda mi?”. RK ya faɗa yana tsatstsare Yazeed da ido. Shima Yazeed ɗin cikin dakiya ya bashi amsa da, “Saboda ita ɗin matar dazan aura ce. Akwai ranar aurena akanta. Kasan kuma nema akan nema haramun ne sai dai idan kana da ƙarancin ilimin addini ne kuma na maka ƙarin bayani yanda zaka fahimta”.      Maganar Yazeed ta ƙarshe-ƙarshe ta zafi RK, amma sai ya danne yama saki murmushi da ƙoƙarin raɓashi alamar zai wuce abinsa. Cikin zafin nama Yazeed ɗin ya sake shan gabansa. Kallonsa RK ya sake yi yana ƙoƙarin danne ɓacin ransa, dan shima fa ya iya zuciyar nan, dalili ne kawai ke sakashi danne tasa ba tsoro ba.        “Yazeed why???”.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖1️⃣5️⃣ ........“Why kake son mu dinga kasancewa a wannan yanayin ni da kai?. Ina fa ganin girmanka ne matuƙa shiyyasa kaga ina barin komai a yanda yake. Please respect your self mana. Kai namiji ne, nima namiji ne kowa ya cigaba da gwada sa'arsa mai rabo sai ya ɗauka a cikinmu. Dan har yanzu banga dalilin da zaisa na iya janyewa ɗin ba”.      “Haka kace?”.   Murmushi RK ya sakar masa da kashe ido ɗaya kawai ya zagayesa ya bar wajen. Hakan ya sake hasala Yazeed matuƙa. Tabbas shi ɗin mutum ne mai haƙuri da dattako. Amma yana da tsananin kishi akan abinda yake so shiyyasa yake zafafawa akan al'amarin Maanal matuƙa. A zuciyarsa yake tunanin dolene ya koyama guy ɗin nan hankali, dan haka a daren yau zai wuce Kaduna dan gara ya zauna ayita ta ƙare shi da Daddy. Mamma dai ce matsalar zai rumtse ido kawai komai ma ya faru daga baya yasan zata sakko ta yafe masa.....      Kiran daya shigo masa a wayane ya katse tunaninsa. Ganin ƙanwarsa Badiyya ce kamar zai share sai kuma dai ya ɗaga. Yana kai wayar kunnensa ya janye da sauri saboda abinda ta sanar masa.. Yana sauke wayar daga kunnensa sai kuma ga text massage ɗin Ammie itama ya shigo masa. Ai bai tsaya sauraren komai ba yabar asibitin......     _____________        “Wai Daddyn Yazeed mikake nufi da ni ne a gidan nan? Katafi kai da matanka holewarku bance komai ba, ka dawo ranar girkina kace baka buƙatar komai daga gareni. Na zuba maka ido nan ma, washe gari Basariyya tai girki ita jiyama haka. Yau kuma ƴar sonka ta amsa”.     Idan kujerun dake falon sun motsa Alhaji Usman ya motsa kenan. Tamkar ma bai san da zaman Hajiya Yaya a falon ba yake kallon labaransa yana shan fruits da Ammie ta haɗo masa. Hakan ne ya sake sakata fusata, cikin matuƙar ɓacin rai ta ja remote ɗin dake a Centre table ta kashe tvn gaba ɗaya. Karo na farko ya juyo ya kalleta fuskarsa a matuƙar haɗe. Itama kallon nasa take tana huci.        “Sadiyya bar falon nan kafin ranki yafi haka ɓaci”. Har cikin ranta taji tsoron fitar kakkausar muryarsa. Amma sai ta dake dan gara dai ayita ta ƙare. Itama a fusacen ta ce, “Babu inda zanje wlhy. Dan nifa na gaji da abinda ake min a gidan nan. Ubana ya dasa inuwa wasu banzaye suzo su zagayeta domin sha suna min gadara.”        “Hummm”.    Ya faɗa kawai yana miƙewa. Bedroom ɗinsa ya shige tare da rufo ƙofar ya barta a falo tana jidali ita kaɗai. Haka dama yake mata, ita kuma sai take ɗauka kamar tsoronta yake ji ko tafi ƙarfinsa ne. Bata san yana hakan bane kawai saboda wani dalilinsa daban, amma badan gorin da take masa ba akoda yaushe. Tsautsayi rabon faɗan nan ya koma kan Ammie sai gata ta shigo sashen batare da tasan Hajiya Yaya na nan ba. Aiko ina wuta Hajiya Yaya ta saka Ammie, nanfa ta shiga mata gori da cin mutunci. Ita dai Ammie komai batace da ita ba ta ajiye basket ɗin hannunta dake ɗauke da kayan abincin maigidan a saman d/table. Rashin tankawar da batai ba itama sai ya sake fusata Hajiya Yaya, a matuƙar zafafe ta nufi d/table ɗin da niyyar kifar da kayan abincin Ammie ta tare tana girgiza mata kai.        “Kiyi haƙuri Hajiya kar kiyi haka dan ALLAH. Koba komai shi ɗin abincine, yana da darajar da wulaƙantashi kuskurene takowace irin fuska”.     “To mama Asiya shawara kike bani ko umarni?”     “Babu ko ɗaya da nake baki a ciki kiyi haƙuri”.          “Anƙi ayi haƙurin munafuka kawai, kullum sum-sum ita a dole ta ALLAH amma dafinki yafi na baƙin kumurcin maciji. Kin mallake min miji da bin bokaye, kin cika mana gida da agololi har kina shirin ganin kin mannawa ɗana. Wlhy Asiya sai naga bayanki a gidan nan”.        “Idan ta juya ba.....”     Alhaji Usman daya fito ya faɗa a zafafe. Juyowa sukai su duka suna kallonsa. Fuskarsa a ɗaure ya cigaba da faɗin, “Idan ta juya kam zakiga bayanta Sadiyya. Amma kiga bayanta akan zama dani har gaban abada bazakiga hakan ba da iznin UBANGIJI. Asiya ajiye abinci, idan kin isa dan ALLAH ki zubar da shi ni kuma wlhy yau sai na baki mamaki irin wanda baki taɓa zato ko tsammani ba. Ke Sadiyya bafa wai ina tsoronki bane a gidan nan. Karki ƙureni a wannan karon wlhy idan ba hakaba zakiyi matuƙar dana sani.”      “Dana sani na nawa kuma ai nayi dana sani tun daga randa na amince na aureka....” sai kuma ta fashe da kuka “Kai dai burinka kullum ka wulaƙantani a ƙasan ƙanwar bayana koma nace sa'ar ɗana ko, shike nan ga gidan nan na bar maka, ka kwaɗata ka cinye dan ALLAH” fuuuu ta fice daga falon. Tsaki yaja kawai tare da juyawa zai koma bedroom ɗinsa. Hankalin Ammie ne ya tashi, cikin sauri tabi bayansa, kusan a tare suka shigo bedroom. Jin yanda ta faɗo masa ya sashi juyowa yana kallonta.        “Dan ALLAH ka bita karta tafi ɗin da gaske, na roƙeka Abban Hameed. Bana fatan kowacce matsala ta kasance tsakaninka da matanka a dalilin.....”       “Asia!”.   Ya faɗa cikin katseta. Kanta ta shiga girgiza masa sai ga hawaye. Zata sake magana kawai ya jawota jikinsa ya rungumeta. Sosai take bashi tausayi, mace ce mai haƙuri da juriya akan komai na rayuwa. Tana da kawaici da saurin sallamawa koda abu zai cutar da itane ko zuri'arta. Duk abinda kaga ta masa musu a kai to ka duba wannan abun kuwa. Komai yace ita mai biyayya ce a gareshi ko bai dace da ita ba. Wannan halayen nata ne suka mamayesa cikin ƙanƙanin lokaci yake jinta ƙololuwa a saman matan da ya aura tun yana da jajayen sawunsa. Hanata duk wata damar sake magana yayi, ba kuma ta sake yi ɗin ba ta haƙura saboda ita ɗin mai biyayyace a garesa. Fitowarsu falo babu jimawa tana zuba masa abinci sai ga Asalamiyya ta shigo tana kuka ita da Basirah.      “Daddy dan ALLAH ka kazo ka hana Mamma tafiya. Gata can ta haɗa kaya zuwa mota zata tafi Daddy”.     A birkice Ammie ke kallonsu, sai kuma ta yunƙura jikinta na rawa zata nufesu. Cikin bada umarni Daddy da tun kallo ɗaya da yay ma su Asalamiyyar bai sake ba ya dakatar da ita. “Asia koma ki zauna”.     Kallonsa Ammie tai kamar zata fashe da kuka. “Daddyn Hameed kana fa jin abinda suke faɗa”.      “Cigaba da zuba min abinci nace. Ku kuma ku bar falon nan!!!”. Ya ƙare maganar a tsawace. Zabura sukai saboda tsawar ta shigesu. Har rige-rigen fita suke daga fallon. Kallonsa Ammie ta sake yi zatai magana ya ɗaga mata hannu. Dole tai shiru ta cigaba da zuba masa abincin hannunta sai rawa yake. Tsaf yake kallon yanda hannun nata ke rawa amma sai bai tanka ba. Tana gama zuba masa abincin yaja ya fara ci hankalinsa kwance.. Abu ya ishi Ammie ta rasa ina zata kama, sai kallon Daddy kawai take. Can dai ta jawo wayarta ta shiga rubutama Yazeed text massage..... ______________★       Yau da wuri Nene ta dawo asibitin. Dan haka ta kora su Amaal gida suma saboda mijinta daya shigo Abuja. Daga nan ma asibiti da yazo ya duba Maanal ɗaukar Amal ɗin yay suka wuce masaukinsa. Itama Shahidah da mijinta yazo sai suka wuce kawai. Hakan yasa Maanal ta kasance daga ita dai Nene a ɗakin. Sai kuma duk kaɗaici ya isheta. Dan Nene da zaran tayi sallar isha'i zakaga ta fara gyangyaɗi abinta. Gashi babu waya a hannun Maanal ɗin, tana Kaduna aka barta, bakuma a kawo mataba har yanzu. Shiyyasa ma taima Shahidah maganar a sayo mata kayan zane-zanen ta dan ta iya sosai, shine Yazeed yaji ya hana Shahidah siyowa shi ya sayo mata. Tun ɗazun daya kawo mata su ta ajiye bata sake bi takansu ba. Sai yanzu ta jawo ledan  ta fiffito da su. Komai da take buƙata akwai, harma da wanda batace a sayo ba ya sayo. Dan haka sai ta gyara zama kawai ta fara zanenta dan shine hubby nata tun tana yarinya. Maanal ta masifar iya zane ta yanda idan ta zana abu sai ma ka ɗauka ba itace ta zana ɗin ba. Da farko ɗakin jiyyar tata ta fara zanawa harda Nene dake zaune a kujera tana famar gyangyaɗi, sai ita kanta a yanayin da take zaune. Koda ta gama taga komai ya mata sai ta tsinta kanta kuma da fara zana agogo. Abinda ta jima batayiba a rayuwar zanenta kenan. Ta zana guda biyu tana akan na uku RK da Doctor Ranjet suka shigo ɗakin. Firgigit Nene ta farka, yayinda Maanal tai ƙoƙarin rufe zanen nata amma sai caraf RK ya rikesa.       “Woow!, this is amazing”. Ya faɗa yana kallon zanen cike da matukar mamaki. Sai kuma ya kalleta. “Dan ALLAH da gaske kece kikayi Baby?”.      Kafin ma Maanal ta bada amsa Nene ta cafe cikin taɓe baki. “Yo in dai Manaalu ce ai baka rabata da zanen aljanai Rafeequ. Tun tana yarinya uwar tayi tayi amma ina harma an barta taitayi itace zata ƙare da mafarkinsu ai ba wani ba”.       “Nene ai abune mai ƙyau wannan ɗin.....”     “Ɗan nan a al'adar yahudu da nasara ba. Amma mudai a musulunce banjin cewar abune mai ƙyau duk da ni ɗin ba malama bace”.        Dariya RK yayi, sai kuma ya miƙama Nenen zanen yana faɗin, “Amma Nene kinyi fa ƙyau a wajen nan kamar wata sarauniya a kujera”.    Ba ƙaramin zare ido Nene tayi ba tana kallon kanta an zane ras harda yanayin atamfarta. Duka ta kaima Maanal itako ta kauce tana ƙara ɓata fuska. Aiko ta shiga zazzaga jaraba shi dai RK da Dr Ranjet na dariya abinsu. Manaal dai ta miskile fuska kamar ba ita tai tsiyar ba. Sai da Nene tayi mai isarta sannan ta fice dan idan anzo duba Maanal ɗin fita takeyi. Bayan fitar Nene Dr Ranjet na duba Maanal RK daya kasa ajiye zanen ya dubi Maanal cikin serious ya ce, “Amma basirar nan naki bai kamata ya tafi a banza ba kawai, yana da ƙyau mutane su amfana da shi”.       “Kamar ya?”. Ta faɗa a ƙasan maƙoshi. Bai damu ba, dan zuwa yanzu ya sake fahimtar miskilancinta mai lasisi ne.    “Akwai Companyn da nasan suna matuƙar buƙatar aiki da mai irin wannan basirar taki”.      A daƙile ta furta, “Ba buƙata”.   Cikin ɗan girgiza kansa ya ce, “Wlhy seriously Baby akwai companyn da zakiyi wannan aikin fa kuma anan Abuja ne, Please kada kice a'a dan ko kina gida zaki iya musu aiki ma”.      Rasama abinda zata cemasa tayi, dan yanda ya wani marairaice fuska ya tsareta da manyan idanunsa sai ta ji ta kasa furta komai. Dr Ranjet ne ya saka baki a zancen nasu, “He is telling you the truth my patient.. Ko game da ciwonki idan kin samu abinda zai dinga maidaki busy zaisa ki rage saka damuwar abubuwa a ranki da har zai dinga yawan tashi akai-akai”.      Shiru kamar bazatace komai ba. Sai zuwa can ta sauke ajiyar zuciya tana ɗan girgiza kanta. “Su Ammie bazasu amince ba ne. Kadai ji abinda Nene ta faɗa ai”.       “In dai har kin amince zakiyin ki barni dasu kawai”.     “Mi zakace musu?”. “Ke dai kawai ki amince zaki ji ai”. “Zanyi tunani”. Ta faɗa a taƙaice tana zamewa ta kwanta. Bai sake magana ba shima sai ɗaukar hoton zanen da yay a cikin wayarsa kawai. Bayan fitarsu kafin barci yay awon gaba da Maanal tai zurfi matuƙa a tunanin zancen RK ɗin da Dr Ranjet.....   __________★          Lokacin da Yazeed ya iso gidan sha ɗaya saura na dare. Dan haka ya samu Daddy ya ma kwanta. Sai ya zarce sashen Ammie, samunsa yay shima a rufe, hakan na nufin tana sashen Daddy kenan dan su Waleed ba nan suke kwana ba suma. Dole sashen Hajiya Yaya ya nufa inda ya tadda ƙannensa zaune a falo jugum-jugum. Hatta da television bata aiki a kashe take yau. Da gudu Amrah tazo ta shige jikinsa tana sakin kuka mai ban tausayi. Rungumetan yay shima yana ɗan shafa bayanta. Kusan mintuna biyu sannan ya ɗagota tare da kama hannunta suka ƙarasa cikin falon. Nuni yay ma sauran da su zauna dan suma duk sun miƙe tsaye. Shima ya kai zaunen Amrah a gefensa.      “Mike faruwa ne?”.    Kafinma ya rufe baki su duka sun saki kuka. Wadda ke bimasa da suke kira Suhana ce ta fara masa bayani muryarta na rawa. “Yaya muma bamu san ainahin abinda ya farun ba. Kawai dai Mamma taje sashen Daddy, babu jimawa sai gata ta dawo kuma tana hawaye. Mun tambayeta bata kulamuba ta hau haɗa kayanta. Bamu sani ba ko sakinta Daddy yayi”.       “Saki?”.........✍️              ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖1️⃣6️⃣ ..........“Haka muke tunani Yaya. Tunda bamu taɓa ganin Mamma ta haɗa kaya tabar gidan nan ba dan sun samu matsala da Daddy.”     Basira ta bashi amsa cikin kuka. A take zufa ta gama wanke masa jiki, harma ya gagara cewa komai. Badiyya ce ta sake katse masa tunani da faɗin, “Yaya kuma wlhy koma minene ya faru da sanya hannun waccan munafukar matar a ciki. Dan tana a sashen Daddyn komai ya faru, ko sanda Mamma zata tafi da muka je kiran sa itace ta hanashi”.       Cikin mamaki ya ce, “Ita wa?”.   Kai tsaye ta bashi amsa da, “Amaryarsa mana”. Hararar daya zuba mata ya sata kame bakinta tana turashi gaba. Dama sun san ai bazai yarda ba tunda agolan ƴarta ce budurwarsa. Bai sake cewa komai ba ya miƙe, sai da ya kusa kaiwa ƙofa ya juyo yana kallonsu. “Kutashi kuje ku kwanta zuwa da safe koma miza'ai sai ayi. Ku kulle nan ɗin”.        Wasu sun amsa masa da to, wasu ko da hararar ƙasan idanu suka rakashi dan sun san babu damar yi a zahiri mutum yaci dukan banza a daren nan balle ma babu Mamma.....      ★★★ Washe gari koda Yazeed yazo ganawa da Daddy sai ya samu har ya fita. Sashen Ammie ya nufa, inda ya taddata zaune jihum alamar tana tare da damuwa harma da ɓacin rai. Gaisheta yay da girmamawa kamar yanda ya saba. Itama ta amsa masa cikin kulawa tana danne damuwarta.      “Yanzu ka iso ne?”.    “A'a tun da daddare. Around eleven na samu kunyi barci shiyyasa na haƙura har sai da safe. Yanzu kuma naje sashen nashi naga alamar a rufe yake”.       “Nima nazo na haɗa masa breakfast na koma naga yabar gidan. Ka ganni tun ɗazun nake kiransa yana rejecting daga ƙarshe ma ya kashe wayarsa gaba ɗaya.”      “Innalillahi wa'inna ilaihiraji'un”. Yazeed ya shiga ambata yana mai dafe kansa da dukka hannayensa biyu.       “Yazeed nikam da zakaji daka haƙura da batun auren nan na Maanal. Dan idan zamu duba gaskiya duk batunsane tushen wannan matsalar. Kayima Hajiya biyayya ALLAH sai ya baka wadda tafi Maanal”.       “Amma Ammie ina sonta, wlhy matuƙar so nakema Maanal dan ALLAH kar kice haka, ke da Daddy ne ƙwarin gwiwata. Sannan shima Daddy ai yanada hakki a kaina kuma yana son auren. Miyasa Mamma bazata fahimta ba. Miyyasa bazata fahimci Aunty Sabuwa tana zugatane kawai saboda ta samu biyan tata buƙatar na auri tata ƴar bane?”.          “Amma Yazeed ƴar uwartace fa, uwa ɗaya uba ɗaya. Taya bazata tayata son abinda take so ba.”     “Amma wlhy Ammie akwai manufa a zuciyar Aunty Sabuwa. Mamma ɗin ce kawai ta kasa fahimta”.    Rasa abincewa Ammie tayi, dan itakam wannan cakwakiya ta ma fara gundurarta wlhy. Tabbas tana matuƙar son Maanal ta auri Yazeed kodan ƙyawawan halayyar yaron. Sai dai tana tsoron halin Hajiya Yaya gaskiya. Sannan tana tausayi da fargabar jefa rayuwar yarinyarta mai raunin ciwo a cikin wani hali. Yazeed shi kaɗai ke son auren nan sai mahaifinsa. Amma ƴan uwansa da mahaifiyarsa da mafi yawan danginta basa so sam.....      ________________★    “ALLAH nazata wasa kikeyi da kikace min gaki nan tahowa Zaria fa.”      “hhhh aina fahimci hakan a muryarki. Bazaki ganeba fitowar ta dole ce. Gidanmu ne keci da wuta na gasken gaske kwana biyun nan”.      “Tofa wuta kuma Aminiya tami?”.   “Uhhm ke dai bari, tushen matsalar daga auren agolar gidanmu ne da maigidan yace zai ƙulla kusan shekara uku kenan.....”     “Kar kice na katseki wai ƴar amaryar ku? To da wa?”.    “Ita fa, dawa kike tunani idan ba ɗan sonsa Yazeed ba. Tunda fa akai maganar dama uwar tasa tace bata yarda ba. Shi kuma Daddyn Huznah bai maida kai ba yarinyar dai tana cigaba da karatu, shi kuma Yazeed yana manne da yarinya. Bayan ta kammala karatun akaso tada zancen bansan miya faru ba dai kuma aka dakata ta wuce service. Indai taƙaice miki batu ta gama service ɗin ne yanzu zancen ya sake tasowa shine aketa dam-barwa. Ita uwar ɗan tace bafa za'ai ba, kwana takwas da suka shige sukazo itada ƴar barikin ƙanwar nan tata sabuwa suka cima uwar ƴar mutunci randa muka bar nan kenan shine itakuma yarinyar ta yanke jiki ta faɗi ta kama aman jini”.        “Aman jini kuma?”.    “Uhm kin san sunce wai ai tana da ciwon zuciya”.    “Tirƙashi, eh lallai dole kice gidanku naci da wuta. Ke nan yanzu yaya ake ciki kuma?”.     “Yarinyar na asibiti a Abuja yanzu haka. Ba shine nake faɗa miki nakoma Abuja ba nima harma naga ƙanin Majdiya”.    “Oh ƙwarai anyi haka. Ko shiyyasa itama taje Abujan ita da yara duka dan gulma shine suka wuce gidan Yaseerah wai ganin ɗaki. Aiko sai da na mata tujara daga ita har mijin nata data dawo”.     Dariya sosai suka kwashe da ita suna tafawa. Hajiya Basariyya ta ce, “Ai kinmin dai-dai wlhy. Kinga gobe ai ta kiyaye”.      “Karma ta kiyaye na koya mata hankali. Mu munafuncin kishiya wanne bamu sani ba kuma”.    “Wlhy kuwa. Sai dai wanda kuma aka ɓoye a zuciya. Yanzu kin san miya sani zuwa Zaria ɗin?”.      “A'a sai kin faɗa”.    “Jiya uwar gadaran gidan namu ce ta wuce gida harda kaya cike da akwatina. Dan ya hanata girki a gidan sai mu biyu mukeyi, shine jiya girkin ita shegiyar ne ita kuma taje ta samesu tai musu ɗibar karan mahaukaciya. To ban sani ba ko sakinta yayi shine ta kwashi kaya ta tafi, dan naga ɗan ma ya dawo jiya da dare su kuma matan sunata kuka. Yau kuma tunda safe mai gidan ya fice rai a ɓace matar son nasa itama dai duk ta koma sukuku. Dan haka malam nakeso ki kira mana nan ina son a ƙarama wutar fetur ne ya sake birkice musu. Sai kuma batun Huznah da yaron nan da suka haɗu a Abuja. Na fahimci kamar itace ta damu da shi, dan sai ta yini kiransa a waya bai ma amsa mata ba sai ya gadama. Ina son a riƙe masa wuta gaskiya san bana son nima ta rasashi. Nayi binciken yaron shi kansa bama ubansa ba wani shege ne. Dan Companys ne da shi na abubuwa. Ga shima uban nasa sune ƙasar. Hakama ƴan uwansa biyu kowa ƙwaron kansa ne duk da dai shi ƙanin ya fisu komai.”        “Humm wato ƙawata kina matuƙar birgeni, sam ke baki da wasa akan abu. Sha yanzu magani yanzu kikema komai shiyyasa da wahala asha gabanki”.      “Yo ai babu zama ƙawata. Lamarin rayuwar nan kana sakaci sai a tafi a barka a ƙarshe bare mu dake zagaye da shegun kishiyoyi, tako ina da hari ake kawo mana mune na tsaka. Kinga ko dole mutum ya nemo garkuwa da takobin kai nasa harin ai.”          “Wannan gaskiya ne. Yanzu dai bara nasa Zaituna ta kira mana shi ta falon baya. Kin san gidan namu dai cike yake da ƴan sa ido. Damma maigidan baya gari ne jiya da yamma yay tafiya.”     “Ato ai ansha hidima dole a koma nema kuma. ALLAH ya taimaki ƴan baya suma haka dai dan wlhy rashin auren yaran nan ya fara tada min hankalina. Rigi-rigi sai samari sunzo kamar za'ayi sai ki nemesu ki rasa”.      “To ke kuwa maƙiya cike da gida za'a barsu haka ne. Ke dai kin san yaƙi da gwagwarmayar da nasha Kafin auren nan na Yaseerah ya yiwu. Yanzu saura Zaituna itama dai wani ya biyota a ƴan bikin so nake na huta gajiyar nan na fara aiki a kansa. Dan babu wasa”.      Dariya suka kwashe da ita su duka suna mai taɓawa. Hajiya Basariyya ta ce, “Haka nake fata a nawa gidan. Dan sai yaran nan sun gama aure kaf kafin yaran ɗakin gadararriyar can suyi sa. Na riga na shirya yaƙarta ta wannan fanin”.     “Wlhy ina bayanki. Shegu ai idan sunce su mugunta suka iya gidan suka taras....”      _________★      Kwanakin Maanal goma sha shida a asibiti sannan aka bata sallama. Dai-dai da cikar Hajiya Yaya kwana tara a gidansu. Daddy dai tun wannan fitar da yay daga gida a washe garin zuwan Yazeed bai koma ba. Sai daga baya suka fahimci yama bar ƙasar ne sabgar gabansa. Dan kwanansa biyu da tafiya yasa Hajiya Basariyya tabisa can. Komai Ammie batace ba akan hakan, damuwarta fushin da yake da ita da batasan laifinta ba. Gefe kuma ga yaran Hajiya Yaya sun tasota da rashin kunya da rashin mutucin a gidan. Sai idan Yazeed na gidan ne take samun sauƙin su. Dai-dai da su Hameed sun takurawa da zagi da duka. Wannan dalilin ya saka yau koda su Shahidah suka kirata akan sallamar Maanal tace Maanal ɗin ta zauna anan gidan Shahidah kawai. Nene sai ta biyo su Amaal ta dawo. Hakan yayma Maanal daɗi dan dama bata son komawa Kadunan. Sai dai ita Nene ta fahimci akwai matsalane amma batace komai ba ta shanye a ranta har sai ta koma. Dama tanata mamakin abinda ya hana Ammie sake dawowa Abujan. Kullum sai dai suyi video call safe da yamma. Takance suyi haƙuri da rashin daowarta akwai abinda take yi ne.       Badan Maanal tasoba ta yarda RK yay musu rakkiya har gidan Shahidah. Cikin farin ciki su Munaya sukazo suka rungumeta. Itama haɗasu tai ta rungume tana mai jin kewarsu dan sau ɗaya sukaje dubata asibiti aka hana zuwa dasu saboda bata son hayaniya a lokacin. Har cikin falo suna manne da ita. Kafin su fara rige-rigen zuwa ɗakko mata gift da kowa ya tanada mata.       “I love you yarana”.    Ta faɗa a hankali tana rungumesu.... “Kina da son yara kamar haka, amma kiketa ɓata mana lokaci”. RK dake gefen kujerar da take ya faɗa a hankali ta yanda itace kawai taji. Ɗago yaran kawai tai daga jikinta batare da ta kallesa ba. Shima sai ya basar saboda isowar Amal ɗauke da ƙaramin tire ta haɗo masa abin sha. Godiya yay mata hankalinsa kwance ya ɓalle ruwa ya tsiyaya a kofi ya hau sha. Ita Maanal ma sai ƙarfin halin nasa ya ɗaure mata kai. Kasa jurewa tai sai da ta ɗan zuba masa ido. Yanda take kallon nasa ne ya sashi sauke kofin daga bakinsa shima yana kallonta. Sai kuma ya wani ɗan ƙyaƙyƙyafta idanunsa. Nata idanun ta ɗauke tana ɗan yamutse fuska da faɗin, “Kai ko kunya baka ji?”..          “Ikon ALLAH kunyar mi zanji?. Gidan yayata nake fa. Idan kuma so kike na fara jin kunyar ki bani damar sakaki a gidana na miki alƙawarin ko'ina naje aka bani ko miye bazanci ba sai naki”.         Kallo ta jefa masa mai kama da harara sai kuma ta girgiza kai kawai ta miƙe. Harta gama hayewa upstairs idonsa a kanta, sai da takai step ɗin ƙarshe itama ta ɗan juyo dan tana jin kaifafan idanunsa na yawo a kanta. Da sauri ya ɗauke kansa ya basar. Ita kuma taja ƙaramin tsaki ta ida hayewa. Daga haka bata sake sanin sanda yabar gidan ba. Dan wanka ta samu tayi a ɗakin Shahidah tai kwanciyarta sai barci. Dama sunce zata dinga samun isashen barci yanzu hakan ne zai dawo da kuzarinta data rasa...        Bayan sallar la'asar Nene dasu Amaal suka wuce. Sai suka koma daga ita sai Shahidah da mijinta da yaranta biyu a gidan kawai. Sai kuma masu aikinta guda biyu. Jitai kuma duk babu daɗi, dan tana matuƙar son ta gansu su duka a waje ɗaya hakan na sakata a farin ciki. Sai dai yaya ta iya aure ya rarrabasu. Hira suke da Shahidah, koma ace Shahidah ke hiran dan Maanal dai daga guntun murmushi sai eh ko a'a ne nata. Muneff ne ya shigo da ɗan gudunsa, autan Shahidah, dan daga shi dai har yanzu bata sake ba ko tana hutawane ko ta tsaya oho mata.      “Muneff ban hanaka wannan guje-gujen ba wai nikam?”.     Shahidah ta faɗa cikin taka masa birki. Yaron bai damu ba ya ce, “Mamy Uncle Yazeed ne yazo”.           “Uncle Yazeed na kd?”.       “Eh Mamy. Yana waje ma”.    Kallon Maanal Shahidah tayi. Itama Maanal ɗin ita take kallo. “Kije ki shigo da shi”.      “Ni Didi ƙafata ke ciwo”.    Kai kawai Shahidah ta girgiza tana miƙewa. Hijjab ɗinta da takan ajiye a falo saboda baƙi irin haka ta ɗauka ta saka sannan ta fita.  Babu wani jimawa sai gata ta dawo Yazeed biye da ita. Yana shigowa idonsa akan Maanal ya fara sauka. Itako ta ƙurama television ido kamar bata san da shigowar tasa ba.........✍️   ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖1️⃣7️⃣ .......Sai da suka gama gaisawa da Shahidah sannan ta ɗan kallesa ta ce, “Yaya Yazeed ina yini”.        Sai da yaja kusan minti ɗaya kafin ya amsa da, “Lafiya lau. Yaya jikin naki?”.     “Alhamdullahi”. “Masha ALLAH”. Ya faɗa yana maida kallonsa ga Shahidah. “Shine aka sallameku Shahidah ban sani ba. Sai da naje asibitin yanzu akace kuna gida”.       “Kayi haƙuri Yaya Yazeed anyi kuskure kam. Amma banyi tunanin zaka dawo yau bane, azatona kuma kasan da sallamar ne ma wlhy. Tunda muma munje kai musu breakfast Nene ke sanar mana ai doctor yace zai sallemeta yau, da daddare yake sanar musu.”       “ALLAH ya ƙara lafiya to, ya kuma kiyaye gaba. Ina su Nenen?”.    “Nene ai yanzu na tabbata suna gab da shiga Kaduna. Mijin Amal ne ya wuce dasu gaba ɗaya”.         “Kai da sauri haka?. Ita Nene ko ɗan hutawa bazatayi ba”.     “Aikam bazata zauna ba. A hakama dan zaman asibiti ne. Yau kam muna dawowa tace bafa zata sake kwana a garin nan ba”.           Murmushi kawai yay da faɗin, “Shike nan zan sameta har gida ai. To kema sai ki shirya mu wuce da safe ko, tunda yanzu yamma dai tayi kam”. Ya ƙare maganar idonsa akan Maanal.       “Ni Ammie tace ai na zauna anan”.   “Anan kuma? To saboda mi?”. Shahidah ce ta bashi amsa da, “Bana zaton wani abune gaskiya. Inaga dai tana son ta ɗan ƙara murmurewa ne dan suma likitocin sunyi gargaɗi sosai akan ta huta a waje mai ƙarancin jama'a da hayaniya. Amma tana ƙara murmurewa zata dawo Yaya Yazeed”.      Badan ya gamsu da bayanin Shahidahn ba ya ce, “Okay shike nan ALLAH yasa kaffara ne. Nima dai ina nan Abujan har zuwa jibi in sha ALLAHU, dan akwai abinda zanyi”.        “ALLAH ya taimaka ya bada nasara”. Shahidah ta faɗa cike da girmamawa. Dan suna matuƙar giramam yazeed, koba komai suma yana girmama musu Ammien su. Su kansu yana mutuntasu, dan bazasuce ya taɓa musu wani abu na ashsha ba tun daga zamansu gidansu har zuwa aurensu. Hasalima a auren nasu ya zame musu tamkar babban yaya ne a komai. Tashi tai ta bar musu falon. Hakan yasa shi tashi ya koma kujerar kusa da Maanal shima. Cike da kulawa murya can ƙasa ya ce, “Baki jin komai dai zuwa yanzu?”.       Kanta ta jinjina masa alamar eh.   “Alhamdullahi haka ake so ai. Nasan kece kikacema Ammie baki son komawa KD ko?”.       Cikin marairaice fuska kamar zatai kuka ta ce, “Ni ALLAH babu ruwana.”        Kallonta kawai ya tsaya yi, sai kuma ya ɗan murmusa tare da duƙo da kansa kaɗan murya ƙasa-ƙasa ya furta, “Adana shagwaɓar nan ba yanzu ba”.     Kanta ta duƙar ziciyarta na gudu da sauri-sauri a ƙirjinta kamar zata fito waje. Sai kuma ta yunƙura zata tashi. Cikin bada umarni ya ce, “Koma ki zauna”. Babu yanda ta iya dole ta koma ta zauna ɗin tana ɓata fuska....    _______________★         “Da alama wannan karon mijinki yana son nai matuƙar cin mutuncinsa Sadiyya. Ki taho gida tsahon kwanaki goma amma bai biyo bayanki ba saboda yana son nuna min iyakata. Ban san yaushe Usman ya fara maida kansa sakarai a gidansa ba. Ace mace ke juyaka yarinya ƙarama”.     Hawaye Hajiya Yaya ta sake matsowa tare da duƙar da kai kamar ta ALLAH. Muryarta na rawa ta ce, “Baba wlhy yamafi yanda kake zatonsa a yanzu. Ni shiyyasa ma nace kawai kasashi ya sakeni na gaji da wannan zaman ƙuncin, ai ba haka mukai da shi ba. Shi da kansa yace min duk macen da zai kawo gidan nan sai dai ta kasance a ƙarƙashin ikona da umarnina. Amma duk ya manta da wannan alƙawuran da girmana agaban ƴaƴana da matansa yake tozartani. Wai har yake iya gaya min sai dai matarsa idan ta juya naga bayanta amma ba'a zaman gidansa ba, wai ni Usman ke tarema mace faɗa a gabana Baba”. Ta fashe da kuka.      “Kinga ya isa kukan haka kinji, barni da shi ai nasan maganinsa. Shi kuma Yazeedu daketa kai kawon ki koma saboda baida kishin uwarsa shima zan gyara masa zama. Share hawayenki abinki zakiga matakin dazan ɗauka jeki kwanta”.      Kai Hajiya Yaya ta jinjina tana miƙewa hannunta a saman ido tana share hawaye kamar wadda akacema baban ne ya mutu. Sai da ta gama ficewa mahaifiyarta dake zaune a falon bata tofa ko a ba a maganar tasu ta nisa a hankali. Tsohuwar kirki mara yawan son hayaniya kenan. Idanunta akan Baba ta ce, “Nikam da zakaji shawarata dattijo da baka goya bayan Sadiyya ba a wannan karon. Kai kanka kasan halin yarinyar nan sarai da abinda zata iya. Tunda kaga kuma Usman ya watsar da ita a wannan karon wlhy ba banza ba. Dan haka ka kirashi cikin dattako ka zaunar dasu su duka kaji bakin kowa. Idan ta kama ma can gidan nasa zakaje ka tasata gaba ka haɗasu har abokan zaman nata. Karfa dan ka raini Usman ya zama kana tauye masa hakki akan ƴar da ka haifa.”        “Ai ke kinji matsalarki, idan har abu zai taso akan yaran nan sai kin nuna ban iya ba ke sarkin tawakkali da gaskiya ko”.     “Ba haka bane Dattijo. Masu iya maganafa sunce kaso naka duniya ta ƙisa, ka ƙisa duniya ta soshi. Usman na maka matuƙar biyyar da kosu ƴaƴan da ka haifa ba kowa ke maka irinta ba. To bai kamata a cigaba da ƙasƙantar da shi ba akan abinda ya isa da shi. Wannan fa rayuwar aurensu ce. Kuma shine shugaba a gidan, yin kutse a al'amarin kamar ƙasƙantar da shi ne. Dan ALLAH kada ka biyema yaran nan ana ganin ka da kima da mutunci irin na uba kuma shugaba”.       Shiru yay na kusan minti biyu, sai kuma ya sauke ajiyar zuciya. “Hakane kuma Adama nagode da tunatarwa. In sha ALLAHU gobe zan tasata gaba muje gidan. Sai dai ance min shi Usman ɗin baya ƙasar, amma dai inada tabbacin kamar yau ne da dare zai dawo”.      “To Alhmdllh gobe idan ALLAH ya kaimu ɗin sai kuje, ALLAH ya taƙaita al'amarin kuma ya daidaita su”. “To Amin ya rabbi. Yarane sai addu'a kawai yanzu, sun maida aure wasan yara”...... __________★         Isowar dare Daddy da Hajiya Basariyya sukai ma gidan. Tafiyar kwana goma har sunyi fresh abinsu. Babu wanda yasan da dawowar tasu, dan ita Ammie ma harta kwanta abinta. Cikin barci taji wayarta na ƙara. Da ƙyar ta buɗe ido ta jawota dan ta manta ne ma bata kashe ba. Ɗagawa tai takai kunne tare da sallama. Sai dai Muryar wanda ya amsa mata da umarnin daya bata ya sata watsakkewa sai kuma ta tashi zaune. Jin abin tai kamar mafarki, amma dai ta miƙe ta ɗauka dogon hijjab ta saka sannan ta nufi kitchen. Tea ɗin daya buƙata ta haɗa masa. Sai ta haɗa da ɗan snacks da fruits da bata rabo da su. Haka ta fito gidan shiru alamar kowa ya kwanta ta nufi sashen maigidan. Takai hannu zatai knocking ta tsaya cak sakamakon jin muryar Hajiya Basariyya na tashi a sama cikin faɗa...        “To amma dare yayi ai, ƙarfe nawa yanzu da zaka ɗaga waya ka kirata wai ta kawo maka abu. Ni banda hannune ko abinda zata kawo makan banda shi a sashena? Randa kuka dawo Abuja wayasan kun dawo ba sai tashi mukai muka ganku a gidan nan ba. Sai ni daka raina. Wai mi Asiya tafimu dashi ne? Mi take dashi na mata da mu bamu da shi da kake son ganin ka fifitata a kammu?!!.......”      “Badariyya wai kina da hankali kuwa. Baki ganin dare yayi zaki zo kina min ihu a kaina. Da kike maganar miyasa zan kirata ta kawo min abu ke da kika dawo daga tafiya mizaki bani? Sannan batun fin sauran mata da kike sai yanzu kika san Asia tafi sauran mata ashe. To lallai kin makaro da kika kasa fahimtar hakan tun tuni. Ita da na saka kika bini a ranar girkinta kinji tayi wani ƙorafi ne. Kuma randa muka dawo Abuja ni Asia bata kwana a sashen nan ba, idan ma ta kwana ai matatace. Dan haka ki fice min anan shasha kawai tana girma bata san ta girma ɗin ba”.       “Ni ce shashashar Daddy Huznah?”.    Banza yay mata bai tanka ba. Sai maida hankalinsa yay a kiran Ammie. Da sauri ta danne wayar gudun kartai ƙara. Sai kuma ta daure tai knocking ƙofar. Umarnin shiga ya bata. Koda ta shigo kai tsaye a Centre table ta ajiye tray ɗin, sai kuma ta shiga gaishesu su duka a tare da yimusu barka da dawowa. Daddy ne kawai ya amsa mata. Zata juya tabar falon ya katse hanzarin ta. “Ina zaki kuma”.    Juyowa tai ta kallesa. “Zanje na kwanta ne, kuma ku samu ku ɗan rintsa ku huta gajiya ko”.       “Dawo ai anan zaki kwana”.    “Anan kuma Daddyn Hameed amma ai....”    Cikin katseta ya ɗaga mata hannu. Dole ta haɗiye abinda take son faɗar. Cikin ɓacin rai Hajiya Basariyya taja akwatinta da hand bag ta fice a sashen tana jan tsaki. Da kallo Ammie ta bita harta gama ficewa. Tai wani kalar masifar bugo ƙofar har sai da Ammie ta zabura. Cikin sanyin jiki ta maida dubanta ga Daddy dake ƙoƙarin fara shan shayinsa hankali kwance. “Daddyn Hameed dan ALLAH....”       “Asia! Kin san bana son jan zance ko!”.      Ajiyar zuciya Ammie ta sauke kawai, badan taso ba tabi umarninsa a yanda yake buƙata....... __________★       Washe gari kusan ƙarfe goma na safe sai ga baƙi. Ammie na tsaka da haɗama Daddy abinci zai fara ci maigadi ya isar da saƙon zuwan Alhaji Mamman sirikin na Daddy kuma uban gidansa. Da sauri Daddy ya miƙe tare da shiga ciki ya canjo kayan jikinsa zuwa jallabiya. Yayinda Ammie kuma ta fita ta ƙofar baya domin ƙaro abincin. Bata wani jimaba ta koma ɗauke da wani kayan abincin. Ta samu har Daddy ya shigo da shi falonsa shi da babban amininsa sai Hajiya Yaya. Ajiye kayan Ammie tai cike da girmamawa ta rissina ta gaishesu batare data damu da hararar da Hajiya Yaya ke mata ba. Sun amsa mata da kulawa. Dan haka kawai sai Alhaji Mamman ɗin yaji Ammien ta masa kwarjini da shiga ransa. Bai fi sau biyu ya taɓa ganinta ba. Lokacin ruguntsumin aurenta sai kuma da sukaje da Daddy gaishesa bayan sun dawo Hajiya Yaya ta dinga zuba tujara daga nan Ammie ta ɗau aniyar bazata sake zuwa gaidashin ba. Daga mutunci sai abu ya zama fitina da cin mutunci, tun daga nan ko Daddy yace tazo suje sai tayi yanda tai ta zame jikinta. Abincin ta shirya a gabansu sannan ta fita domin basu damar ci, duk da dai Baban yace sun gode bazasu ci ba sukam. Amma Daddy nata roƙonsu. Dole dai suka ɗan taɓa kaɗan, kafin Baban yasa Daddy kira masa su Ammie su duka. Dai-dai nan kuma Yazeed ya shigo falon daga gani isowarsa garin kenan. Dan tunda daren jiya Ammie ta tura masa sako akan dawowar su Daddy ɗin, tare da bashi shawarar ya taho da safen dan ta samesa a gida shiyyasa yay sakkon tahowa kafin ya sake guduwa. Yana fatan iyayen nasa su sasanta kansu komai ya wuce kada abun yayta ƙara girma. Sai kuma akai sa'a ya samu kakan nasa yazo tare da mahaifiyar tasa gidan. Cikin girmamawa ya gaida kakan nasa sannan ya gaida abokinsa. Sun amsa masa da kulawa da tambayarsa aiki tare da tsokanarsa akan ƙara zama tuzuru babu aure. Murmushi kawai yay ya maida hankalinsa a gaida Daddy sannan ya gaida Hajiya Yaya itama. Dai-dai nan Hajiya Basariyya da Ammie suka shigo suma. Gaidasu yayi suma da girmamawa. Ammie ce kawai ta amsa masa da kulawa. Hajiya Basariyya kam sama-sama dan tana cikin haushi ne. Ko su baba sama-sama ta gaishesu kamar an mata dole. Anan ma sai Baban ya sake karantar abubuwa da dama. Bayan an natsa da gaishe-gaishe aminin Baba da suke kira Alhaji Kallah ya buɗe taron da addu'a. Daga haka ya kalla Daddy cikin mutuntawa ya kirayi sunansa.         “Usman!”.     “Na'am Baba”. Daddy ya amsa masa da girmamawa dan shima yana ɗaukarsa matsayin uba ne. Kai duk ma abokan Alhaji Mamman a rayuwa Daddy na basu girma irin na uba ne. Alhaji Kalla ya cigaba da faɗin, “Mike faruwa tsakaninka da iyalinka ka turata gida har tsahon kwanaki babu wani bayani”.        “Baba ni bani na tura ba”..........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖1️⃣8️⃣ .......“Ban gane ba Usman, kamin bayani yanda zan gane da ƙyau”.     Kai Daddy ya jinjinama Baba Kallah. Kafin ya gyara zamansa da ƙyau ya shiga zayyano masa abinda ya sani. Kuma ma duk ita Hajiya Yaya ce ta kirashi a waya ta sanar masa. Daga ƙarshe ya dora da faɗin, “Gasu nan baba ka tambayesu daga Asia ɗin har Basariyya akwai wanda na zaunar naima magana akan batun? Na barsu ne har sanda yarinyar zata samu lafiya dan shine mafi muhimmanci. Amma sai ita ta nuna min ban isa ba. Nace taje ta duba yarinyar ita da yara sashenta tace ban isa ba ita kuma Basariyya taje, hakan yasa na dakatar da ita da shigowa wajena.....”         “Dolene to sai naje. Itama Basariyyan ai munafunci da gulma ne ya kaita badan ALLAH ba”. Hajiya Yaya ta faɗa cikin katse Daddy. Tsawa Babanta ya daka mata shima, dole tai shiru tana kumbura fuska.    “Usman kamin dai-dai, dan abinda kayi ɗin shine mazantaka.” baba Kalla ya faɗa, sai kuma ya juya ga Hajiya Yaya yana mai kiran sunanta. “Sadiyy! Dukkan abinda Usman ya faɗa haka akai?”.      Babu musu ta jin jina kanta. Sai kuma ta ɗora da faɗin, “Baba nifa tsakanina da ALLAH koda aurena zai ƙare ne tsakanina da Usman sai dai ya ƙare a yau. Dan haka ku zama shaida ban amince Yazeed ya auri ƴar Asiya ba. Idan kuma ba hakaba a shirye nake na fiddashi a cikin ƴaƴana na barma Asiya tunda haka naga yake buƙata. Na gaya masa na masa faɗa amma yana maidani ban san abinda nake ba, to tunda haka ne dai ya zaɓa ko ni ko yarinyar”.      Hankali tashe Yazeed ke duban mahaifiyar tasa. Zai yi magana Baba Kalla ya dakatar da shi ta hanyar ɗaga masa hannu. Dole Yazeed yay shiru.         “Sadiyya miyyasa baki son shi haɗin nasu? Yarinyar nada wata illane da musulunci ya hanamu auren irinsu?”.      “Illoli da yawa kuwa Baba. Ciwuwwuka sun gama zagaye rayuwarta. Sannan mu har yanzu bamu da tabbacin ma suna da uba tunda mudai bamu taɓa ganin dangin uban nasu ba balle mu shaida, har bikin yayunta akai a gidan nan mudai bamuga kowa ba, wama ya sani ko basu da uban ne shiyyasa sam ni jinina bai wani haɗu da nata ba dan bana ƙaunar yarinyar nan, ba kuma na ƙaunar uwarta gata nan”. Ta ƙare maganar da nuna Ammie babu nauyi ko kara. Kai baba Kalla ya girgiza da faɗin, “Ashsha Sadiyya, wannan magana tayi tsauri da yawa. Kiyi ƙoƙari ki dinga gyara harshenki yayin magana. Dan haka karna sake jin irin wannan zancen banzar ya fito. Munji baki son wannan haɗin, wacece kika fidda masa ke a matsayin matar?”.       “Baba Nazeefar Sabuwa. Idan har Yazeed yana son yaga farin cikina to ya aurenta dan ita nasa tushenta. Idan ko ba haka ba ya shirya rayuwar auren ƙunci da baƙin ciki, sannan duk abinda zata haifa babu ruwana da su kamar yanda shima na ciresa daga cikin ƴaƴana.....”     Cikin takaicinta da harzuƙa Daddy ya ce, “Aiko baki isaba wlhy, Maanal na zaɓama yarona matsayin matarsa ko kina so ko baki so, kuma wlhy first and last da zaki sake sheganta yaran nan idan ba hakaba kuwa sai ranki ya ɓaci fiye da yanda kike zato....”         “Kaima kuwa baka isaba Usman, dan yanda kake jin kai uban Yazeed ne nima nice mahaifiyarsa. Nina ɗauki cikinsa na tsawon wata tara, nai naƙudarsa na kumayi rainonsa haɗe da tarbiyya har yakai girman da wata banza a banza daka kawo gidan ka kake ɗaukar ta a mutum ta isa ta mallake min shi, kai wlhy duk abinda kake ji ka iya na iya fiye da iyawarka Usman, dan....        “Sadiyya!!!”.   Babanta ya katseta a tsawace. Shiru tai amma a ranta tana ƙunƙuni, dan ta ɗau aniyar koma miza'ayi sai dai ayi amma Yazeed bazai auri ɗiyar Asiya ba dan ita zuwa yanzu ma ta fara tunanin basu da uban. Ganin ran baba ya kai ƙolokuwar ɓaci hakama Daddy da ita Hajiya Yayan Ammie dake saurarensu kawai ziciyarta na mata ƙuna cike da girmamawa ta kalla Baba. “Baba dan ALLAH ina neman alfarma”.        “Faɗi ko minene ɗiyata in dai ina da shi zan miki”.     Wani takaici ne ya lulluɓe zuciyar Hajiya Yaya ganin yanda Babanta ke bama Ammie muhimmanci a zaman fiye da ita. Baki ta buɗe zatai magana ya harareta. Dole tai shiru ta cigaba da hare-harenta. Ammie bata nuna ta damu ba ta cigaba da faɗin, “Baba dan ALLAH ku barta ta aura masa wadda take so. Domin gaskiya ta faɗa Maanal bata dako isashiyar lafiya ma. A yanzu haka likitocin ma sunce tana matuƙar buƙatar hutu ta yanda al'amuranta zasu dai-daita. Shi kuma Yazeed za'a cigaba da tauyesa babu aurene saboda hakan. Bayan UBANGIJI ya halatta masa auren mata har uku ne. Idan har Maanal matarsa ce ko zuwa nan gaba sai ayi......”       “Allah ya kiyaye, har abada bako za'ayi ba idan abinda kike tunani kenan ki ciresa kuwa....”     Hajiya Yaya ta katse Ammie a harzuƙe. Shima Daddy a harzuƙen ya katseta da faɗin, “Ashe kuwa zaki mutu bayan anyi, dan Maanal ita na zaɓama Yazeed kuma shima itace zaɓinsa aure tsakaninsu babu fashi da izinin UBANGIJI ko da Asiya data haifeta bata yardaba kuwa. Baba ku ƙyaleta, tunda ita bata san masalaha ba dan ALLAH mu zuba aga ni da ita waye keda ƙarfin iko akan Yazeed ɗin.....”         “A'a Usman duk baza'a kai ga haka ba”. Baba Kalla ya faɗa. Batare da ya jira cewarsu ba ya cigaba da faɗin, “Ku duka ku kwantar da hankalinku kuji. A matsayinku na iyayen Yazeedu duk kuna da iko a kansa, amma fa ku sani shima yanada hakki a kanku. Aure dai ba wasa bane, ba kuma jeka ka dawo bane ba. Dan haka ku masa adalci ku barshi ya zaɓi wadda ransa ya kwanta da ita koda a cikin zaɓin naku ne. Idan kuma babu a cikinsu itace ma babbar masalaha ya auro daga can gefe shike nan matsala ta kare. Saboda haka kai Yazeedu kana da wadda kake so ne?”.        A hankali kuma karo na farko Yazeed ya ɗago idanunsa da suka kaɗa sukai jajur saboda damuwa. Cikin danne ƙuncin daya mamaye masa zuciya ya ce, “Baba idan har auren duka zaɓin nasu zai zama masalaha na karɓa. Zan auri Maanal ɗin da Nazeefa....”     “Baka isa ba sai dai ka auri Nazeefa ita kaɗai....” Hajiya yaya ta katsesa cikin daka tsawa. Babanta ne shima ya katseta a tsawacen. “Sadiyya bana son shashanci fa. Yaro ya kawo mafita kinama mutane rashin hankali, ko kunyar idona baƙyaji bare nauyi. Shin kokin manta mune a gabanki bashi mijin naki kaɗai da kika raina ba. Ana binki ta lalama kina wani botsarewa saboda wulakanci. To wlhy ki shiga hankalinki. Idan kuma ba hakaba zan hanashi auren Zazeefa ɗin naga yaya zakiyi. Shashancin banza kai”.        Haƙuri ta fara bashi ranta a matuƙar dagule. Tayi hakanne kawai dan ganin yanda ransa ya ɓaci, ta kuma san halin mahaifin nata idan yay magana baya canjawa. Gara ta lallaɓashi suje a haka ita tasan duk ma hanyar da zatabi dan ganin ta tarwatsa wannan aure.... Shima Daddy haƙurin yaba baban, dan haka ya cigaba da faɗin, “Shike nan magana ta ƙare zai auresu su dukan. Dan haka sai kuje ku fara shiri dan nan da watanni biyu za'ayi a wuce wajan. Rana ɗaya za'a ɗaura auren.”         Wani irin motsawa zuciyar Ammie tayi da ƙarfi. Hakama Hajiya Basariyya da tun da aka zauna bata tofa komai ba zuciyarta wani irin raɗaɗi take mata. Ina bazai yiwu ta bari ai wannan haɗin ba, sannan bazata taɓa yarda aima Yazeed auren gata shi kaɗai ba wlhy, Gara a cigaba da wannan fitinar hakan yafi sakata nishaɗi, zai kuma fi bada armashi idan yazam anyi auren Nazeefa da Yazeed ne farko. Ammie zatai magana tai saurin katseta ta hanyar fara yi. “Baba mun gode ALLAH ya saka da alkairi ya kuma sanya albarka a al'amarin. Sai dai nakega maganar ɗaura auren rana ɗaya kamar akwai damuwa musamman ga ita Maanal. Tunda likitoci sunce abarta ta ɗan huta mizai hana a fara yin na Yazeed da Nazeefa daga baya sai ayi da ita Maanal. Komai ma zaifi tafiya a cikin masalaha ni dai anawa ganin, zuwa lokacin itama Maanal ta murmure dan yarinyar ta fyaɗu sosai a wannan karon, wlhy abin tausayi kamar bazata rayuba ma. Sai itama Huznah ta samu miji, Inaga sai a haɗa dana Yazeed ɗin kawai ko yaya kukace”.         A maganar farko Hajiya Yaya wani irin daɗi da godema Hajiya Basariyya ta shigayi a zuciyarta. Daga ƙarshe kuma sai taji zafi danta fahimci hassada Hajiya Basariyya ke son nunawa. Amma zata bita a hakan dan itama ta ribantu. Itama dai Ammie har ranta taji daɗin zancen Hajiya Basariyya, duk da tasan tayi hakanne badan ALLAH ba sai wata manufa tata. Shiko Daddy wani irin ƙuna zuciyarsa ta shigayi, saboda ya jima da fuskantar wacece matar tasa. Cikin takaici kawai yake mata wani kallo mai kama da harara. A ɓangaren Yazeed kuwa wani irin tsanar matar uban tashi ya fara ji a karo na farko a rayuwarsa. Duk da ya jima da fahimtar halinta na munafunci dan ta sha haɗashi da Daddy a baya bai taɓa maida hankali ko damuwa da lamarinta ba. Amma a yau ji yake kamar ya maketa dan baƙin ciki. Shifa ya amshi auren Nazeefa ne kawai dan ya samu dai Mamma ta haƙura ya auri Maanal. Amma shine munafukar matar nan zata kawo wannan ƙauli da ba'adin. Kasa daurewa yayi cikin sanyin murya ya ce, “Ummi anawa tunanin ai ba komai bane. Idan ta dawo ƙarƙashina zama tafi samun kwanciyar hankalin da su likitocin ke buƙata. Maanal na buƙatar hutu ne da kulawa. Kuma ina sha ALLAHU duk bazan gaza yin hakan akansu su duka ba”.       Ganin kamar zancen ya shigi baba yasa Ammie saurin tare numfashinsa. “Hakane Yazeed, amma dan ALLAH nima ina roƙonka da abi shawarar Hajiya. Saboda ya kamata aje neman auren Maanal wajen dangin mahaifinta. Ita kanta kuma sake samun nutsuwar zaisa komai ya tafi mana dai-dai yanda ya kamata. Idan akayi na Nazeefar kamar da wata biyar haka itama sai ayi natan. Kamar yau ne ai ka kwantar da hankalinka kaji Yazeed”.      Ji Yazeed yay kamar ya fashe da ihu. Dan idanunsa har wani ɗan tara ƙwalla sukayi. Baba Kalla ne ya ce, “To da gaskiyarsu kuma ta wani fanin idan muka kalla. Tabbas mai irin wannan ciwo mai haɗari ya kamata abi dokar likitocin domin samar mata da nutsuwa. Sannan kamar yanda mahaifiyarta ta faɗa yana da ƙyau aje neman aurenta wa mahaifinta. Dan haka kayi haƙuri Yazeedu kamar yau ne in sha ALLAHU. Kaima idan akai haka zaifi baka nutsuwa da kwanciyar hankali. Ai rabon baima zoba ballantana ya wuce”.       Albarka duk suka saka da fatan ALLAH yasa haka shi yafi alkairi. Sai dai a ɓangaren Yazeed zuciyarsa a matuƙar ƙuntace take. Haka shima Daddy sam wannan tsarin bai masa ba. Kawai dai dan anfi ƙarfinsa ne. Amma ya ƙullaci Ammie da Hajiya Basariyya. Da haka dai taron ya watse.....      _________★      Bayan wucewar su Baba Ammie ta samu Daddy akan zataje gaishe da Nene tai mata godiya da ban gajiya. Amma sai yace bai yarda ba. Abin ya bata mamaki, saboda a fusace yay maganar. Zata roƙesa kuma ya ɗaga mata hannu da nuna mata ƙofa alamar ta fita. Tsantsar biyyarta garesa yasa bataja zancen ba ta fitan, dan ta fahimci a fusace yake da ita ne, sai dai bata san ainahin laifin nata ba ita kam. Koda ta kira Nene ta sanar mata ya hana, sai tace ta jirata gata nan zuwa ita....    ________★       Hajiya Basariyya kam dariya ta dinga sheƙawa. Sai kuma tai kiran aminiyarta ta lambarta mata komai. Dariyar suka haɗu sukayi tayi su duka. Sai da sukai mai isarsu cike da zolaya Hajiya Kamila daga can tace, “Aminiyata ke kwalba ce wlhy uwar sharri. Cikin ƙanƙanin lokaci kinsa dole anbi yanda kike so. Ho tawajena kina wuta fa”.          “To ni ɗin ta wasa ce aminiya ai idan sun san wata basu san wata ba. Idan har ina raye Asiya bata isa samun abinda ni ban samu ba. Ita kanta Hajiya Sadiyya da take ganin kamar na mata aiki ne ta saurari shirina akanta.”       “Kai ta wajena mi kike shirya mata ita kuma?”.    “hhhhh karki damu sai mun haɗu zaki ji komai da komai. Ke dai yanzu kice da Malam Nagode. Zuwa gobe kuma zan turo miki Huznah ya mata dukkan abinda yace dan ina son shap-shap yaron nan ya kawo kasa tunda har na gumtsa musu zancen kada a fara ɗaukata maƙaryaciya”.      “An gama ai karki wani damu kanki”.    “To shike nan sai tazo.” Daga haka sukai sallama kowa ya yanke wayar. Hajiya Basariyya ta faɗa saman gado tana mai jin kanta a sama can ƙolokuwa da tabbatar ma da kanta yau sa'a tata ce........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖1️⃣9️⃣ .......Sosai ƙannen Yazeed sukai farin cikin dawowar mahaifiyarsu gidan. Gaba ɗaya sun zagayeta anata cakai-cakai kowa na bata labarin abinda ya faru da bata nan. Itako sai murmushin jin daɗi take yi musamman akan abinda suka dinga ma Ammie. Suna a hakan Aunty Sabuwa ta samesu. Tashi Hajiya Yaya tai suka shige ƙuryar ɗaki suka rufe kansu. Dama itace tai kiranta tunɗazun bayan wucewar su Babansu. Sai da Aunty Sabuwa tasha fresh milk ɗin data ɗakko daga falo sosai sannan ta dire tana sauke ajiyar zuciya da faɗin, “Kai nafa kwaso rana da yawa. Kin ganni nan daga tudun wada nake. Kin san munata shirye-shiryen bikin ƴar ƙawata Sailuba. Ko sanda kika kirani muna tsaka da meeting ne ma dan tun sassafe na baro gida”        “Kai kar dai kice min bikin yarinyar nan har yazo?”.    “Wlhy kuwa yazo Yaya ai abin babu wuya...”     “Gaskiya ba wuya kam. Abin mamaki wai Sailuba da aurar da ƴa”.    “Hhh kai yaya da abin dariya kike. Yo ALLAH na tuba komu badan yaran nan sun tsaya ruwan ido ba ai da tuni jikoki sun cika mana ko'ina.”      “Ai dan ubansu dole kam suzo su fito da mazajen aure dan na gaji da ganinsu ɗirka-ɗirka a gida sai yawo bikin wasu da taron birthday party. Ba maneman nan suka rasa ba amma narasa mi sukema hange-hangen”.      “A'a to yadai kamata wlhy Yaya. Yanzu abin sha'awa bakiga yarinyar nan yanda mijin ya haɗo lefe na nunama sa'a da tsara ba. Jiya mukaje muka duba gida komai yaji gidansa kamar ka zauna kaita kallo. Kuma karki daɗa karki raga yaron shagone wlhy. Amma komai babu raini”.         “To Sabuwa ai dama abin zuciya ce ba dukiya ba. Sai dai kuma kana gudun inda yaronka zai je ya ƙasƙanta ne. Ko ka saida akuya ta dawo tana ci maka danga.”     “Da wannan kuma dan wannan. Yanzu dai zakije min baici ko?”.    “A mizai hana, ranar yinin biki insha ALLAHU zan zo, ai Sailuba nada mutunci da girmamawa. Yarinyar nan ko sanda kike zaune a Kano indai tayo tanan anguwar dai ta shigo mun gaisa”.      “Sailuba ai bata da damuwa Yaya. Damma ALLAH ya bata shegen miji ne kawai. Wai shi uztazu. Ko akan bikin nan sai da muka bisa ta ƙasa sannan fa ya amince da wannan shagulgulan amma da duk ya hana”.       “Oh kice dai kuna nan da halin bin malam nan maƙaryata ko Sabuwa?”.    “Ko ɗaya aunty kawai dai sai ta kama. Wani lokacin ne halin mazan nan sai ka haɗa da dabaru. Yanzu ko ke abinda Yaya ke miki a gidan nan da zaki bari ai masa ɗaurin huhun goro ai da kin wuce wajen. Ko su su Basariyyan haka nan suka zauna ne kike gani. Ai wlhy ba banza ba yake wannan rawar jikin akansu har shi ma Yazeed ɗin”.      “Zan iya yadda dake wlhy Sabuwa, dan yau naga abu a gidan nan. Kai Basariyya makirar mata ce. Tabbas na tsani Asiya kuma bana sonta amma wani lokacin gara min ita sau dubu akan Basariyya..........”    Tsaf Hajiya Yaya ta labartama Sabuwa yanda komai ya faru yau a zaman da akayi, har hukuncin da su Baba suka yanke. Sosai Aunty Sabuwa ta sauke ajiyar zuciya da har sai da Hajiya Yaya ta ce, “Lafiyarki kuwa irin wannan ajiyar zuciya haka?”.        “Wlhy ƙalau Yaya. Naji kawai abubuwan duk sun zo da sauƙi ne. Koba komai ai mu munafuncin Basariyyan yaman rana yau, dan in dai an rigada anyi na Nazeefar Asiya kuma sai dai ta nema ma ƴarta wani mijin amma ba Yazeed ba”.      “Nima haka nace ai, shiyyasa ma na ƙyalesu aje a hakan. Amma kuma kin san Basariyya maciji ce bata ramin kanta. Mi kika fahimta a wannan salon nata?”.     “Hassada ce kawai wlhy Yaya. Tasan auren Yazeed sai ya zama na nunama tsara a gidan nan shiyyasa take so ta cusa na ƴarta ayi tare. Kuma tayi na banza dan babu abinda zamu fasa sai ma mu ƙara in sha ALLAHU. Ita waye ƴar nata zata aura ma shin?”.           “Yo waya sanan musu bata faɗa ba. Ai kin santa ita komai nata ƙunshe-ƙunshe saboda munafunci bata so a sani. Amma nidai tunda nake a gidan nan ban taɓa ganin wani fitaccen baƙon mutunci da za'a kirashi mijin aure yazo wajen Huznah ba. Sai dai idan ba'anan gida ake taɗin ba”.      “Eh ai munafuka ce zata iya tsara komai. Shiyyasa wlhy Yaya ki zagargari yaran nan suma su fiddo mazan aure, in ba hakaba zataita kutsawa ne dan taga ta gama aurar da nata yaran duk ɗan abin arziƙin su wawashe a barsu su da saura. Kina dai gidan nan agololi biyu sukai aure Yaya ya dinga ɓarin kuɗi kamar babu gobe. Badan mun daƙile wannan ba ma dana uku kenan. To shi dama aurar da yara haka yake na farko-farkon nan sunfi morewa, dan anfi kashe musu dukiya”.         Sosai zancen Aunty Sabuwa ya shigi Hajiya Yaya. Cikin juyayi ta ce, “Oh dama haka abin yake Sabuwa? Amma shine baki fargar dani ba tuntuni”.      “Ba fargar dake ne banyi ba Yaya. Kin san auren agololin can munafuntarmu akai akaita komai kamar talakawa zasu aura shiyyasa bamu bama abin muhimmanci ba. Sai daga bayan nan muke ganin ashe lulluɓin biri akai mana da fatar kura. Kuma ko rantsuwa nayi banyin kaffara Yaya ne ya samawa yaran nan mazansu. Shegu da yake suma burin su kenan gasu nan har da ƴaƴa bibbiyu”.        “Humm ai Daddyn Yazeed ya jima yana zaluntata a gidan nan ban farga ba. Kiga fa Asiya ta bayan bayana wai itace da waɗan nan nasarorin. Babu komai zamu ɗauki mataki”.     “Babban ɗaukar mataki ALLAH Yaya kuɗi zaki fiddo ko ki shirya ma dake muje ayo miki aiki ɗan gaske. Mufa ba bokaye muke bi ba. Malamai ne na zaure, kin ga ko kaje wajen malami ba bokaba ai babu batun rasa sallar da ake cewa ta kwana arba'in ko?”.       “Hakane kuma. Inaga dai wannan karon zanje ɗin”.     “Haba koke fa yaya”.     (Humm ALLAH ai ba'a masa wayo ko dabara Sabuwa. Idan abu ya dameka ka miƙa lamarinka ga UBANGIJI shi baya barci kuma baya mantuwa. Fafi yawan wasu abubuwan da muke ɗaukarsu damuwa a rayuwarmu hassada ke mana jagora akansu. Amma mu sani rabonkafa rabonka ne. Sannan wani baya canja maka ƙaddararka. Duniyar nan cike take da arziƙi, ka tsarkake zuciyarka ka nema naka kaima in dai nakan ne wani bai isa tare maka wannan samun ba ko ya ƙarama kansa. Shima iya nasa kawai zai ci. Ya rabbi ka yafe mana kurakuranmu😭🙏 ka gafartama iyayenmu 🙏). ____________★        “Tabbas da manufa kam ta ƙarfafa maganar taki Asiya. Amma kada ki wani damu. Mu ALLAH yasa haka shine mafi alkairi. Dan nima ta bakinki zuwa yanzu auren Maanal da yaron nan ya fita a raina. Duk kuwa da shi ɗin mutumin kirki ne. Amma halin uwarsa da ƴan uwansa bazai bar Maanal zama lafiya ba. Gata ita mai rauni. Ni yanzu abinda nake gani kawai mu lallaɓa Maanalu ta bama yaron nan Rafeeq dama ya shigo sosai, shi kansa Yazeed ɗin ba lallai idan sun aura masa tasu ba su barshi haka ai”.      Tabbas hakanne Nene, ni kaina wlhy yaron nan Rafeeq yamin. Yaron a haka dai kamar baida wata damuwa. Gashi kuma ɗan uwan Majdiya uwa ɗaya uba ɗaya. Majdiya mutuniyar kirkice ga addini. Dan hatta yaranta tarbiyyarsu ta banbanta da sauran ƴaƴan gidansu. To dan dai yaran yanzu ne kai kana hango musu alkairi su suna wani hange daban. Amma dai yanzu zanyi duk yanda zanyi ta cigaba da zama can Abujan dan bana sha'awar dawowar Maanal gidan nan a yanzu kuma sam Nene wlhy”.       “Wannan ma tunani ne mai ƙyau. Gara ta zauna a can ɗin kusa da ƴar uwarta. Tunda shima can yake Rafeeq ɗin sun ma fi samun shaƙuwa. To amma shi maigidan naki bazaiga an masa ba daidai ba?. Kinga dai yanda yake matuƙar ƙaunar yaran nan da musu hidima. Tunda kuka dawo hannunsa bai taɓa bambanta al'amarin su dana ƴaƴansa ba”.      “Tabbas hakane Nene. Nima idan na tuna hakan jikina yana sanyi. Dan ya musu abinda mahaifinsu da ƴan uwansa suka gagara musu. To amma yaya zamuyi, matar nan wlhy ta wuce duk yanda kike tunani. Nata ma mai sauƙi ne, dan babbar matsalarta itace ƙanwar nan tata. Saboda mashawarta ne bata moreba kawai, amma duk masifarta ta wani fannin tafi Basariyya sauƙi”.           “To mu cigaba da addu'a, ALLAH ai bai manta da kowa ba. In sha ALLAHU komai zai kasance da sauƙi. Yanzu dai sai kisan dabarar da zaki masa akan zamanta ɗin can dan a rabu lafiya har su gama wannan bikin nasu. Saboda yanzu kam kema fa sai kinyi haƙuri, zakiga abubuwa da yawa wanda za'a dinga miki su da gayyane.”     “Hakane Nene. In sha ALLAHU babu damuwa. Dama dai matsalar tawa Maanal ce. Dan su wannan samarin babu ruwansu. Itace dai dama ina tsoron a jangwalo ciwon nan nata. Amma idan bata gidan koma mi suke shirin yi suyita yi”.         Nene ta gamsu sosai. Dan haka suka cigaba da tattauna batun Maanal ɗin dai. Nene bata bar gidan ba sai bayan magrib. Ammie ta rakota sukaci karo da Hajiya Yaya itama ta rako Sabuwa. Kallon banza suka dinga musu. Dan Nene ma na gaishesu amma ko kulata basuyi ba sai ma tsaki da Sabuwa taja musu mai ƙarfi. Abin ya ɓatama Ammie rai amma sai ta danne. Itama Nenen duk da nata ran ya ɓaci sai ta danne dan bata son ƙarama Ammien damuwa...    _________★        Damuwa da ɓacin rai da tashin hankalin hukuncin da aka yanke yasa a ranar Yazeed ya koma Abuja batare da sanin kowa ba. Ita kanta Hajiya Yayan sai da dare ta aika Basira kiransa ta dawo ta sanar mata ɗakinsa ma a kulle yake. Waya ta ɗaga tai kiransa. Batare da amsa sallamarsa da gaisuwarsa ba tace yazo tana nemansa. Haƙuri ya bata akan shi fa ya koma Abuja. Dan ya samu kira na gaggawa. Ranta ya matuƙar ɓaci amma sai ta danne bisa shawarar da Sabuwa ta bata na a dinga lallaɓashi yanzu har ayi a gama lafiya. Cikin sauƙaƙa murya tace shike nan idan ya dawo sayi magana. ALLAH ya bada sa'a.      Ya amsa mata da Amin, dan ko yaya ya ɗan ji sauƙi a ransa na jin bata fushi da shi. Yazeed mutum ne mai kiyaye fushin iyaye, sannan yana da takatsantsan akan al'amarinsu. Ko wannan maganar Manaal ɗin da ace babu goyon bayan Daddy duk son da yake mata da tuni ya haƙura saboda mutuntasu....    ________★        A Abuja dai kam RK ya riƙema Maanal wuta. Dan kullum sai yazo gidan Shahidah sai ya fake da dubata yazo yi kasancewar dama sun sanar dasu hakan. Sai dai abinda basu sani ba duk tsarin RK ne dama akan batun zuwa gida dubatan kullum. Ya cigaba da kwaɗaita mata zancen aiki. Tun tana dojewa harta sanarma Shahidah. A mamakinta sai Shahidah ta bata goyon bayan mizai hana ta amshi tayinsa. Ai abune mai ƙyau neman nakanka musamman a wannan zamanin. Cikin damuwa Maanal ta ce, “Amma Didi kin san Ammie bazata yarda ba. Hakama Daddy zaiga kamar mun nuna gazawarsa ne musamman idan mukai dubi da duk yaransa mata babu wadda ya bari tayi aiki, ko ku sai da kukai aurene yace idan mazanku sun yarda kuyi aikinku. Idan ni kuma nazo masa da sabon tsari sai yaga kodan bai haifemu bane ba”.          “Hakane Maanal. Amma idan aka duba naki al'amarin ke ai yana buƙatar uziri. Bazamu yanke hukunci ba yanzu ki bari zan sanarma Ammie to. Itama Amal zanyi magana da ita. Amma ko nan Daddyn su Barru shi goyon baya ya bada ɗari bisa ɗari, ya kuma ce in dai dan Daddy ne shi a barsa zaiyi magana da shi. Kinga an samu sauƙi kenan ai”.      “Shike nan ALLAH ya zaɓa mana abinda yafi alkairi.”     “Amin ya rabbi, wannan dama itace addu'ar daya kamata kiyi tun farko. Sannan dan ALLAH idan yazo ki daina ɗaɗɗaure masa fuskar nan taki, hakama idan ya kiraki kina ɗauka Auta. Wulaƙanci sam bashi da ƙyau”.        “Didi ba wulaƙantasa nake ba nima. Bana son ya saki jiki akan abinda bazai samu bane kawai”.     “Hummm Maanal kenan. ALLAH dai ya zaɓa mana abinda yafi alkairi”.     Maimakon ta amsa da Amin sai Maanal ɗin kawai ta koma ta kwanta dama tana a ɗakinta ne tana karatun novel ɗin nata na fama Shahidahn ta sameta........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖2️⃣0️⃣ ........Shahidah ta kira Ammie ta sanar mata da komai game da abinda RK yazo ma Maanal da shi. A mamakin Shahidah sai ji tai Ammie na maimaita kalmar Alhamdullah. Kasa daurewa tai ta ce, “Ammie kin amince kenan kema tayi aikin?”.      “Sosai kuwa Shahidah. Dan wannan wata mafita ce da masalaha UBANGIJI ya kawo mana. Ban sanar daku bane kawai amma tunda muka baro Abuja na dawo gidan nan a cikin cakwakiya ake da tashin hankali duk kuma akan batun auren Maanal da Yazeed ne. Namayi mamaki da kikace yau kusan kwana biyar bai leƙoku ba tunda yana Abujar shima.”      “Wlhy kuwa bai zoba Ammie, nama zata ko yana Kaduna ko yayi tafiya ne wani waje. Amma naga yana ƙoƙarin kiranta a waya yaji lafiyarta. Wai Ammie miya faru ko ɗaura musu aure kukai? Ko har yanzu Mamma ɗin ce ke tijarar bata son?”.     Ƴar dariya Ammien tayi da faɗin, “Kefa daɗina dake shirme Shahidah. Auren lafiya kuma yarinyata na a wannan halin na ciwo mai girma irin wannan hauka nake zan bari a mata aure bada amincewarta ba. Akan dai Hajiya Yaya ne da batun auren......”     Tsaf Ammie ta zayyanema Shahidah yanda komai ya faru da kuma matsayar da ake akai yanzu.         “Kai wannan mata ALLAH ya rabamu da masifarta Ammie. Ita dai ta sani mu ALLAH yasa haka shine mafi alkairi ma, dan wlhy garama ta auri Rafeeq ɗin amma haɗata kishi da wannan ƴar iskar yarinyar sangartacciya ai wani hatsarinne. Zasu iya haɗe kai su dinga cutar da ita watarana mu wayi gari zuciyar tata ta buga. Amma kinga Rafeeq ɗin nan wlhy Ammie yana da hankali da tarbiyya. Damma Maanal ɗin ce taƙi sakin jiki da shi kin dai san halinta”.        “Karki damu a hankali ne. Kudai ku cigaba da tayata da addu'a. Watarana ai sai labari. Amma in sha ALLAHU batun Yazeed kam nima bana mata fatansa kuma suje can su ƙarata. Yanzu ki bani zuwa gobe zan yi magana da Daddyn naku, idan ya tirje sai shi mijin naki ya masa magana ko naje Zaria na haɗashi da abokin nasa.”       “Shike nan ma Ammie wlhy dama haka kikayi”.     “A'a bari dai na fara masa magana dan bana son butsutsunsa. Yaya jikin autar?”.     “Alhamdullahi Ammie jikinta na ƙyau sosai. Dan naga har ta koma karance-karance novels ɗin nata na fama. Gata can ma tana shiri Abban Barru yace idan ya dawo zai kaita bookstore ta samo wasu”.        “To Masha ALLAH, ALLAH ya ƙara lafiya. Nima zan shigo na sake ganinta in sha ALLAHU zuwa next week haka komai ya ƙara lafawa.”    “ALLAH ya kaimu Ammie muna nan muna jiranki. Itama Amal tace next week zata dawo”.       “To shike nan idan naga zai mana dai-dai sai kawai mu taho tare, amma ni ranar zan dawo gaskiya”.     “Kai Ammie miyasa bazaki kwana ba?”.     “Daga dubiya sai kawai na kama kwana. Tunda ina jinku kullum a waya ai Alhmdllh ya wadatar, ba kuma sai na zauna na kula da tsohon mijina ba da ƙananun ƴaƴana”.    Dariya sosai Shahidah ta sanya. Daga haka sukai sallama.... ___________★         Kamar yanda Ammie taima Shahidah alƙawari ta tunkari Daddy da batun aikin Maanal. Sai dai kuma kamar fa yanda tai tunani ya nuna ɓacin ransa. Ya kuma tujareta da masifa dan dama yana riƙe da takaicinsu ita da Hajiya Basariyya a rai. Kasa magana Ammie tai sai duƙar da kanta kawai tai tana saurarensa. Sai da yay mai isarsa yay shiru dan kansa sannan ta tashi ta kwanta dan dama itace da shi a yau ɗin. Wasu irin hawaye ne masu zafi suka dinga rige-rigen sakko mata. Sosai tausayin kanta dana iyalanta ke ƙara girma a zuciyarta. A rayuwarta tayi farin ciki ne da samun ƴancin kai na shekarun ƙuruciya kawai. Amma tun daga randa aka lulluɓa mata zanen aure zata iya cewa daga lokacin ƘADDARARTA ta fara. Daga lokacin ta fara tantance gatan iyaye da ɗacin rabuwa da su. Daga lokacin komai ya canja, sunanta na Asiya sarauniya ya canja zuwa Asiya baiwa. Eh dole tace bauta, duk da a zahiri baza'a kalli rayuwar tata ata mai bauta ba kasancewar wasu abubuwa sun mata ado a bayyane. Sai dai wanda yasan ainahinta ne kawai zai san minene mizanin bautar da take magana da ƴancin kai. Ansha gwagwarmaya na tsawon shekaru kafin ALLAH ya iyakance, iyakancewar bai zama sauƙi ba kai tsaye, wata sabuwar jarabawar aka sake shiga, ta yanda zaren ƙaddarar ne ya kawota a wannan matsayin da take a yanzu kuma. Bazatai butulci ma UBANGIJI ba, domin kuwa Alhamdullah, ta samu canje-canje masu yawan gaske a sabuwar rayuwarta, sai dai anan ɗin ma ta gamu da wata jarabawar rayuwa a cikin mugayen kishiyoyi da kansu kawai suka sani......         “Asia! Kuka kike yi?”.     Furucin Daddy ya katse mata tunaninta. Da sauri ta saka hannu cikin dabara ta share hawayenta, sannan ta juyo garesa fuskarta da murmushi. “A'a Daddyn Hameed wane irin kuka kuma. Kawai dai na kwanta ne”.       “Humm Asia kenan, nasan kuka kike, kina kuka saboda kina ganin kamar na tauye hakkin ki dana ƴaƴank.....”     “Ya arrahaman”. Ta faɗa da sauri tana mai gaggawar ɗaura tafin hannunta a saman bakinsa. Zuuuu hawayen da take riƙewa suka shiga zirarowa. Kanta ta fara girgiza masa da sakin kukan gaba ɗaya. “Dan ALLAH kada kace haka Daddyn Hameed, ban taɓa raba ɗayan biyu a tsakanin su Maanal da sauran yaranka ba. Ni kaina inama mantawa bakai ka haifesu ba, saboda kana musu dukkan abinda uba kema ƴaƴa. Kana musu abinda mahaifinsu ya gagara musu. Taya zan kasance butulu waje rarrabe gaskiya da akasinta. Dan ALLAH ka gafarceni idan nayi kuskure, wlhy ban nema amincewarka ga Maanal tayi aiki dan baƙanta maka rai ba ko ƙasƙantar da dokar ka b.....”      “Shiiiii!! Ya isa kukan haka to”. Daddy ya faɗa yana mai jawota jikinsa ya rungume murmushi shimfiɗe a fuskarsa. A hankali yake shafa bayanta cike da lallashi. Tsahon minti ɗaya kafin ya furta, “Nasani Asia. Na kuma yarda dake ɗari bisa ɗari. Domin nasha gwadaki akan yaran nan batare da kin sani ba ke kanki kuma kina cinye jarabawar. Babu abinda zance dake sai godiya. Domin tabbas a cikin matana kina gaba a wadda nake alfahari da ita. Bance miki suma sauran sun gaza ba ko basu da martabar da nake kallonsu da ita ba. A'a ku dukanku kowa da inda yake tausasa min da kuma inda yake tsaurara min, amma kina da manyan lambar yabo kashi-kashi a gareni da bazasu lissafu ba Asia. Hakama su Shahidah, ni kaina biyayyarsu a gareni da girmamawa yakan sani manta ma bani na haifesu ba, ina jin alfahari da su, ina kuma godema ALLAH daya bani su matsayin ƴaƴana a yanzu. Ba aiki bane bana son Maanal tayi, domin nima na fahimci hakan zai taimaka mata ya ɗauke mata kewa musamman da nima nasan harkar zane-zane hubby nata ne. Kawai dai ina jin haushinki ne da tunanin baki son haɗa jini dani, shiyyasa yau ba fanshe haushin ta nan, sai nake ganin kamar baki son wannan haɗin da nake sonyi ne Asia. Alhalin ni kuma na ƙwaɗaitu ƙwarai da gaske da son ganin jinina ya sake gauraya da naki kozan cigaba da samun nagartattun zuria daga tsatsonki a cikin zuri'ata. Hakan zai sake dunƙulemu ya curemu waje guda. Tun akan Amal naso nayi wannan haɗin, sai na fahimci hankalin Yazeed akan Maanal yake shiyyasa na ƙwallafa raina a kanta.”        “Kayi haƙuri Daddyn Hameed sam ba haka bane kamar yanda kake tunani. Ka fahimceni dan ALLAH. Wlhy koda bana aurenka zan iya bama Yazeed auren Maanal. Domin ya taimakemu a gaɓar da muke matuƙar bukatar taimako. Zanma iya cewa ALLAH ya ƙaddara Manaal nada sauran kwana ne a duniya amma ya saka sanadin hakan a hannun Yazeed. Domin da ace kwannata ya ƙare tun a randa muka fara haɗuwa da sai dai wani zancen ake ba wannan ba. Dan haka ban taɓa jin bazan bama Yazeed Maanal ba. Kawai dai hankalina na matuƙar tashi kasancewar bakowane ɓangare bane ke buƙatar wannan haɗin, hakan kuma zai iya cutar da Yazeed ɗin kansa da ita kuma Maanal ɗin dake fama da rauni irin na ciwo mai haɗari. Amma yanzu masalahar da aka samu zai taimaka komai ya zama dai-dai itama ta samu sassauci haka shima Yazeed ɗin. Dan koba komai Hajiya Yaya mahaifiyace tana da tata darajar. Sannan Yazeed ya san komai daya shafi rayuwar Maanal, basai anyi sabon zama da zagaye-zagayen faɗa masa da fargabar zai amsheta ko zai canja ra'ayi”        “Hakane Asia. Na kuma fahimceki yanzu ɗari bisa ɗari. Zan kuma cigaba da addu'ar zaɓin ALLAH akan al'amarin insha ALLAHU. Sannan abinda ya shafeta ki daina wani damun a kansa kanki ai ƙaddara ce, bata wuce kan kowa ba kuma, ALLAH kuma shine shaida bataje takai kanta ba domin yin hakan jarabawace, wanda ma suke aikatawa kai tsaye ko suke zuwa bariki su kama ɗakin kansu suke auruwa cikin salama da kwanciyar hankali yanzu a ƙasar nan balle ita. Saboda haka na amince Maanal tayi aikinta. ALLAH ya sanya albarka ya kuma sa hakane yafi alkairi.”      Wani irin daɗi ne ya ratsa zuciyar Ammie. Ta ƙanƙame Daddy da ƙyau tana amsawa da amin. Shima murmushi ya saki mai faɗin gaske da karɓarta sosai ya rungume. A ransa kuwa yana sake ganin fara aikin Maanal ɗin wata masalaha ce. Dan zai fake da shi bayan anyi auren suyi zamansu acan, ita kuma wannan zaɓin uwar Yazeed ɗin anan cikin gidan yake son ta zauna tare da su saboda wasu dalilansa......       Tofa, mi kuke tunanin wai ya faru da Maanal ne?🥺. Sannan zamuga yanda wannan cakwakiya zata ƙare😂🏃. __________★         Wani irin farin ciki ne ya mamaye Maanal lokacin da saƙon Daddy ya risketa akan amincewarsa tayi aiki. Su kansu su Shahidah sai da suka tsaya suna kallonta ganin yanda taketa murmushi yau kamar ba Maanal ba. Sai suma hakan ya sakasu a farin ciki. A karo na farko na tarihi Maanal taima RK text massage da albishir ɗin amincewar Daddy. Ai ba'a haɗa awa guda ba sai ga bawan ALLAH a gidan. Yau ko lallaɓatan da Shahidah keyi na taje ta samu RK ɗin ba'ai ba. Yana kiranta yace gashi a gidan sai gata babu jimawa ta fita. Tunda ta fito ya zuba mata ido, sai ya zam tana takune tamkar da bugawar zuciyarsa. ALLAH ya jarabcesa da son wannan halittar ƙwarai da gaske. Yana kuma fatan mallakarta in har hakan shine alkairi a garesu. Maanal ta tsani kallo, dan haka sai da ta masa tsogumi akan kallon ƙurillar da yake matan. Baice komai ba face basarwa yana sakin murmushi. Itama sai ta sharesa kawai ta shiga gaishesa. Ya amsa mata da kulawa, kafin ya ɗora da tambayar yanda abubuwa suka kasance. A taƙaice ta faɗa masa, bai damu ba dan ya gama karantar ta zuwa yanzu. Bata da son yin doguwar magana sai idan itace taso hakan da kanta. Shine ya dinga zuba mata zance da yanda abubuwa zasu kasance. Ya kuma tabbatar mata nan da kwana biyu zaizo ya amshi takardunta. Ya kuma buƙaci ta ɗan zazzana wasu samples na agogunan zaizo ya amsa gobe idan ALLAH ya kaimu dan zai sake nunama mai Companyn. Duk da dai ya nuna masa wanda ta zana a asibiti. Ta tabbatar masa babu damuwa zatayi ɗin, daga haka sukai sallama ya fice ita kuma ta shiga gida.       Kamar ko yanda sukai alƙawari a wannan daren ta nutsu ta zana agoguna masu shegen ƙyau da ɗaukar hankali fin kala goma. Dan har gabannin asuba tana wannan aikin. Hakan ya saka mata makara. Tana yin sallar asubahi kuma ta sake kwanciya. Bata farka ba sai ɗaya saura. Ta samu RK yazo ya amshi zanen ma. Dan sun sanar masa tana barci yace kada a tasheta a barta tai barcinta, a bashi zanen kawai. Yana kuwa amsa bai jima ba ya wuce abinsa. Sai da ta tashi take jin yazo ɗin ya amsa. Har ta ɗauka waya kamar zata kirashi sai kuma dai ta fasa kawai. Tata tsumayen nasa kiran amma shima sai bai kira ɗin ba har dare. Sai da tana shirin kwanciya ne ma saƙonsa ya shigo.         _“Ina Kaduna yanzu haka. Mun gana da Daddy da Ammie, na kuma amso takardunki suna hannuna. Amma sai da safe zan dawo Abuja in sha ALLAHU. Kiyi barci cikin aminci tare da mafarki mai nutsuwa gimbiyar mata”_.      Baki kawai ta taɓe tare da jefa wayar saman gado ta cigaba da saka maɓallan rigar barcinta. Sai kuma ta tsaya cak kalamansa na dawo mata. Ya gana da Daddy da Ammie kamar yaya? Kai itafa shishshigin mutum nan ya fara bata tsoro. Kaji bala'i ko mi ya kaisa Kaduna?. Rashin mai bata amsa ya sakata jan ƙaramin tsaki ta haye gadon kawai ta kwanta. Addu'a tayi kamar yanda ta saba sannan ta kashe wutar ɗakin tana sauke ajiyar zuciya.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖2️⃣1️⃣ .......Maanal bata sake jin labarin RK ba tun ranar. Ya dai kirata washe gari yace ya dawo Abuja. Daga haka bata sake jinsa ba. Gashi ita kuma ta ƙagu taji yaya ake ciki. Dan haka kawai sai ta ƙwallafa ranta a aikin saboda zaman waje ɗayan kuma ya isheta. Da yaran Shahidah sun wuce makaranta itama da mijinta duk aiki suke fita, sai ita sai mai aiki kawai. Bata da aiki sai karatun novels da kwanciya. Amma kasancewarta sarkin kamewa da dakiya sai bazaka taɓa fahimtar hakan ba kai tsaye. Sati ɗaya dayin hakan sai ga Ammie da Amal sunzo. Matuƙar farin ciki Maanal ta kasance a wannan ranar, gashi weekend ne duk masu gidan suna nan. Yini sukai dan Ammie tace bazata kwana ba. Babu irin shagwaɓar da Maanal bataima Ammie akan ta kwana ɗin ba amma tace sam ita bata sanarma Daddy zata kwana ba. Haka babu yanda zasuyi bayan magrib suka rakasu train station kasancewar jirgin ƙasan zasu bi. Dama a cikinsa suka zo....       Kwanakin su Ammie biyar da zuwa da daddare tana shirin kwanciya sai ga kiran RK. Ido kawai ta sakama wayar tana kallo harta tsinke sannan ta kauda kanta. Sake kira akayi nan ma kamar bazata ɗauka ba sai kuma dai mita tuna oho mata tai yunƙurin ɗaukar, sai kuma taga bashi ɗin bane Ya Yazeed ne. Fuska ta ɓata shima kamar bazata ɗaga ba ta dai daure ta ɗauka. Gaisheshi ta farayi da girmamawa kamar yanda ta saba. Shi kuma ya amsa mata cikin nutsatstsiyar muryarsa dake nuna alamar a kwance yake. Sun ɗan yi shiru sai kuma ya katse shirun da faɗin, “Ina muka kwana akan batunmu Maanal?”.       Shiru tai kamar bazatace komai ba. Sai da ta mula dan kanta ta amsa masa da, “Yaya ni mikake son nace to. Ni duk abinda su Daddy suka yanke zanyi biyayya a kansa kawai”.     “Saboda dama baki sona?”.   “Ni dai Yaya bance ba. Amma ka tausaya mun mana. In dai kai namiji ka haƙura ka musu biyayya ni kuma sai naje nace ba haka ba.”       “Humm shike nan, amma ke yanzu baki jin kishin na fara auren wata kafin ke?”.      Karan farko ta saki murmushi mai faɗi, sai kuma ta zame ta kwanta. “Yaya ko naji kishi yaya zanyi. Ni dan ALLAH mubar ma maganar nan kawai ALLAH yasa haka shine yafi alkairi”.      Murmushi taji ya saki da ga can, sai kuma ya ce, “Okay shike nan an barta. Tunda dai na gane ana kishina na gode”.     Shiru ta masa batace komai ba. Shima daga haka yay mata sallama akan maybe gobe ma ya shigo Abujan,  zai kuma leƙo ya fara ganinta kafin ya fara sabgoginsa. Daga haka sukai sallama. Kamar jira RK yake dama, Yazeed yana yankewa kiransa na shigowa shi kuma. Sai yanzu ma ta lura ya mata kira yafi goma ashe sanda take wayar. Kanta kawai ta ɗan girgiza. Sai da tana gab da zata tsinke sannan ta ɗaga. Muryarsa a cinkushe ya mata sallama. Amsawa tai itama ciki-cikin tai shiru. Tsahon minti ɗaya babu wanda ya sake magana.        “Oh bama zaki gaisheni ba?”.     RK ɗin ya faɗa daga can. Yitai kamar bazata tanka masa ba sai kuma ta ce, “Good evening”.      “Humm good evening to baturiya. Fatan kin yini lafiya?”.    “Lau”. Itama ta amsa masa a daƙile jin yana mata magana cikin wani ji da kai.           “Humm! saboda kina waya da wannan tsohon tuzurun saurayin naki da baya dariya shine kika shareni.”     Ita dariya ma zancen nasa ya bata. Amma sai bata dara ɗin ba ta ce, “Hummm ashe kaima tsohon tuzurun ne tunda ba girmarka yay ba”.     “Oh zaki shigar masa faɗan ne kenan?”.     Shiru ta masa taƙi tankawa. Shima sai ya saki zancen kawai. Amma ransa fal kishin Yazeed ɗin. “Baki da kirki ALLAH, kwana kusan goma baki jini ba amma baki neman ba. Wannan wace irin soyayya ce?”.      “Kai dai ka sani. Rashin jinka kuma ai nasan lafiya ce ke ɓuya”.     “Humm borin kunya, ALLAH dai ya shirya min ke. Duk da baki tambaya ba bara na faɗa miki. Auntyna ce bata da lafiya a randa na dawo Kaduna da yamma jikin ya tsananta, dole mukai gaggawar barin ƙasar da ita. Tashin hankali yasani manta wayar da number ɗinki ke ciki. Jiyan nan muke dawowa”.           A hankali Maanal ta sauke numfashi da faɗin, “ALLAH sarki, ALLAH ya bata lafiya yasa kaffara ne. A wace anguwa take?”.    “Amin ya rabbi nagode sosai. Zakije dubata ne kike tambayar anguwarsu?”.     “Ina ruwanka to. Kai dai ka faɗa min mana”.    Murmushi yayi daga can har tana iya jin fitar sautinsa. Sai kuma ya ce, “Okay ba damuwa zan tura miki address ɗin. Sai dai kuma yanzu ma na kiraki ne akan batun aikin can. Sun buƙaci ganinki, sai ki shirya gobe idan ALLAH ya kaimu kamar around eleven thirty haka zanzo na ɗaukeki”.       Wani irin sanyi ne ya tsargama Maanal. Amma sai ta danne cikin dakewarta ta ce, “Miyyasa bazaka bani address ɗin ba kawai naje da kaina”.       “Kina tsoron na saida ki ne?”.   “Ai nasan nafi ƙarfin siyarwa”. “Hhhh haka dai kikace. Bari na barki ki kwanta lokacin barcinki na wucewa. Sai nazo”.     Daga haka ya yanke kiran kafin tace komai. Murmushi ta saki itama, ta jima da fahimtar bayan naci RK ɗan rigima ne na bugawa a jarida. Sam daga ganinsa baya jin magana. Bazatace tana sonshi ba. Amma wasu abubuwa nashi sun ɗan fara birgeta kaɗan. Fasa kwanciyar tayi, ta tashi ta ɗauro alwala ta hau nafilfilin neman nasara da zaɓin alkairi akan wannan aiki. Duk da dai dama tunda aka tsira zancen taketa gayama ALLAH. Tayi raka'a biyun farko ta sallame ta ɗauki wayarta ta turama Ammie text. Tasanta bata wasa da ƙiyamullaili, kusan za'ace ma ita suka gado dan tun suna yara tai musu wannan horon na ibada. Kuma Alhamdullah su dukansu sun horu da wannan tarbiyyar tata. Dama itace mai ɗan raunin cikinsu lokacin tana a ganiyar rashin ji. Amma yanzu Alhamdullah kam komai ya sauya kamar yanda jiyanta ta zama tarihi mai ciwo da raɗaɗin tunawa agareta.....       *_WASHE GARI_*   Da safe ta sanarma Shahidah da mijinta komai. Sun tayata murna da fatan alkairi suma. Ta kumayi waya da Ammie da Daddy dan itace da shi jiya da yau. Hakama Amal. Bayan wucewar su Shahidah nasu ayyukan itama tai nata shirin. Kasancewar ta mai jinkirin shiri yasa ten nayi ta fara shirin nata. Sai ya zam kafin eleven ma tayi ta gama komai duk dama bawani shiri bane na'azo a gani. Amma tayi ƙyau sosai cikin Abaya ƙirar saudia baƙa. Daga ciki ta saka wandon jeans blue mai duhu da farar riga datai mata ƙyau. Ɗan kwalin abayar kawai tai rolling a kanta ta saka turare mara ƙarfi bayan na wuta da kayanta keyi dama jikinta gaba ɗaya da yuni gyara yasa ƙamshi ya kama. Sai ƴan tarkacenta data haɗa a hand bag ɗinta sannan ta fito. Kitchen ta shiga ta saka ruwa a ƙyaƙyƙyawar bottle water ɗinta ƴar zamani sai ta ɗan saka Linda ta daka mata snacks da basa rabo da shi a gidan kaɗan wai ko taji yunwa. Dan ta tsani sayen abincin waje a rayuwarta. Shiyyasa da wahala kaga Maanal ta fita anguwar data san zata yini babu wani abin ci a tare da ita. Tun Ammie na faɗa har ta saka mata ido ma. Falo ta dawo ta zauna kasancewar akwai sauran mintuna ashirin, sai kawai ta buɗe novel ɗinta ta cigaba da dubawa. Tanayi tana ɗan cin shawarma ɗinta guda ɗaya data ɗakko da drink a kofi. Batafi mintuna goma a wajen ba kira ya shigo wayarta. Ƙaramin tsaki taja a ranta tana addu'ar ALLAH yada ba Yazeed bane ba. Numfashi ta ɗan sauke ganin RK ne. Sai da ta kalla agogo sannan ta ɗaga. Yau dai bai roƙaba ta gaishesa. Sai shi kuma batare daya amsa ba yace ta fito gashi a waje. Sake kallon agogo tayi da mamaki ta ce, “Akwai fa sauran ten minutes”.      “Oh kona koma sai ya cika na dawo?”.     “Humm”. Ta faɗa kawai tana yanke wayar. Linda ta ƙwalama kira. Da sauri sai gata tana faɗin, “Yes Aunty kina bukatar wani abu ne?”.        “No Linda zan wuce ne dai. Dan ALLAH ki kula sosai da gidan duk da dai nasan kina ƙoƙari dama. Ai baki manta ba dai Didi tace kima Uncle tuwon shinkafa ko?”.     “Eh aunty ban manta ba har ma na ɗora”.     “Yauwa to yayi, sai su Barrah kuma kisaka musu white rise kin san bazasu ci tuwon nan ba. Tunda akwai stew a fright kema kin huta kenan. Nima na wuce sai na dawo”.        “To aunty, ALLAH yasa ayi nasara. Amma ke baza'a miki komai ba?”.     “No Linda na huttashsheki kinji, bamma san ni sanda zan dawoba. Komai na dawo na samu a gidan zanci bye”.     “Okay bye bye”.            Tunda ta fito ya wani zuba mata idanu ko ƙyaftawa bayayi kamar yanda ya saba. Bashi kaɗai ba kowa na faɗa a zuciya ko'a fili Maanal ƴar gayu ce gata kuma ƙyaƙyƙyawa. Ko bada kwalliya ta saka kaya ba zakaga sun mata ƙyau. Balle kuma ace tayi kwalliyar ai abin sai wanda ya gani. Gata dai ba fara ba, amma da wahala namiji ya kalleta bai sake mata kallo na biyu ba duk ustazancinsa da kamewa. Badan tafi sauran mata ƙyawu ko wani abu ba, a'a itama kamar kowacce mace take, kuma komai nata irin na kowacce mace ne. Sai dai yanayinta na kamewa da ɗaure fuska kan taka musu birki wajen yimata magana ko fuskantarta kai tsaye. Sam bata da sakewa da mutane, sannan bata da yawan fara'a ko magana sai a inda taso yi ko ga wanda taso yimawa....       Sai da ta tsaya a gabansa ta ɗan yamutse fuskarta da babu walwala sam. Dan bata son kallo sam, ko yaya ake kallonta takan tsargu taji a jikinta, shi kuma taka kallo ɗabi'arsa ce. Yanda take faman yamutse fuskar da sake ɗaureta ya sakashi sakin murmushi da warware hannunsa daya harɗe a ƙirjinsa. Sai kuma ya ɗan furzar da iska mai nauyi a bakinsa yana sake zuba mata idanun. “Wannan ɗaure fuskar fa? Ko duk laifin rashin cikar lokacin ne?”.          Maimakon amsa masa zancen nasa sai kawai ta basar tace masa, “Ina kwana?”.        “To lafiya ba ƙalau ba”.    Kamar zata sharesa sai kuma ta ɗan kallesa. Fuska ya marairaice mata kamar wani ɗan yaro. Janye idanun nata tai kawai. Shima sai ya saki murmushi. Ƙofar motar ta buɗe mata yana faɗin, “Bismillah”. Komai batace da shi ba ta shiga. Shima ya zagaya nasa ɓangare ya shiga. Motar yayma key suka fice a gidan. Sai da sukai ɗan nisa a tafiya ya kalleta kaɗan ya maida hankalinsa ga titi. “Nace miki ina lafiya amma ba Lau ba, baki tambayeni mike damuna ba?”.       Hankalinta na'akan novel ɗinta ta amsa masa da, “Ai banga alamar ciwo a tare da kai ba. Nasan neman maganarka ne”.       “Oh oh, ni Rafeeq bin Kasheem. Ni har wani neman maganane da ni kuma?”.     “Humm”. Kawai tace a taƙaice. Shima sai ya murmusa yana mai jinjina miskilancin yarinyar nan. Bai sake cemata komai ba sai zuwa can a bazata yaji tana ce da shi “Yaya jikin Aunty?”.        Har cikin rai yaji daɗi, dan haka ya amsa mata fuskarsa ƙawace da murmushi. “Jikin Aunty babba Alhamdullah. Duk da dai yau ban leƙata ba sai zuwa anjima. Da ƙyar ma na kuɓuto kaina a asibiti dan na zo na kaikin nan.”     “Ai sai da nace ka barni naje kawai”.    “Bazan iya hakan ba ai. Shi abu mai daraja killacesa ake. Kaffa-kaffa da shi kuma akeyi. Fatana ma na samu na ɓarar da waccan gwamnatin data tare min ko'ina. Sai kuma nayi sakaci wasu ƴan bani na'iya su shigo neman hanyar min kutse?. Ko baki yarda ba”.         “Kaima kasan mi kake nufi”.     “Ki rantse kema baki sani ba?”.   Shiru ta masa. Dan tama gaji da surutun. Yasa ko fahimtar labarin batayi ma. Sun iso katafaren comyanin *_MAWAAD_* daya tsaru da gini na zamani. Gashi babba sosai ta yanda hasashenta bai taɓa hasaso mata ba. Yanda aka tsara ƙaton harabar wajen da furanni koraye da jajaye harma da wasu kalolin abin ƙayatarwa, ga kwalta lafiyayya shimfiɗe. Hatta ababen hawa na ma'aikata an fakasu ne cikin tsari da birgewa. Bawani hauma-hauma ko hayaniya. Sai securitys dake kula da tsarin shiga da fitar kowa a wajen hatta cikin harabar. Dole ne wajen ya birgeka, dan duk iyayin mutum idan yazo *_MAWAAD COMPANY_* sai tsarinsa ya birgeka..........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖2️⃣2️⃣ .........“Ya kikaga companyn?”. RK ya katse mata tunaninta. Ɓoyayyar ajiyar zuciya ta saki tare da juyowa ta ɗan kallesa. Ganin shima ita ɗin yake kallo sai ta ɗauke kanta kawai. Cikin ɗan yamutse fuska ta ce, “Balaifi komansu da tsari gaskiya. Sai dai ina fatan ba ƙawar gini bace kawai”.     Dariya ya ɗan yi a taƙaice. Ya ce, “Maanal bari na baki a buɗe, Mawaad Company ko kamfanin Rolex bazasu nuna masa yatsa ba a ɓangaren agogo. Basa ɗaukar ma'aikaci sai wanda yasan abinda yake yi. Sannan babu zancen sai ɗan wane ko sanayya, akwai turawa ma'aikata anan tun daga Chinese harma da Europe da sauran ƙasashen baƙaƙen fata. Komansu da ƙa'ida da doka yake tafiya. Kayansu ba kayan yara bane, manyan sarakuna da attajirai ke iya sayen kayansu a kowacce kusurwa ta duniya, tunda kikaga turawan nan da larabawa na tururuwar amfani da agogunan Mawaad ai ba sai na cigaba da cewa komai ba. Barama dai na daina cewa komai, ke da kanki zakizo kina bani labari watarana in sha ALLAHU. Abinda nake so dake dai ki nutsu wajen interview nan. Dan harda boss ɗin companyn da kansa za ai miki ita, ina nufin CEO na companyn. Duk da dai nasan banda matsala dake in sha ALLAHU. ALLAH ya bada sa'a da nasara idan alkairi ne. Muje na rakaki har ciki. Zan jiraki har ki kammala sai muje ki duba Aunty babba ko?”.         “A'a ka koma wajen aikinka kawai ba damuwa. Idan na gama zan koma da kaina. Tunda bamu san yanda abin zai kasance ba. Duba Aunty kuma basai ka kaini ba zanje da kaina ne”.      “Hummm” ya faɗa fuskarsa ɗauke da murmushi. Daga haka suka fito a tare. Idan ka gansu dolene su birgeka matuƙa. Dan sun dace da juna. A jere suke tafiya cikin tsari da nutsuwa. Dan shima RK dai-daita tafiyar tasa yay data Maanal duk da kasancewarta mai sanyin tafiya da tsantsar nutsuwar iya taku. Sam bata da hauma-hauma ko garaje a tafiya ita. Sun tsaya a haɗaɗɗiyar ƙofar wajen data kasance ta zallar gilashi, koda yake bama ƙofarba shi kansa ginin akwai gilashi sosai a cikinsa shiyyasa ya zauna da ƙyau kaikace ba'a Nigeria kake ba a wata Chaina ce can dan sune mayu. Sai dai kuma a cikin Abuja wannan ba komai bane kasancewar akwai gine-gine na ƙawa da ƙasaita da sukafi Mawaad Company komai ma. Duk da sanin da securitys ɗin ƙofar sukaima RK sai da ya saka I'd card ɗin aikinsa akan wani computer sannan ƙofar ta buɗe masa da kanta. Ya gaisa da securitys ɗin idanunsa akan Maanal datai kicin-kicin da fuska. Juyawa yay ya musu ɗan taƙaitaccen bayani a kanta. Cikin gamsuwa suka shiga jinjina masa kai...         (Eh lallai ashe kallo na daga ciki) cewar Maanal a zuciya. Dan kuwa tabbas Companyn nan ya ginu da iya nasa tsarin da ƙawa. Sun fara iske reseption, anan suka tsaya suka saka sunansu sukai signing kamar yanda tsarin Companyn yake ga baƙo ga ma'aikaci, kafin ma'aikatan dake a floor na farko, zamu iya cewa wani department ne anan na sashen Companyn, duk sun duƙufa aiki, yayinda wasu ke faman kai kawo da uzirin gabansu daya shafi aiki. Tunda suka shigo wasu ke kallonsu, wasu na zungurar wanda basu gani ba, yayinda wasu ke ƙuskus, wanda ke ɗan kusa da su kuma na gaishesu. RK kaɗai ke amsawa, Maanal kan ɗan jinjina kanta kawai itadai tana mai kallon komai. Daga haka suka isa ga elevator, shi ya danna ta buɗe, ya mata nunin ta fara shiga sannan shima ya shiga. Shine ya sake daddana number floor ɗin da zasuje sannan ya matso kusa da ita yana magana a hankali. “Kin fara ganin yanda tsarin yake ba?”.      Maimakon amsa masa da baki sai ta ce masa, “Uhmm”. Kawai, dai-dai nan suka iso inda suke son zuwa. Sai da ta gama buɗewa suka fito. Sun samu matashiyar budurwa ɗauke da files a hannu zata shiga elevator ɗin. Tana ganin RK ta saki ɗan murmushi da faɗin, “A'a ashe shiyyasa yau garin kamar da hadari, ashe babban baƙo ne damu a Mawaad”.     Murmushi yay mata da amsa mata da, “Kedai masheranciya ce Labibah. Ykk ya aikin?”.      “Babu wani sharri sai gaskiya. Aiki gashi nan muna ciki. Nikuma ina lafiya”.      “To Masha ALLAH. Iji dai boss na nan?”.     “Humm zaune kuwa. Kasan baya wasa ai sai da dalili ko zai leƙa office ɗin gwamnati. Yanzu naga ya dawo dan ya shigo da safe sai kuma ya fita.”     “Okay, to bari mu ƙarasa”.   “Babu damuwa. Sis.. barka tunda shi ya kasa gabatar min dake”.    Karan farko Maanal data ɗauke kai daga garesu ta ɗan juyo ta kalleta. Hannu ta bata kawai alamar suyi musabaha batare da tace komai ba. Sai shine ya ce, “Labibah bazaki taɓa canjawa ba. Da kinyi haƙuri ai zanzo da ita har office ɗinki ne idan na gama da boss”.     “Ato shike nan babu damuwa kuje. Nima zanje office ɗin CMO ne”.   “Okay tom ba damuwa sai mun fito”.   Daga haka ta saki hannun Maanal ta shige elevator ɗin su kuma suka wuce. Office ɗin Assistant ɗinsa shine farko kafin na boss dake ciki. Ya tarbesu da girmamawa alamar akwai sanayya tsakaninsa da RK ɗin sosai. Dan RK ɗin yata tsokanarsa kafin yace masa bari ya sanarma boss ɗin zuwansu. Ita dai Maanal hankalinta ma nakan ɗan bin Office ɗin da kallo. Komai tsaf kuma ƙal babu wani tarkace ko hayaniya. Baifi mintuna huɗu ba ya fito yana sanarma RK oga yace ya shiga shi kaɗai. Murmushi kawai RK yay da ɗan girgiza kansa. Kafin ya matsa inda Maanal take zaune dan shi  dama yana daga tsaye ne.     “Kinga ina zuwa. Minti biyar kawai”.    Kanta ta jinjina masa batare da nuna damuwar da yay tsoro ko ɓacin rai daga fuskarta ba. Daga haka ya wuce ita kuma ta ciro novel ɗinta daga bag ta cigaba da karatunta. Shima Assistant ɗin barin Office ɗin yay da alama akwai inda zaije. Kusan mintina huɗu sai gashi ya dawo. Mazauninsa ya koma ya zauna bayan ya ajiyema Maanal ruwa da lemo. Baice mata komai ba itama batama kulashi ba balle kallon abinda ta ajiye. Tana nan a zaune fin mintuna goma sannan RK ya fito. Zama yay a kusa da ita yana bata haƙurin daɗewarsa. Cikin nuna rashin damuwa ta ce, “Ba komai”. Ta maita hankalinta ga book ɗinta. Shima dai wayarsa aka kira, dan haka ya miƙe ya fita aka sake barinta ita da Assistant. Suna nan a haka wani ɗan abu dake desk ɗinsa yay ƙara, miƙewa taga yayi ya nufi hanyar officer ɗin ogan kamar yanda suka faɗa. Bai wani jima ba ya dawo, cikin mutuntawa yace mata ta taso suje. Littafinta ta saka a bag ta miƙe batare da tace dashi komai ba. Ta wani elevator ba wanda suka shigo ita da RK ba suka shiga da Assistant ɗin, cikin sakanni ya saukesu inda suka nufa, koda suka fito nan ma sai taga offices ne a wajen. Sun shiga wani waje da alama ta nuna conference room ne, sai dai bai ƙarasa da ita can ciki ba ya nuna mata wajen zaman daga nan ta inda aka shirya kamar masauƙin baƙi. Tana zama wata ta kawo kofin coffee ta ajiye mata da drink. Atare suka bar wajen ita da Assistant ɗin sai ita kaɗai kenan. Babu abinda ta taɓa ta sake ciro novel ɗinta ta cigaba da karatu......       Fin tsahon mintuna talatin tana a wajen babu wanda ya sake zuwa, har ranta ya ɗan fara sosuwa sai ga wasu mutane uku sunzo sun gittata sun shiga conference room ɗin, tsakanin inda suka bin da inda take akwai ƴar tazara, shiyyasa bata wani shaida kowa ba. Bayan shigewarsu fin mintuna biyar wasu biyu suka sake wucewa, kasancewar bata ɗago ba a yanzu sai da suka gama shigewa taji motsin rufe ƙofa. Ƴan mintuna kaɗan Assistant ya zo wajenta yace ta shiga. Kanta kawai ta jinjina masa tare da maida book ɗinta a bag ta miƙe. A ranta tana mamakin wannan abu kamar wulaƙanci, ana tattalin ɗaukar ma'aikaci da alama su nan yanga sukeyi. Da wannan tunanin ta tura glass door ɗin a hankali ta shiga da sallamar da bata tunanin zasuma iya jinta saboda yanda ta yi ta ciki-ciki, dan wani irin bugawa ziciyarta ke mata da sauri-sauri da batasan dalili ba, amma haka ta danne tana ƙarama zuciyar tata ƙarfi. Sai dai kuma da alama sun ji sallamar tata ɗin, dan wasu a cikinsu sun amsa. Taji hakan ne a bayyane dan ba kallonsu take ba su duka. Sai da ɗaya a cikinsu ya furta, “Bismillah zaki iya zama”. Sannan ta ɗan ɗago ta kallesu tana mai jinjina kanta zuciyar tata dai na cigaba da bugu.       Mutane ukun dake fuskantar inda zata zauna kawai ta iya ma kallo cikin sakan biyu. Wanda ke zaune kuma a kujerar dake gefen inda take bata ko kallesu ba. Sai kujerar dake tabbatar da oga kan zauna yayin meeting shima bata wani dubesa ba. Shima kuma kansa a duƙufe yake yana duba wani magazine kamar ma bai san da zaman kowa ba a wajen. Kujera ɗaya taja ta zauna zuciyarta na mamakin ai mutane biyar kawai taga sun shigo, ya akai taga kusan takwas anan?, rashin mai bata amsa ya sata shiga gaidasu. Amsa mata duk sukayi, sai dai bata jin shi wancan ya amsa ɗin. Shiru kamar na mintuna biyu kafin ɗaya a cikinsu ya fara mata tambaya. Babu ko ɗar a tare da ita ta amsa masa. Kansa ya jinjina sosai dukansu suna mamakin ta. Wanda ke tsakkiyar sa shima ya sake jeho mata tasa tambayar. Nan ma ta sake amsawa babu ko wani ɗar. Dukansu kam sai da suka sake dubanta wannan karon saboda jarumtarta da kaifin basira da suke kallo a bayyane, sai dai abinda basu sani ba dannewa kawai takeyi, dan tana cikin wani hali da ita kanta ta gagara bashi fassara. Gashi a masu mata interview ba wai baƙaƙenmu bane balle ma ace hausawa. Hausawa biyu ne ma kawai a cikinsu sai CEO ɗin da har yanzu bataga fuskarsa ba. Amma dai hannunsa dake saƙale da wani shegen Designer agogo da zoben dake neman harmutsa tunaninta na azurfa ya nuna bakin fata ne duk da kallon fisha tai masa kawai.    Na ukunne da baice komai ba tun ɗazun a yanzu cikin turancinsa mai fita da harshen Chinese ya furta “Woow, You are amazing young lady”. Sai kuma ya shiga tafa mata. Suma sauran tafa matan suka farayi suna mai kallon boss ɗin nasu da har yanzu bai tanka ba baima maida hankalinsa a kansu ba yanata duba magazine ɗinsa hankali kwance. Ganin dai bashi da niyyar kulasu suka haƙura suka daina. Sun bata takarda da kayan aiki tai zanen agogo a take anan, zanen da yay mugun basu mamaki da ƙaryatar dasu. Daga haka File suka tura mata da mata bayanin zata cike tai singing a take anan. Bata musa ba taja file ɗin gabanta. Ta ɗan dudduba abinda ke cikinsa kafin ta shiga gudanar da dukkan abinda suka buƙata zuciyarta na mata wani irin sanyi ƙalau dan kuwa dai sun tabbatar mata da ɗaukarta aiki ne. Acan ƙasan ranta kuwa tana mamakin nasu tsarin. Daga interview a take a wajen kuma babu batun kaje ka jira sai a tabbatar maka da an ɗaukeka aiki. Haka dai ta gama cike komai tana zancen zucinta ta basu. Bayan sun dudduba suka miƙama ogan nasu da sai a yanzu ya ajiye magazine ɗin ya fara duba file ɗin.      A karo na farko oga kwata-kwata da yay kamar bashi nan a wajen ya ɗago kansa bayan kammala duba komai na file ɗin, cikin wani irin dakewar murya ya jeho mata tasa tambayar data tilastata kallonsa. A yanzu ba bugun zuciya kawai taji ba, zuciyar tatace gaba ɗaya zata iya cewa ta tarwatse a dalilin kallon ido cikin ido da sukaima juna. Suma, ɗaukewar numfashi, ko gushewar hankali ko tsatstsagewar zuciya batasan yanda zata kira yanayin data tsinta kanta a wannan lokacin ba ma.........✍️     _Tofa jama'a mi kuma ke shirin faruwa anan?. CEO na Mawaad Company da Maanal? Kumuje zuwa wasan na ainahi ma yanzun ne zai fara a duka ɓangarorin😆 in sha ALLAHU 😉👌_. ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖2️⃣3️⃣ ........Fin mintuna biyu sunama juna kallon tsakkiyar idanu babu ko ƙyaftawa, yayinda sauran sukai kasare suma suna kallonsu da mamaki. Da wani irin shegen salo CEO ɗin nasu ya juya mayan oily ayes ɗinsa masu matuƙar haske kamar madara dake cikin haɗaɗɗen siririn farin gilashi tas tare da kauda fuskarsa gefe yana mai furzar da wani irin huci. Sai kuma ya sake dawo da idanun nasa a kanta cike da barazana da isa da basarwa ya furta, “Miss Maanal! Answer my question”.     Duk da cikin nutsuwa da sassanyar murya yay furucin, sai Maanal ta dinga jin kalaman ɗaya bayan ɗaya suna mata wani irin amsa kuwwa da tartsatsi a cikin kunne, acan kuma sama ƙololuwa. Ga wani irin sanyi yana saukar mata a gaɓan jiki da ƙasusuwanta tamkar yanayin yammaci ko safiya a lokacin tsananin hunturu irin na ƙarshem Janairu ɗin nan.         “You are not serious Miss Maanal”. Ya faɗa cikin gizago da nutsatstsen sauti mai cike da aji yana mai ɗan buga desk ɗin da yatsunsa biyu. Firgigit Maanal ta dawo a hayyacinta tamkar wadda aka farkar da ga barci. Sai dai har yanzu sanyin nan na cigaba da ratsata tun daga saman kai har yatsun ƙafafu. Sam bata san ta yanda akai ta buɗe lips ɗinta cikin dakiya da tarin nutsuwa ta bashi amsar tambayar tasa ba. Har lokacin kuma idanunsu na a cikin na juna. A karo na biyu shine ya sake kauda kansa. Sai kuma ya ɗan yamutse fuska da ɗaureta yana maida hankalinsa a kan sauran da sukai jugum-jugum suna kallon ikon ALLAH. Duk da kuwa wannan ba sabon abu bane a wajensu. Ƴammata da yawa a cikin Companyn nan sun jima da mutuwa akan boss ɗin nasu. Hakama masu shigowa domin bussines suka shiga fiye da irin yanayin da Maanal ta tsinta kanta a yanzu. Bakuma wai dan ogan nasu yafi sauran maza bane, badan yafi kowa ƙyau da iya ado bane, badan yafi kowa dukiya da cikar kamala bane. Kawai dai ALLAH ya bashi farin jini da wani irin kwarjini da ko su kansu mazan yana cika musu waje duk da kasancewarsa yaro matashi da bai wuce 30+ ba a duniya. Boss ɗinsu nada wasu qualities da mata da yawa ke buƙata a tattare da mazan zamani na wannan ƙarni. Duk da dakewarsa da kamewa da ƙasaita hakan bai hana ƴammata kawo masa hari ta kowacce kusurwa ba. Koda yake kuɗi fa babu abinda basa saka matan wannan zamanin, kai Bama mata ba kowafa a wannan ƙarnin ya koma girmama matsayin bawa da abinda ke a hannunsa ne kawai. Sai kana motsi akeyi da kai, sai ka zama wani ake girmamaka da son raɓarka. Da zarar baka dasu ko sun bar hannunka sai kaga kowa ma ya janye jikinsa an zubar da kai a kwandon shara saboda dama can ana maka soyayya da girmamawar ne saboda kana amsa sunan wane....       Miƙewarsa ta saka tunaninsu katsewa. Document ɗin ya tura gabansu tare da miƙewa da ƙyau yana haɗe rigar suit ɗinsa ya saka botirin dake jikinta ƙwaya ɗaya tak. Batare da ya sake kallon inda Maanal take ba ya nufi hanyar fita yana faɗin, “Zata fara aiki damu gobe in sha ALLAH”.      Daga haka ya fice abinsa cike da takun mazantaka da ƙasaita har ma da gayu na matasan samarin wannan zamanin musamman irinsa da ke ji da kansu da MANDA A GIDAN SANYI😉😂👌.... ___________★       A lokacin da anan Maanal ke Maawad company domin yin interview acan Kaduna su Daddy ne ke shirin miƙa kuɗin auren Yazeed ga mahaifin Nazeefa ɗiyar Aunty Sabuwa saboda matsawar Hajiya Yaya akan al'amarin. Ganin abin na neman zama wata fitinar kuma a tsakaninsu Ammie ta saka baki tanata roƙon Daddy dan yace shifa sai ƙarshen shekara. Da ƙyar dai ya amince za'a kai ɗin bayan ita kanta Ammien ya gaya mata baƙar magana. Duk da abin yay mata zafi sai tai murmushi kawai ta ƙyalesa.       An kai kuɗi inda suka samu tarba ta musamman kamar wasu bare. Dan abin har mamaki ya bama Daddy ɗin. Amma dai sai ya danne kawai akai gaisuwar mutunci. Dana shi ne da amininsa Alhaji Sunusi na Zaria. Sai maƙwafcinsa Alhaji Isa da wani abokinsa Alhaji Sulaiman. Abinda ya sake ɗaure musu kai ana maganar tsaida date caraf mahaifin Nazeefa yace ai wata ɗaya ma ya isa. Dan shi a shirye yake dama. Kallon kallo aka koma yi a tsakanin su Daddy, sai dai babu wanda yace komai sai Alhaji Isa ne ya ce, “Amma Alhaji kodai a ɗan ƙara, ko kuma shi Alhaji Usman ɗin aji ta nashi ɓangaren”.      Caraf yace, “Alhaji bazaka gane ba, yanzu idan ƴarka ta samu miji ba'a sanya wlhy, mu da Alhaji Usman ai duk ɗaya ne. Kawai a taimakeni ayi a hakan, kai ko auren ne a ɗaura to daga baya sai ayi bikin”.     Rasama abin cewa sukai su duka. Sai Daddy ne ya ɗan girgiza kansa kawai. Sai kuma ya gyara zamansa tare da faɗin, “Shike nan ALLAH yasa haka shine mafi alkairi. Amma bayan wannan ɗin shi yaron akwai wata kuma, itama idan anyi an gama kamar nan da watanni biyar haka sai ayi nata. Naso ma ayi gaba ɗaya ne a huta sai kuma larura ta gitta, to shi ciwo ya wuce komai a rayuwa shiyyasa aka ɗan ɗaga natan za'a fara shi wannan ɗin”.        Ɗan jimm Baban Nazeefar yayi, sai kuma zuwa can ya saki guntun murmushi da faɗin, “Babu damuwa Alhaji Usman, ai duka gidane tunda itama ɗin dai ta gida ce. ALLAH ya kaimu lokacin”.    Da amin duk suka amsa baki ɗaya. Daga haka suka ƙarasa abinda ya rage aka bar saka rana a matsayin wata biyu ɗin.     Suna fita a gidan Aunty Sabuwa dake laɓe ta afko falon, rungume mijin nata tayi cike da farin ciki, shima sai yay murmushi a ransa yana faɗin (wannan farin cikin nawane ba naki ba Sabuwa, dan lokaci yayi da zan maidama Alhaji Usman martani, lokaci yayi da zan ƙwaci abinda ya hanani a baya da ƙarfin tuwo. Lokaci yayi da wasan na gaskiya zai fara tsakanina da shi....)     _Tofa masu karatu, shin mike a tsakanin Alhaji Badaru mahaifin Nazeefa da Daddy kuma?. Ku dai kumuje zuwa mutanena🏃😋👌_ ___________★        “Wai hawayen nan basu isa haka ba ne Maanal? Tunda muka taho kike sharar hawaye inata magana kinƙi cewa komai. Kin san kuwa yanda zuciyata ke ɗagawa da wannan yanayin naki. Please! Tell me! Is something bothering you? Wani abu suka faɗa miki mara daɗi ne? Ko basu ɗaukeki aikin bane sukace?”.       Yanzun ma komai ƙin cewa da shi tayi, sai hankalinsa ya ƙara tashi matuƙa. A haka suka iso gidan Shahidah. Ko parking kuma bai gama yi ba ta buɗe motar ta fita, shima saurin fitowar yayi sai dai harta shige abinta cikin sassarfa da ɗan gudu-gudu. Hankalinsa ne ya sake tashi, sai kuma ya rasa inama ya kamata ya kama. Kamar zai bita sai kuma ya dakata. Yayi hakan yafi sau uku sai kuma ya koma cikin motar da sauri ya mata key ya bar gidan. Wani irin gudu ya dinga shararawa daya kawosa Mawaad Company cikin ƙanƙanin lokaci. Yana shiga kai tsaye office ɗin Boss ɗin ya nufa. Ko jiran Assistant ɗinsa ya masa iso baima yi ba yanzu. AS ɗin ne ya biyosa yana ƙoƙarin tsaida shi da sanar masa Boss yace kada abar kowa ya sake shigo masa sai in har shine ya buƙata amma sam RK bai sauraresa ɗin ba ya afka Office ɗin kansa tsaye cike da fushi kuma.     Shi dai shi kuma ƙoƙarin sake sanarma RK yake yi cikin damuwa da tashin hankali, dan tunda yake aiki a ƙarƙashin ogansa bai taɓa ganinsa a wannan yanayin na yau daya gansa ya fito daga conference room ba. Ya kuma tabbatar ba ƙaramin abu bane zai sakashi cewa kada abar kowa ya shigo inda yake ɗin.      Daga shigowar RK harta AS ɗin nasa da abinda yake ƙoƙarin faɗama RK ɗin duk a kunnensa ne, dan yana tsaye jikin ƙaton ƙayataccen gilashin da akai ma kusan kowanne bango na Companyn gaba ɗaya ado da shi hannayensa duka biyu a cikin aljihun suke ya zubama harabar wajen Companyn idanu koma ace ƙayatattun gine-ginen birnin na Abuja. Sai da ya basu kusan mintuna uku kafin ya ɗan juyo kamar mai fama da ciwon wuya ya zuba musu ido su duka biyun, sai kuma ya wani watsa musu ɗan iskan kallo ya ɗauke kansa.. Hakan yasa AS ƙoƙarin fara kare kansa cikin rawar murya da damuwa. Amma sai yay masa alamar yaje da yatsunsa biyu cike da salo. Kai AS ɗin ya jinjina masa cike da girmamawa yana mai haɗiye abinda yaso faɗar. Koda ya fice ya rufe musu ƙofar sake maida kansa yay ga kallon wajen batare da yayi magana ba kamar yanda shima RK ɗin baiyi magana ba har lokacin.        Iska mai ƙarfin gaske RK yay wani irin fesarwa ta alamar tsantsar takaici. Sai kuma ya sake takowa cikin Office ɗin sosai har inda yake shima ya tsaya kamar yanda yake a tsayen, batare daya kallesa ba ya furta, “Miyasa tun farko ka yarda zaka ɗauketa aiki cikin girmamawa da darajtawa! Amma ka saɓa hakan? Kasan matsayinta a wajena kuwa AA!?”.           Idanunsa da suka kaɗa sosai ya lumshe. Sai kuma ya saki wani ɗan siririn tsaki mai ɗan sautin da har RK ɗin yaji. Shiru na tsawon mintuna fin huɗu har RK ɗin daya sake ƙuluwa da haushi ya fidda ran amsawar tasa sai kuma ya ɗan karkato da kansa ya duba RK ɗin. Shima juyowar yay ya kallesa sukaima juna kallon ido cikin ido kowanne ƙwayar idanunsa na bama ɗan uwansa dai-dai da amsar da yake buƙata ko nemar mata fassara da fashin baƙi. AA ɗin ne ya fara janyewa yana sake sakin wani lalataccen murmushi a karo na farko mai kama dana rainin hankali ko tsantsar takaici. Sai kuma ya maida fuskarsa ya tsuke tamkar ba shiba, a dakensa a kuma karo na farko cikin muryarsa mai zurfi da amo ƙasa-ƙasa ya furta, “Calm down first, let's talk when you're ready. Right now I need to be alone”.        Wani irin zuba masa ido RK yay cikin takaici, sai kuma ya saki murmushi mai ciwo shima daya sake bayyana tsantsar bacin ransa. Juyawa yay yana kallon AA ɗin daya sake maida hankalinsa gaba ɗaya ga kallon garin. Taunar lips ɗinsa ya shiga yi da ƙarfi kafin ya juya ya fita a Office ɗin batare da ya sake cewa koman ba. A yanda ya ɗan bugo ƙofar ya sake saka AA lumshe idanunsa daga inda yake bai kuma juyo ba.        RK daya fita baiko kalla AS ba ya shige elevator. Har zai danna sai kuma ya fasa ya fito. Dogon hanya ɗin yabi sai gashi ya fito wani wajen da jerin Offices duke har kusan guda biyar. Office na biyu yay knocking. Kai tsaye aka bashi izinin shiga dan duk wanda ke'a cikin Office ɗin yana kallonsa ta hanyar camara. Ɗaya daga cikin wanda sukama Maanal interview ne. Fuskarsa ƙawance da murmushin daya bama RK ɗin mamaki ya tarbesa. Bayan ya nuna masa wajen zama zai miƙe ɗauka masa wani abun ya dakatar da shi.        “Director Mustapha thanks you basai ka kawo komai ba muyi magana kawai mana”.     “To ALLAH yasa dai lafiya?”.   Director Mustapha ya faɗa yana komawa ya zauna a mazauninsa.    “I'm sorry nasan dokane a companyn nan abinda zan tambayeka. Amma ina neman alfarmar sani ne sakamakon wani dalili mai ƙarfi. Please yarinyar nan da kukama interview yanzu wani abu ya faru da ita ne a wajenku ko aikin ne bata samu ba?”.      Ajiyar zuciya mai haɗe da murmushi Designer Director Mustapha ya saki, sai kuma ya girgiza kansa. “No Doctor babu wani abu daya faru gaskiya. Hasalima an bata aikin dan har CEO ya bata damar fara zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu. Yanzun nan R&D Director ya fita anan na gama bashi list ɗin abinda office ɗin ta zai buƙata a yau komai za'a gama haɗa mata shi. Shin wani abu ya faru ne?”.      “No! No! Babu wani abu daya faru. Nagode sosai”.   “Ai babu zancen godiya a tsakaninmu, yarinyar ta cancanci samun aikin dan gaskiya she is very smart and amazing because she demonstrated excellent problem-solving skills and an innovative approach during the interview. Tunda kaga babu wani ja'inja Boss ya bata dama da wuri haka ai kasan bata wasa bace. Haka muma kowa ya gamsu da brain ɗinta wlhy”.      Murmushi RK ya masa cikin jinjina kai, sai kuma ya miƙa masa hannu yana miƙewa da faɗin, “Thanks you Director”       “No worries doctor. I am on my job”.   Daga haka yay masa sallama ya fito a office ɗin dukkan damuwarsa da AA ya dasa masa na guduwa daga cikin ƙirjinsa. Sai dai kuma hankalinsa nakan dalilin halin da Maanal ɗin ta shiga........✍️ _Tofa ƙaƙa raƙa ƙaƙa. Shin minene alaƙar Maanal da AA?, sannan minene alaƙar RK da AA kuma. Dan tabbas alamu sun nuna akwai sanayya mai ƙarfin gaske a tsakaninsu. Hhhh badaƙala kenan, mi kike son ji?😂 Ga wuri ga waina. To kawai mu haɗe a comments section 🤣🤣🤣🤣🏃._ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖2️⃣4️⃣ .........Wata irin ajiyar zuciya director Mustapha ya saki. Sai kuma ya saki murmushi a ransa yana mamakin kansa da ɓoyema Doctor Rafeeq ɗin sauran gaskiyar abinda ya faru da yay... Kirane ya shigo daga landline ɗin office ɗin, ganin daga office ɗin CEO ne ya sashi saurin ɗagawa. AS ne ya sanar masa CEO na buƙatar ganinsa yanzun nan, kuma ya taho da file ɗin sabuwar staff ɗinsu. Bai wani tsaya wasa ba ya miƙe yana dariya. A fili ya furta, “Anya babu wata a ƙasa akan yarinyar nan kuwa? To madai ji ma gani wai an binne tsohuwa da ranta”.        Sai da AS ya shiga yay masa iso sannan ya shiga. A yanzu kam AA ɗin na zaune ne a kujerarsa ta aiki saɓanin a yanda RK ya samesa ya kuma barshi. Gaisuwa Director Mustapha ya miƙa daga tsayen batare daya zauna ba. Shima AA ɗin da hankalinsa ke kan computern desk ɗin batare daya amsa ba yay masa nuni da vesitors chair ɗin gaban desk ɗin kawai. Zama yay, kafin cikin girmamawa ya ce, “Gani Sir. Dama ina ƙoƙarin ƙarasa haɗa komai ne na kawo sai kuma ga kiran AS akan kana son ganina”.       Shiru bai amsa masa ba, yanata aikin gabansa kawai har lokacin hankalinsa nakan screen ɗin computer ɗin, sai da yaja kusan mintuna uku kafin ya ajiye tare da maido hankalinsa kan Director Mustapha ɗin. “Am sorry ina wani abune”. Ya faɗa cikin muryarsa mai zurfi. Da sauri Director Mustapha ya ce, “Babu komai Sir”.      Kansa kawai ya jinjina masa. Sai kuma ya miƙa masa hannu alamar ya basa file ɗin. Miƙa masa yay da sauri cikin girmamawa. Yayinda shi kuma ya shiga buɗesa yana duba komai daki-daki. Sai zuwa can ya ɗan ɗago. “Baku ƙarasa bane?”.         “Eh sir! Saboda kana fita itama ta miƙe ta fice muna ƙoƙarin tsaidata amma bata sauraremu ba. Mun cigaba da abinda ya dace ne kawai saboda ka bada umarnin hakan. Dan mu harma mun fara tunanin ko tanada wani c......”     Muƙutt ya haɗiye zancen saboda wani shegen kallo da AA ɗin ya jefa masa. Sai kuma ya duƙar da kansa yana shashshafa ƙeya. Shiru office ɗin ya ɗauka na kusan minti biyu kafin yay masa nuni da hannu alamar yaje. Miƙewa yay tare da ɗan rissinawa na girmamawa sannan ya fice a office ɗin..... Duk yanda yaso cigaba da aikin zuwa lokacin break hakan ya hagaresa. Dan wani irin zazzaɓi ne ma ke neman rufesa. Ga ciwon kai. Dan hatta fararen idanunsa launinsu ya canja zuwa jaa sosai alamar akwai wani abu dake damunsa. Sai dai sam fuskarsa bata nuna komai. Kwanciya yay a office ɗin bayan dawowa sallar azhar, kamar wasa zazzaɓi mai azabar zafi ya rufesa, ga wani irin sanyi da yake ji. Ya kulle kofar tare da ma AS gargaɗin baya buƙatar kowa. Hakan yasa ko lokacin Asr AS bai masa knocking ba dan yasan ogansa baya wasa da salla. Ganin har biyar na yamma lokacin ma'aikata sun fara tashi babu alamar zai fito hankalin AS ɗin ya fara tashi, ya dai daure dan yasansa da iya yin over work. Kamar wasa har magrib companyn yayi shiru sai securitys. Dole fa yaje ya fara masa knocking amma shiru kake ji wai malam yaci shirwa. Hankali tashe AS yay kiran wata number, bayan an ɗaga yayi gaisuwa cikin girmamawa ya sanar da halin da boss ɗin nasa ke ciki. Banji mi aka sanar masa ba, sai dai ya amsa da girmamawa yana sauke wayar. Yana nan yana faman kai-kawo a bakin ƙofar sai ga wani nutsetstsen mutum da zai iya kaiwa shekara arba'in haka. Sosai yake kamanni da AA ɗin, hatta da rashin yawan fara'ar fuska kamar AA ɗin dai. Gaisheshi AS yay da girmamawa. Ya jinjina masa kai yana amsawa, sai kuma ya fiddo wani ɗan card a aljihun jallabiyarsa fara ƙal ya goga a jikin handle ɗin ƙofar. A take kuwa ta rabe gida biyu ta buɗe. Gaba ɗaya an kashe wutan office ɗin, hakan ya saka gabansa faɗuwa, dan sun san minene ganin AA a duhu yake nufi, wayarsa ya zaro ya kunna fitilar, hakan ya bashi damar ƙarasawa ga makunan fitulun office ɗin ya kunna. A take haske ya gauraye ko'ina. Idanunsa suka sauka akan AA dake kwance a kan sofa. Cike da sassarfa ya ƙarasa garesa yana kiran sunansa, amma shiru babu allamar zai amsa, har ya zauna a saman table ɗin gaban sofa ɗin tare da kai hannunsa saman na AA daya dafe kai da shi, hannun ya janye a hankali ya maye gurbinsa da nashi, sai da gabansa ya faɗin jin wani irin hucin zafi, sanyin hannunsa yasa AA buɗe manyan oily idanunsa gently, sunyi wani irin mugun kaɗawa jazur, sam babu hasken nan mai kama da madara a cikinsu yanzu, sai ƙyallinsu daya sake saka jan yin bauuu. Ga kuma jijiyoyin kansa da suka sake fitowa ruɗu-ruɗu.... “Ya arrahaman Auta! Baka da lafiya amma kazo nan ka kwanta? Are you mad da baka san muhimmancin lafiyarka bane?”. Maimakon amsa masa sai AA ɗin ya maida idanun nasa kawai ya sake lumshewa. Tsaki mutumin yaja tare da miƙewa ya tada AA ɗin shima. “Oya get up and go home?”. Bai masa musu ba ya miƙe ɗin, haka ya kamashi suka fito yana bama AS da hankalinsa ya tashi da ganin halin da boss ɗinsa yake ciki umarnin tattaro abubuwan AA ɗin. Cikin sauri ya amsa shi kuma ya wuce da shi...... _____________★        A hankali yake juya steering kamar baya so. Yayinda gaba ɗayan hankalinsa ke akan al'amarin Maanal. Yama rasa yaya zai fassara lamarin, musamman a yanzu daya koma Maawad yaji komai daya faru. Shin murnar samun aikin ce ta sakata kukan? Ko kuwa mike faruwa?. Rashin mai bashi amsa ya sashi ɗaukar hanyar gidan Shahidah, dan gaskiya yana buƙatar ganin Maanal ɗin. Ya ɗan yi nisa da tafiya kira ya shigo masa. Kamar bazai ɗauka ba sai kuma dai ya ɗauka saboda ganin abokin aikinsa ne na asibiti. Neman gaggawa ake masa zuwa asibiti yanzun nan, dole yay reverse zuwa asibitin dan yanda yaji Doctor ɗin a rikice yasan akwai babbar matsala. Kafin ya isa kiran wasu doctors biyu ƴan uwansa ya sake shigo masa. Dole ya ƙara gudu cikin ƙanƙanin lokaci sai gashi ya iso.....         _________★           A ɓangaren Maanal kuka taci sosai na tashin hankali. Dan har yamma ta kulle kanta a ɗaki taƙi ta fito. Yara da suka dawo makaranta sunata buga mata bata kulasu ba. A haka shima baban nasu ya dawo ya tarar da al'amarin. Linda ce ta sanar masa iya abinda ta sani na shigowar Maanal ɗin da gudu tana kuka ta wuce ɗaki ta kulle kanta...       Hankalinsa ne ya tashi shima. Ya shiga knocking ƙofar yana kiran sunanta amma shiru. Sai ya fara tunanin kodai batama rayene? Gata tare da ciwo mai haɗari. Wayar Shahidah ya kira yace ta dawo gida yanzun nan. Hankali tashe ta shiga tambayarsa lafiya? Dan ita bata tashi a nata aikin ba. Amma sai yace ba komai tazo dai kawai. Daga haka ya yanke kiran ya fita neman maigadi dan yazo su gwada ɓalla ƙofar. Babu jimawa suka dawo, zuwa lokacin yaran nata kuka suna sake buga ƙofar. Sunta ƙoƙarin buge ƙofar amma bata ɓallun ba, dole maigadi ya ce, “Yallaɓai sai dai fa a nemo wanda yasan aikin karma ayi ɓarna. Bara muga na kira wani yaro dana sani”.         Kai kawai Uncle Sadeeq ɗin ya iya ɗaga masa. Dai-dai nan Shahidah ke shigowa a ruɗe. Cikin tashin hankali take tambayarsa abinda ya faru. Bayani ya mata kamar yanda Linda ta masa. A take jikin Shahidah ya kama rawa. Itama ƙofar ta fara bugawa muryarta na rawa tana kiran sunan Maanal ɗin amma shiru. Wani tunani ne yazo mata, ta fita cikin sassarfa zuwa can baya inda windows ɗin ɗakin suke. Binta shima mijin nata yay. Kwance suka hango Maanal sharɓan a gado babu alamar rai a tare da ita. Ai Shahidah bama tasan tayi wani irin yin baya ba tana neman faɗuwa sai da mijinta ya tarota. Cikin rawar baki data murya ta ce, “Honey ta rasu ko? Da alama Maanal bata numfashi”.       “In sha ALLAHU bata rasu ba Honey cool down. Zata iya yiwuwa suma tayi ko barci take”.     “Barci! Ina badai barci ba Honey.....” Isowar su maigadi ya hanashi bata amsa. Kamata yay suka koma cikin gidan. Cikin abinda bai wuce mintuna goma ba aka ɓalle ƙofar ɗakin. Daga Shahidah har mijinta da yaran a guje suka afka ciki. Lokaci ɗaya ita da yaran suka zagaye Maanal ɗin. Koda ta cacumota sai tai mata wani jagab alamar babu rai tare da ita. “ Innalillahi wa'inna ilaihiraji'un”. Ta shiga ambata jikinta na rawa. Yayinda yaran suka fara ihun kuka suna kiran Maanal ɗin. Shi kam mijinta ƙoƙarin neman number RK yake yi, sai dai sam taƙi shiga. Dole ya koma neman Dr Ranjet. Cikin Sa'a kuwa sai ita ta shiga. Bayani ya masa a taƙaice, hankali tashe Dr Ranjet yace gashi nan zuwa gidan RK ya shiga theater ɗin gaggawa ne tun ɗazun shiyyasa bazai samesa ba.       Alhamdullah Dr Ranjet ya iso akan lokaci tare da wata abokiyar aikinsa. Dandanan ya saka kowa ya fito suka kasance su biyu kawai a ɗakin. Taimakon gaggawa suka shiga bama Maanal ɗin, sunfi awa ɗaya kafin cikin amincin UBANGIJI ta farfaɗo. Dama ya tabbatar musu su kwantar da hankalinsu bugun zuciyarta ne yay ƙasa sosai shiyyasa numfashinta ya dakata ma amma tana da rai. Basu bari kowa ya shigo ba sai da suka gama dai-daita komai suka saka mata ruwa da allurai sannan.     Bayanin da Dr Ranjet yamusu ya saka su dinga sauke ajiyar zuciya a tare. Shahidah ta dinga share hawaye. Su duka suka shiga tare da yaran da mijin nata, ganin Maanal ɗin na barcinta hankali kwance ya sake saka musu nutsuwa. Bayan fitowarsu ne Dr Ranjet ke sanar musu dolene su kula sosai da shan maganin Maanal ɗin, dan yanzu ma yana tunanin sakacin hakanne ya kawo wannan matsalar, duk da ya fahimci akwai damuwa tattare da ita bai faɗa musu ba dai. Hakan kuwa ɗin ne kamar yanda yay hasashe, dan yasa an kawo masa magungunan ya duba ashe kona safe bata sha ba ta fita. Ya sake tabbatar musu da kula da shan maganin nata da shigarta kowacce matsalar damuwa komai ƙanƙantarta sannan suka wuce.       Dole yau Shahidah tare ta kwana da Maanal. Alhamdullah ta tashi cikin aminci kuma. Dukkan wata kulawa Shahidah ce ta bata a wannan safiyar, harda yara kowa tattalinta yake yi, hatta da abinci tara suka bata a baki, hakan ya sakasu makarar fita dan sai da ta sake komawa barci sannan. Bayan ta farka Linda tai ƙoƙarin taimaka mata tai wanka taci abinci tare da sanar mata zuwan RK gidan har sau biyu, amma sai Maanal ɗin taƙi cewa komai tana zaune kawai tana hawaye. Ana haka RK ya sake dawowa. Babu lallashin da Linda batai mata ba akan taje su gaisa ko shi ya shigo amma taƙi, tanata kukanta kawai. Hankalinta sai ya sake tashi tai kiran Shahidah dake a wajen aiki ta sanar mata. Cikin ƙanƙanin lokaci kuwa sai gata ta dawo gidan...      ★ “Haba Maanal wai mike faruwa ne duk kinbi kin ɗaga mana hankali. Jibafa office na baro saboda kiran da Linda taimin duk da tarin ayyukan dake a gabana. Amma inata magana kinyi shiru sai kuka kikeyi. Idan jikin naki ne kuma muje asibiti. Ko na kira Ammie ne dai?”.       Da sauri Maanal ta shiga girgiza mata kanta tana sharce hawayen da suka gagara tsaya mata. “Didi kar ki kirata dan ALLAH. Ba wani abu baneba fa”.         “Haba Maanal ya zakice bawani abu bane gaki kinata faman kuka. Idan baki son na kira Ammien to ki faɗa min mike faruwa ne? Wani abun Rafeeq ɗin ya miki jiyan da kuka fita? Ko aikin ne basu ɗaukeki ba?”.      “A'a Didi babu ɗaya daga ciki, ina son yai zan koma KD”. “Okay mune mukai miki wani abu kenan?”. “Kai Didi ni mi zaku min. ALLAH ki kwantar da hankalinki babu komai”.       “Batun kwantar da hankali kam bazai kwantu ba Maanal, yanzu fa kike cewa zaki tafi KD. Amma dai bara na kira Ammien ni kam, ƙila ki sanar mata ko Nene. Ga Rafeeq can Linda tace yayi mayawa takai huɗu tunda safe amma kinƙi fita, kinƙi cin abinci, kinƙi wanka Maanal why? Gara nai kiratan dai zai fi”.   Caraf ta riƙe mata hannun tana girgiza kanta. Yayinda idanunta suka cika da ƙwalla tab. “Please Didi karki kirata zan gaya miki”. Kai Shahidah ta jinjina tare da sauke numfashi sai kuma ta sakar mata wayar da faɗin, “To ina saurarenki, mike faruwa?”. Sai da Maanal taja kusan mintuna biyu kafin da ƙyar ta iya furta, “Didi sun ɗaukeni aikin amma bazanyi ba”.      “Baza kiyi ba kamar ya? To saboda mi?. A wannan lokaci da aiki ke wahala Maanal. Kin samu cikin sauƙi haka amma kice baza kiyi ba. Ko auren Yazeed ɗin kike so to? Ko kuma dan kinji jiya ankai kuɗinsa gidan su Nazeefa ne har kika nema tadana kanki ciwo?”.          “Didi mizai sa na damu da auren Yaya Yazeed tunda ba'a kaina zata zauna ba.”     “To mike faruwa? Wajen aikin ne ya miki alamu na marasa ɗa'a ko me?”.     “A'a Didi kawai dai”. “Miye kawai dai. Maanal ki fito kimin bayani mana yanda zan fahimta na kuma gamsu”.        Rasa yanda zataima Shahidah ɗin bayani tayi, ta fito fili ta sanar mata abinda idanunta suka gani a jiyan ko kuwa ta shanye al'amarin a cikinta kawai ta dage akan aikinne bazatayi ba. To amma tasan nacin RK, shima bazai barta ba ai. Sannan ita kanta Didi ba barinta zatai ta huta ba har sai ta san gaskiyar al'amarin. Sanin gaskiyar kuma na nufin abinda zata ɓoye a yanzu dan sai sun san komai. (Ya arrahaman) ita ina ya kamata ta kama ne?.....      “Maanal!!” Shahidah ta kirata tana mai girgizata. Firgigit ta dawo hayyacinta kamar wadda aka tada daga barci, sai kuma ta sauke ajiyar zuciya tare da kai hannunta saman goshi tana murzawa a hankali.        “ALLAH Maanal tambaya ta ƙarshe zan miki daga nan zan kira Ammie ne kawai tunda ni baki son nasan damuwarki”.   Jin yanda Shahidah tai maganar a hasale tana ƙoƙarin miƙewa yasa Maanal saurin kamo hannunta ta dawo da ita. Idanunta cike da ƙwalla ta ce, “Didi ba ɓoye miki nake ba wlhy, kema kin sani bana taɓa ɓoye muku komai a rayuwata. Kawai dai na fasa yin aikin ne saboda companyn na Bes...” sai kuma ta canja ta ce,  *_“AA Darma_* ne?”.      Cikin matuƙar razani Shahidah ta miƙe zumbur hannunta dafe da ƙirji ta ce,  “What!! Kina nufin *_Ajwaad!!_* Maanal!”.         “Shi Didi, shi! Shi! ɗin dai.” Maanal ta faɗa wasu hawaye masu zafi na sake gangaro mata.    Jagwab Shahidah ta koma ta zauna tana mai dafe kanta da duka hannaye biyu, ita kanta jikinta tsuma yake, sai kuma ta ɗago tare da jawo Maanal ɗin jikinta ta rungume dan kuka take mai ban tausayi da tsuma zuciya. Cikin sarƙewar murya ta ce, “Maanal kuma kin gansa ya ganki? Kin tabbatar shi ɗin ne dai?”.      Kai Maanal ɗin ta jinjina mata, “Ya ganni sosai, amma ya nuna kamar ma bai taɓa sanina ba tamkar a wancan ranar da yay......” nan dai ta labarta mata duk yanda komai ya faru. Gaba ɗaya mamaki ya gama kashe Shahidah, amma sai ta danne ta shiga Lallashinta har sai da tai shiru. Daga haka ma ta ciro maganinta ta bata kasancewar lokacin shan na rana yayi. Tana sha babu jimawa ta ɓingire wani barcin. Lallaɓawa Shahidah tai ta gyara mata kwanciya, sannan ta saka mata ac kaɗan ta kashe mata fitilar ɗakin ta fice..........✍️ _Tofa, wanene *AA Darma* a rayuwar Maanal Habeeb Giro?. Karku gajiya kumuje zuwa dan yanzune labarin AJIYA A DUHU ma zai fara. Labarin nan fa akwai cakwakiya ta musamman mutane na. Ni bamma san team ɗin wa zan kasance ba bana. Karna zaɓi AA ace min mayyar kuɗi🥲🥱🤪🏃_ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖2️⃣5️⃣ ........Nata ɗakin ta nufa tanata faman sauke ajiyar zuciya. Yayinda abubuwa masu yawa ke mata kaikawo a cikin rai tamkar sun faru sun wuce ne a cikin film. Tana shiga ɗakin wayarta ta ɗauka domin kiran Ammie. Har tayi dailing no ɗin nata sai kuma ta katse da sauri, dan kuwa ziciyarta ta tsawatar mata akan ba ita ya kamata ta kira ba. Cikin gamsuwa da hakan ta maida alaƙar kiran ga Amal duk da tasan itama dai tana wajen aiki yanzu haka. Sun gaisa kamar yanda suka saba cikin so da ƙaunar juna. Tare da tambayar yara da bayan rabuwa. Sai kuma Amaal ta ciga da faɗin, “Didi ya naji muryarki duk ta canja kamar wadda ke'a cikin damuwa? Kuma kamar ma a gida kike bakije office bane?”.        “Him ke dai bari Amaal, abin duniya ne ya isheni wlhy dawowa nayi. Akan Auta ne fa”.     “Ya ilahil'alamin miya faru kuma?. Kin saka gabana faɗuwa badai jikin nata bane kuma?”.     “Bashi bane duk da dai jiya taso rikita mana lissafi gaskiya. Amma Alhamdullah yau ta tashi normal. Sai dai abinda yaso zama sanadin tada ciwon nata har yanzu yana tare da ita.”       “ Innalillahi wa'inna ilaihiraji'un. Didi kimin bayani dan ALLAH yanda zan gane. Mi kuma ya sake faruwa da Autar?”.     Komai daya faru Shahidah ta labartama Amaal kamar yanda Maanal ta sanar mata ita da kuma wanda ya faru anan gidan. Ai Amaal batama san ta rikito a kujerar office ɗinta ba tana zunduma wata ƙatuwar ashariya da maimaita sunan “Ajwaad fa? Na gidan Oum?”.        “Shi kuwa wlhy Amaal.”    “Kan babbar b... uba. Ke nan dama suna ƙasar nan Didi?”. “To bazamu ce ba Amaal ALLAH kaɗai ya sani, amma nayi mamaki matuƙa nima, dan banyin zaton haka daga Oum ba. Shin miya hanata neman mu?.”       “Humm Didi wannan maganar ta wuce ta waya. Ki saurari zuwana anjima kaɗan koda sassafe ne na dawo saboda office. Kin gayama Ammie?”.      “A'a ki rufan asiri kin santa dai ai. Ke kaɗai na gayamawa. Ko Abban su Barrah ban sanarma komai ba ma. Amma Daddyn Munaya zai barki?”.   “In sha ALLAHU zai bari barima kiga”... _____________★        Sosai Hajiya Yaya da Aunty Sabuwa da ƴaƴansu suka haɗa wata ƴar ƙwarya-ƙwaryar walima a gidan Aunty Sabuwa ɗin wai na murnar saka rana. Abin ma sai ya baka dariya da mamaki. Dan dj aka ɗakko ya saki speakers iya maƙura aka cashe akaci kaji da lemuka. Ga taron ƙwayen Aunty Sabuwar ƴan duniya, dan mafi yawansu zawrawa ne. Dan ita dai Hajiya Yaya tun abin na birgeta tana murmushi har ya fara tsikarin zuciyarta. Amma sai ta danne ta basar. Kasancewar tasan Daddy na gari anayin la'asar ta tattaro su Asalamiyya sukayo gida ransu a ɓace. Dan so sukai ta barsu su kwana acan su ƙara ɓararrajewa da ƙyau.      To ashe wasa farin girki, dan kuwa tafiyar su Hajiya Yaya kamar an buɗe wani sabon babin shagalinne a gidan. Tsabar taɓara da zubewar mutunci sai ga mahaifin Nazeefar ya shigo fili wai shima ya taka rawa, liƙi Sabuwa ta fara masa sauran ƙawayen ma suka rufu a kansu suna liƙesu ana dariya da shewa da shaƙiyanci tunda shima ɗan duniyar ne. Sai daga baya ya fita ya barsu ya shige ciki, su kuma suka cigaba da shagalinsu. Yayinda guri yay guri Sabuwa tama manta da wanzuwar miji a gidan, babban aminiyarta ta zame jiki tai wuff tabi bayansa. Dama sun jima tare ita Sabuwa ce bata sani ba. Aiko ya sama ƙofa key suka hau shagalinsu suma.      A taƙaice dai wannan taro bai tashi ba sai kusan sha biyun dare. Duk sun bi sun hana ƴan anguwa barci anata musu ALLAH wadarai. Koda suka nutsu Sabuwa ke tambayar Hajiya Malika aminiyarta ina ta shige, sai cemata tai ai gida taje saboda oga ya dawo neman wasu takardu bai gansu ba. Sai da ta koma ta bashine ta dawo. Cike da shaƙiyanci suka hau tsokanarta wai bawasu takardu kodai-kodai. Dariya ta dinga tuntsurawa ita dai. A haka Mijin Sabuwa ya sakko daga sama. Suna haɗa ido da Hajiya Malika suka wani kashema juna idanun cike da salon shaiɗanci batare da kowa ya lura da su ba.       (Humm ALLAH ya ƙyauta. Hajiya Malika dai matar abokin Alhaji Sajid ce, kai yama wuce ace aboki sai dai amini ɗan uwa. Hakan yasa suka ƙulle matansu suma suka zama aminan Sabuwa da Malika ɗin kenan. Sosai suke aminta dan babu wani sirri na Sabuwa da Malika bata sani ba, hakama duk wani sirrin Malika Sabuwa ta sanshi. Abota ce tun ta ƙuruciya. Ko lokacin da Sabuwa ta rabu da Alhaji Sajid ɗin Sabuwa da Malika na tare, kusan ma za'ace da taimakonsu ne aka maida auren bayan Sabuwar taje tayi auren kisan wuta saboda saki uku ne. Shi mijin Hajiya Malika sam ba mazauni bane ba, ɗan kasuwa ne da kullum yana wacan ƙasa gobe yana waccan kamar wani ɗan sama jannati, da wannan damar Mijin Sabuwa ya samu kan Hajiya Malika suke sheƙe a yarsu. Dan a yanzu haka ƴaƴan Hajiya Malika ba duka bane ɗiyan mijinta idan za'a tantance, akwai gauraye dana mijin Sabuwa saboda yanda suke tare matuƙa kamar wata matarsa. UBANGIJI kuma yay musu talala har yanzu babu wanda ya taɓa sanin wannan alaƙa tasu duk da tsahon shekaru sai wata mai aikin da Hajiya Malika ta taɓa yi, ita kam ta kamasu dumu-dumu cikin aikata al'amarin ta tsorata, itama hankalin Hajiya Malikan ya tashi amma sai Mijin Sabuwa yace karta damu ta jira taga mi zaiyi. Aiko taga abinda zaiyi ɗin, dan a gabanta yayma yarinyar nan ƴar aikinta fyaɗe, daga nan yaja mata dogon gargaɗi akan idan ma taje ta tona musu asiri saita haɗa da kanta, ya nuna mata video ɗin daya saka Hajiya Malika ta ɗauka sanda yake tare da yarinyar. Hankalinta ya tashi, ta dinga kuka tana ramtsuwar bazata faɗa ba wlhy. Basubi takanta ba sukace ya haɗa kayanta washe gari aka maida ta ƙauyensu. To tundai daga nan babu abinda ya sake faruwa sai dai UBANGIJI na kallonsu, ba kuma su san ya musu talala bane ba)    🏃 ALLAH ka tsaremu da ikonka da rahamar ka😭🙏. _________★     Kamar yanda Amaal tai alƙawari ta iso Abuja kusan takwas na dare. Alhamdullah zuwa sannan Maanal ta farka. Dan shigarta wanka kenan Amaal ɗin ta iso. Ta fito taci karo da ita a ɗakinta sai tayi turus. Dariya Amaal ta sanya mata tare da buɗe mata hannayenta alamar tazo gareta. A yanzu kam babu musu Maanal ɗin ta nufota suka rungume juna, kai kace ba kwanan nan suka rabu ba.     Sai da Maanal ta shirya tai sallolin dake kanta sannan ta dawo tsakiyar yayun nata maganin kukanta ta zauna. Abinci suka fara ci, yayinda Maanal ta shagwaɓe musu wai ita hannunta na ciwo bazata iya ci da shi ba. Aiko su biyun duk suka dinga bata a baki. Hakan da sukai mata ma sai taci abincin sosai. Dagan nan ne suka nutsu akan abinda ya tarasu.       Da farko dai sun fara lallashinta akan batun aiki tace ita fa ta fasa bazatayi ba. Hasalima tana son komawa Kaduna ne kawai wajen Ammie.     Baki Amal ta taɓe cikin ɗan ɓacin rai dan dama tafi Shahidah zafi ta ce, “Oh Kaduna ko? Kenan auren Yazeed ɗin kike son yi?”.        “Yazeed kuma? Didi ni na taɓa cema wani zan auri Yazeed?”.    “Ai basai kin faɗa ba gashi yanzu kin nuna mana. Wai Manaal mike damun kanki ne dan ALLAH?. Ke gaba ɗaya tunaninki a bauɗe yake dana mutane, sai shegen taurin kai da kafiyar tsiya. To wlhy bari ma na fito miki a mutum ki tattara hankalinki waje guda ki maidashi jikinki. Har mi akai akayi wani Ajwaad can da zai hanaki samun cikar burinki....”    Hannun Amaal Shahidah ta jimƙe a nata tana girgiza mata kai alamar tayi shiru. Hakan ya saka Amaal ɗin jan ƙaramin tsaki. “Didi ki barni da ita. Na kula sam Maanal bata tausayin kanta bata tausaya mana mu ƴan uwanta. Wace irin rayuwace wannan ace mutum da taurin kai....”       “Kinga ya isa haka. Maanal bani hankalinki nan muyi magana ta gaskiya”. Shahidah ta faɗa tana kamo hannun Maanal data tsurama Amaal idanu cikin nata. Dole ta janye daga kan Amaal ɗin ta maido kan Shahidahn. “Maanal kiyi haƙuri bazamu takura miki ko tirsasaki akan abinda baƙya ra'ayi ba. Amma ina son ki fahimci wani abu, mufa a yanzu bamu da maraba da marayu da suka rasa mahaifi da dukkan dangi. ALLAH ne gatanmu sai Ammien mu sai kuma Nene kawai sai kammu. Dolene fa mutattara komai daya faru a baya mu zubar da shi muyi mantawa irin ta AJIYA A DUHU duk da nasan akwai tabo da bazai taɓa goguwa ba a zukatanmu amma komai na ALLAH ne. Sannan dole musan kammu mu kuma gina gobe yaranmu masu tasowa. Maanal Daddy ya riƙemu babu banbanci da ƴaƴan daya haifa a cikinsa tunkan Ammie ta haifa masa Waleed da Hameed. Kuma muma a yanzu babu wanda mukema kallon uba sama da shi. Sai dai fa mu sani iyakarmu kiransa uban ne kawai a iyakar kayinmu, amma a wajen al'umma sunanmu AGOLOLI a gidansa. Maanal ba fata nake ba, amma ki sani a yanzu ALLAH ya ɗauki rayuwar Daddy wlhy ko Amminemu bazasu bari ta rayu a wannan ahalin ba. Saboda su Waleed ƙanana ne, basu kai girman da zasu ƙwata mata ƴanci ba. Mu kuma komu yarda ko karmu yarda munada iyakarmu a gidan nan. To mikike tunanin ya kamata muyi? Wannan aikin tuƙuru domin gina gobemu da goben yaranmu. Bazamu so mu sake maimaita rayuwar baya ba Maanal, bazamu so mahaifiyarmu ta sake maimaita wahalhalun data sha a kammu ba a shekarun baya, idan sannan muna da ƙuruciya yanzu munkai girman share mata kukanta, mun girma Maanal mun girma”.     Kuka ya sarƙeta. Suma duk sai suka fara kukan, koda yake dama Maanal ita tuni ta fara hawaye. Kusan mintuna biyu Shahidah ta share hawayenta da cigaba da faɗin, “Maanal bamu san mi gobe zatazo mana da shi ba. Dan muma mata ne. Idan har Ammie zata iya riskar kanta a irin rayuwar da mukai a shekarun baya bai kamata mu mushagala da tunanin komaima bazai faru ba saboda a yanzu rayuwarmu ta inganta. Karfa mu manta da irin labarin gata da rayuwar Ammie tasha a hannun iyayenta, amma hakan bai hanata fuskantar ƙalubale ba a hannun mijin aurenta da kowa ke gani hakan bazata faru ba. To muma bai kamata ganinmu a cikin irin waɗan nan manyan gidajen yasa mu shagala ba. Bai kamata mu cigaba da zaman jiran kullum a mana ba. Saboda haka ki dawo cikin hankalinki Maanal, ki tuna su waye mu a yanzu. Ki ajiye abinda ya wuce baya ki manta da shi, ki kaishi cikin duhuwa ki ajiyesa tamkar ma ba'a taɓa yin komai ba. Yanda Ajwaad ya nuna bai sanki ba ki zama JARUMA kema ki nuna baki sanshi ba, ki manta da shi, ki manta da abinda ya shafesa, ki tsaya da ƙafafunki, kisa a ranki shi bai isa hanaki kaiwa ga cikar burinki ba, karki wani damu da zamowarsa shugaban kamfanin ko matsayin nasa ke aiki ya kaiki domin kanki. To kiyi kuma aiki tuƙuru a companyn nasa domin kanki da cigabanki. Maanal ki duba yanda Rafeeq ke hidima dake da son ganin farin ciki ki, hatta Yazeed ma ni wlhy ban taɓa ƙin kasantuwar aurenku ba saboda mutumin kirki ne. Koba komai yasan mutuncin mahaifiyarmu, ya taimakemu a lokacin da muka rasa taimako daga jininmu ma. Kawai mahaifiyarsa ce matsala. Idan kuma da alkairi a zamanku sai ALLAH ya ɗauketa ku zauna ɗin babu yanda zatayi. Amma dan ALLAH ki amshi al'amarin Rafeeq ki gwada ki gani shima. Ki kwantar da hankalinki addu'ar mu na zagaye dake ki manta da baya, ki saka a ranki ƙaddarar data gitta rayuwarki bazata hanaki aure ki zauna a gidan mijin ba har kuma ko samu farin ciki fiye da zatonki. Dan ALLAH shine shaida baki je kin aikata dan son zuciyarki ba. Dan haka ki manta komai, dan ALLAH ki manta komai kije ki fara aiki, abu nagaba kuma kiyi ƙoƙarin fidda mijin aure tsakanin Rafeeq da Yazeed kodan ki tabbatar ma Ajwaad kina rayuwane domin kanki. Dan kuwa cikakkiyar amsa kika samu a jiyanki game da shi, idan a baya hasashe kawai mukeyi bisa dalili yanzu ya tabbatar miki shi da kansa”.       Sosai Maanal take kuka yanzu kam, Amal ta jawota jikinta ta rungumeta itama tana kukan, sam basa son tunawa da bata, basa son tunawa da ƙaddarar data ratsa rayuwar autarsu, basa so ba sa so. Cikin rawar murya da son ture komai Amaal ta ce, “Duk abinda Didi ta gaya miki shine gaskiya wlhy Auta. Ki dake zuciyarki kiyi abinda ya dace da rayuwarki a yanzu. Ki manta da abinda ya wuce kamar ma ba'ayi komai ba. Koda wasa kada ki zubda daraja da kimarki ta ɗiya mace. Ki amshi ƙaddarki kamar yanda muma muka rungumi tamu. Hakan da zamuyi sai ya ƙara ƙarfafa Ammien mu, ki duba kiga rayuwar data baro, mai cike da tarin gwagwarmaya amma a yanzu ALLAH ya mata canji, canjin kuma baisa ace babu wasu jarabawoyin ba kuma. Tunda anan ɗin ma tana fuskantar ƙalubalen bawai sun ƙare bane. To haka rayuwa take duk yanda ka kai ga samun sauyi da nasara da jin daɗi dole ƙaddararka aminiyar NUMFASHINKA ce Maanal. Tare suke tafiya a jefe ƙafa da ƙafa. Aminan juna ne tamkar gangar jiki da numfashi. Hakama jarabawarka abokiyar gangagar jikinka ce. Kinga ko har abada babu ɗayan da zai rayu babu ɗaya a tsakanin gangar jiki da numfashi ko?”.........✍️ 🏃🏃🏃Hummmmmmmmmmmmmmm🥲 ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖2️⃣6️⃣ .........“Hakane ƴan uwana, na gode da shawarwarin ku, kuma in sha ALLAHU zan yi aiki da su. Dan ALLAH kuyi haƙuri da ɗaga muku hankalin da nakeyi a koda yaushe. Har yanzu ni mai RAUNI ce a cikinku, ina da matuƙar rauni ƴan uwana na sani....”       Kuka ya sarƙeta, rungumeta sukai su duka tausayinta na sake ratsasu. Tabbas gaskiya ta faɗa ita ɗin mai rauni ce a cikinsu. Dan ko lokacin ƙiruciyarsu kadai faɗama Maanal tsiwa da rashin kunya ga shegen tsokanan faɗa. Amma akwai tsoro kamar farar kura. Sai kuma da jarabawar tasu ta fara ita ta ninku mata sau biyu, duk da kuwa suma sau bibbiyu ne, amma ita tata tafi tasu ƙarfi ne. Ba komai yasa hakan ba sai dan sun fita ƙarfin zuciya, sannan su dama basu samu kansu a irin yanayin data samu kanta ba a wancan lokacin kasancewar sun fita hankali da wayo sosai. Sannan su komai dama anyinsa a wasa-wasa ne bakamar ita ba.     Kusan raba wannan daren sukai zaune. Suna sake bama Maanal ƙwarin gwiwa da nasiha data sake ƙarfafata ta kuma ji ta gamsu zataje tayi aikin. Hakan yasa washe gari yanda kowa yay shirin zuwa office itama tayi, yayinda Amaal tun asuba ta kama hanyar Kaduna tunda dama da mota tazo. Sun fito Maanal na ƙoƙarin shiga motar Shahidah sai ga motar RK ta shigo gidan. Dole ta ɗan dakata yayinda Uncle Sadeeq ke dariyar ƙeta cike da tsokana ya dubi Maanal ɗin yana faɗin, “Ga majnoon nan lailah sai ki dakata”.     Dariya Shahidah tayi itama tana amsa masa, “Aifa sai Majnoon ɗin, Rafeeq sam baya gajiya shi kam”.    Maanal dai batace komai ba har RK ɗin ya daidaita parking ya fito a motar. Yayi matuƙar ƙyau cikin farar shadda ɗinkin tazarce. Sai dai babu hula a kansa. Wajen Uncle Sadeeq ya fara zuwa suka gaisa cike da mutunta juna da kulawa. Dan ta ko'ina fa RK ya kafa jam'iyyar sa. Sai kuma ya juya ga Shahidah itama ya gaisheta da mutuntawa. Itama ta amsa masa da kulawa tana tambayarsa yaya aikinsa. Idanunsa akan Maanal ya amsa mata da Alhamdullah.       Ganin irin kallon da yake mata ta ɗan hararesa sannan ta gaishesa a cinkushe. Maimakon amsawa sai ya kalla agogon dake a tsintsiyar hannunsa yana faɗin, “Ashe da banyi sauri ba dana makara?”.      “A gaskiya kam daka makara. Amma ALLAH ya taimakeka, bari kaga muma muyi nan karmu makaran wajen kallon lailah Majnoon”. Uncle Sadeeq ne da wannan magana cike da tsokana yana kallon Maanal. Yayinda Shahidah ke ƴar dariya itama dai hankalin nata akan Maanal ɗin. Motocinsu suka shiga suka fice abinsu aka bar Maanal tsaye sororo, wani irin daka zuciyarta ke mata yau a kansa. Sotake ta ƙarfafa kanta game da shi ta bashi damar kamar yanda ƴan uwanta suka bata shawara a daren jiya. Sai dai ina ji take anya kuwa zata iya hakan? Amma sai wani sashe na zuciyarta ke sake ƙarfafata....        “Good morning my queen”.    RK ya faɗa yana ɗan duƙowa kaɗan saitin kunnenta. Wani irin numfashi taja tare da jan jikinta baya duk da bawani ya matseta bane akwai tazara a tsakaninsu. Murmushi yayi da ɗan ɗage mata gira sama ita kuma ta hararesa tana kauda kanta. Sai kawai ya fashe da dariya. “Oh ni ɗan Mamana irin wannan harar da akemin sai na sace amarya ai ko a sallar isha'i a ɗaura mana auren daga baya. ALLAH ki daina mun wannan hararar rikita min lissafi kike gimbiya. Balle irin yanda nai kewar nan taki kwana biyu dubeni har wata rama nayi marayan ALLAH abin tausayi”.       A yanda yake maganar batama san sanda taji murmushi na neman suɓuce mata ba. Amma sai ta dake abinta ta danne tare da ɗan girgiza kanta ta ce, “ALLAH dai ya shiryeka”.          “Amin matar Rafeeq Kasheem Kura”.     Manaal bata kulashi ba, dan wayarta dake neman agaji, ƙoƙarin cirota ta shigayi a bag shi kuma ya amshi ɗan lunch box ɗinta na abinci data haɗa. Yazeed ne ya bayyana ɓaro-ɓaro akan screen ɗin. Hakan ya saka RK taɓe baki cike da basarwa yabar wajen. Da kallo kawai ta bisa ƙasa-ƙasa tana mai kai wayar kunnenta a nutsenta tai masa sallama. Da kulawa ya amsa mata da ga can tare da tambayarta jikinta tace Alhamdullah ta samu sauƙi.      “Masha ALLAH nima zuwa anjima zan shigo duk kin bi kin tadamin hankali da rashin ganinki tunda nazo aikin ma yaƙi yuwumin yanda nake so. Amma yanzu na ɗan ji ƙarfi tunda na jiki Alhamdullah”.           Shiru tai ta kasa cemasa komai. Shima sai kawai ya saki murmushi daga can, tare da faɗin, “To sarkin kunya bari na barki nima zan fitane ma na kiraki”.    “ALLAH ya tsare ya bada sa'ar abinda za'aje nema”.        “Amin ya rabbi mar'atussaliha”. Ya faɗa can ƙasan maƙoshi cike da shauƙin so da ƙara jin tarin ƙaunarta har ƙarƙashin zuciyarsa. Wayar tai ƙoƙarin maidawa cikin bag ɗin dai-dai da isowar RK wajen da mota. Fitowa yay ya buɗe mata mazaunin gefensa ta shiga ta zauna ya rufe sannan ya zagaya ya shiga shima yay ma motar key suka fice. Yanata dai ɗaɗɗaurewarsa bata kulashi ba. Dan ta fahimci yana masifar kishin Yazeed. Koyaya yaga wani abinda ya shafi Yazeed a tattare da ita zai fara fushi. Itako sai dai yay tayi, dan Yazeed dai tare ya gansu, yazeed kuma abin girmamawarta ne dan ya taka rawar gani a rayuwarsu a lokacin da kowa ya guje musu. Shiko fa daga sama ya tsinceta.      Sunyi nisa a tafiyar motar shiru dan kansa ya yanke shirun nasu ta hanyar ɗan juyowa ya kalleta fuskar dai babu walwala. Sai kuma ya maida kansa ga titi yana faɗin, “Har yanzu baki sanarma su Zulaiha kina Abuja ba ne?”.      Shiru kamar bazata tanka masa ba sai kuma a can ƙasan maƙoshi ta ce, “Sun sani wani abu ya faru ne?”.          “No babu komai, nagane basu zo dubaki ba har yanzu”.       “Ni nace su barshi basai sunzo ba.” “Okay”. Ya faɗa yana ƙara damƙe steering da ƙyau. Daga haka suka sake yin shiru har suka iso Mawaad Company. Yauma kamar wancan ranar komai a tsaftace a kuma nutse yake a companyn. Sai da ya daidaita parking da ƙyau tana ƙoƙarin ɓalle murfin motar ta fita ya dakatar da ita. “Na musu reporting akan baki da lafiya shiyyasa baki zo jiya ba kamar yanda suka buƙata. Dan haka ko sun tambayeki sai kisan amsar da zaki basu. Please dan ALLAH ki kula, wajen nan cike yake da ƙartin banza kar'a tsinceni a titi muna raba hali da al'umma”.       Ɗan kallonsa tai a karo na farko sai kuma ta janye lokaci guda tana mai girgiza kanta. Maimakon amsa masa batunsa ta buɗe kawai ta fice abinta. Ta ɗan fara tafiya taji alamar ana binta a baya, juyowa tai da taga shine riƙe da ƴar lunch box ɗinta. Tsayawa tai tare da miƙa masa hannu, amma sai ya girgiza mata kai yana nuna mata hanya alamar suje. Babu yanda ta iya haka suka jera har cikin Companyn...       Wani irin lumshe idanu AA Darma dake zaune cikin motarsa daga baya dan driver ne yau ya kawo shi Office ɗin tare da datse leɓensa ba ƙasa da ƙarfi. Sai dai sam bazaka taɓa fahimtar hakan ba kasancewar jarida a hannunsa yana dubawa. Shima isowarsu kenan, kuma tun a hanya a wajen fitilar bada hannu yaga motar RK ɗin, ya hango mace a motar amma baiga wacece ba. Sai dai haka kawai zuciyarsa ta bashi wacece ɗin, dan haka koda suka iso kasancewar sun riga su RK ɗin shigowa Companyn sai bai fita a motar ba. Komai daya faru a kan idanunsa ne dake sakaye a cikin glass mai matuƙar haske daya ƙawata ƙyawun nutsatstsiyar fuskarsa. A hankali yay wurgi da jaridar hannun nasa a sit ɗin gefensa.        Shi dai driver bai san mike faruwa ba, amma yana tunanin ko wani abin ogan nasa yake shiyyasa. Suna a haka RK ya fito fuskarsa cike da walwala kamar ba shine ya gama fushin kishin Yazeed ba. Motarsa ya shiga abinsa yabar harabar companyn, securitys ɗin gate suka ɗage masa karfe da aka gitta a ƙofar bayan gate ya fice. Wani siririn tsaki AA Darma ya saki a can ƙasan maƙoshinsa. Sai kuma ya ɓalle murfin motar aɗan fusace ya fito batare daya ɗauki komai nasa dake a motar ba. Sanye yake cikin ash color ɗin suit masu haske da sukai masa shegen ƙyau. Daga ciki black rigace mai wuyanta har saman wuya. Yanda yake taku cike da bada faɗi da cika waje ma kawai abin kallo ne. Securitys sai gaidashi suke amma hannu kawai yake iya ɗaga musu batare da ko kallonsu ba. Koda yazo ga ƙofar shiga da sauri aka buɗe masa ya shige drivern sa biye da shi da tarkacensa. Tsitt kake ji ma'aikatan dake wajen sakamakon shigowar tasa. Sai kuma kowa ya shiga faɗin, “Good morning Sir!”. Hannu kawai ya ɗaga musu sau ɗaya yay wucewarsa batare da ko kallon kowa ba anan ma. Hakan ya sakasu fahimtar yau fa gizagon boss ɗin yafi na kullum, sai kowa ya ƙara kama kansa.      Elevator ya shiga tare da danna floor ɗin ƙarshe 6th da office ɗinsa yake, shima drivern nasa ya shiga. Ƙofar zata fara rufewa Maanal da AS da yay mata rakkiya office tai singing da ake buƙatar tayi suka iso wajen. Shigowa sukai da sauri batare da hankalin AS ɗin yakai ga wanda ke cikin elevator ɗin ba kasancewar ya ɗan juyama ƙofar baya yana danna waya. Balle kuma Maanal da itama gaba ɗaya nata hankalin ke akan wayarta. Sai da suka gama shigowar AS ya shaƙi ƙamshin turaren boss. Sai kuma sukai ido huɗu da driver. Ya juya da sauri nan ma sukai ido huɗu da AA Darma.         Cikin ɗan rawar baki ya ce, “So...sorry sir good morning. ALLAH bamma lura kaine a ciki ba. Zan kai new staff ɗinmu office ɗinta ne bisa umarnin Director Mustapha”.       Kai kawai AA ɗin ya jinjina masa, yayinda Maanal da zuciyarta ke wani irin bugawa da sauri-sauri ta sake dakewa abinta dan tunda AS ya fara magana ta ɗan ɗago ta gefen ido ta saci kallon wanda yakema wannan rawar bakin sai ta ɗauke kanta. Ɗan duƙowa yayi kaɗan ƙasa-ƙasa ya furta, “Boss ne kiyi gaisuwa”.       Shiru tai kamar bazata kulashi ba sai kuma a hankali a can ƙasan maƙoshi batare data kalla kowa ba ta furta, “Morning”. Daga haka taja bakinta tai shiru. Ita tai abin amma AS ta bari da ruɗani, sai wani irin haɗiyar yawu yake yana kallon AA ɗin ta gefen ido ko zaice wani abu akan gaisuwar rainin wayon sabuwar ma'aikaciyar tasu.... __________★         Fuska cike da murmushi Hajiya Basariyya ke kallon kayan da ƴar Tata Huznah ta baje a gabanta. Ba kayan ci bane ba kuma na sakawa ba kayan da malam ne na Zaria ya haɗoma Huznah ɗin bayan ta ɗauki tsawon kwanaki tana acan ana tsumata da wasu aikin. Ba kuma akan kowa akai hakan ba sai sabon saurayinta data samo a birnin tarayya Abuja lokacin bikin ƴar ƙawar Hajiya Basariyya ɗin. Sam kayan babu wani ƙyan gani ko birgewa a kallonsu. dan kuwa tarin guraye ne da ruwayen magani da layu sai garin magungunan da turarruka na shafawa harda su hoda da kwalli na idonka idona. Sai da ta gama mata bayanin komai dalla-dalla kafin ta ta fuska ɗauke da murmushi ta ce, “Kin daiga komai Ummi, bayan kuma wanda yay mun a jikina dan na aikata iya aikatuwa. Yanzu dai babu zama dole na shirya na wuce Abuja. Dan ya tabbatar min da in dai nayi komai yanda ya dace babu fashi auren mu zai kasance tare da na Yazeed ne a gidan nan”.        “Kai Alhamdullah Masha ALLAH. ALLAH dai ya sakama malam da alkairi wlhy. Shiyyasa bana baƙin cikin biyansa duk abinda ya buƙata dan shima ana samun biyan buƙatar daga nasa aikin. Tafiya Abuja kam dole ne. Sai dai Daddynku nake tsoro dan yana gari. Dama da yaya ya bari kika tafi Zaria ɗin nan. Yanzu ko akace Abuja nasan da rigima”.      Cikin matuƙar damuwa Huznah ta ce, “To Ummi yanzu yaya zamuyi kenan, dan ni dai ko ana ha maza ha mata sai naje Abujar nan wlhy??”......✍️             _Tofa, maji ma gani wai an bizne tsohuwa da ranta jama'a 😂🏃._ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖2️⃣7️⃣ ........Maimakon Hajiya Basariyya taji haushin furucin ƴar tata sai ta tuntsure da dariya tana faɗin, “Ja'ira wato ke ƴar daɗi soyayya ko? Kwantar ma da hankalinki komai zaizo da sauƙi bani lokaci dai nayi tunani.”      “To Ummi nidai dan ALLAH kar tunanin naki ya wuce yau da gobe dai. Dan a matse nake gashi nayi kewarsa ina son ganinsa.”      Anan ɗin ma dariya Hajiya Basariyya ta sanya abinta. __________★       A can ɓangaren Aunty Sabuwa ma shiri takema ƴarta na mugayen mallaka, dan hatta da Hajiya Yaya aba'a ƙyaleba tuni sunanta na wajen boka. Kai shi kansa Daddyn ba tsira yay ba da sauran ƙannen Yazeed mata. Dan tace tako ina sai ta bama ƴarta garkuwa. Tako bayar ɗin gwagwargwadon abinda take ganin ya wadaceta. Ga maganin mata ana ɗirkama Nazeefa kamar babu gobe, gefe kuma fetsararrun ƙawayen uwarta su Hajiya Malika na koya mata kissa da kisisina harda salon kwanciya da miji.      A tacan ɓangaren Mahaifinta kuwa yana nasa shirin ne akan Daddy. Dan a wannan karon yaci alwashin samawa kansa nasara akan Daddyn. Sai kuma shirin biki na ƴar gata da sukeyi da ga shi har Aunty Sabuwa ɗin.      Ata nan ɓangaren Hajiya Yaya shirin suma suke na garari, dan a satin nan zata wuce Dubai ita da Baraka da Asalamiyya su haɗo lefe da nasu kayan cin bikin. Da farko Daddy ya hana tafiyar, saboda ya fahimci ana komai ne dan ƙuntatama Ammie. Amma sai Ammien ta dinga masa roko da magiya dan tasan hanawar wata sabuwar rigima ce, kuma dai laifin a kanta da baya so zai ƙare. Dan tuni Hajiya Basariyya tayi uwa tayi maɗaukiya a bikin shiyyasa ita ake kiranta ƴar baƙin ciki. Haka dai dole Daddy ya bari dan yana matuƙar jin kunyar Ammie ta roƙesa abu ya kasa mata saboda dattakonta itama, sai dai da sharaɗin karsu wuce sati ɗaya, idan kuma hakan ta faru zasu sha mamakinsa. To a hakan ma dai Ammie bata tsira ba dan sai da tasha zagi da habaice-habaice. Ita dai bata kulasu ba kamar yanda ta saba. Sai ma ta maida hankali akan shirin Daddy da shima yake yi dan wannan shine karo na biyu da zai aurar. Na farko ya aurar da su Shahidah da Asalamiyya a rana ɗaya, duk da dai an kwashi matuƙar rikici a wannan aure dan Hajiya Yaya cewa tai baza'a haɗa mata auren ƴa da agololi ba. Shiko yace tayi kaɗan tayi tsororo ma.  Bayan dai an sha fama dole ta haƙura akayi yanda ya tsara ɗin. Sai dai ita Asalamiyya ma nata auren bamai jimawa bane. Dan a gida ma ta haifi ƴarta. To yanzu ko Yazeed kaɗai za'a aurar. Babban ɗansa kuma namiji, sannan ɗa mafi soyuwa a garesa da Hajiya Yaya. Damma ALLAH ya ragewa aya zaƙinta auren ba wanda yake so bane ba. Saboda har yanzu sam Daddy baya son wannan haɗin kawai dai babu yanda zai yi ne ya haƙura. Amma yaci alwashin sai ya bama kowa mamaki a auren Maanal da Yazeed in sha ALLAHU.     To daga can gidan Alhaji Mamman ma dai shirin suke. Dan jikokin duka biyu nasu ne, dan haka dole suma su taka tasu rawar da aljihunsu da kuma matsayinsu. Dan haka suka kasance cikin irin nasu shirin su da sauran ƴaƴansu da dangi. Dan ko tafiya Dubai ta zama kamar za'ayi ta a tare ne bisa ɓangarori biyu. Ba Hajiya Yaya da Asalamiyya da Baraka bane kawai a tafiyar harda mahaifiyar su Hajiya Yaya ɗin da kuma wasu ƙannensu Hajiya Yayan su biyu, da harda Aunty Sabuwa amma ta zamewa tafiyar dan akwai binne-binnen da suke son zuwa suyi a inda za'a saka amarya duk da ma Daddy ya ɓata musu tafiyar da buri wai anan gidan su Yazeed ɗin zasu fara zama a tare da su. A yanzu hakama ana kan gyara sashen samarin gidan da dama shine dai zaune a ciki kasancewarsa namiji tilo a baya sai yanzu da Ammie ta haifi Waleed da Hameed. Suma acan ɗin suke amma yanzu Daddy yasa ana musu nasu ginin ata can bayan na Yazeed ɗin kasancewar akwai fili sosai. Sai suka dawo sashen Ammie yanzu tunda ita kaɗaice. A wannan gini ma dai sai da akai ɗan rikici, ɗan daga Hajiya Yaya har Hajiya Basariyya nunawa sukai basu yarda ba. Sai da Daddyn yay musu kaca-kaca yace idan akwai wadda ta haifesa a cikinsu kota saya masa gidan ko suka haɗa kuɗi suka saya to tazo ta hanashi yima yaransa wajen zama sannan suka kama kansu. Amma hakan bai hanasu komawa gefe suna zagin Ammie ba da aibantata. ___________★        Shine ya fara fita a elevator ɗin, hakan yasa AS da driver rufa masa baya cikin hanzari. Cikin takaici da ƙunar zuciya Maanal ta raka bayansu da harara kafin itama ta fito tana jan tsaki. Maimakon tabi bayansu sai kawai ta samu waje ta zauna anan wajen elevator ɗin. Tsahon mintuna goma sai ga AS ya dawo wajen. Da mamaki yake faɗin, “Ina can inata tunanin inda kika maƙale ashe kina nan.”     Ɗan ɗagowa tai kawai ta kallesa batare da tace dashi komai ba. Shima sai ya kama kansa dan ya fahimci Maanal irin mutanen nan ne masu masifar miskilanci da kame kai. Har office ɗin Directors Mustapha ya kaita, sai dai sun samu baya ciki da alama ya ɗan fita. Wajen zama ya nuna mata yana faɗin, “Ki jirasa anan duk inda yake nasan baiyi nisa ba”. Kanta kawai ta iya jinjina masa. Shima sai ya juya ya fita abinsa. Bayan futarsa ajiyar zuciya ta ɗan sauke da numfashi mai ƙarfi. Dai-dai lokacin idanunta suka sauka akan hotuna huɗu da aka saka daga can saman saitin inda kujerar mai office ɗin take. Hoton farko shugaban ƙasa ne a jiki, sai Ministan Abuja. Hoto na biyu AA Darma ne da yay wani kalar masifar ƙyau, sanye yake cikin wasu shegun suit baƙaƙe da adon gold a jikinsu mai matuƙar ƙyalli, yaɗan zauna a saman kujera mai tsaho ɗin nan, sai ya kasance kamar ya zauna a karkace ƙafarsa ɗaya ya sakko ƙasa sosai ɗayar na daga jikin ƙarfen da akaima kujerar kwalliya. Takalminsa baƙi da kwalliyar gold shima. Bai saka rigar suit ɗin ba, yana riƙe da ita ne kawai da hannunsa na dama dake sanye da agogo kalar gold a saman kafaɗarsa, sai farar long sleeve shirt ɗin data sauna ɗaran a jikinsa ta fiddo da girman jikin dake a buɗe. Ya saki wani mayataccen murmushi daya sakata ƙurama cikakkiyar fuskarsa mai kwarjini da adon gashi ido. Idanunsa sanye da farin gilashi da tun ƙuruciya tasan yana sakawa. Sun wani haska oily idanun nasa da suke farare tas kamar an watsa musu madara tsabar yanda suke ƙyalli da ɗaukar idanu.... Kaɗan Director Mustapha ya ɗan bubbuga desk ɗin, dan sai sallama yake amma babu alamar tasan da shigowarsa. Numfashi ta ɗan ja ta fesar cike da kame kanta da vasarwa ta dawo hayyacinta. Murmushi ya ɗan yi a ƙasan ransa yace (Boss Sarkin sa'a. Akoda yaushe cikin kama zuciyar ƴammata yake).     Ita kam kicin-kicin ta sake yi da fuska sannan ta shiga gaishe da Director ɗin. Ya amsa mata da kulawa tare da mata barka da zuwa. Kanta kawai ta jinjina masa shi kuma yakai zaune yana ɗaukar file ɗinta ya shiga dubawa. Sai lokacin ta sake bin office ɗin da kallo daki-daki, idonta ta ƙarasa saukewa akan hoton AA ɗin, sai kuma ya janye ta maida kan ɗayan hoton dake kusa da nasa da bata kalla ba. Mace ce sanye cikin baƙin hijjab da niƙab, hatta idanun nata ana iya ganinsu ne kawai ta cikin sirrin farin gilashin data sanya. Hakan yasa baka isa tantance wacece a hoton ba duk iya kallon ƙurullarka da bin ƙwaƙwaƙwafi, dan hoton yasha editing ta yanda aka ɓadda kamanin komai.       A hankali ta taɓe baki da sake kauda kanta zuciyarta na ayyana ma maybe matarsa ce. Tunkuɗe tunanin tayi gefe ta maida hankalinta ga Director Mustapha dake mata magana. Umarnin biyosa ya bata, babu musu ta miƙe tare da ɗaukar hand bag ɗinta tabi bayansa. Wani office dake kusa da nashi suka shiga. Nan ma sun sami mai office ɗin daya kasance ba bahaushe ba. Bayan sun gaisa ya amshi file ɗin hannun Director Mustapha ya saka hannu. Daga haka suka fito. A ƙofa suka haɗu da wani matashin saurayi, cike da girmamawa ya shiga gaida Director. Shima ya amsa masa da kulawa yana nuna masa Maanal. “Itama Watch Designer ce, kaje da ita department naku, sit ɗin da aka shirya jiya nata ne”. Fuskar saurayin da murmushi yana kallon Maanal ya amsa ma Director da girmamawa. Ita ko sai wani basarwa take. Bai damu ba ya fara gaidata, sai ta amsa kamar wadda taji kunya. Shi dai director kallonsu kawai yake yana sake jinjina miskilancin yarinyar. Saurayin daya kira sunansa da Yaqub tun'a cikin Elevator ɗin ya gabatar mata da kansa matsayin Watch Designer shima. Ɗan murmushi kawai Maanal ta masa. Dan ta fahimci yana da nutsuwa. Koda suka fito anata kallonsu, bata damu ba dan ita babu wanda take kallo har suka iso rukunin su daya kasance matsayin office. Su takwas ne, kuma duk artists ne suma ɗin, sai dai abin damuwar ita kaɗai ce mace a cikinsu. Amma sai ta dake, dan tasan zata iya zama da kowa. Ta gaishesu tana sake ɗaure fuska ganin yanda suke kallonta. Yayinda Yaqub ya gabatar da ita a wajensu shi dai. Suma ya shiga gabatar da su da sunayensu ɗaya bayan ɗaya. Kafin ya nuna mata wajen zamanta dake a farko. Sun mata maraba da zuwa cikin farin ciki, itama sai ta ɗan musu murmushi kaɗan. Daga haka takai zaune tana dudduba komai nata dake a wajen. Batare data damu dasu ba kuma wayarta ta ɗauka ta shiga ɗaukar komai na iya wajenta hoto, Ammie ta turamawa, alamar wayar a hannun Ammie take mintuna biyu ba'a ƙullaba sai ga video call ɗin Ammien ya shigo. Murmushi mai sanyi Maanal ta saki tana mai gaggawar amsa kiran sai ga Ammie tar-tar ta fito. Cikin murmushin farin ciki Maanal tace, “Uhm kaga amaryar Daddy”.      Daƙuwa Ammie tai mata itama tana murmushin ta ce, “Ungo naki nan ja'ira yau kuma nice bar tsokanrki”.        Karo na farko Maanal ta sanya dariya, abinda kakan daɗe a yanzu baka gani ba a tare da ita. Duk ko sai samarin suka shagala suna kallonta duk da su basa ganin Ammie sabo a desk ta ɗaura wayar. Ita ko cikin rashin damuwa da wanzuwar su a wajen tace da Ammie, “Tom yi haƙuri Hajiya Ammie na. Ina fatan kin tashi cikin aminci da ƙoshin lafiya tare da farin ciki a wannan rana ta laraba ranar samu inji Nene”.        Sosai murmushin Ammie ya sake ƙawatuwa. Da kulawa ta ce, “Alhamdullah Auta. Ya ƙarfin jikinki? Ya kuma sabon office?”.      “Alhamdullahi Ammie na warke abuna. Sabon office kuma gashi ki sanya masa albarka daga bakinki mai tsarki”. Tai maganar tana miƙewa da wayar a hannu ta maida back camara tana haska mata ko'ina na office ɗin, sai dai koda wasa bata yarda ta hasko samarin nan ba. Sosai Ammie ta shiga yabawa da sanya albarka. Ta kumayi addu'oi sosai ga autar tata. Sannan suka ɗan yi hira sukai sallama tace ta fara aikinta. Fuskarta da murmushi ta ajiye wayar, ita kaɗai tasan irin tari-tarin ƙaunar da takema wannan baiwar ALLAH. Mahaifiyarsu dabance a cikin daban ɗin da bazai ƙididdigu a zukatansu ba. Fatansu dai ALLAH ya ƙara mata lafiya da nisan kwana masu albarka. (Tare da iyayenmu baki ɗaya. Ka gafartama wanda muka rasa ka yafe musu KURAKURANSU😭🙏 damu da muke raye baki ɗaya).      Jan kujerar tata tai har zuwa gaban kantar da aka ajiye musu a office ɗin dan kusan da ita ma aka zagaye wajen. Komai na kayan zane-zanen da zasu iya buƙata akwai a wajen. A haka ta zazzaɓo duk abinda take buƙata a lokacin ta sake burko tayoyin kujerar ta dawo da ita mazauninta. Sosai ta ringa ƙoƙarin ture komai a ranta ta maida hankalinta ga fara abinda ya kawota duk da tana ji a jikinta sauran abokan aikinta hankalinsu na a kanta ta wani sharesu tamkar ita ɗaya ce a wajen. Wani zanen Designs na agoguna data ƙirƙira yanzun nan a kanta ta fara cike da ƙwarewa. Cikin ƙanƙanin lokaci ya haɗa su tsaf su biyu kamar ka saka hannu ka ɗauka daga takardan. Bayan ta gama zana su a dunƙule sai kuma ta koma zana ɓangare-ɓangare ɗin jikinsu kowanne tana saka masa suna da amfanin da zai yi a cikin agogon. Hakanne ya ja mata lokaci sosai dan har ƙarfe ɗayan rana. Jin ana kiran sallar zuhur daga masallacin cikin companyn ya sata sauke ajiyar zuciya da ajiye kayan aikin nata ta miƙar da hannunta da ya ɗan sage da ambaton sunan ALLAH.       Miƙewa tai zuwa window ɗin office ɗin ta leƙa batare data ma kowa magana ba, dan daga wajen ana hango masallacin. Hango ma'aikata tayi nata fita zuwa ƙatuwar harabar companyn. Ganin mazansu da matansu ne yasa ta fahimci masallacin harda mata kenan. Dan wasu ma na ƙoƙarin shigane yayinda wasu suka kasance rukuni-rukini suna hirarsu. Sai wasu dake alwala ta can ƙarshen katangar inda aka tanada domin hakan. Huci taɗan furzar daga bakinta tare da barin wajen, dai-dai suma su Yaqub na miƙewa. Sauran fita sukai gulma fal bakinsu, yayinda shi kuma Yaqub yazo inda take. Shine ya sanar mata tazo suje salla. Kanta kawai ta jinjina masa ta baro wajen ALLAH ya sota ta taho da hijjab kasancewar yau ma shigar Abaya ce a jikinta ƙirar Dubai ruwan ƙasa. Hijjab ɗin ta buɗe ta saka bayan ta zame hularta da ɗan kwalin abayar data naɗo a kanta ta ajiye saboda hijjabin ya rufe mata gashinta sosai. Hankalinta kwance kuma kanta tsaye ta fito a office ɗin daga ita sai wayarta kawai a hannu. Kusan duk an fice ma, dan wajen yayi tsitt, dan haka a gaggauce ta nufi elevator jin za'a tada sallar kasancewar su suna a 4th floor ne. Bata gama dai-daita tsaiwarta ba kawai taji shigowar mutum babu ko sallama. Dan haka ta ɗago manyan idanunta domin ganin wane sallamemmen ne haka........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖2️⃣8️⃣ .......Saurin janye idanun nata tai ƙirjinta na wani masifar dokawa. Sai dai ta wani dake a zahiri yayinda fuskarta ke sake komawa ciɗin-ciɗin fiye da yanda tashi take. Boss ne da kansa ba wani ba. Wato AA Darma, da alama shima ya makara fita sallar ne, dan illahirin fuskarsa da hannayensa da ƙafarsa dake sanye da slippers daya saka dan ba takalman da yazo dasu a ƙafarsa bane cover shoes sai nason ruwa suke yi. Elevator na tsayawa itace tai saurin fara ficewa dan harga ALLAH jinta take kamar an matse a cikin rami tsabar yanda ya cika ko'ina da kwarjininsa. Da kallo ya ɗan bita, sai kuma miya tuna oho yay saurin janye idanunsa shima yana fita daga elevator ɗin.         Dukansu basu samu raka'ar farko ba. Koda aka idar da sallar mafi yawan ma'aikatan sun wuce kitchen ne kai tsaye, dan ana musu abincin rana a wajen harma dana safe. A manyan dai ba kowa ne ke nufar kitchen ɗin ba sai wanda yaso hakan kasancewar suna da damar sakawa a kawo musu har office. Manaal ma daba gama sanin tsarin tai ba duk da an bata komai a rubuce tun a ranar interview karantawa ne batai ba office ta koma. Hankalinta a rarrabe sai dai tana iya ƙoƙarin ta na ganin ta saita kanta ta buɗe lunch box ɗinta ta fidda abincinta ta hau ci tana cigaba da sarrafa computer ɗinta domin maida aikin zanen da tayi a ciki. A haka a shiririce ta gama shigar da komai kafin ta naɗesa a flash drive ta ajiye. Koda an buƙacesa a wajen meeting da shi zatai amfani. Knocking ƙofar akayi, batare da ta canja daga yanda take ba ta bada iznin shigowa dan ita kaɗaice har yanzu su Yaqub babu wanda ya dawo. Wata budurwa ce da bazasu wuce sa'anni ba. Sanye take da skirt da riga na atamfa sai ɗan mayafi data yana. Cikin girmamawa ta gaishe da Maanal ɗin. Amsa mata tai da kulawa. Hakan sai ya saka yarinyar farin ciki dan yanzu ake gulmar Maanal ɗin a ƙasa cewar dagani zatayi girman kai, sai kuma ita tazo taga ba hakan ba yanzu.       “Sunana Mabaruka Rabi'u. Ina ɗaya daga cikin Sales and Marketing Department. HOD ne yace a sanar miki ana buƙatarki a ƙasa idan babu damuwa”.      Cikin ɗan sakewar fuska da ba murmushi take ba Maanal ta ce, “Okay sister Mabaruka ba damuwa gani nan tafe”.      Murmushi Maburaka ta mata tare da sake ɗan rissinawar girmamawa ta furta, “Na barki lafiya”. Daga haka ta fice a office ɗin. Ajiyar numfashi Maanal ta ɗan sauke, sai kuma ta shiga tattara tarkacen kayan da taci abinci ta maidasu a lunch box ɗin. Ruwa tasha ta ɗan gyara fuskarta sannan ta miƙe ta fice a nutsenta daga ita sai wayarta a hannu. A First floor ta samu kusan dukkan ƙananun ma'aikatan harda waɗanda ba nan ɗinne mazauninsu ba. Sai dai da'alama duk an tattarasu anan ɗinne dan har su Yaqub ma suna a wajen ashe. Duk da cika mata idon da sukai haka ta dake ta gaishe da HOD dake ta faman sakar mata murmushi. Yana ɗaya daga cikin wanda sukai mata interview. Amsa mata yay da kulawa, kafin ya juya ga ma'aikatan yay sallama. Duk amsawar sukayi duk da kuwa ba dukane musulmai ba a wajen. Ɗan juyowa yay tare da nuna musu Maanal cikin harshen turanci ta ce. “Wannan itace sabuwar _Watch Designer_ ɗin Mawaad Company da aka sake ƙaro mana in sha ALLAHU, zatai muku introducing kanta”.       Tafi suka shiga yi gaba ɗayansu. Hakan yasa Maanal ɗan sakin murmushi tana binsu da kallo, sai da suka lafa sannan ta gyara tsaiwarta cike da nitsuwa ta furta, Sunana Maanal Habeeb Giro. Junior Watch Designer kamar yanda aikina HOD ya faɗa. Ina fatan zan samu haɗin kai da yarda daga gareku baki ɗaya”.      “In sha ALLAHU!!”. Suka faɗa cikin haɗa baki. Murmushi ta sakar musu a karo na biyu mai matuƙar taushi. Sai kuma ta haɗe hannayenta waje guda ta sake furta, “Ina mika godiya a gareku da fatan alkairi baki ɗaya. ALLAH ya bamu ƙwarin gwiwar sauke hakkin dake kayinmu baki ɗaya”.     Nan ma sun amsa mata da amin. Daga haka HOD ya ɗan ƙara mata bayani akansu. Kafin ya sallamesu kowa ya koma kan nasa aikin. Ita kuma suka nufi elevator tare da shi. Sai faman zuba mata surutu yake ita dai batace komai ba sai ɗan murmushi da take masa na karar haɗuwar farko. Conference room suka nufa kai tsaye daga nan. In da ta sami dukkanin shugabannin da alama su ake jira ma a wajen. Wajen zama duk suka nema, a dai-dai kuma lokacin CEO ya shigo AS ɗinsa biye da shi. Duk miƙewa sukai alamar girmamawa, sai da ya zauna AS ɗinsa ya ajiye masa kayan hannunsa gabansa sannan ya ɗan ɗago ya dubesu. Zaunen suka kai suma a nutse, daga haka room ɗin yay ɗan shiru na kusan mintuna uku kafin ya ajiye tab ɗin hannunsa da yake sarrafawa yay gyaran murya yana kallonsu cike da dakewa da nutsuwarsa. Suma sake nutsuwar sukai da maida hankalinsu garesa. Banda Maanal da tun kallon farko data masa a sanda yake shigowa ta ɗauke kanta bata sake ba. Gaba ɗaya jinta take a takure a wajen dan su biyu ne kawai mata. Sallama yay musu kafin ya sauke dubansa ga tab ɗin gabansa ya fara magana acan ƙasan maƙoshi. “Wannan taro ne daya haɗa ɓangarori guda biyu, wato na shugabanni da kuma ƙirƙira da zane na wannan company. Wato Executive Team da kuma Design and development. Kafin kai tsaye mu fara abinda ya kawo mu akwai sabuwar staff data shigo cikinmu zai ƙyautu ta gabatar da kanta anan”.        Ji Maanal tai kamar ta kai masa naushi dan haushi, amma sai ta dake taƙi koda motsi sai da CTO dake gefenta yay mata magana ƙasa-ƙasa. “Sistet Maanal”.          Komai batace ba ta miƙe cike da kamewa ta furta, “Sunana Maanal Habeeb Umar Giro. Junior Watch Designer in sha ALLAHU”.      Sunyi welcoming nata baki ɗaya tare da mata fatan alkairi. Bayan ta koma ta zauna ya cigaba da faɗin, makasudin shi wannan zaman akan sabon project namu ne in sha ALLAHU. Wasu sun san da shi wasu basu sani ba saboda rashin samun zaman meeting da ba'aiba a wancan satin gaba ɗaya. Akwai Companyn da zamu fitar ma sabon agogo, sun kuma bamu zaɓi kafin mu sake zama dasu. Dan haka Design and development ko kuna da wani sabon design da zaku gabatar mana mu duba?”.      Bayan Maanal akwai Watch Designers Directors har uku a wajen, sai dai dukansu kowanne nada iya limit ɗin aikinsa ta yanda baya shiga aikin wani. Hakan yasa ɗaya daga cikinsu ɗagowa ya ɗan dubi Boss ɗin. “E to Sir bamu san ko yaya tsarin project ɗin zai kasance ba. Sai musan a cikinmu wazai bada sample”     Kansa ya ɗan gyaɗa, sai kuma ya kai dubansa ga Sales and Marketing Manager. Da sauri ya miƙe dan yasan minene ma'anar kallon. Bayani yay a taƙaice, Dan haka sai duk suka maida hankalinsu ga Director Steven. Kansa ta gyaɗa shima tare da maida kallonsa ga Maanal, suma sauran duk sai suka koma kallonta. Yanda suke kallon natane ya bata mamaki, kafin ta nema ƙarin bayani Director Steven ya ce, “Wannan aikinki ne Sister Maanal. Idan kinada wani sample na zane a ƙasa company na buƙatar gani, idan kuma babu zaki iya neman lamanin samarwa”.     Gaba ɗaya sai Maanal taji ma kamar zata daburce. Amma ta shiga ambaton ALLAH tare da aro jarumta. Cikin ƴar dakiyar da nutsuwar data azama kanta ta dole ta bata ta jinjina ma Director kanta. Sai kuma ta ɗan kallesu itama ta fara bayani. “Zan iya gabatar da wanda ke a hannuna ɗin idan basuyi ba sai na sake wasu sabbi”.        Cikin gamsu duk suka gyaɗa mata kai, kafin boss ya gama shan ƙamshinsa batare daya kalleta ba ya furta, “Zaki iya nunawa”.     Bata tanka ba, sai dai ta miƙe hannunta ɗauke da flash drive data naɗe zanen ɗazun da tayi. Amsa Director Steven yayi a matsayinsa na shugaban sashenta, ya nufi ƙaton television dake kusan bango guda a room ɗin yay connecting, atake ɗan tambarin data saka na farko mai ɗauke da zanen agogo mai ƙyau da zanen fuskarta a tsakkiya ya bayyana. Remote ɗin Director Steven ya miƙa mata, dole ta fito daga inda take tsaye ta koma gaban tvn. A nutsenta ta fara danna hoto na biyu ya fito, agogone mai ƙyau da tsari matuƙa duk da kasancewar a zane yake. A take duk suka shiga ambaton, “Woow!! Woow!!” a hankali. Shi dai boss kaimai baice ba, amma fa ya zubama hoton idanu yanda ya kamata, bayani tayi cikakke akan agogon da tsarinsa da nauyinsa. Sai kuma ta koma nuna sassan jikinsa da sunayen data basu da yanda yakama ace ingancinsu ya kasance. Da ƙarshe tai bayanin yanda agogon zai iya buƙatar ingantaccen aiki kafin fitar da shi. Tafa mata suka shigayi tamkar conference room ɗin zai buga shima. Dan har ga ALLAH tayi matuƙar gama birgesu, tayi dukkan bayanin da har sauran ɓangarorin zasu iya yi. Ashekaru kaf ɗinsu babu wanda bai bata fin shekara goma zuwa ashirin ba, dan itace ƙarshen ƙanƙanta da ƙarancin shekaru a cikin nasu, hatta da ɗayar macen zata iya girmar Shahidah ma balle ita. Taji daɗin yanda suka yaba mata duk da shi mai gayya da aikin baice komai ba dai. Sai da duk suka lafa itama ta dawo ta zauna a nata mazauni kafin yay ƴar gyaran murya.        “Zamuyi nazari akan wannan ɗin, amma WD Maanal zata iya samar mana da wasu samples kamar uku bayan wannan daga nan zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu. Sai ku haɗasu a sake tattaunawa”.      Duk sun gamsu da hakan. Dan haka ba'a wani sake jan zancen ba taron ya watse. Shine ya fara ficewa a room ɗin AS ɗinsa biye da shi. Duk miƙewa suma sukai hankalinsu akan Maanal suna sake jinjinama ƙoƙarin ta da ƙarfafata. Itako sai wani ɗan karen daɗi take ji kamar ta ciji uwawunta. Ta ƙara ta fita a wajen ta kira Ammie ta bata labari, kai har RK sai yasha labari yau....      Koda Maanal ta koma office zaman wasu sabbin samples na zanen ta fara dan babu wasa batare data kula kowa ba. Garama Yaqub ya mata sannu da zuwa. Tayi nisa a aikin nata akai mudu knocking ƙofa. Batare data ɗago ba ita dai taji sauran na magana da shi. Saurayine kamar su Yaqub da zai iya girmarta ita kam a shekaru, amma kasancewarsu oganninsa cike da girmamawa ya gaishesu. Sai kuma ya maida hankalinsa kan Maanal. Hakanne ya sata ɗagowa ta ɗan kallesa. Duk da tayi mamaki sai ta danne, ta amsa masa da kai. Bai damuba ya cigaba da faɗin, “Sister Maanal kinada visitor”.      “Visitor?”.   Ta maimaita da mamaki. Sake tabbatar mata da hakan yay ta ha hanyar jinjina kansa. Ta ɗan yi shiru kamar mai nazari tana wasa da pencil akan lips ɗinta sai kuma ta ce, “Okay ina zuwa”.       Da girmamawa ya amsa mata da, “Ai kamar ɗan gida yake. Bari na masa iso”. Bai jira amsarta ba ya juya ya fita. Ba'a rufa mintuna biyar ba aka sake knocking ƙofar. Zamanta ta gyara da veil ɗinta, yayinda hankalin su Zaharadeen duk yana akan mai shigowar. Yana buɗe ƙofar ƙamshin turarensa na rige-rigen fara iso mata a hanci, hakan yasa ta ɗan ɗago idanu ta kallesa. Murmushi ya sakar mata yana jingina da ƙofar tare da harɗe ƙafafunsa da hannayensa a ƙirji. Sai kuma ya laluba aljihunsa ya ciro wayarsa ƙirar kamfanin Samsung mai ƙyawu da tsada ya shiga mata hotuna. Hararsa ta ɗan yi tana mai girgiza kanta ta maida ga abinda take yi. Sai da ya gama dan kansa kafin ya kai duƙe ya ɗauki abinda ya ajiye a ƙasa yana ƙarasa shigowa da faɗin, “Oh oh my queen Kinga kuwa yanda kujerar nan tai matuƙar dacewa da ke. Kin gama cika Watch Designer Maanal ɗinki Tawajena. Dan haka ina tayaki murnar shiga sabon Office. Amin afuwa dana kasance a late, tun safe naso nayi hakan uziri yasa ban zauna ba na koma asibiti. Naso tahowa da rana hakan bai yiwu ba kuma dai”.       Ita dai kallonsa kawai take yana tsiyaya surutunsa kamar yanda sauran ma ke kallonsa suna murmushi. Hannu ya shiga basu, suna amsa da sauri da kuma girmamawa dan sun san yana da wani babban matsayi da kima a companyn. Dai da ya gama gaisawa da su ya maido hankalinsa kanta yana fiddo cake mai ƙyau daga cikin kwalinsa. Sai kuma ya tsitstsira abu a kansa kamar wata mai shirin hure birthday cake ya kunna masa wuta. Ɗauka yay ya zagaya ta inda take ya ajiye a gabanta sosai bayan ya tattare kayan zanen dake a gabanta ya ɗauke su gefe........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖2️⃣9️⃣ .........“Bismillanku”. Ya faɗa idonsa akansu Zaharadeen. Sai kuma ya koma ga ƙofa yana faɗin, “Kuma ku shigo”. Mamakine ya kamata ganin ma'aikatansu kusan su goma sun shigo harda AS ɗin Boss. Gaishesu sukai saboda kusan dukansu suna a sama da su. Da kai kawai ta iya amsa musu ita dai saboda al'ajabin RK. Daga haka ta juyo tana masa wani kallon. Ganin yanda ta zuba masa manyan idanun nata masu rikitashi ya wani langaɓe kansa da marairaice fuska yana ɗan duƙowa gab da ita ta yanda ita kaɗaice zata iya jinsa a maganar da zaiyi. “Please ki daina min irin kallon nan kina rikita min lissafi na ne”.      Harara ta ɗan sakar masa tare da janye idanun gaba ɗaya. Babu yanda ta iya da fitinar RK dole ta hure kamar yanda yake buƙata, dan ya tabbatar mata idan batayi hakan ba babu inda zaije yau. Ganin yaja kujera ya zauna ga mutane ya cika musu office da su ya sata hurewar kawai dan kaɗan kenan daga aikinsa ya zauna ɗin. Cake ne dai duk yanda yayi taci ta gutsira ta bashi a baki ƙi tayi, sai ma tai kicin-kicin da fuska ta yanda dole ya haƙura dan baya son yaga ta haɗe masa ƙyaƙyƙyawar fuskar nan tata damuwa yake shiga. Haka dole da kansa ya gutsira yaci ya miƙama wanda ya gayyato da su Yaqub dake a office ɗin kowa ya yanka yasa a baki. Daga hakan nutsuwa yay sosai yay mata addu'oin fatan alkairi da nasara a wannan aikin, ita harma hakan yaso bata mamaki, yayinda sauran ke amsawa da amin.     Bayan ficewar kowa ya wani zabga tagumi yana kallonta. Itako ta sake maida hankalinta ne a aikinta. Sai da taji kallon nasa na neman cutar da ita ta ɗago ta kallesa tare da sakar masa ƴar harara, sai kuma tai masa nuni da su Yaqub da ido. Murmushi ya saki mai ƙayatarwa da gyara zamansa. Ita kuma ta maida kanta yay ƙoƙarin dakatar da ita ta hanyar kiran sunanta.      “Maanal”.   Har tsakkiyar kanta taji yanda ya ambaci sunan nata. Kodan ba cika kiranta da sunan yay ba akoda yaushe oho. Sake ɗagowar tayi ta dubesa batare data amsa ba. Bai damuba ya cigaba da faɗin, “Maanal dan ALLAH ki iyakance min wahalar nan mana, na isa aure fa, ga kuma mata a kusa dani miya rage kuma dan ALLAH?”. A hankali yake maganar yanda ita kaɗai ke jinsa, duk da kuwa su Zaharadeen sarakan gulma sun baza kunne amma basa jiyo komai.        Lips ɗinta ta ɗan cije zuciyarta na mata nauyi, (miyyasa su basa fahimta ne, miyyasa bazasu gane ba. Ita fa Maanal, wannan Maanal ɗin da suke gani gaba ɗaya a yanzu babu zuciya a ƙirjinta, in dai zuciyace ta soyayya ta ta jima da mutuwa......)     “Maanal!!”. Ya sake katse mata tunani, yanzu ma bata amsa ba sai dai ta janye idanunta da suka cika da ƙwalla daga kansa. Aikinta ta cigaba da yi tana ƙoƙarin haɗiye hawayen. Shima sai yay murmushi kawai tare da miƙewa gaba ɗayansa.       “Ƙarfe nawa zaki tashi?”.    Batare data ɗago ba dan bata son yaga yanayinta ta ce, “Bazan iya cewa ba, saboda ina son kammala aikin nan duka a yau ɗin”.     Ɗan jimm yay sai kuma ya jinjina kai da faɗin, “Okay bari na kiraki kawai, ko kuma zuwa six, I will come back kawai”.       “Okay thanks”.   Ta faɗa a taƙaice. Shima sai ya ɗan murmusa kawai ya juya ya fita abinsa yana ma su Zaharadeen dallama. Fitarsa bai fi da mintuna biyar ba kira ya shigo a wayar gabanta. Koda ta ɗaga sai ta samu AS ɗin Boss ne, wai boss ɗin na son ganinta a office ɗinsa. Idan tace kaɗan ya rage zuciyarta ta wantsalo ta baki kar kuyi mamaki, ta jima shiru da kan wayar a kunnenta bata iya ta ajiye ba. Sai zuwa can ta kife ta da ƙyar ta miƙe cikin ƙarfafa kanta. A dakenta ta isa office ɗin, bayan sun gaisa da AS ya miƙe yana faɗin, “Bismillah”. Komai batace masa ba, yana gaba tana biye da shi har cikin office ɗin. Karo na farko kenan data shigo office ɗin. Ƙaton gaske ne, ya kuma ƙayatu da abubuwan more rayuwa matuƙa gaya. Tamkar ba office ba komai dake a cikinsa fari ne ƙal, hatta da kujerar zamansa da desk kai komai da komai. Sai kuma Mable's ɗin da aka shimfiɗa a ƙasan ya kasance baƙi wulik tamkar wata ajiyayyar kwalba. Ƙamshi kam ba'a magana, ga ac kamar an ƙuresa da gayya. A cikin sakanni da basu wuce biyar ba taima office ɗin wannan kallon.     Yana zaune a mazauninsa hankalinsa gaba ɗaya nakan computer ɗin gabansa, yayinda hannunsa ke danna keyboard dinta, na haggu kuma riƙe da document. Yanzu kam ya cire rigar saman suit ɗin nasa sai ta cikin kawai. Duk da shigowar tasu bai ɗago ba balle ya nuna yasan da su. Cike da girmamawa AS da ya ɗan matsa kusan gaban desk ɗin sosai ya ɗan rissina tare da faɗin, “Sir gata tazo”.           Sai da ya ɗan ja sakan kusan biyu kafin ya ɗago mayan fararen idanunsa da ke nuna matuƙar gajiya da aiki ya sauke akan AS ɗin nasa. Sai kuma yay luu da idanun ya ɗaukesu daga kansa ya maida ga computer ɗin tare da ɗan kai hannu ya gyara gilashinsa. A can ƙasan maƙoshi ya furta, “Zaka iya tafiya”.     Sake rissinawar girmamawa AS yay ya juya ya nufi ƙofa. Sai da yazo saitin da Maanal ke tsaye tayi kicin-kicin da fuska matuƙa a hankali ya furta, “Sister Maanal bismillah ki ƙarasa”. Daga haka ya fice. Yitai kamar bazata ƙarasa ɗin ba, dan ta ɓata fin minti ɗaya kafin ta ɗaga ƙafarta da ƙyar. Koda tazo inda yake maimakon ta zauna sai tai tsaye abinta. Shima yi yay tamkar ya manta da ita sai aikinsa yake kawai hankali kwance. Sunja fin mintuna uku a haka kafin ya ɗago kansa a hankali ya wani zuba mata idanu, sai kuma ya sake ɗaure fuska fiye da yanda ta shigo ta samesa. Cikin ƙausasa harshensa, da tsaurara kalamansa ya furta, “Ba'a baki tsare-tsare da dokin wannan companyn bane?”.       A yanda yay maganar yasa ta ɗago nata idanun ta kallesa. Kallon ido cikin ido suka zubama juna, fin miti ɗaya kafin ta janye nata, sai kuma ta canja yanayinta, cikin yanayin girmamawa irin na oga dana ƙasa ta furta, “Am sorry Sir, an bani tun ranar farko da nazo”.       Kamar wanda yaji haushin yanda tayi ɗin sai ya wani cije lips tare da ɗauke kansa a lokaci guda. Buɗe-buɗen document ɗin gabansa ya fara yi, sai da ya sake jan minti ɗaya a hakan, sannan ya cigaba da magana batare da ya kalleta ba. “Wannan Companyn ba lambu soyayya bane ko club. Idan buƙatar ganinki yake ko zuwa gareki ai yasan inda kike. Karya sake zuwa min nan da shirme in ba haka ba zan ɗauki mataki a kanku ku duka zaki tafiya”.         Tafasa zuciyar Maanal take, tafasa irin mai yunƙurowar nan daga ƙirji zuwa maƙoshi har ka dinga jin turirin a cikin bakinka. Karo na biyu ta ɗago ta dubesa kamar zatayi magana sai kuma ta haɗiye, shiru ta sake yi tana daidaita kanta. Zuwa wasu sakanni kanta a duƙe da girmamawa ta ce, “Kayi haƙuri sir, in sha ALLAH zamu kiyaye. Na barka lafiya”. Daga haka ta juya ta fita abinta. Wani irin wurgi yay da file ɗin hannunsa tare da dukan desk da ƙarfin masifa, sannan yay baya ya kwantar da jikinsa gaba ɗaya a kujerar yana furzar da huci masu masifar zafi...     Tofa, wai yaya take ne🤔 nifa na kasa ganewa🥱 Amin ƙarin bayani mana mutanena😁🏃. ____________★          “Abuja?”.     Daddy ya faɗa da wani irin mamaki ƙarara a fuskarsa yana ƙarema Huznah kallo daga sama har ƙasa. Cikin dake yanayin tsoronta dake neman bayyana ta jinjina masa kai.   “Eh Daddy, dan ALLAH ka barni naje sati ɗaya kawai zanyi. Kaga tunda muka duba Maanal sau ɗaya babu wanda ya sake komawa a cikinmu. Shiyyasa nake son naje na sake dubata na kuma sada zumunci kodan su Shahidah su cirema kansu tunanin dan bakai ka haifesu ba shiyya bama son zumunci da su”.       Rasama abinda zaice mata Daddyn yayi, sai kawai ya zuba mata idanu sosai fiye da farko. Shi ba mazaunin gida bane kam koda yaushe, amma yana hankalce da abubuwa da yawa da suka shafi gidan nasa da iyalansa baki ɗaya, zai iya cewa ko lokacin auren su Shahidah a kaf ƴaƴansa idan ka cire Yazeed babu wanda yay ma su Shahidah rakkiya gidan miji, a lokacin ma su duka anan Kaduna aka ajiyesu, dan daga bayane ita Shahidah suka koma Abujan sakamakon ƙarin girma da mijinta ya samu.....      “Uhm Daddynsu dan ALLAH kada ka kawo komai a ranka..” Hajiya Basariyya ta faɗa cikin son kauda ma Daddy hankali, dan duk tattaunawar tasa da Huznah itama tana a falon kasancewar girkinta ne, juyowa yay yana kallonta dan haka ta sake marairaice fuska ta cigaba da faɗin, “Nasan zakai tunanin abubuwa da yawa a ranka game da hakan, sai dai ka tuna al'amarin UBANGIJI yafi na kowa, shi kuma mai canja kowa ne a lokacin da yaso, eh tabbas da anyi kuskure, sai dai abinda ya faru a ɗan tsakanin nan yasa na koyi darasi da yawa, sannan ina da burin naga na gyara kuskurena ni da yarana duka. Dan ALLAH ka barta taje, na baka tabbacin in sha ALLAHU ba zaka ji komai mara ƙyau ba sai daddaɗa.”        Shi Daddy ma rasa abinda zaice yayi, ga uwar da ƴar sun wani tsatstsaresa da idanu. Yafi mintuna uku a haka kafin yaja numfashi ya fesar, cikin ɗan jinjina kai yace, “Kije zanyi tunani”.      Jiki a sanyaye Huznah ta miƙe tana masa godiya. Koda ta fita sai Hajiya Basariyya ta sake fuskantarsa, cikin kwantar da murya da daɗin baki taita tsara masa magana, tun bai maida hankali gareta ba har ya nutsu yana saurarenta. Sai dai amsar da taso ji bai bata ɗin ba a wannan daren. Da safe kamar yanda ta saba bayan ya baro massaci sallar asuba, kasancewa baya shigowa da wuri sai gari yay shaa ya wuce sashen Hajiya Yaya, haka yake yi a kowacce safiya in dai yana gida zai shiga ya duba kowacce a sashenta, hatta mai girgi yana shiga dan ganin lafiyar yaransa. Bayan ya koma nasa sashe kuma duk su bishi su gaishesa.      Daga sashen Hajiya Yaya na Hajiya Basariyya ya shiga, duk kuwa da ita tana nashi sashe, bai wani ja lokaci ba ya wuce na Ammie. Kamar yanda ya sani ya sameta zaune tana azkar itama. Dan sam bata barcin safe. Zama yay daga bakin gadonta daya sha gyara, dan tana tashi sallar asuba take gyara kayanta kafin ma ta shiga toilet. Cikin nutsuwarta da dukkanin ƴaƴanta suka gada ta ajiye littafin hannunta ta juyo tana gaishesa. Da kulawa ya amsa mata fuskarsa da ɗan murmushi, itama murmushin ta sakar masa kafin ta miƙe, fita tayi, babu jimawa ta dawo ɗauke da ƙaramin tray da kofi a samansa daketa tururi. Rissinawa tai ta miƙa masa, ya ɗauka yana murmushi da faɗin, “ALLAH yay miki albarka ke da zuri'arki baki ɗaya”.       “Amin ya rabbi tare da kai da zuri'arka kaima”. Ta amsa masa da girmamawa. Ba wani abu bane shayi ne mai ɗan karan daɗi na wasu itatuwa masu muhimmanci da take dafa masa safe da yamma. Idan ranar girkinta ne takan basa, idan ranar da ba girkinta ba ne kuma idan ya shigo da safe yakan sha anan, da yamma kuma taba yara su kai masa ko idan ya shigo yimusu sai da safe. Da farko an ɗauki rikici akan wannan bada shayi tsakaninsa da sauran matansa, dan sai da suka bi kwaf-kwaf suka gane abinda ke sakashi jimawa a sashen Ammie ɗin a duk sanda zai shiga da nufin gaisuwa. Rikici yay rikici Ammie tace ya raba musu kayan shayin kowa ya dinga dafo masa a ranar girkinsa. Badan yaso ba yayi hakan, sai dai baya jin kaf ɗin su sunyi masa sau bibbiyu suka ɓarar wai su gaskiya bazasu iya wannan wahala ba, ace daka yi sallar asuba sanda zaka koma ka huta ka wani tafi dahuwar shayi kitchen, daga nan aka samu maslaha Ammie jurau ɗin ta cigaba da dafa masa.     Sai da ya kammala shan shayinsa tsaf kafin ya fuskanceta. Cikin tausasawa da kulawa ya dubeta tare da kiran sunanta. Amsa masa tayi itama da girmamawa.      Ya ce, “Jiya Huznah da uwarta sun sameni wai tana son zuwa wajen ƴar uwarta Shahidah tai sati ɗaya”.    Wani irin bugawa da ƙarfi ƙirjin Ammie yayi, babu shiri ta ɗago da sauri ta zubama Daddy idanu.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖3️⃣0️⃣ ........Shima kallonta yake tashi zuciyar na rawa. Amma a mamakinsa sai ya ga ta saki murmushi kamar yanda ta saba. Cike da jarumtar danne dukkan abinda zuciyarta ke kissima mata ta ce, “ALLAH na gode maka da naga wannan rana Daddyn Hameed. Wlhy bakaji yanda naji wani irin shock ba. Wannan ai abun farin cikine a garemu, dan wata hanya ce ta samun haɗin kan yaran nan ne da muketa fata tuntuni. Ni Huznah ta biyani ALLAH yay mata albarka”.       “Humm Asia! Shin baƙya tunanin akwai wani dalili?”.    “Haba Daddynsu wane dalili kuma? Dan ALLAH kada ka ɓatama yarinya ƙyaƙyawar niyyarta mana”.         Ajiyar zuciya ya sauke mai nauyi, acan ƙasan ransa yana sake jin matuƙar ƙaunarta da jin alfahari da ita. Ita ɗin ta dabance a duniyarsa. Shi yasan da sauran ne cikin ƴaƴan Asia wani yace zai je gidansu sai anyi bala'i kuma ace wani daliline zai kaisu. Amma ita gashi maimakon tai zaton sharri kai tsaye saboda komai a bayyane yake sai tayi na alkairi. Jawota kawai yay jikinsa ya rungume. Murya a raunane ya ce, “Asia ALLAH yay miki albarka kinji. Tabbas UBANGIJI yamin babbar ni'ima da samunki”.      “Nima haka Daddyn Hameed, kai ɗin babbar ni'ima ce a gareni daga cikin ni'imomin UBANGIJI na. Bani da abin faɗa sai cigaba da godiya a garesa”.     Sosai ya saki murmushi mai ƙayatarwa, sai kuma ya sake kai hannu ya rungumota tare da ƙoƙarin haɗe bakinsu. Da sauri ta kauce tana dariya, sai ma ta zare jikinta gaba ɗaya ta miƙe daga kusa da shi. Fuska ya ɓata da mata nunin ta dawo amma ta maƙe masa kafaɗa.        “Shike nan ni kike ma rowa ko?”.    Murmushi ta masa kawai. Ya ɗan ƙara jinjina kansa da nufar ƙofa yana faɗin, “Zan rama”. Ya fice. Nan ma murmushin kawai tayi, sai da taji ficewarsa daga sashin gaba ɗaya ta koma jagwab a saman gadonta zuciyarta na wani irin harbawa. _(Jiya Huznah da uwarta sun sameni wai tana son zuwa wajen ƴar uwarta Shahidah tai sati ɗaya)_ kalamansa suka shiga dawo mata cikin kunne da amsa kuwwa. A bayyane cikin dafe kanta ta ce, “Ya ilahil'alamin Basariyya mi kike shirya min kuma? Ni nasan dole wannan zancen akwai wata a ƙasa”. Rashin mai bata amsa yaa sata yin shiru ta cigaba da zancen zuci. Ta jima a haka kafin hankalinta ya dawo jikinta ta miƙe ta shiga kitchen haɗama su Waleed abincin breakfast dana tafiya makaranta. Tana aikin tana tunani nan ma harta kammala. Tana cikin haɗa musu suka shigo sanye da uniform ɗinsu. Duk gaisheta sukayi suna mai rungumeta, tai musu murmushi tana amsawa. “Har an shirya ƴan makaranta?”.         Kawunansu duk suka shiga ɗaga mata. Sai kuma cike da shagwaɓa irin ta autoci Waleed ya ce, “Ammie mikika dafa min?”.    “Oh tama dafa maka bata dafa mana ba, kuji min ɗan iya”. Cewar Hameed yana hararsa da kai dankali bakinsa. Murmushi Ammie tai da faɗin, “Ni dai kunga kuyi ku wuce bana son surutu yau ɗin nan. Kowa ya duba abinda yake so shi aka dafa masa”.     Murna suka shiga yi, sai kuma suka ɗauki wanda zasu ci suka koma work table dake kitchen ɗin kowa yaja kujera sukai zaman ci. Ammie kuwa ta fara ɗan wawwanke kwanikan data ɓata dan bata son taga ambar kaya da datti, duk da tasan yanzu mai aikinta zata zo ta fara aikin ta gwammace ta tsaftace waɗan nan ɗin kafin ta iso. Tana kammalawa suma suka kammala. Sallama sukai mata kowa ya ɗauka lunch box ɗinsa suka fice. Sai kuma six dan makarantarsu tana tare da islamiyya ne...      Koda ta koma ɗaki saita gagara shiga wankan datai niyya, zama tai ta ɗauki waya ta shiga kiran Nene. Ba'a wani ɗauki tsawon lokaci ba Nenen ta amsa kuwa. Sai dai suka gaisa da tambayar juna gida kafin Ammie ta ce, “Nene yau zan sameki a gida?”.     Daga can Nene ta ce, “Eh bazanje ko'ina ba. Dama nina naso kiran naki ai sai kika kirani, zaki shigo ne?”.         “Eh Nene indai ya bari zuwa anjima kaɗan zan shigo”.     “To shike nan sai kinzo ɗin ina saurarenki”.   Daga haka sukai sallama kowa ta yanke.....      ★ Sai kusan sha biyu Ammie ta samu damar barin gidan. Dan da ƙyar Daddy ya barta dan ma tace masa kitso zataje. Da yake yasan tana zuwa kitson kuma bai kawo komai a ransa ba. Shi irin mutanen nan ne da sam basa son yawan fitar iyalansu, sunfi buƙatar ko yaushe kina gida, shiyyasa a cikinsu babu mai fita aiki ko wani business. Ammien ce ma taga bazata iya wannan kashe kan ba komai sai abinda namiji ya baka tuni ta fara kasuwancinta a gidan Nene. Kuma Alhamdullah komai yana tafiya dai-dai.     Gidan Nene gida ne a matsayin family house. Dan kuwa ita da duka matan ƴaƴanta suna a cikinsa. ALLAH yayima mijinta rasuwa tuni, ita ta cigaba da gwagwarmaya da yaran har suka girma. Yanda ta horesu yasa duk suna da sana'o'in su, dan babu mai zaman banza. Badai kuɗi garesu ba amma ci da sha gwargwado da sutura irin ta gidan mai rufin asiri sun wuce da wannan kam. Sashen Babban ɗan Nenen ta fara shiga, matansa biyu, yaso auren Ammie a baya matarsa nata zuba rashin mutunci akan hakan sai ALLAH ma bai ƙaddara ba, to ashe kishiyar dai na bibiyarta, dan bayan Ammien tayi aure ya auro budurwa gal a leda yanzu haka haihuwarta uku a gidan itama. Wannan dalilin ne yasa sama-sama suke da Ammien. Koda ta shiga a kitchen ta samu Maman Salima kamar yanda suke kiranta, ta wani zubama Ammien ido zuciyarta na bugawa, tuni murmushin fuskarta kuma ta ɓace. A yanzu kam ba kishin Ammie ne ke damunta ba hassada ce. Ko'a jikin Ammie ta gaisheta da tambayarta yaranta. Daga kitchen ɗin ta amsa a daƙile, sai dai idonta na'akan suturar jikin Ammie.       “A'a Aunty Asiya ce a gidan namu?”.     Amarya dake leƙowa daga falonta ta faɗa. Murmushi Ammie tai mata da faɗin, “Aiko nice Amarya”.     “To sannu da zuwa Bismillah ki shigo”. Babu musu Ammie ta shiga, falon ƙal an gyara shi sai ƙamshin turaren wuta yake kamar bamai ƙananun yara ba. Gashi da gani tana fama da laulayin wani cikin ne ma. Cike da girmamawa ta gaida Ammie kafin ta fita sai gata da ruwa.     Ammie ta ce, “Amarya ai da baki wahala ba ma. Ina yaran nawa ko duk an wuce makaranta?”.       “Duk sun wuce shiyyasa ai muka samu lafiya Aunty, sai Ameen kawai yana barci ne”.     “A'a ai shima ko ya kamata a sakashi makarantar tunda naji bakinsa akwai surutu”.        cikin dariya Amarya ta ce, “Sosai kuwa Aunty”.   Bayan Ammie ta sha ruwan ta fito, amarya biye da ita har ɗayan sashen. Nan kam mace ɗaya ce, itama ta amshi Ammie da girmamawa da mutuntawa, bayan sun gaisa ta fito ta shiga wajen sauran suma su biyu. Daga haka ta shiga wajen Nene. A falonta ta sameta zaune ta baje kaya tanata lissafi. Sai wata dake gefenta tana tayata. Da mamaki Ammie ta furta, “A'a Saratu yaushe a gari? Nene shine baki sanar min munada da baƙuwa ba?”.      Murmushi wadda aka kira Saratun tayi, yayinda Nene ta ɗan taɓe baki da faɗin, “Zuwan nata ne dama ya sani nemanki, tunda ita dai fitinar gidanta bata ƙarewa”.     “Tofa wani abunne kuma ya faru Nene?”.     “Humm Asiya ke dai cire mayafi a kawo miki abinci, ga waina can nasa tun ɗazun aka sayo miki gidan Hajiyayye ALLAH yasa ma bata huce ba. Saratu ɗakko mata”.     Kasancewar Ammie na son wainar sosai ta zauna taci, sai da ta ƙoshi sannan suka fara maganar Saratun. Sosai ran Ammie ya ɓaci, tace bako zata bar gidan ba har sai sauran ƴan uwanta sun dawo ai zama akan al'amarin Saratun, wannan karon dole su ɗauki mataki akan mijin nan nata mara mutunci, dan bazasu yarda da auren duka ba. Bayan sun gama tattauna wannan suka koma batun nasu gidan, ita kanta Nene ta jinjina batun zuwan Huznah Abuja. Amma sai ta kwantarma Ammie da hankali akan ta barta taje ɗin, amma sun kira Shahidah sun gaya mata komai, sun kuma mata gargaɗin ta sanya ido sosai. Ammie dai bata bar gidan nene ba sai bayan magriba da sauran ƴaƴan Nene huɗu ringis suka dawo kasuwa suka tattauna batun Saratun. Da zata tafi sai ta wuce da Saratu can gidanta akan zata huta kwana biyu. _________★        Washe gari ƴan Dubai suka wuce domin haɗo kayan lefe dana shagalin biki harma da kayan ɗakin amarya. Itama Huznah ta wuce Abuja, sai dai abinda ya sake tabbatar ma da Ammie akwai wata a ƙasa ko sallama Huznah batai mata ba. Sai bayan ta tafine uwar ta shigo tana cema Ammien tayi hakuri wai driver ne ya azalzali Huznah ɗin shiyyasa bata shigo ba. Murmushi kawai Ammie tai ta ce, “Babu komai ai ALLAH ya tsare hanya ya kaisu lafiya”. Daga haka bata sake tofa komai ba dole Hajiya Basariyya ɗin ta fito tana taɓe baki, dan taso ne Ammie ta biye mata su ɗan yi gulmar ƴan tafiya Dubai. Itama Ammien kuma ta ganota shiyyasa ta mata haka...      Maanal bata san wainar da ake toyawa ba. Da safe dai sanda Shahidah zata sauketa ne a office take gaya mata zuwan Huznah ɗin. Dan yanzu itace ke kaita, wani lokacin ta dawo a taxi. Tun randa AA Darma yay mata wannan gargaɗin ta so yima RK magana, sai kuma wani ikon ALLAH ma a daren ranar RK ɗin yay tafiyar gaggawa har yanzu bai dawo ba. Dan itama a waya ya kirata ya sanar mata. Busy kuma da yayi sosai yasa ba koyaushe suke waya ba sai ya samu lokaci. Amma ya tabbatar mata bazai wuce kwanaki biyar ba. Yau kuma kwanansa huɗu kenan gobe idan ALLAH ya kaimu take saka ran dawowarsa. Yazeed dai ne da yake yana garin yanzu kullum da dare sai yazo gidan Shahidah ɗin, dan da farko yaso ya mata fushi akan batun aiki wai bata sanar masa ba sai Daddy ya gaya masa, haƙuri kawai ta bashi da nuna masa ai Daddy ɗin dan ya isa da su ne su duka shiyyasa. Ya dai ƙyaleta kawai, amma a ransa ya gama ƙudirar wannan aikin sai ta barsa duk da yanada planing ɗin anan Abuja ɗin zata zauna ita ko anyi bikin su.       A gajiye ta fito daga office ɗinta zuwa office ɗin Designer Director ɗin dake kula da aikin nata, har yanzu dai suna akan project ɗin nan daya haye mata. Bayan tayi knocking aka bata izinin shiga. Ganin yana haɗa kaya alamar zai tashi ne a sanyaye tace, “Director badai zaka tashi bane ba?”.     Kallonta yay fuskarsa da murmushi, dan yanzu kam ta fara sabawa da su. Yanda kuma take girmamasu da bawa kowa hakkinsa da kame kanta yasa su jin ƙaunarta a rayukansu.        “Lallai baƙya kallon agogo, bakiji yanda company yay tsit ba kusan duk an wuce ai”.    Agogon ta kalla kafin ta sake dubansa, dan tabbas magrib tama kusa. “Ayya ALLAH ban lura ba. Dan ALLAH ka samun hannu a document ɗin nan, so nake yanzu na miƙasa office ɗin CEO idan ALLAH ya taimakeni da safe sai ya duba shi da wuri kafin zaman meeting”.       “Wayyo baƙya jin tausayina ALLAH, kinji bayana kuwa ga Madam nata kira na yau birthday ɗinta. Amma kawo nayi sauri”.     Godiya ta masa tare da matsawa ta ajiye masa file ɗin, tana daga tsaye ya shiga dubawa. Ɗagowa yay ya dubeta cike da tsokana ya ce, “Anya ba kwanan nan zan baki kujerar nan ba Manaal Giro? Ke ɗin ƙuruwace fa. Ɗan murmushi kawai tai masa kanta a ƙasa dan iyakarta da su kenan, shiyyasa duk da yanda take girmamasun wasu ke mata kallon mai girman kai da faɗin rai. Wasu a cikinsu duk sun ƙyasa, sai dai kamewarta na zame musu barazana, ga kuma RK da kowa ya tabbatar budurwarsa ce a companyn yanzu duk da kuwa yau ne take cika kwanta na takwas a Companyn. Bayan ya saka mata hannun ta karɓa tana masa godiya. Sallama ta masa ta fice, haka ya bita da kallo zuciyarsa na zallo. Tun ranar farko da sukama Maanal interview yarinyar tai masifar shiga masa rai. Abinda ya faru tsakaninta da Boss yaso taka masa birki, amma daga baya sai yaga kuma komai bai sake faruwa ba, sai sabon soyayyarta a zuciyarsa ya dawo fil, sai dai kuma Maanal babu sakin fuska........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖3️⃣1️⃣ .......Ita kam koda takai file office ɗin Boss ta ajema AS office ɗinsa ta koma ta cigaba da aiki, dan akwai abinda take son kammalawa kafin ta wuce gida. Kiran sallar magriba ya sata ƙarasawa sauri-sauri sannan ta tashi tayo alwala ta haɗa kayanta ta kashe komai ta fito dan su Yaqub tuni duk sun wuce sai ita kaɗai. Shiru babu motsin kowa duk an wuce. Sai offices ɗai-ɗaine ƴan over work irinta koma wanda suka fita ke'a buɗe. Ƙananun ma'aikata ma ta wuce kusan mutane huɗu basu wuce ba, koda ta fito harabar companyn ma motoci biyar kawai ta gani sai mashin biyu alamar na wanda suka ragene. Idanunta suka sauka akan motar boss. Janyewa tai tana taɓe baki, shi dama ai yafi kowa iya over work, dan kullum shine ƙarshen barin office. Masallaci ta nufa domin gabatar da magriba. Bayan an idar koda ta fito bata koma ciki ba, hanyar gate ta nufa abinta a ƙafa. Street ɗin shiru babu yawaitar mutane a ƙafa sai motoci, sai dai ko'ina akwai haske kamar kana wata ƙasa ba Nigeria ba. Taxi nada wahalar samu a wajen kasancewar duk manyan ma'aikatu ne ata wajen, sai gidajen cin abinci da suma ba laifi suke da yawa ta wajen da shopping malls guda biyu dake can farkon shigowa. Tsoron kar dare ya sake mata ya sata cigaba da tafiya a ƙafa tana jin nadamar kaiwa haka bata tafi gida ba, har Shahidah cewa tai zata aiko a ɗauketa idan ta gama tunda tace ita karta biyo ɗaukarta yau tana da aiki amma tace mata a'a zata hau taxi. Tayo tafiya babu laifi zuciyarta ta fara karaya, dan ƙafafunta sun fara gajiya. Mamakine ya kamata ganin ƴammata tsaitsaye kamar masu jira azo ɗaukarsu, amma abinda zai baka mamaki suna da yawa duk da kowanne yana tsaye ne shi kaɗai ko su biyu. Cigaba tai da tafiyarta dai tana ɗan kallonsu sai taji ana horn, da sauri duk hankalin ƴammatan ya koma wajen motar, wasu ma duk sun nufi motar ne, sai dai kuma mai motar bai tsaya ba ya cigaba da bin bayan Maanal ne ana kuma horn ɗin dai. Da sauri ta ɗan ja da baya sakamakon shan gabanta da akai da motar, cikin wani irin ɓacin rai ta ɗago dai-dai mai motar na sauke glass ɗinsa. Babban mutum ne da a shekaru ma zai iya haihuwar su Shahidah bama ita ba, yana daga baya kwance driver ɗinsa a gaba, cikin tsareta da ido ya sakar mata murmushi. Ɗauke kanta tai da sauri ta raɓa ta wuce wani irin ɓacin rai na mamayeta. Jin an ƙara biyo bayanta da mota ana mata horn again ta tsaya cak, cikin matuƙar fusata da harzuƙa ta ɗago dan ta gama shirya yima tsohon banzar nan zagin ƙare dangi, amma sai kawai taga motar boss ba wancan bane. Kafin ta iya haɗiye abinda ke bakinta AS ya fito daga gaba, kai tsaye inda take ya iso, furkarsa da murmushi ya furta, “Sister Maanal bismillah ki shiga”. Yay maganar yana miƙa mata hannu da nufin amsar kayan hannunta. Kai ta girgiza masa tare da janye hannun nata tana faɗin, “Karka damu na gode”.           “Idan shi bai dace ba, inaga ni kamar zan dace tunda dama ni na fara tayawa”. A bazata taji muryar tsohon nan cikin kunnenta daga bayanta. Jitai gaba ɗaya kamar ta daburce, ga zuciyarta na wani kalar bugawa da sauri-sauri har numfashinta na neman fara yin sama-sama. Babu alamar wasa ko ragi a tare da ita ta juya ga tsohon nan, hannu ta ɗaga da nufin nunashi a hankali taji saukar wani tattausan hannu ya riƙe mata yatsu, batare da cewa komai ba yaja hannun nata. Ƙoƙarin fisgewa ta fara sai dai bai bata damar hakan ba har ya iso da ita jikin mota. Sai lokacin ta iya zuba masa manyan idanunta da suka kaɗa, shima kallon nata yake cikin ido. Kusan minti ɗaya suna kallon juna kafin ya zare kayan hannunta tare da motsa lips ɗinsa a hankali ya furta, “Get in”.         Rasama mi zata ce masa tayi, dan sam babu ko ɗigon wargi a fuskarsa. Yayi masifar yin kicin-kicin da ita kamar zatai aman wuta. Bai kuma sake cemata komai ba ya zagaya ɗaya side ɗin ya shiga mazauninsa ya ɗauke kai. Dattijon Alhajin nan dake tsaye ransa a matuƙar ɓace ya sake takowa inda Maanal take. Ai yana buɗe baki zaiyi magana kawai ta shige motar, shiko AS ya rufe mata murfin ruf tare da kallon Alhaji fuska da murmushi ya furta, “Bye bye grandpa”. Shima ya zagaya ya shige motar driver yaja suka wuce.       Da wani irin kallon ɓacin rai dattijon yabi motar da kallo, sai kuma ya jinjina kansa tare da cije lips da ƙarfi ya koma tashi motar. Da sauri driver ɗinsa ya buɗe masa ya shiga ya maida ya rufe suma suka bar wajen....         Sosai Maanal ta takure jikinta waje guda, yayinda idanunta ke'a lumshe bugun zuciyarta kuwa gaba ɗaya ya sauya daga normal bugu. Ambaton sunan ALLAH kawai takeyi tare da ƙoƙarin danne kukan dake son kufce mata.       AA Darma dake a gefenta kam tunda ta shigo bai ko kalleta ba. Gaba ɗaya ya tattara hankalinsa ne ga document ɗin hannunsa da dama shi yake dubawa kafin suga Maanal ɗin, koda yake bama shine ya ganta ba, AS ne ya ganta cike da mamaki ya furta (kai wannan ai Sister Maanal ce Alhaji Bukar ya tsare a hanya halan bata sami abin hawa bane har yanzu). Driver na tambayar AS wacece ita ɗin AA Darman ya daka masa tsawa akan su dakata, shine dalilin tsayawar tasu.         A yanzun ma driver ne cikin ɗari-ɗari ya furta, “Sir! Zamu fara saukeka ne kafin a kaita?”.      Shiru bashi da alamar amsawa. Sai da ya mula dan kansa batare da ya bar abinda yake ba ya bashi amsa a taƙaice. “Fara ajiye ta”.      “Okay sir. Sister ina muka nufa?”. Ya maida akalar tambayarsa akan Maanal. Shiru bata amsa ba sai da ya sake maimaita tambayar sannan ta dawo hayyacinta. Cikin ƙoƙarin danne komai da yanayin nan nata na kamewa ta furta, “Samu waje kawai zan sauka na ƙarasa a taxi”.       Kallon AA Darma drivern yay ta mirror ɗin gaba da tunanin ko zaiyi magana. Amma sai yaga ko kallon inda wani cikinsu yake bai yiba ma. Dan haka sai ya kalla AS cikin marairaicewa. Murmushi AS yayi tare da juyowa saitin inda Maanal ɗin take, “Please Sister Maanal bafa zamu ajiyeki ko'ina ba sai gida”.       Rasama mi zatace tayi, sai kawai ta faɗa masa sunan anguwar a taƙaice. Bai gaji ba ya sake tambayar street, nan ma kamar bazata kula shi ba sai kuma dai ta faɗa. Daga haka bata sake magana ba ta maida idanunta ta rufe. Cikin ƙanƙanin lokaci suka iso abinka da lafiyayyar mota a saman lafiyayyar kwalta. Shigowarsu cikin street ɗin ya sa AS sake mata tambayar inda za'a sauketa. A taƙaice ta ce “Nan ma yayi”. Shi dai driver tunda taƙi faɗar no ɗin gidan da zataje ai sai kawai ya samu waje ya tsaya abinsa. Itako ta kama handle ɗin motar ta buɗe da nufin fita. Sai kuma ta ɗan juyi domin ɗaukar kayanta da AA Darma ya amsa a ɗazun akai rashin Sa'a shima ya kawo hannu kan kayan da nufin ɗauke file ɗin daya ɗora kawai ta riƙe masa hannu. Da sauri ta jiyo jin ta kama abu, dai-dai shima yana kallon hannun nasa da yaji an cafke. A tare suka dubi hannun sai kuma suka kalli juna. Maanal ta saurin yarfar da hannun tamkar wadda ta kama wuta, yayinda shi kuma ya wani irin dunƙule hannun nasa waje guda tare da dimtse lips ɗinsa da hakori tamkar zai kai naushi. Sauka Maanal ɗin tayi tare da zare kayan nata ta ajiye masa file ɗin batare data sake gigin kallon ko inda yake ba taima AS godiya da driver tai gaba abinta ko waiwayen motar bata sake yi ba. Shima driver sai kawai ta tada motar suka wuce.        Tunda suka tafin AA Darma hannun nasa kawai ya zuba ma ido tamkar mai karanta wani abu a jikinsa ko cigaba da ganin hannun Maanal ɗin. Kamar ance ya kalla inda ta tashi idonsa ya sauka akan ɗan abin hannunta da alama wajen yarfar da hannu da tai sanda ta kama nashi ya cire batare data kula ba. Hannu ya kai a hankali ya ɗauka ɗan hannun ya juya. Mai ƙyau ne sosai kalar golden, an masa kwalliya da fararen stones, da gani ba wani mai tsada bane, amma yayi ƙyau sosai. Yanda ya tsirama ɗan hannun ido yana kalli da jujjuyashi haka su AS ke kallonsa zuciyarsu cike da gulma, suna ganin zai ɗago suka kama kansu. Shi ko a cikin aljihun jacket ɗin suit ɗinsa na ciki ya cusa ɗan hannun kawai ya gyara zamansa......       Ni dai nace, “Hummm. Idan tayi wari dai maji🤪🏃”. _____________★         “Wai ni wannan yaron zaima gadara? Ni nan! Ni a garin Abuja”.    Abokansa uku da suka zuba masa ido cikin mamaki ɗaya daga cikinsu ya ce, “Sen.. Bukar wai kai da waye haka? Ka shigo kamar wanda aka wancalo kuma kanata kai kawo da zantukan da bamu gane ba”.      Tsaki mai ƙarfi ya sake ja, sai kuma ya ɗauka bottle na ruwa ya ɓalle murfin ya hau kwankwaɗa. Tas ya shanye yay jifa da robar, kafin ya dubi abokan nasa ɗaya bayan ɗaya yana furzar da huci. “Wannan yaron ɗan gidan Darma mana, lokaci yayi da zan koya masa darasin rayuwa. Saboda na fahimci tashen balagar iskanci ne ke ɗibarsa da giyar ƴan kuɗaɗen da yake gani ya tara kamar yaje dai-dai da kowa....”        “Halan AA!? Dan nasan shine tsageran cikin ƴaƴan Darma”. Ɗaya daga cikin abokan nasa ya faɗa shima cikin ɓacin rai.     “In ba shi ɗin ba sai wa? Wato wannan yaron shifa jinsa yake dai-dai da kowa yanzu a garin Abuja. Haka ranar Alhaji Badamasi yace min ya masa rashin mutunci. Wai yaje masa da business amma yaƙi ƙarɓa harda gaya masa baƙar magana. Tsageran cin yaron kullum sake ƙaruwa yake yi”.         “Kufa daina ɓata bakin ku, wannan yaron duk abinda yake ɗaurin ƙugu ya samu, ba daga kowa ba kuma sai Mr president, tunda ya ɗauki muƙamin nan ya bashi yake jin kansa dai-dai da kowa. Sannan kaima kayi ganganci, da girmanka da mutuncinka a ƙasar nan bama garin Abuja ba minene na sauka yima yarinya magana. Ko ƴar uban waye zaka aika a ɗakko maka ita har gidane balle nasan bai wuce karuwan dake tsayawa a wajen bane ba. Na gaya maka kana gidanka kwance duk ƴar da kake so za'a kawo maka amma ban san miya kaika wannan kwamacalar ba haka”.           “Karka ɓata min rai kai kuma, ai na faɗa muku yarinyar tafiya kawai take ina zaton daga cikin wani Companyn ta fito ne, kuma a yanda nake cikin ɓadda kamar nan kaima kasan babu yanda za'ai wani ya ganeni, koshi bana tunanin yasan nine akwai dai wata tsakaninsa da yarinyar shima ɗan iska, saboda naji wannan shegen yaron daya maida kamar bindinsa ya kira sunanta wai Sister Maanal”.       “Eh to da gaskiyarka akwai alaƙa kam, amma bincike ya kamata muyi”.    Duk sun gamsu da yin hakan, daga nan suka saki zancen suka fara wanda ya tarasu a wajen. Dan dama meeting ne zasuyi daya shafesu. Su duka biyar ɗin manyan ƴan siyasa ne kuma ƴan kasuwa a bayan fage, a wata fuskar kuma dattijan ƙasa wai....     Wai.... Ne ma kenan ba manyan ƙasar bane🏃 Bily wataran sai kinci duka idan baki kiyayi bakinki ba😌. _________★       Maanal kam data shiga gida tamkar wadda aka koro har ta bama maigadi tsoro waje ta samu a harabar gidan ta zauna, sai da ta huta taci kukanta sosai ta ɗan samu nutsuwa sannan ta miƙe. Wajen fanfo da ake bama flowers ruwa taje ta wanke fuskarta sannan ta shiga ciki. Turus taja ta tsaya tana kallon Huznah dake zaune a falo tana cin abinci. Yayinda su Barrah dake homework sukayo kanta da gudu suna mata oyoyo.....       Rungumesu tai idanunta na kan Huznah ɗin da itama ita take kallo, dai-dai nan Shahidah ta fito daga kitchen. “Aini yanzu nake tunanin zuwa na biki kafin Daddynsu Barrah ya dawo gidan nan”.     Shahidah ta katsema Maanal da Huznah kallon-kallon da sukema juna da furucinta. Dan murmushi Maanal ɗin tayi da kaiwa zaune tana faɗin, “Didi ai nima kaɗan ya rage na kiraki a waya, ashe wajen nan haka ake wahalar taxi”.        “Ai dolene, waje duk ma'aikatu ke kuwa. Ya aikin?”.    “Alhamdullah ya naku?”.   “Yana can mun baro sai kuma gobe idan ALLAH ya kaimu. Bakiga baƙuwa ba ne?”.      Sam Maanal babu ruwanta da ɓoye-ɓoye dan ita ƴar sak ce, sai ta ɗan kalli inda Huznah take da faɗin, “Na ganta Didi. Mamaki ne ya kasheni ai na kasa magana. Sannu da zuwa”.      Cikin ɗan basarwa Huznah ta ce, “Yauwa sannunki kema”. Daga haka ta maida kanta ga abincinta. Itama Maanal sai bata sake magana ba ta miƙe.      “Didi bara na ɗan watsa ruwa, ina Linda dan ALLAH ta dama min kunun gyaɗa kafin na fito, Barrah jeki gaya mata”..     Amsawa Barrahn tai tare da miƙewa ta nufi kitchen ɗin da ɗan gudu tana jiran Linda, ita kuma tai hanyar ɗakinta.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖3️⃣2️⃣ ......Da mamaki Maanal ta dinga bin akwatin Huznah da aka kai ɗakinta da kallo, sai dai batace komai ba ta tuɓe kayanta ta nufi bathroom. Wanka tayo da alwala, sai da ta gyara jikinta tsaf tai sallar isha'i sannan ta dawo falon. Kunun da ta saka Linda ta haɗa mata kawai ta ɗan sha, sai magungunanta da Shahidah ke bata da kanta dan ma kada tai wasa. Suna nan suna ƴar hira ita da Shahidahn dan Huznah ba saka musu baki take ba sai ma latse-latse take a waya kamar bata falon mai gidan ya dawo...      Dalilin dawowar tasa yasa Shahidah shigewa part ɗinsa, aka bar su Maanal kawai. Sai itama ta miƙe ta taimakawa Linda suka kwashe su Barrah da sukai barci a falon. Daga haka tacema Huznah ita zata shige ta kwanta. A ciki Huznah ta amsa mata, Maanal bata damu ba tai wucewarta. Ita kuma ta rakata da harara. Maanal na shiga ɗakin kiran RK ya shigo mata, bata ɗaga ba sai da takai kwance, ta gaisheshi a mutunce kamar yanda ta saba, daga haka ta fara mata hira da albishir ɗin gobe in sha ALLAHU yana hanya. Ganin yanata jan hirar ta fara masa hamma, dole yay mata sallama. Kamar jira sai ga Yazeed shima ya kira, jitai kamar zatai kuka, haka dai ta ɗaga.       “Dawa kike waya haka Maanal?”.    Furucinsa na farko kenan maimakon amsa mata sallamar da tai masa, muryarsa a cinkushe. Sai da ta ɗan yi jimm kafin a nutsenta ta bashi amsa da, “Rafeeq ne!”.       “Rafeeq!?”.   Sai da ta ɗan lumshe ido saboda yanda ya maimaita sunan RK ɗin a kausashe yanzu kafin ta ce, “Uhhum!”.        “Okay yayi ƙyau”. Ya faɗa yana yanke wayar. Shiru tayi na mamakinsa, Yazeed mutum ne mai nutsuwa da fahimta, sannan yana da haƙuri, zata iya cewa tunda ta haɗu da RK bai taɓa tunkararta akan al'amarinsa ba sai dai can a tsakaninsu. Amma yau minene ya hasalashi haka? Kai ita kam taga takanta. RK ya nuna fushi idan ya ganta da Yazeed ko tana waya da shi, yanzu shima kuma ga Yazeed ɗin zai fara nashi. Ita kam dan ALLAH karsu rikita mata lissafi mana, suma barta da abinda ya dameta...        Tana cikin wannan yanayin Huznah ta shigo, bata mata sallama ba dan haka itama tai kamar bata san da shigowarta ba. A gadarance ta jefa wayarta saman gadon, fuuu ta wuce bathroom, ita dai Maanal binta tayi da kallon mamaki, bata jimaba ta fito, ta buɗe akwatinta ta canja kaya sannan ta hawo gadon. A mamakin Maanal dai taji Huznah na jera fillos a tsakkiyarsu, sai kawai abin ya bata mamaki ta saki murmushi. Bata kulata ba tai addu'a taja barko.     Barci take son yi saboda gajiya da tayi ga gobe ma dole ta fita aiki, amma Huznah ta hanata sai charting take, kuma voice note. Tun Maanal na dauriya har dai ta miƙe tsam a gadon ta koma saman sofa doguwa dake a ɗakin, kwanciyar bata mata wani daɗi ba amma ta haƙura anan ɗin duk da nan ɗin ma ba tsira tai ba tana jin Huznah ɗin da bata fasa abinda take ba harda su ɓaɓɓaka dariya kamar ba dare ba. Daga ƙarshe bata san sanda tayi barci ba ita dai, dan itama ALLAH ya taimaketa barcin yay awon gaba da ita. Da asuba kuma koda ta tasheta ƙin tashi tayi, sai kawai ta ƙyaleta. Har gari ya waye tai shirin fita aiki Huznah taƙi tashi salla. Sai kawai ta fice abinta tana nema mata shiriyar UBANGIJI.      Yau ma Shahidah ce ta ajiyeta a office sannan ta wuce nata aikin, tun a harabar companyn suke gaisawa da mutane har ta shigo. Dama dai tsakaninta da kowa gaisuwar ce, rashin yawan fara'arta da yawan magana ma kesa mafi yawansu ke kiranta da sunan mai girman kai. Ƴan rukuninsu mutum uku ne kawai sukazo, ta gaisa da su taja kujerarta ta zauna. Dama ita kaɗaice mace a cikinsu, shiyayasa daga gaisuwa sai zancen aiki ke haɗata da su. ALLAH kuma ya taimaketa kujerarta itace farkon shigowa, suma ganin yanda take haɗe fuska da kame kanta yasa suke shakkar shige mata duk da wasunsu na kwaɗayin hakan tun ma a ran farko da tazo. Aikinta ta kamayi kawai kamar yanda ta saba, a haka sauran suka iso, kowa yazo zata ɗago su gaisa daga haka ta maida kanta ga aikinta. Kusan eleven ta tashi zuwa office ɗin Director Mustapha. Duk da kallo suka bita, wanda ke zama kusa da ita cikin yin ƙasa da murya yace ma na kusa da shi, “Wato yarinyar nan akwai girman kai wlhy Ema..”.      Caraf Yaqub da ke facing ɗinsa ya ce, “Ba wani girman kai wlhy, ta dai san kanta ne. Idan mace ta cika faran-faran ace ma ballagaza, idan ta kame kanta ace girman kai. Kufa lura ita kamar yanayintane ma haka, miskila ce kawai”.      “Tab ai ni kuma bana son miskilar mace gaskiya. Ita mace ko yaya da sauƙin kai tafi daɗin rayuwa”.     “A wajenka ba.....” “Oh to kodai santa kake yine wai Yakub”.        “To laifi ne idan na sota Zaharadeen, naga dai namiji ne ni. Kuma ɗin inda zata amsa muku son nata kuke shiyyasa kuke gulmarta. Yarinya na girmamaku amma bakwa gani. Yanzu da sakewa take cikinmu da surutu da fara'a sai kuma ace ta saki kanta a tsakkiyar maza. Ta kuma kama kanta kunzo kunayi da ita mtsooww!”.     Ya miƙe ya bar musu wajen. Duk da kallo suka bisa, sai kuma suka kalla juna cikin yamutse fuska. “Wannan guy ɗin na kula fa son yarinyar nan yake”.        “Oh kai sai yau ka gane, ai na jima da fahimtar hakan. Kuma banga laifinsa ba dan koni ALLAH na ƙyasa”.      Dariya suka sanya a tare harda tafawa.     Maanal kam da bata ma san sunai ba kanta tsaye office ɗin Designer Director Mustapha ta nufa. Tana shiga Elevator massage ya shigo wayarta, ƙoƙarin dubawa ta fara yi sai taga Yazeed ne. Nutsuwa tai a karanta saƙon, sai ya zam har elevator ɗin ta tsaya hankalinta nakan wayar, a haka tai ƙoƙarin fitowa batare da duban gabanta ba. A dai-dai lokacin da CEO AA Darma ke isowa ga elevator ɗin Assistant ɗinsa biye da shi. Ya riga ya kawo jiki, kamar yanda itama ta riga ta taho gashi hankalinta ba a wajen yake ba balle taja da baya kawai sai jitai ta bugi abu. A ɗan razane tayi baya, wayarta ta suɓuce ƙasa hakama gilashin idanunta da document ɗin duk suka tarwatse kasa.      Sosai ta ɗago cikin ɓacin rai dan ganin wanene da wannan aikin bayan ta gama bin kayan da kallo ɗaya bayan ɗaya. Shima sai hakan ya zam dai-dai da tashi ɗagowar bayan ya gama bin kayan da kallo musamman zanen agogon da yay masifar ɗaukar hankalinsa. Wani kalar zubama juna ido sukai kowanne fuskarsa a matuƙar tamke, sai dai na Maanal ɗin ya ɗan cika da ruwan hawaye dan har ƙyallinsu ya nuna. Yanda tai masa ƙiri da idanu sai ka ɗauka zata fara zazzaga masa ruwan bala'i ne, dan tuni AS ɗinsa da wasu da suka zo wajen bayan faruwar accident ɗin duk sunyi kasare cikin ɗunbin mamaki suna son suga mizai faru. Amma mi, a mamakin kowa sai suka ji cikin sanyin murya Maanal ɗin ta furta,       “I'm sorry Sir”.     Ta ƙare maganar da rissinar da idanunta harma da kanta cikin nuna girmamawa. Shi kansa wani irin rumtse idanu yay da masifar ƙarfi, sai kuma ya zagayeta ya shige cikin elventor ɗin batare da yace komai ba. Wannan abu ya bama kowa mamaki, hatta da AS ɗinsa daya gama tattaro ma Maanal kayayyakinta. Wannan shine abu na biyu daya faru tsakanin Boss da Maanal ko yace na uku harda kaita gida da sukai jiya. Shi sai ma ya rasa kalar tunanin da zai yi akan al'amarin.      Sauran ma duk sun ma Maanal sorry, kanta kawai ta jinjina musu da ɗan yin murmushi ta wuce zuwa office ɗin Director Mustapha. Bayan tayi knocking aka bata iznin shiga. Ta gaishesa da girmamawa kamar yanda ta saba yima kowa. Shiko ya amsa fuskarsa da murmushi tare da nuna mata kujera. Kanta ta ɗan girgiza masa da ajiye document ɗin hannunta saman desk ɗinsa.        “Sir dama na kammala ne shiyyasa nace bara na kawo maka sai ka duba”.      “Yauwa sister Maanal dama kamar kin san yanzu nake shirin nemo ki, dan ban jima da baro office ɗin CEO ba akan batun. Woow ai sai naga ma kamar waɗan nan sunfi ma wancan ɗin ƙyau”.       Ita dai Maanal komai batace da shi ba kanta a ƙasa, sai da ya gama santinsa sannan ya sallameta akan ta zama cikin shiri koyaushe za'a iya nemansa a conference room. Koda ta koma saita samu har gulmar abinda ya faru tsakaninta da CEO ɗin taje can. Dan ta wuce wasune nayi batare da su sun farga da ita ba. Kowa bata kula ba har abokan zamanta da wasu ke ɗan ƙus-ƙus ta zauna ta cigaba da aikinta.     Bayan anje break daga massalaci Maanal ta dawo kan aikinta, dan tunda tazo companyn bata taɓa zuwa kitchen cin abinci ba. Kullum da abinda zata ci take zuwa daga gida, dan haka bata taɓa maida hankalinta ba. Tana cikin aikin ta samu kira daga head of design office ana nemanta a conference room. Tashi tai ɗauke da drive ɗin data haɗa abinda zata gabatar ta wuce. Batayi mamakin ganin duk manyan companyn a wajen meeting ɗin ba, dan ta fahimci project ɗin nada matuƙar muhimmanci. Sai da ta gaidasu cikin girmamawa sannan ta zauna a kujerar da aka nuna mata. Kusan zaman mintuna biyu sannan CEO ya shigo AS nashi biye da shi. Dukansu miƙewa sukai domin girmamawa, sai da ya zauna a kujerar da AS ya gyara masa sannan yay musu nunin su zauna. Duk zaman sukayi, ita dai Maanal bata yarda ko inda yake ta kalla ba. Sai da Director Steven ya mata magana sannan ta tashi. Kamar waccan ranar yau ma ta gabatar da sabbin zanenta, tare da bayanai akan yanda zai iya kasancewa. Yau ɗin ma dai kowa ya yaba mata matuƙa, dan hatta shi kansa CEO ɗin a mamakinta ya wani zuba mata ido, ita dai kame kanta ta ƙarayi. Tattaunawar ta cigaba da gudana, musamman ta ɓangaren Head of design and engineering da R&D Director da Sales and Marketing Manager sai shi CEO ɗin dake ɗan saka baki. Sun kwashi kusan awa ɗaya da rabi kafin a tashi, yau kam Maanal ita ta fara fitowa daga conference room ɗin tana sauke numfashin gajiya. Har ga ALLAH ta gaji sosai, dan surutun nan na wahalar da ita matuƙa. Kai tsaye elevator ta nufa. Koda ta fito floor ɗinsu sai ta samu anata ƙus-ƙus, bata fahimci ƙus-ƙus ɗin na minene ba sai da ta ƙarasa group ɗinsu. Sama-sama take tsintar gulmar da su Zaharadeen suke suma, wai wata ƙyaƙyƙyawar budurwa ce tazo neman CEO. Sai dai an hanata shigowa kasancewar yana meeting tana a reseption dan tace ko zai kwana a meeting ɗin zata jirasa. Abinda ya kawo gulmace-gulmacen kuwa securitys da suka hanata shigowa taima tas tare da sanar musu cewar basu san matsayinta bane shiyyasa, to itace matar da CEO ɗin zai aura. Wannan furuci nata shine dalilin ƴan ƙananun maganganun dan kowa dai yasan wanene CEO ɗin akan mata. Hatta hoton dake zagaye da duka offices ɗin companyn kowa yayi gulmarsa ya bari dan babu wanda yasan matsayin mai hoton ko sanin wacece ita. Musamman ma daya kasance bawani gane ainahin wanda ke'a hoton ake ba sam. Abinda kowa ya yarda da shi kawai koma wacece tanada muhimmanci a wajensa. Sai kuma ga ita wannan budurwa tazo da sabon zancen daya ɗauki hankalin kowa.       Shigowar wani abokin aikinsu sai dai ba'a rukuninsu yake ba ya sakasu maida hankali wajensa su duka banda Maanal da kunnenta ne kawai ke wajen. Cikin gulma yake sanar musu gafa shi can AS na CEO yazo ya shiga da budurwar nan da'alama zancen dai gaskiya ne ita ɗin matar da CEO ɗin zai aura ɗin ce. Duka sosai zuciyar Maanal take yi, sai da ta dinga ambaton sunayen ALLAH da sauri-sauri sannan ta ɗan fara jin dai-daituwa. Daga haka taji gaba ɗaya aikin da take yama fita mata a rai........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖3️⃣3️⃣ .........Yau kam za'a iya cewa itace ta riga kowa fara tattara kayan tashi tun lokaci bai gama cika sosai ba. Dan zuciyarta gaba ɗaya a ƙuntace take. Ga ƙirjinta ya mata wani irin nauyi sosai. Tamkar an saita sai ga kiran RK ya shigo mata. Kamar bazata amsa ba sai kuma ta ɗaga, sallamarta kawai ya amsa yace ta fito gashi a waje yana sauri ne bazai shigo ciki ba. Ajiyar zuciya ta sauke tare da amsa masa da gata nan. Daga haka taima sauran sallama kamar yanda ta saba ta wuce.       “Kai mutuniyarku kamar fa yanayinta ya sake canjawa tunda akace ga budurwar CEO”. Zaharadeen yay maganar yana gumtse dariya.    Caraf Yusuf yace, “ALLAH nima na lura da hakan, anya kuwa itama bata faɗa tarko ba? Kasan CEO da farin jini wajen matan kamfanin nan kamar ya musu turaren asiri”.       Dariya suka kwashe da shi, Ema dake jin hausar sama-sama dan da Hausa suke gulmar ya ce, “Baku ji labarin ɗazu ba, itama sonshi take shiyyasa take mana wulaƙanci, in dai CEO ne duk zasuyi su gama maitarsu”.     Tsaki yakub yayi tare da miƙewa yana faɗin, “ALLAH ya shirye ku, kuna maza amma gulma ta riga ta muku katutu. Haka kawai kuna ma baiwar ALLAH ƙazafin abinda baku da ilimi a kansa.”     Caaa suka yo masa da masifa suma, bai kulasu ba yay wucewarsa ya barsu....      ★ ★★ ★ “Baby anya kinyi murna da dawowata kuwa?”.     RK dake kallon Maanal cikin wani yanayi ya faɗa murya a raunane. Karo na farko ta ɗan dubesa, sai kuma tai murmushi da bata cika yi ba. Shi kansa saida ya lumshe idanu saboda yanda murmushin nata ya wani ratsa masa zuciya. Idanunta ta ɗan janye daga kallonsa ganin yanda yake wani ƙanƙance nasa idanun. “Daga dawowa zaka fara rigimar taka ko”. Ta faɗa ƙasa-ƙasa batare da tunanin zai jita ba.      Amma a mamakinta sai taji ya saki ƙaramar dariya da faɗin, “Oh ashe kallon rigimamme ake min ni Rafeeq”.        Murmushi kawai ta sake yi batace komai ba. Shima sai ya tada motar suka fice a kamfanin. Sun ɗan yi nisa da tafiyar yanata mata labarin inda yaje. Ita dai bata cewa komai shi kuma bai damu ba. Sai da suna gab da shiga anguwar su Shahidah tace masa, “Yaya jikin Aunty kuwa? Kaƙi dai bani address ɗin naje na dubata”.          “Ayya! Amin afuwa gimbiya. Kin san tafiyar nan ce da babu shiri kawai ta kawo tsaikon. Amma idan babu damuwa gobe idan ALLAH ya kaimu dai ki shirya nazo muje bayan sallar magrib”.      Ɗan jimm tai sai kuma ta ce, “Okay ALLAH ya kaimu, zan dai fara sanarma Didi yanda tace”.       “Ba damuwa hakan ma yayi”. Ya ƙare maganar dai-dai yana horn a ƙofar gate ɗin. Da sauri maigadi ya wangale ƙofar bayan ya leƙo yaga shine. Sun saba sosai saboda RK akwai sauƙin kai ga ƙyauta, da wannan halayen nasa yake saurin saye zuciyar mutane da yawa. Mutum ne mai sauƙin kai matuƙa, da wahala ka zauna da shi bai shiga ranka a lokaci ɗaya ba. Sai da ya gama dai-daita parking idanun Maanal suka sauka akan motar Yazeed. Motar ta zubama idanu na tsayin sakanni, sai kuma ta buɗe ta fito. Shima RK ɗin fitowar yayi hannunsa ɗauke da ledar da bata san da ita ba, sai lunch box ɗinta daya haɗa ya ɗakko. Ganin inda take kallo shima sai ya kalla wajen, a take fara'ar fuskarsa ta canja, har zai miƙa mata kayan dan baida niyyar shiga ciki amma sai ya fasa. Cike da basarwa yace mata, “Muje”.    Kallonsa tayi, sai ya ɗauke kansa. Baki ta buɗe kamar zatai magana amma sai ta fasa, dan ta tabbatar sai ya shiga ɗin tunda yaga Yazeed ɗin na ciki. Ita kam bata san yaya zatai da wannan mutanen ba ƴan rigima. A tare suka shiga falon tana gaba yana biye, Yazeed kuwa na zaune tare da su Barrah kasancewar yau babu islamiyya alhamis ce. Tunda ta shigo shima idonsa kyam a kanta, sai dai yana ganin RK ya tsuke fuska. Jitai kamar ta fasa ihu, amma ta daure dai ta ƙarasa, sannu da zuwa tai masa tare da gaishesa. Shima RK sai ya miƙa masa hannu a ɗage. Shima Yazeed ɗin a ɗagen ya bashi nashin suka gaisa sama-sama. Daga haka RK ya kai zaune yana janye ra'ayin su Haneeff. Shi kuma Yazeed sai ya maida hankali ga Maanal duk da dai yanzu babu fara'ar data shigo ta ɗan gani a fuskarsa. Dama dai can shima ɗin kamar ita ne ba gwanin fara'a bane ba.         Magana Yazeed ɗin ke mata ƙasa-ƙasa tana bashi amsa cikin yanayinta na rashin son magana. Yanda RK ya maida hankalinsa akan shirmen su Barrah sai ka ɗauka bai damu dasu ba, sai dai gaba ɗaya kunnesa da hankalinsa na akansu. A haka Shahidah tai sallama ta shigo falon. Wata irin ajiyar zuciya Maanal ta saki acan ƙasan maƙoshi, kamar an saita sai ga Huznah itama ta shigo, sai dai ita tana cin karon da Yazeed tayi wani turus na ɗan firgici, shima ɗin kallonta yake da mamaki. Cikin ɗari-ɗari ta gaida shi gefe kuma tana satar kallon RK da tunda yay mata kallo ɗaya ya ɗauke idanunsa ya maida ga Maanal. Amsa mata Yazeed ɗin yay da faɗin, “Ke daga ina haka? Yaushe kika zo Abuja?”.      Daburcewa Huznah tayi, dan duk fitsararsu suna tsoron Yazeed kasancewar baya ɗaukar raini dukansu uban kowa yake ci a gidan. Cikin ɗan sarƙewar murya ta buɗe baki zata masa bayani Shahidah ta tari numfashinta.      “Ayya yaya Yazeed zumunci tazo yi mana. Jiya ta iso zata mana hutu ne”.     Shahidahn ya kalla kamar zai yi magana sai kuma ya fasa. Da wannan Huznah ta samu ta gudu ɗaki cikin sassarfa. Maanal nason shigewa ta ɗan watsa ruwa babu dama, sunzo sun sakata tsakkiya. Haka dole ta haƙura har ALLAH yay balling ta akai kiran sallar magriba sannan suka miƙe dan zuwa massalaci. RK dai ya mata sallama alamar bazai dawo ba. Amma Yazeed baice komai ba, hakan ba nufin shi yana nan kenan.      Sanda ta shiga ɗaki baje-baje ta iske Huznah a gado tana waya. Sai ƙyalƙyala dariya takeyi. Komai Maanal batace da ita ba ta wuce bathroom. Daga cikine take ɗan jiyo hirar Huznah ɗin.          “Ai ki bari kawai guy ɗin nan ƙarshe ne. Ga ƙyau, ga aji, ga kuɗi ga iya wanka. Kin san ALLAH yau jinai kamar na rungumesa.”    Dariya ta ƙyalƙyale da shi alamar ana magana daga can, caraf ta cigaba da faɗin, “Ai gara kam kuyi sauri ku kaini kada naja muku abin kunya a gari, wlhy har gida yasa aka kawoni a wata azababbiyar motarsa. Wa ai gobe ma komawa zanyi dan ya tabbatar da ƙarfina na shigo”..          Kai kawai Maanal ta girgiza da taɓe baki, sai ma ta ɗauke hankalinta daga sauraren zantukan shirmen. Ita dama tasan ba banza ta kawo Huznah Abuja ba, ashe kuwa namiji ta biyo. Kai wannan abun kunya dame yay kama mtsoww!. __________★         Washe gari sai ga Yazeed wai yazo kaita office da kansa. Rasama abin cewa Maanal tayi, tadai cigaba da cusa breakfast ɗin da Shahidah ta tsareta yi saboda shan magani. A haka yazo ya samesu. Ta gama shan maganin tana tattara kayanta sai ga maigadi yazo yana sanar mata ga RK yazo, wai ya kira wayarta switch off. Gaba ɗaya sai Maanal ma ta kasa motsi, idanunta cike da ƙwalla ta kai dubanta ga Shahidah da abin yama fara bata dariya. Dan ita kam Yazeed da RK ɗin yanzu dariya al'amarin nasu ke bata. Kowanne baya iya ɓoye kishinsa akan Maanal. Ta wani gefen kuma tausayi suke bata su duka ukun ma. Inda Yazeed yake Shahidah ta juya, sai ta samu wayam alamar ya fita.     “Tofa, shi kuma Ya Yazeed yaushe ya fita”.    Da sauri Maanal ta juya inda Yazeed ɗin yake, itama ganin wajen empty sai ta ɗan waro idanunta tare da maida kallonta ga Shahidah. “Didi ina kuma yaje?”.       “Wajen abokin takararsa mana. Ai wannan samari naki Maanal na kula kowanne da zafinsa yake. ALLAH dai yasa a rabu lafiya kawai. Kinga muje kawai ni na saukeki da kaina sai a raba rigimar. Ya kamata ma su duka ki hutar dasu zuwa kaiki da ɗakkokin nan dan na fahimci abin yana neman ɗaukar wata hanya ne a tsakaninsu”.      Koda suka fito sun samu rayukan Yazeed da RK ɗin duk a ɓace, kallo ɗaya Maanal tai musu ta wuce ga motar Shahidah tai shigewarta. Sai ita Shahidahn ce ta ƙarasa wajensu. Maanal bata san mi yayar tata ta sanar musu ba, koda ta dawo motar kuma batai mata bayani ba ta tayar suka fice.           Haka ta kasance a office babu wani walwala a tare da ita. Dan fuskarta tafi kowacce rana kasancewa a tsuke. Yau ma anyi zama tsakaninta da Marketing and sales manager, sai Head of operation da quality control manager, bayan sun gama meeting akai kiranta da mata tambayoyi akan dai wannan zane nata da company zai fitar. Yau ma da yake bata buƙatar kowa yazo ɗaukarta da wuri ta tashi. Ta fito harabar companyn hankalinta akan agogon hannunta tana kallon lokaci suka kusa cin karo da assistant ɗin CEO. Haƙuri ya shiga bata itama ta bashi. Ta raɓesa zata wuce idonta ya sauka akan AA Darma ɗin dake tsaye shi da wani dattijo suna magana. Yau dai sanye yake cikin farar shadda ƙal datai masa shegen ƙyau da sake fitowarsa a cikakken bahaushensa ɗan arewaci dan harda hula. Da sauri ta kauda kanta tare da ƙara sauri a takunta duk da hakan bai hanata kasancewa a nutsenta ba.       Sarai AA Darma ya ganta shima. Amma ya basar ya cigaba da maganarsa da Alhaji Wakili. Alhaji Wakili tamkar uba ne a wajensa, dan kuwa abokine ga mahaifinsu, sai kuma huɗɗar kasuwanci ta haɗasu, dan yanzu haka ma akan wannan project da zasuyi wanda Maanal tai zanen agogon Alhaji Wakili ɗinne ya kawo mutanen....    Dai-dai Maanal ta fito gate ɗin da nufin samun abun hawa wata taxi ke ƙoƙarin shiga cikin Companyn. Sai dai securitys sun hana mai taxi ɗin shiga, sun tabbatar masa da dole wanda ke ciki sai dai ya fito ya ƙarasa ciki da ƙafarsa. Yanda aka buɗe ƙofar motar a fusace ya ɗan ja hankalin Maanal, a mamakinta sai taga Huznah ce ke fita a motar. Jitai ma gaba ɗaya ta ƙame a wajen ganin yanda Huznah ɗin ke musu masifa da tabbatar musu akanta zasu iya rasa aikinsu. Sukuwa dai securitys ɗin sunce bafa zasu bar mai taxi ya shiga ba dan dokar companyn ce hakan. Ko ma'aikatan wajen indai motar haya suka shigo ƙa'ida anan suke sauka su ƙarasa ciki da ƙafarsu.      Ran Huznah ya kai maƙura a ɓaci, kuma dole ta haƙuran ta sallami mai taxi ɗin ta ƙarasa da ƙafar zuwa ciki. Ga ma'aikatan sun fara fitowa sai kallonta ake ana ƙus-ƙus, itako tana wani yauƙi da taku ɗai-ɗai. Maanal dai tuni ta shige taxi ɗin da Huznah ɗin ta fita. Haka ta iso gida al'amarin nata mata kaikawo. Har jitai ta ƙagara Didin ta ta shigo. Zuwa duba Auntyn RK yasata watsar da komai bayan tayi wanka ta shiga kitchen. Da taimakon Linda ta fara haɗa cake da wasu ƴan kalolin snacks da suka shirya zatayi dan dubiyar ita da Shahidah. Suna tsaka da aikin Shahidah ta shigo tare da yara data biya ta ɗakko a makaranta yau da kanta. Dama haka take musu duk juma'a sai dai idan aiki ya mata yawane tabar driver ya ɗakko su kamar yanda ya saba.      Joining ɗinsu tayi a kitchen ɗin, anan ne Maanal ke labarta mata batun Huznah. Itama mamaki sosai tayi Shahidahn, sai dai basu iya hasaso abinda ya kai Huznah Maawad company ba, har kuma suka kammala aikin bata dawo gidan ba. Dama ba kowa take sanarma zata fita ba, ko jiya Shahidah bata san da fitar tata ba hakama yau ɗin. Ganin har anyi la'asar RK bai kirata ba bai kuma zo gidan ba ta fara tunanin ko lafiya? Gashi ta riga ta ɗauri niyyar zuwa dubiyar nan yau dai ta huta. Kuma jiya da dare ta sanar masa da anyi la'asar yazo ya kaita dan Didi tace bata yarda sai bayan magrib ɗin nan ba. Jitai kamar ta sharesa, sai kuma dai ta danne zuciyarta ta tura masa gajeren saƙo, daga haka ta koma falo ta zauna dan ta shirya tsaf hakama Barrah da Haneeff da zasu mata rakkiya tsaf suke.         Sai kusan huɗu da rabi RK ya iso gidan, yana sanye da shadda shima yanzu ruwan zuma harda hula. A ranta ta ɗan taɓe baki da faɗin (idan anga kuna wankan shaddoji sai juma'a kawai) a fili kam tayi kicin-kicin da fuska daga gaisuwa bata sake kulashi ba, dan shima dai fuskar tashi yau babu walwala. Da alama tun fushin safen ne bai gama sakinsa ba........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖3️⃣4️⃣ ........A motar ma gaba ɗaya sai ya maida hankalinsa akan tuƙi da surutun su Barrah ya shareta, itama dai hankalin nata naga duba wasu novels da Aneesa ta tura mata sunayen su. Tafiyar tasu ba wata mai nisa bace suka iso. Gidane daya amsa suna gida, dan ko'a cikin garin Abujar kasan mai shi yaci ya ƙoshi. Sai da security ɗin ƙofar yazo har inda suke yaga waye sannan ya danna remote ɗin hannunsa gate ɗin fari tas ya zuge kansa. Godiya RK ya masa tare da shigewa cikin katafaren gidan daya yalwatu da shuke-shuke masu matuƙar ƙayatarwa da bama zuciya nutsuwa. Kafin yau Maanal na jinjina girma da tsaruwar gidan Daddy, hakama gidan Didinta Shahidah gidane mai ƙyau da ƙawa. Sai dai gidan nan ya matuƙar disashe mata waɗan can da take tunanin babu kamarsu. Hatta da parking space a tsare yake anan.        Tunda suka fito su kansu yaran ke bin ko'ina da kallo baki a buɗe, Haneeff dai daya kasa haƙuri matsowa yay kusa da Maanal cikin raɗa ya ce, “Mie-mie! Uncle R house ya haɗu kamar ba'a Nigeria ba”.         Kasa cema yaron komai tayi, sai hannunsa daya riƙo nata ta ɗan matsa kaɗan. Dai-dai nan RK dake tattaro kayan tsarabar da bai san ko minene ba ya juyo garesu. Ƙaramin murmushi ya mata ganin yanda take binsa da kallo, batare da yace komai ba ya nuna mata hanya alamar suje, tare da kama hannun Barrah. Ɗauke kanta tayi kamar bata fahimta ba, sai ya sake sakin murmushi yay gaba, dan wannan yana ɗaya daga cikin halayenta dake matuƙar birgesa. A gidan sassa ne har kusan shida. Kuma kowanne da tsarinsa, sannan tsakaninsa da ɗan uwansa akwai ƴar tazara ta yanda baka isa sanin mi nacan keyi ba, ko shi yasan mi kakeyi a naka part ɗin.      Part na tsakkiya a hannun dama suka nufa, RK ya danna bell tare da ɗan juyowa ya kalla Maanal. “Ni dai kar aje ana fushi dani a gaban Aunty na”. Yay maganar yana kashe mata ido ɗaya. Harararsa ta ɗan yi kawai, tare da ɗauke kanta. Shi kuma sai ya sake sakin murmushi. Zaiyi magana aka buɗe ƙofar. Matashiyar budurwa ce da bazata wuce sa'ar Maanal ba, cike da girmamawa ta ɗan rissina tanama RK ɗin sannu da zuwa. Duk da jikinta fes yake cikin tsafta a kallo ɗaya zaka fahimci mai aiki ce, sai dai masu aikin ma irin wanda ke samun kular nan dan babu wani nakasu a tare da ita. Kayan hannun RK ɗin ta amsa, yayinda shi kuma cikin dakewa kamar bashi ba yake tambayarta “Aunty fa!?”.        “Tana upstairs....”    Kansa kawai ya jinjina mata, batare da yace komai ba suka ƙarasa shiga cikin falon da yasha black & golden color na kujeru da labulale, sai wani irin ƙamshin turaren wuta ke tashi mai ratsa zuciya. Ga sanyin ac mai kashe jiki. Gaba ɗaya jikin Maanal sai ya ƙara sanyi. Bata sake tsinkewa da al'amarin ba sai da ya danna wani maɓalli ƙofar glass ɗin dake kamar bango guda ta zuge kanta suka shigo wani falon, nan kam komai golden yellow & white ne, shima dai babu kowa sai ƙamshi dake tashi, wayar da yake dannawa ya kai kunnesa, ba'a wani jima ba aka ɗaga.       “Aunt mun iso”. Ya faɗa cike da girmamawa. Maanal dai data zama kamar wata gunkiya bata san amsar da aka bashi ba taga ya juyo ya kalleta da murmushi, sai kuma ya furta, “Okay gamu nan”. Yana yanke wayar.       “Sorry muje tana sama”. Ya sake faɗa idanunsa akan Maanal ɗin. Kanta kawai ta jinjina masa batare da tace komai ba. Sai dai tana mamakin ta ina kuma zasu bi zuwa saman dan bataga hanya ba sam anan. Amma a mamakinta sai ya nufi wata ƙofa da su, anan ne taga ƙafar benen da shima aka ƙawata matuƙa, dan hatta a ƙasansa ma wasu kujeru ne guda biyu aka tsara da gani wajen zaiyi daɗin hutawa. Haka dai suka haura upstairs ɗin Maanal na sake jinjina jin daɗin da masu hannu da shuni keyi a ƙasar nan. Dole su manta da talaka, dole talaka yasha wahala dan bataga ta yanda za'a iya tunawa da rayuwarsa ba anan. A sama ma wani tsararren falon suka samu, wanda aka ƙawata da ash color na kujeru dama labulalen, nan ɗin ma dai ƙamshin turaren ne yay musu sallama da sanyin ac kaɗan, sai kuma nutsatstsiyar muryar dattijuwar dake musu lale marhabun cike da ƙasaita. Kasancewar RK ya rufe Maanal yasa bata ganin dattijuwar itama bata ganinta, sai dai muryar ta wani irin dakar mata ƙirji.       “Rafeeq ƙaniyarka, dalla gyara ka wani rufe min ƙanwar tawa bana ganinta”.      Dariya RK yayi tare da matsawa gefe yana faɗin, “Oh Aunt ni yau baki son ganina kenan?”.         Baki ta buɗe zata bashi amsa amma sai ta gagara hakan, sakamakon saukar idanunta akan Maanal da ita nata idanun ke kallon ƙasa, dan RK ɗin na matsawa daga rufetan da yay ta rissinar da idanunta saboda yanda bugun zuciyarta ke ƙara ƙarfi. Ga wani irin yanayi mai wahalar fassara dake ratsata. Hakama zuciyarta ta mata nauyi matuƙa a cikin ƙirjinta.....    Gaisuwar Barrah da Haneeff ce ta katse dattijuwar daga kallon Maanal, ta saki ajiyar zuciya da sakin murmushi tana miƙama yaran hannu da faɗin, “Ƙanwata kinga ƙaraso mana, Bismillah zo gareni”.      Sake motsawa zuciyar Maanal tayi a karo na babu adadi, dan Muryar nan tana mata wani irin amsa kuwwa ne da maimaita kanta a matsayin wata murya da amonta ya faru ya kuma shuɗe a duniyarta ta baya. Amma sai ta dake, cikin yanayinta na nutsuwa ta cigaba da taka lallausan carpet ɗin dake tsakkiyar kujerun zuwa inda dattijuwar take zaune, dan tana zaune ne daga ƙasa abinta duk da tima-timan kujerun dake falon. Cak Maanal ta tsaya yayinda take gab da kaiwa inda dattijuwar take, bakomai ya sakata tsayawar ba sai murya ta biyu data daki tsakiyar kunnenta tayi amsa kuwwa a cikin kanta. Sam batai zaton akwai wani bayan dattijuwar a cikin falon ba duk da taji wani ƙamshi bayan na turaren da aka saka a gidan da wanda ta tabbatar dattijuwar keyi. Sai da RK ke faɗin, “Wai dama da gaske kake daga massallaci gida zakayo ashe?”.        “Kaje nemana ne?”.     AA dake kishingiɗe a saman lallausan carpet ɗin kusa gab da dattijuwar dan filo ne kawai ya raba tsakaninsu gabansa wasu document ne barbaje, sai dai a hannunsa shi novel ne yake karantawa, a maimakon shaddar ɗazun yanzu kam ƙananun kaya ne baƙaƙe a jikinsa. Amsar da RK ya bashi yana nuna Maanal da faɗin, “No naje ɗaukar Maanal ne kawai dai” ya sashi wani kallar ɗago idanunsa ya sauke a kan Maanal ɗin data kasa gaba ta kasa baya. Dai-dai nan itama Dattijuwar da hankalin ta ke akan su Barrah ta ɗago tana maimaita sunan.        “MAANAL!” Sai kuma ta miƙe zaram. “Rafeeq da gaske Maanal ɗina ce kamar yanda zuciyata ta ayyana min yanzu-yanzu ko suna ne yazo ɗaya, to amma akwai kamanni mafa” ta kai ƙarshen maganar tana ƙarasowa inda Maanal take. Lallausan hannunta mai ɗauke da zabba masu ƙyau da ɗaukar idanu, tare da bangles takai kan haɓar Maanal data lumshe idanunta da suka cika da ƙwalla ta ɗago. Sosai take raba idanunta akan fuskar Maanal ɗin, sai kuma ta juyo ta kalla RK da shima ya miƙe cike da mamaki, janyewa tai ta maida ga AA da ya maida idanunsa ga book ɗin hannunsa sai dai tuni abinda yake karantawar ya suɓuce masa.         “Auta gane min nan, wlhy Maanal ce ko? Ko Auta Manaal ɗina ne dai ba wata ba. Ajwaad taso, taso dan ALLAH ka tayani gani ko idanun nawane dai ba Baby ba bace....”      Da wani irin ƙarfi AA ya rumtse idanunsa batare daya ɗago ɗin ba, ko motsima baiyi ba daga yanda yake. Sai RK ne ya ƙaraso wajen cikin sassarfa yana faɗin, “Aunt da gaske kin san Maanal ɗina? Maanal Please! Da gaske kema kin san Aunty na?”. Duk ya ruɗe da farin ciki shi kam.           Cikin rawar muryar kuka Maanal da tausayin yanda dattijuwar ta rikice ya sake mamayeta, a hankali ta shige jikinta tana faɗin, “Oum nice, Maanal ɗinki ce Oum. Dama baki manta dani ba, dama zan sake ganinki? Ashe muna da rabon sake haɗuwa kafin na koma ga ALLAH”. Wani irin kuka mai ban tausayi ya suɓuce mata, sai dai hakan bai hana muryarta fita cikin nutsuwa da sanyi ba. Sanyin dake bayyana tasirinsa a jikin AA, duk yanda yake sake kamewa da dakewa abin na neman fito da kansa. Dan Barrah da kukan Auntyn tasu ya sakasu yin narai-narai da idanu suma zasuyi kukan ta matsa gab da shi tana faɗin, “Uncle kaga Mie-mie na kuka ita da Grandma”. Amma ina baiji yarinyar ba, sai da ta ɗan girgiza shi sannan firgigit ya buɗe idanunsa da suka kaɗa matuƙa tare da ɗagosu ya sauke akan yarinyar. Dai-dai kuma Barrah ta miƙe ta nufi inda Maanal take ta rungume mata ƙafafu tana kiran sunanta.         Ɗago Maanal Oum tai daga jikinta itama tana share nata hawayen ga murmushi yaƙi barin fuskarta. Hannayenta duka biyu tasa tana sharema Manaal hawayenta da suka gagara tsayawa, dan gaba ɗaya ma ta kasa cewa komai saboda ita kaɗai tasan irin kalar farin cikin da take ciki. Juyawa tai ga RK da ke kallonsu cikin ruɗani, murmushi ta sakar masa shima. “Rafeeq ALLAH yay maka albarka kaji, yau kam kayi mun babbar ƙyauta daka kawo min ɗiyata har gida.....”        “Aunty duk kin ruɗar dani wlhy, wai kin santa ne daman?”.      “Sosai kuwa Rafeeq, zan iya cemaka kusan nice na raini Maanal ma”.      “What!? Raino fa?”.   “Ƙwarai ma kuwa. Haihuwar Maanal ne kawai ba'ayi a gabana ba. Kunga bismillah kumuje mu zauna”.       RK dai da ƙyar ya kai zaune, sai dai idanunsa akan Oum da Maanal kamar mai tsoron su ɓace masa. Waya Oum ta ɗauka tare da bada umarnin a kawo ruwa. Babu jimawa kuwa sai ga yarinyar nan data buɗe musu ƙofa ɗauke da tray wata da bazata wuce sha huɗu ba biye da ita. Cike da ladabi da girmamawa suka ajiye kayan a saman Centre table, sai kuma suka shiga gaishe da su RK. A dai-dai nan Oum dake riƙe da hannun Maanal kamar mai gudun a ƙwace mata ke tambayarta,      “Ina ƴar uwata Maanal? Ina su Shahidah da Abban ku?”.          “Oum Ammie na nan lafiya Lau, hakama su Didi, wannan ma yaran Didi Shahidah ne”.      “Masha ALLAH! Masha ALLAH! Yanzu yaran Shahidah ne wannan? Kai jama'a ALLAH mai alkairi. Kuzo nan kuyi haƙuri ganin ƴata ya ɗauke min hankali”. Tai maganar tana kamo su Haneeff da sukai ƙwale-kwale saboda kukan Maanal ɗin. Cikin ɗari-ɗari bakamar ɗazu da farko ba suka ƙaraso wajen Oum ɗin, sai da Maanal ta kallesu da sakar musu ɗan murmushi ta ce, “Itama Grandma ce ku gaisheta ku faɗa mata sunayenku”.       Karo na farko yaran suka saki ajiyar zuciya, sai kuma suka shiga gaishe da Oum ɗin. Barrah ta faɗa mata sunanta, da sauri Oum ta kalla Maanal. Murmushi Maanal ɗin tai mata da jinjina kanta. “Eh Oum sunanki aka saka mata, Ammie ce taso sakawa tun akan su Waleed, sai kuma suka kasance maza. Shine Didi na haihuwa aka saka”.           Wani irin rungume Barrah Ammie tayi a jikinta, ƙauna matuƙar ƙaunar Ammie na ratsa ƙashinta da ɓargo. Muryarta na ɗan rawa ta ce, “ALLAH sarki ƴar uwata. Ashe Asiya bata manta da ni ba”.     Murmushi mai ciwo da ƙuna Maanal ta saki batare data iya cewa komai ba. Sai wasa take da yatsunta kawai. Oum ta juya ga AA tana faɗin, “Auta kaji fa ashe Asiya bata manta dani ba. Sunana aka sakama ɗiyar Shahidah”.             Karo na farko ya saki wani irin murmushi mai ban mamaki, irin mai maƙalewa a gefen bakin nan da sai kana kallon mutum kake sanin yayi, sai kuma ya yunƙura a hankali ya riƙo hannun Barrah, matsota yay jikinsa kawai ya rungumeta. A mamakin kowa dake falon sai ji sukai ya furta, “I love you so much tunda kikaci sunan Oum na, ALLAH ya albarkaci rayuwarki”.     “Uncle ni banda ni?”. Haneeff ya faɗa babu zato. Dariya Oum da RK da masu aikin nan sukayi, yayinda Maanal tai ɗan murmushi da girgiza kanta. Shi kam AA idanunsa ya buɗe sosai a kan yaron, sai kuma shima ya sakar masa murmushin da miƙa masa hannu ya riƙosa, cikin maganar nan tasa ƙasa-ƙasa ya ce, “Kaima ALLAH yay maka albarka”.      Cike da farin ciki Haneeff ya amsa masa. Shima RK da Oum duk suka amsa............✍️     🤔Nayi tambaya ko nayi shiru wai???.. kai Bara dai na haɗiye kayana🥱. Idan kuma akwai mai irin tunani na mu haɗu a comment 🏃🏃🏃🏃🏃 ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖3️⃣5️⃣ ........Sosai zuciyar RK ke yin kaikawo a ƙirjinsa matuƙa akan wannan al'amari. Ba komai ya kawo hakan ba mamakin Maanal da AA da koda wasa basu taɓa nuna masa sun san juna ba. Sannan miyyasa AA ɗin bai sanar da Oum fara aikin Maanal a companyn sa ba kusan sati uku kenan. Ko shima dai bai san Maanal ɗin bane? Alaƙar iya Oum ɗin ce kawai da su Maanal ɗin?. Zuciyarsa na ƙoƙarin gamsuwa da hakan sai ga sallamar yayan AA ɗin, da'alama ma yanzu ya shigo gidan daga wajen aiki.        Zama yay a kujera yana sauke numfashi. Oum dake kallonsa cike da tausayawa na jera masa sannu. Amsawa yay fuskarsa da murmushi sai kuma ya ɗora da gaisheta. Sai kuma ya juya ga RK yana faɗin, “Barka da juma'a Uncle”.        Amsa masa RK yay shima yana murmushin. “Wai sai yanzu kake dawowa gida? Ƙarfe biyar fa?”.      “To ya muka iya Uncle. Bakaga shi Autan Oum da yake ɗan shagwaɓa ne ya gudo wajenta da wuri ba”. Dariya RK yayi ganin yanda AA ya dallo musu harara su duka ya maida idonsa ga novel ɗinsa batare da yace komai ba. Sai da suka tsagaita Maanal da kanta ke ƙasa ta shiga gaisheshi ita da su Barrah. Kallonta ya ɗan yi, sai kuma ya ɗauke idonsa ya maida gasu Barrah yana amsa musu da murmushi. Kasancewarsa mutum mai barkwanci idonsa akan RK yake faɗin, “Uncle R kodai Momyn tamu ce ne wai? Dan ɗazun Oum ke sanar min zaka kawota yau”.        Kallon Maanal RK yayi yana mai jinjina kansa fuska ɗauke da murmushi. “Gatanan ai na kawo muku”.     “Kai kai Masha ALLAH, Momyn mu ai ban san ke bace dana durƙusa har ƙasa. Matar Uncle Rafeeq fa. Bara kiga na taso ki saka min albarka ga ɗanki yazo gaisheki”.      Dariya Oum da RK sukayi, yayinda Maanal ta ɗan ɗago ta kallesa a karo na farko. Dai-dai yana ƙoƙarin sake yin magana amma sai maganar tasa ta maƙale a saman harshe saboda saukar idanunsa akan Maanal. Ɗan wara idanunsa yayi na rikicewa, sai kuma ya maida kallonsa ga Oum dake sakin murmushi itama idonta a kansa. Ai da wani irin sauri ya miƙe ya ƙarasa kusa da Oum ɗin ya zauna, tare da kai bakinsa saitin kunnenta ya ce, “Oum idona ne kokuwa dai kaina ne ya kwance da gajiyar aiki? Wai kin san wa nake gani kuwa? Little fa, Bestyn Auta?”.        Kai Oum ta jinjina masa fuskarta na ɗan komawa damuwa, itama a hankalin ta ce, “Itace Fawzan, Maanal ce. Itace kuma Rafeeq ya kawo mana matsayin wadda zai aura”.      Ai zaram sukaga Fawzan ya miƙe yana faɗin, “What!!” gaba ɗaya idanunsa a waje sosai, sai kuma ya juya yana kallon AA daya wani share kowa yana sauraren surutun Haneeff, idanunsa kuma nakan novel da tunda su Maanal suka shigo ya daina fahimtar labarin. Sake ɗaukewa yay daga kan AA ɗin ya maida ga Maanal daketa ƙoƙarin saisaita kanta. Murmushi ta sakar masa mai sanyi, cikin muryarta mai zurfi da rashin son hayaniya ta ce, “Yaya F”.      Maimakon amsawa sai yakai zaune jagwab a kujera yana faɗin, “Ya ilahil'alamina da gaske Little ɗin ce dai Oum. Ni abin ma sai yake min kamar mafarki wlhy”.         “Bakai kaɗai ba Fawzan, ni kaina kallon komai nake kamar a mafarki, yau Rafeeq ya haɗa zuminci sai dai ALLAH ya saka masa da alkairi. Kalla yaran nan yaran Shahidah ne su duka, macen sunana aka saka mata ma”.         Kallonsa ya maida ga yaran, sai kuma ya kalla Maanal. “Little! Su Shahidah duk sunyi aure kenan?”.      Kan Maanal a ƙasa ta ce, “Eh yaya. Itama Didi Amal yaranta biyu”.     Wani murmushi ya saki mai kama dana damuwa, sai kuma ya jinjina kansa, “ALLAH sarki rayuwa komai sai kaga yana faruwa kamar a mafarki. Oum jiba dai Autar ki duk ta canja, komai na Little ya canja kamar ba ita ba. Ji yanda ta zama shiru-shiru, ba surutu yanzu, komai nata ya canja, ta girma ta ƙara tsayi”.      Murmushi sosai Oum tayi itama idonta akan Maanal datai ƙasa da kanta kawai tana wasa da yatsun hannunta. “Sosai kam Auta ta canja Fawzan, badan fuskar na nan ba ma sai nace an canja min ita gaba ɗaya. Girma yazo”.       “A girma yazo kam Oum, ko'a mafarki akace min little zata koma shiru-shiru haka za'a kwana gardama dani ban yarda ba. Little ina Ammie da Abbah fa?”.         “Lafiya lau Yaya, Ammie na Kaduna itama”.      “Ban gane ba, kun dawo Kaduna ne yanzu?”.     Kai kawai Maanal ta jinjina masa. Cikin mamaki ya ɗan juya ya kalla Oum, itama shi take kallo, kamar zaiyi magana sai kuma yay shiru saboda maganar da RK yayi....        “Nifa gaba ɗaya sai sake sakani a wani irin dogon tunani mai rikitarwa kuke wlhy Aunty, wacece Maanal a wajenku dan ALLAH? Ya akai kuma ni ban santa ba?”.      “Ai kwantar da hankalinka Uncle kada ka wani ruɗar da kanka. Maanal dai ɗiyar Oum ce, mu kuma ƙanwa ce. Abinda yasa baka santa ba lokacin da mukai zaman Kano ne, kai kuma sannan kuna Paris”.      Da mamaki RK yace, “Kenan har AA ya santa?”.     Su dukansu juyawa sukai suka kalla AA ɗin da furucin RK ɗin ya wani daki zuciyarsa, hakan ya sashi tsayawa cak da karatun da yake duk da dama tun ɗazun ba fahimta yake ba. Kai Fawzan ya jinjinama RK. Sai kuma ya ce, “Tabbas ya santa”.         Cike da mamaki RK da ke kallon AA ya ce, “Lallai, amma gaskiya na sake yarda kai abin tsoro ne AA. Amma shine koda wasa baka nuna min kasanta ba. Aunty kusan fa 3 weeks da fara aikin Maanal a companynsa shiyyasa kikaga inata ƙara jinjina mamakina ai”.         Kallon juna Oum da Fawzan sukayi, sai kuma suka kalla AA ɗin da har yanzu dai yana a yanda yake, sai ka rantse baya falon ko kuma baya jin mima suke faɗa akansa. Fawzan ya girgiza kansa kawai da murmusawa, “Ai autan Oum sai addu'a Uncle. Little kice har an kammala karatu?” ya maida hankalinsa ga Maanal.      Idanunta ta janye daga satar kallon AA ɗin itama. Ta amsa ma Fawzan da, “Eh Yaya har sarvese nayi”.         “Kai Masha ALLAH, kinga rigimarki ta saka kin kammala karatu da ƙarancin shekarunki, kai Little rigima”.       Hannu Maanal tasa ta rufe fuskarta dan tuna baya. Yayinda Oum keta dariya itama tana tuno abubuwa kamar labarin Film. A mamakin su sai sukaga AA ya miƙe batare da yacema kowa komai ba ya nufi hanyar ficewa daga falon. Da kallo kawai suka bisa.... Sai da ya taka step na farko batare daya jiyo ba ya ce, “Oum na wuce massalaci”. Murmushi Oum tayi da masa addu'a, yayinda RK ya miƙe yana faɗin, “Ɗan rainin hankali shine bazakace mu tashi lokacin salla yayi ba”. Fawzan ma miƙewa yay yana dariya. Sai kuma ya fara raira waƙar Hamisu breaker _Ƴar Arewa_. “Duk wanda yay gamo da abin ƙauna baisan rabewa, in dai ko ya rabe duk nishaɗi nai yay tarwatsewa. Sirrin farin ciki soyayya in ba takurawa, mai so aso shi kanso babu abinda bazai iyaba. Na durkusa akan gwiwata idan kuskure nai. Kiyafiya gyaran dan kamin har maganai. Nemanki na karaɗe kauye na koma birane, fito na ganki Ni kallon kauna kinji yar arewa... Sissiran dake cikin raina duka ne zan baiyyanawa. So yayi tsitstsige na takawa yay min illatarwa. Ni bani fasa yarda domin kin zam rayuwata, manta dake hakan ban san yaushene zan iya ba Kukan da ni nake da kishirwa bata gushe ba, duk da na sani rabuwa bata zamto mutuwa ba..... Harara mai lasisi AA ya wurgama Fawzan tare da wucewa da sauri-sauri kan stairscase ɗin. Hakan yasa Fawzan kwashewa da dariya Oum kuma na murmushi. Shi ko RK da bai fahimci inda waƙar Fawzan ɗin ya nufa ba sai ca yay “To ɗana kodai kaima waƙa zaka koma ne?”. Shi dai Fawzan dariya kawai yake yi yana cigaba da bin AA da har ya gama sauka daga steps ɗin da kallo... Haka suka fice harda Haneeff. Oum kuma ta shiga da Maanal da Barru ɗakinta. Gaba ɗaya idanun Oum sun kasa daina kallon Maanal da dukkan motsinta har suka idar da salla. Tana son mata tambayoyi sai dai yanayin Maanal ɗin yasata haɗiyewa, sai ɗan abinda ba'a rasa ba dai da take tambaya Maanal ɗin na bata amsa. Kiran Shahidah yasa Maanal cema Oum zasu tafi gida. Amma sai Oum ɗin ta amshi wayar tai kiran Shahidah back.        Koda Shahidah ta ɗaga taji ba muryar Maanal bace sai tayi ɗan jim. Cikin girmamawa ta shiga gaida Oum. Itako ta amsa mata tana murmushi. “ALLAH sarki Shidan Abba an girma, an zama iyaye”.     Da wani irin zabura Shahidah ta dafe ƙirji da faɗin, “Oum!”. Sai kuma ta cire wayar daga kunnenta tana sake duba number ɗin. Da gaske no ɗin Maanal ce dai, amma kuma sunan da aka kirata da shi mutum ɗaya ke kiranta da shi a duniyar nan, sake maida wayar tayi kunnenta ta ce, “Maanal!”.         “Ni ɗin ce dai har yanzu Shahidah. Oum ɗinku ce, yau gani ga ɗiyata a kusa dani Rafeeq ya kawo min ita har gida”.   Ba ƙaramin motsawa zuciyar Shahidah tayi ba. Ai babu shiri ta furta, “Oum kenan kece auntyn Rafeeq da Maanal suka zo gaidawa?”.          “Tabbas nice Shahidah, kinga wata hikimar UBANGIJI kuma ko. Dan haka ina roƙon a bar min ɗiyata da jikokina su kwana anan, gobe in sha ALLAHU da kaina zan maidosu gida tunda weekend ne”.      Koda wasa Shahidah bazata taɓa iya musu da Oum ba, dan haka babu jayayya ta sallama. Sai dai tana yanke wayar ta maida akalar kiran nata ga Amaal.      ★★ “Ni wlhy gaba ɗaya kin hatgitsani Didi wai dan ALLAH da gaske kike yi?”.      “Humm Amaal wlhy nima a hargitsen nake. Kema kin san bazanyi miki wasa da wannan zancen ba”.    “Tofa wannan fa shi ake kira da rikita-rikita. Kenan fa idan lissafin yayi dai-dai Rafeeq Uncle ɗin Ajwaad ne? Amma ya akai bamu san Rafeeq ba duk yanda yake da kusanci da Oum haka?”.     “Nima wannan tunanin nakeyi, sai dai kuma wani abu yazo raina. Kin san iyayen Oum na ainahi a lokacin basa Nigeria kamar. Idan baki manta ba muntaɓa jin tana sanar ma Ammie riƙonta akai a gidan Alhaji Abdulkarim Sardauna. Kingako kenan Rafeeq a lokacin baya Nigeria.”          “Tab ɗin, UBANGIJI mai hikima. Didi ni wlhy ma sai yanzu nima wani abu ke dawo min a rai. Kin manta randa muka fara gabin Hajiya Majdiya nake cemuku kamar tana min kamanni da wani amma na manta mai fuskar. Ke da Ammie kukace na cika ƙwaƙwale-ƙwakwalen cewa mutane na kamanni da wasu. To ALLAH kamanin Oum na gani a tare da ita”.      “Ya ALLAH, tabbas anyi haka kuwa Amaal. Kigafa wani al'amari mai ban mamaki, an rabu amma ashe ana tare da juna ta inda sam ba'a sani ba. Ni yanzu ma yaya zamu tunkari Ammie da zancen nan Amaal?”.      “Abinda nake hasasowa a zuciyata kenan, Ammie zatai matuƙar farin ciki. Sai dai kuma Auta Didi, ita nake tausayi da tunani a wannan gaɓar, dan dole ne ɗayan biyu, rabuwa da Rafeeq duk da dama bawani ta amshesa bane, sai kuma auren Yazeed”.       “Humm Amaal kenan, na fahimci kumafa har yanzu kun kasa fahimtar  Ajwaad na'a zuciyar Auta daram, shiyyasa ta kasa amsar kowane namiji a rayuwarta. Abinda ya faru ne kawai ke danne soyayyar da tsiya-tsiya.”      “Na sani Didi, sai dai kema kin san kafiyar Maanal. Kin san idan har tace tabar abu tofa ta barsa ɗin kenan, kuma shi kansa Rafeeq alaƙarsa da Ajwaad sai shi zaisa ta rabu da shi rabuwa ta gaske a yanzu. Kinga kuwa babu wata mafitar data rage mata kuma sai na auren Yazeed, dan dama shigowar Rafeeq ɗin rayuwarta ne kaɗai hope ɗin mu. Babu shi kuwa da kunya a tunkari Daddy da batun ƙin auren ɗansa ko?”.        “Wato Amaal wannan batun na buƙatar zama gaskiya. In sha ALLAHU next week zan shigo kd. Badan ma Oum ɗin tace gobe zata shigo nan ba da goben zanzo.”      “Hakan ma yayi ALLAH ya kaimu, dan nima ban jima da zuwa Abujan bane, yanzu ko nace zanzo sai Abban Munaya yata mita.”         “Ai yama yi ƙoƙari, tsakanin nan kunsha zarya sosai. Ki bari zan shigo ɗin kawai. Bara naje kin san ƴar iskar yarinyar nan na nan gashi babu su Maanal sai Linda kawai, da safe mayi waya”.         “Okay ba damuwa ALLAH ya tashemu lafiya”.... ________________         “Ranka ya daɗe nazo ne domin sanar maka sakamakon binciken ne daman”.      “Rabilu da wuri haka har komai ya kammala?”.    “Ai naga kamar kana buƙatarsa ne da wuri ranka ya daɗe shiyyasa nima nai himma”.       Dariya irin ta manya Sen.. Bukar Kaugama yayi, cike da jin dadi ya ce, “Lallai Rabilu kana son cin mota ashe kuwa”.    Wani kalar daɗi ne ya mamaye fuskar Rabilu. Bakinsa a washe matuƙa ya ce, “To ALLAH ya cidani ranka ya daɗe. Yarinyar dai sunanta *_Maanal Habeeb Giro_*. A gidan Alhaji Sadeeq Busam take zaune, dan matarsa yayarta ce uwa ɗaya uba ɗaya. Sai dai bawani ta daɗe a gidan bane bama, duk da dama tana yawan zuwa tai hutu a wasu lokutan. Tana aiki a companyn Mawaad ne......”      “Oh! Kace shegen takema aiki shiyyasa ashe?”.   Senator ya faɗa cikin katsesa. “Eh tabbas a kamfaninsa take aiki, amma bata wuce ma 3 weeks da farawa ba. Kuma an tabbatar min yaron wajen Doctor KK ne ya samar mata aiki kuma koda yaushe suna tare da shi ma, yanzu haka zancen da nake maka ya ɗauke ta zuwa can gidan Ambassador Aliyu Darma”.       “Ɗan gidan Doctor Kasheem Kura?!”.     “Eh kwarai ranka ya daɗe”.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖3️⃣6️⃣ ______________ https://chat.whatsapp.com/KU8Mqd2Mo530Pc14hc7QOG *ROYAL JELLY* *(MAIDA TSOHUWA YARINYA)* 🔥💃💃 Wani kayan sai amale wannan supplement shi akecema maida tsohuwa yarinya ita Kuma yarinya ta koma jaririya😂💃 Ina kuke Mata masu aji waanda sukeso suga suna walwali kamar tauraro toh gafa dama tasamu kiyi washar washar abinki.....🔥⭐⭐👑 Royal jelly nasa jikin mace yayi glowing mace jikinta yayi Kamar tangaram😍😍 ⭐👑 Royal jelly natsoro da gashin mace yayi kyau ⭐👑 Royal jelly na gyara mace ciki da wajenta ⭐👑royal jelly na fidda shape din mace...💃💃⭐👑 Royal jelly na Hana fatar mace tamukewa , yasa tayi looking fresh ⭐👑 Yanasa mace yayi looking under age dinta💃💃💃kiji ana wacce ke kullun kamar wata budurwa🔥🔥 ⭐👑 Royal jelly nakara hasken Ido yakuma gyara gashin ido 🔥⭐👑 Royal jelly na tsirar da farce da kwarinshi... Idan kinji ana maganar glowing to kici birki a royal jelly 🔥🔥⭐👑💃🏼💃🏼 Haseer supplements ta kawo muku supplement kaloli sai wanda ranki keso hajiya a cikin farashi mai sauqi Phone: 08038796871 _____________ ..........“Alhaji Aliyu Darma ba shike auren babbar ɗiyar Dr Kasheem Kura ba kuwa?”.     “Eh shine, kamar ma itace ta haifi shi yaron nan AA Darma ɗin ai”.       “Okay! Ok! Ok na gane. Yanzu ita yarinyar minene aikinta a kamfanin?”.      “Eh wannan ne dai nake kan bincike ranka ya daɗe. Amma in sha ALLAHU a cikin satin nan zan kammala shima. Na fara kawo maka wannan ɗin ne dai”.      “Ba damuwa Rabilu, hakan ma kayi ƙoƙari. Amma ina son ka binciko min ainahin mahaifin yarinyar shima”.      “To ranka ya daɗe in sha ALLAHU an gama. Wannan itace lambar wayarta”.         “Ok ka samu Oler a waje zai baka kuɗin zuba mai”    “Nagode sosai ALLAH ya ƙara girma da ɗaukaka Ranka ya daɗe”. Rabilu ya cigaba da jera godiya kamar ba gobe...      Yana ficewa Sen.. Bukar yay wani murmushin ƙasaita, tare da shafo sajensa da furfura ta gama yima ƙawanya. Tabbas love at first sight ne ya shigesa na yarinyar nan. Dolene ta shigo a cikamakin matansa uku matsayin ta huɗu, koba komai ya samu ta sakawa a gaban mota dan amaryarsa ya fahimci itama yara sun fara tsofar da ita. Dan ta bari ƙiba ta fara zama mata, shiko sam baya ƙaunar mace tayi ƙiba, hakanne ma ya sakashi ƙara aure na biyu saboda uwargidansa itama haka ta zama rabkekiya, yayi yayi suje a rage mata ƙiba taƙi, sai kawai yayi ta biyu. Itama ɗin dai kwana biyu ta ƙibe masa. Haushi ya sashi auro ta uku, amma abin mamaki itama yaga yanzu ta ɗakko hanyar yin ƙibar, to gara tun kafin ma suje ga hakan yayma tufkar hanci. Dan Maanal zatai dai-dai da ra'ayinsa, gata ƙaramar yarinya. Murmushi ya sake saki, yana jin kamar ya tashi ya fara taka rawa. Dan babu abinda yake sai siffanta surar Maanal a zuciyarsa......      Tofa, Maanalu sarkin farin jini, ga shuger daddy mun samu🏃🏃🏃. ___________★         Tsaye yake kawai ya zubama harabar gidan ido hannayensa duka a cikin aljihun baƙin wandonsa. A kallo ɗaya zaka fahimci yayi matuƙar yin nisa a duniyar tunani. Dan har Fawzan daya shigo sashen nasa ya iso inda yake babu alamar yasan da shi. Sai da ya kai hannu saman kafaɗarsa ya ɗan bubbuga sannan ya juyo...         Murmushi Fawzan yay masa tare da masa alamar minene? da idanu. Sake tsuke fuska AA yay tare da kauda kansa ya ce, “Nothing”.      Ƙaramar dariya kawai Fawzan yayi yana mai girgiza kansa. Sai kuma ya matsa jikin ƙarfen balcony ɗin ya jingina tare da harɗe hannayensa a ƙirji shima ya zubama AA ɗin idanunsa. “Auta kenan, kai kasan ko zaka ɓoyema kowa kanka banda ni nan. Dan na sanka fiye da yanda nasan yunwar cikina ai ko?”. Ya ƙare maganar da wani ɗan ɗage gira sama.      Idanu AA ya lumshe tare da buɗewa duk a lokaci guda. Kamar zai yi magana sai kuma ya maida bakinsa ya tsuke. Murmushi Fawzan ya saki sai kuma ya juya ya kalla inda idanun AA ɗin suke kallo, flat ɗin Oum ne dan haka ya sake maido kallonsa ga AA ɗin.        “Ajwaad nasan har yanzu kana sonta, ba kuma zaka taɓa daina sonta ba. Wannan dama ce ta biyu ALLAH ya sake baka, duk da nasan damar tazo da ƙalubale masu yawan gaske. Ka manta da abinda ya faru a baya domin ƙaddararku ce kai da ita, babu wanda ya isa hana faruwarta. Tun kafin Uncle Rafeeq yay wuff da ita kasan mai yiwuwa, dan yanzu 2025 muke ba shekarun baya da suka shuɗe ba, wannan Maanal ɗin ba wadda ka sani bace a baya, dan tabbas Uncle Rafeeq shima yana sonta sosai.....”     Da ƙarfi AA ya rumtse idanunsa da suka sake kaɗawa, tare taune lip ɗinsa. Kalmar _Sonta..._ ɗin nan na sukarsa.      Fawzan ya cigaba da faɗin, “Sai dai hakan ba yana nufin kai bazaka nuna taka bajintar ba, sai dai ka sani wannan shiru-shirun naka fa da miskilanci dole ka ajiyesa gefe ka koma mata Bestien ta nada da kukai wasan ƙuruciya tare, mai tare mata faɗa, mai damuwa da damuwarta sama da kowa. Dan bana raba ɗayan biyu har yanzu kana nan daram a zuciyarta itama. Nasan Oum zata baka goyon baya ɗari bisa ɗari. Sai kuma ƙalubale na biyu batun Nuratu, kasan dai su Abbah sun fara magana, akoda yaushe kuma zasu iya kai kuɗi idan har baka kawo zaɓinka ba kamar yanda sukace. Dan haka sai kaje kayi tunani kafin lokaci ya ƙure maka. Ina maka fatan nasara”. Ya ƙare maganar da ɗan bubbuga kafaɗar AA ɗin batare da ya jira cewarsa ba yabar balcony ɗin.       Kasa ko motsi AA yay har Fawzan ya fita a sashen gaba ɗaya, daga ta harabar gidan ya kallosa yana nuna masa kansa sai kuma ya ɗaga hannunsa yay masa nuni da agogo alamar lokaci daga haka yay wucewarsa. Da kallo ya cigaba da binsa har ya shige sashensa. Dai-dai nan kira ya shigo wayarsa. Iska ya ɗan furzar mai ƙarfi daga bakinsa kafin ya zarota daga aljihu yana kallon mai kiran. Oum ce da kanta, dan haka ya ɗaga a kasalance ya kai wayar kunnensa yana mai zubama flat ɗinta idanu kamar zai iya hangota daga nan.           “Auta na kana ina ne wai?”.      Idanunsa ya lumshe sai kuma ya saki ɗan murmushin gefen baki daya kasance ɗabi'arsa. Muryarsa can ƙasa ya bata amsa. “Ina sashena Oum”.      “To maza zo ina nemanka”. Daga haka ta yanke kiran. Wayar ya sauke daga kunnesa yana furzar da iska, sai kuma ya maidata a aljihun batare da yace komai ba yabar balcony ɗin..... ____________      Gaba ɗayansu suna a kan d/table kamar yanda Oum ta sakasu yi. RK da Oum ne kawai ke hira, sai dai kuma idanunsa nakan Maanal dake ta faman juya spoon a abincin da RK ɗin ya zuba mata da kansa. Tunda ya zuba matan bata kai ko lauma ɗaya bakinta ba, da farko ma hankalinta na'a kan Novel ne. Sai da Oum tai mata magana sannan ta rufe book ɗin ta ɗauki spoon ɗin. Shine kuma taketa faman juya abincin, ta kuma zuba masa idanu kamar mai irgashi ko tantance abinda aka dafashi da shi. Ita Oum ta fahimci abinda ya saka Maanal ɗin komawa hakan game da abincin, shiko RK sai ya ɗauka ko bata sonshi ne ko kuma dai hankalinta na gida... Kaɗan yay gyaran murya tare da kiran sunanta. A hankali ta ɗago manyan idanunta da kalarsu ta sauya kaɗan, a mamakinsa sai ta sakar masa murmushinta mai sanyi dake narkar da shi. Hakan kuma yayi dai-dai da isowar AA dining area ɗin, kuma a kanta idanunsa suka fara sauka dan haka yaga murmushin data sakar ma RK ɗin. Cak ya tsaya kamar wanda akama tsawa. Shiko RK sam baima gansa ba, dan haka ya maidama Maanal ɗin murmushinta cikin ɗan ranƙwafowa gareta ta yanda ita kaɗai zata ji abinda zai faɗa ya furta, “Gimbiya irin wannan murmushi haka ai sai kisa na ɓace ɓat. Dan ALLAH kici abinci nan fa gidanku ne. Kin san kowa na cikinsa kafin ki sanni ma. Idan kuma baƙya sonshi a canja miki da wani?”.        “Oum gani!”.    AA ya faɗa cikin kaushin muryar data fargar da kowa kasancewarsa a wajen. Sai kuma yanda yay maganar da zafi-zafi ya bama RK mamaki dan abune da bai saba gani ba. AA bashi da yawan hayaniya, amma kuma baida faɗa. Barshi dai da fushi da baƙar maganar tsiya kamar jikan banbaɗawa. Oum ko data fahimci inda fushin ya dosa sai tayi murmushi kawai da faɗin, “Yauwa Autana maza zo ga abinci kada yay sanyi, dan favorite ɗinka akayi”. Tai maganar tana kamo hannunsa ta zaunar da shi a kujera. Maanal kam ko ɗagowa batai ba balle ma ta kalla inda AA ɗin yake, kai bama ta nuna tasan da zuwansa wajen ba sam. Hakan kuma sai ya ƙara baƙanta masa rai, koda Oum ta zuba masa abincin ma ya ɗau kusan mintuna biyu kafin ya fara ci, sai da ma ta sake masa magana da taɓashi.      Maanal ma dai ta fara tsakurar abincin. Duk da kuma yanda ta share kamar bata san da zuwan AA ɗin ba tana satar kallonsa ne ta gefen ido. Yayinda RK ke mata magana lokaci-lokaci, sai dai maimakon amsa ɗan murmushi kawai take masa da jinjina kanta ko girgizawa. Sai yanzu ne maganar Barrah ta sakata ɗagowa, sai idanunta caraf cikin na AA. Wani shegen kallo ya zuba mata data fassara dana tsananin tsana da ƙyama. Babu wani yanayi data nuna ko a fuska ta janye nata idanun zuwa kan Barrah ɗin. Daga haka bata sake yarda ta kalla inda yake ba ma har suka kammala. Itace ta fara barin dining area ɗin, hakan yasa RK tashi ya bita shima.        Da wani kalar yanayi AA ya lumshe oily ayes ɗinsa, batare da ya lura ba ya hankaɗe glass cup ɗin ruwan da aka ajiye masa. Tarwatsewar kofin da ruwan cikin saman ƙyaƙyƙyawan farin tils ɗin ya saka hankalin kowa dawowa wajen. Oum ta miƙe tana mai kamo hannun nasa da sauri ta ce, “Subahanallahi Auta bakaji ciwoba dai ko?”.      Idanunsa dake lumshe har yanzu ya buɗe, sai kuma ya girgiza mata kansa batare da yayi magana ba. RK da tuni ya ƙaraso wajen shima ne yay kiran masu aiki ta landline, kafin ya juyo ga AA ɗin yana masa sannu. Ko kallonsa AA ɗin bai yi ba, shima kuma sai bai damu ba. Dan halinsa babu wanda bai sani ba a gidan dama dangi baki ɗaya. Maanal dai na zaune daga inda take tana kallonsu kawai, amma bata da niyyar tasowa ma. Haka masu aiki suka gyara wajen kamar komai bai faru ba, shima sai ya miƙe.         Oum ce dake binsa da kallo ta ce, “Abincin fa?”.       “Oum na ƙoshi, zanje na kwanta sai da safe”.      “Kwanciya da wuri-wuri haka? Gobe fa babu office”.    RK ne yay maganar yana binsa da kallo. Kansa ya jinjina masa kawai, sai da yaje ƙofa batare da ya juyo ba ya furta, “Anan zaka kwana ne?”.         Kallon agogo RK yay, “No zan wuce dan inada aiki a asibiti ma zuwa nine. Dan har ma sun fara kirana. Zanyi sallama da Maanal kawai”.      A taƙaice ya ce, “Okay” yay ficewarsa. Shima RK wajen Maanal ya koma, yayinda Oum tai shiru kawai zuciyarta na mata kaikawo a ƙirji. Batare data sani ba ta zubama RK da Maanal idanu. Abubuwa ne da yawa ke cuɗa kansu a zuciyarta fiye da yanda take nazarinsu tun ɗazun. Sai dai bata da wani abincewa a wanan gaɓar gaba ɗaya....      ★ ★ ★ Wanka yake son shiga yayi, sai dai haka kawai ya samu kansa da tsayawa jikin window ɗin falonsa ya zubama harabar gidan ido ko nace flat ɗin Oum. Shi kansa bai san ma'anar tsaiwar tashi ba, amma ya cigaba da tsayawar. Hannunsa ɗaya a aljihu ɗayan kuma yana faman ɗagosa ya kalla agogo alamar duba mintuna. Mintuna ashirin ya ɗauka cif a wajen kafin abinda zuciyarsa ke jiran gani duk da yana faman ƙaryata hakan su fito. RK ne gaba Maanal a bayansa, sai dai suna gama fitowa RK ɗin ya dai-daita tafiyar tasu kafaɗa da kafaɗa, tare da ɗan ranƙwafowa gefen Maanal yana magana fuskarsa da wadataccen murmushi hannayensa duk biyu goye a bayansa. Gani yay Maanal ɗin ta tsaya cak, tare da hararar RK ɗin, amma shi sai hararar ta juye masa zuwa kallon soyayya ne, musamman daya ga yanda RK ɗin yay wata irin dariya cike da nishaɗi yana kuma maganar da shi sam baya iya jiyowa daga nan. Da ƙarfi ya rumtse idanunsa tare da datse laɓɓansa da haƙori tamkar zai hudashi. Haka yake idan har abu zai ɓata masa rai ko zaiyi magana yanada ɗabi'ar rufe idanu.     Kamar wanda aka zabura ya wani irin buɗe idanun tare da fara takawa cike da nitsuwa da ƙasaitarsa yayo waje. Kai tsaye sashen gaban Oum ya nufa tamkar wanda ake ingizawa, dai-dai nan motar RK ta gama ficewa a gidan, yayinda Maanal dake tsaye har yanzu ta yunƙura zata koma sashen Oum ɗin tana sauke ajiyar zuciya. Haka kawai yau kuma sai abubuwan RK ɗin ke mata tasiri a zuciya. Duk da dai tasan a tsakanin nan tabbas bata jin zafinsa kamar sanda suna a Jos.        Da sauri taja da baya tare da tsayawa cak ganin mutum a gabanta gingirin. Sai a lokacin ni'imtaccen ƙamshin turarensa ya wani bulala mata cikin hanci saboda yanda iska ta kaɗo mata shi sosai. Ɗan lumshe idanunta dake a cikin gilashi tayi sai kuma ta buɗe a lokaci guda tana ƙoƙarin daidaita kanta. A dakenta, a kuma nutsenta ta ɗago manyan idanuntan ta sauke akan ƙyaƙyƙyawar fuskarsa dake a tsuke, sai dai tsukewar tata bai hana kwarjininsa da mutumtaka da gizagonsa bayyana ba. Shima idanun nasa dake cikin fari tas ɗin eyeglasses ɗinsa dake matuƙar sake ƙawata fuskarsa da gwarzantashi akanta suke. Hakan yasa suka zubama juna ido, kallo irin na tsakkiyar idanun nan. Sai dai sam Maanal bazata iya jurewa ba, dan haka ta janye nata a hankali tare da rissinar da kanta. Cikin sabon yanayinta dake baƙanta masa zuciya da ƙona masa ita ta furta, “Kayi haƙuri sir, ban san kataho bane”. Tai maganar ƙasa-ƙasa da ƴar muryarta mai zurfi tana sake jan jikinta baya, tare da raɓawa ta gefensa zata zagayesa ta wuce.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖3️⃣7️⃣ ______________ https://chat.whatsapp.com/KU8Mqd2Mo530Pc14hc7QOG *ROYAL JELLY* *(MAIDA TSOHUWA YARINYA)* 🔥💃💃 Wani kayan sai amale wannan supplement shi akecema maida tsohuwa yarinya ita Kuma yarinya ta koma jaririya😂💃 Ina kuke Mata masu aji waanda sukeso suga suna walwali kamar tauraro toh gafa dama tasamu kiyi washar washar abinki.....🔥⭐⭐👑 Royal jelly nasa jikin mace yayi glowing mace jikinta yayi Kamar tangaram😍😍 ⭐👑 Royal jelly natsoro da gashin mace yayi kyau ⭐👑 Royal jelly na gyara mace ciki da wajenta ⭐👑royal jelly na fidda shape din mace...💃💃⭐👑 Royal jelly na Hana fatar mace tamukewa , yasa tayi looking fresh ⭐👑 Yanasa mace yayi looking under age dinta💃💃💃kiji ana wacce ke kullun kamar wata budurwa🔥🔥 ⭐👑 Royal jelly nakara hasken Ido yakuma gyara gashin ido 🔥⭐👑 Royal jelly na tsirar da farce da kwarinshi... Idan kinji ana maganar glowing to kici birki a royal jelly 🔥🔥⭐👑💃🏼💃🏼 Haseer supplements ta kawo muku supplement kaloli sai wanda ranki keso hajiya a cikin farashi mai sauqi Phone: 08038796871 __________ ........Babu shiri taja ta tsaya cak, sakamakon jin an cafke tsintsiyar hannunta. Idanunta ta lumshe da ƙarfi sosai, zuciyarta na wani irin mahaukacin bugawa tamkar zata faso ƙirjinta ta fito. Sai dai me wannan Maanal ɗin ba Little Maanal bace ta shekarun baya. Wannan Maanal ce, Maanal cikakkiya ɗiyar Ammien ta. Wadda taga jiya taga yau take kuma fata da ganin gobe. Maanal ɗin data iya ɗauka da shanye abubuwa masu nauyin gaske da ko namiji sai jarumine zai iya zama irinta. Tuni ta saita kanta cikin dakiya da jarumta. Batare da ta juyo ko yin magana ba tai ƙoƙarin fisgar hannun nata. Sai dai me wannan rikon bana rago bane, ba kuma na sakaran namiji bane. Dan riƙone akai mata irin na manyan sadaukai. Ta fahimci hakan ta yanda koda ta fisgi hannun nata duk da da ƙarfi tayi shima bai ko motsa daga yanda yake ba, bai kuma juyo ya kalleta ba balle yin magana.      Sosai zuciyarta ta fara hasala, hasala irin wadda har take jin ɗacinta a maƙoshi. Cikin bayyanar ɗacin a harshenta ta furta, “Minene ma'anar hakan da kake yi?”.       Idan ginin gidan ya tanka shima zai tanka kenan, maimakon yin maganar ma sai fisgarta yay da ƙarfi yay sashensa da ita. Tana ƙoƙarin tirjewa amma hakan bamai yiwuwa bane gareta. A haka ya bugi ƙofar sashen nasa da ƙafa tare da tura kai ciki. Da wani kalar salo ya jefa Maanal saman lallausar kujerar falon, kafin tai wani yunƙuri ya rufu a kanta ta hanyar ɗaura ƙafarsa ɗaya a kujerar ya dogare, ɗayar na a ƙasa.          Wani irin matsewa da matuƙar takura Maanal taji da tsaiwar tasa a haka, tuni jarumtar tata ke neman suɓucewa, dan yanayin neman tuno mata da babban al'amarin daya shuɗe yake a rayuwarsu ta baya amma tana fisgo dakiyarta da tsiya-tsiya. Komai ta haɗiye daga fuskarta da harshenta idanunta a rissine dan bazata iya kallonsa ba ta furta, “Sir minene kake yi haka ne?......”       “Oh you're still pretending?”.    Ya faɗa cikin wani irin kaushi da ɗacin murya mai razanarwa. Dan ita kanta Maanal ɗin sai da taji kayan cikinta sun kaɗa. Amma da yake itama yanzu gwanarce. Ta karantu daga kowanne irin salo da taku sai ta zuba masa idanunta, wani shegen murmushi mai saka yin kamar zaka lumshe idanu ta sakar masa. A nutsenta tana mai sake tsatstsaresa da idanu ta ce, “Pretending?! Dan mi zanyi pretending? Akan me kuma? Yallaɓai”.       Wani kalar taune laɓɓansa yay da rufe idanu yana dunƙule hannunsa. Kamar zai kai mata duka sai kuma miya tuna ya fasa. A maimakon hakan sai ya nunata da yatsansa manuniya.        “Na fiki zafin kai”.     Yanda yay furucin yana wani wara mata manyan oily fararen ayes ɗinsa masu girma da cikar gashi dake cikin gilashi sai ta sake jin tsoro na mamayeta. Amma dai tai ƙoƙarin sake dakewa yanzu ma ta taɓe bakinta ta dauke kanta kawai. Cikin ƙunƙuni ta ce, “Ina ruwana to da zafin kan naka”. Hannu ya kai zai cafko fuskar tata, a zabure ta matsar da jikinta tayi ta gefen daya ajiye ƙafarsa, dan gaba ɗaya ji take kamar an sakata a wani kurkuku dama. Hatta da iska bata shaƙa yanda ya kamata saboda kusancin nasu. Haka ta miƙe ta nufi hanyar fita cikin sassarfa. Wani irin juyowa yay tare da sanya mata ƙafa sai gata a saman kujerar ta sake zubewa.     Hannayensa duka ya zuba a cikin aljihun wandonsa yay wani irin tsaya mata bisa kai ya zuba mata idanun sa tamkar zai haɗiyeta da su. “Ni kike ma ƙunƙuni?”.        Baki ta ɗan tura gaba, sai kuma ta kauda kai gefe, “Ni yaushe na maka ƙunƙuni?”.       Ƙwafa yayi cike da sake ƙuluwa, cikin kakkausan lafazin da bata san ya iya ba ya furta, “Na baki nan da kwanaki uku kacal ki fito ki faɗama Rafeeq gaskiya. Idan ba haka ba kuma zaki sha mamaki”.       A karo na farko ta zuba masa wani irin kallo tana miƙewa akan ƙafafunta, a gabansa ta tsaya sunama juna kallon ido cikin ido, cikin kausasa masa harshen itama ta ce, “Oh mamaki? Ai ba yau na fara shan mamaki daga gareka ba daman. Gaskiya kuma bismillah ai ban hanaka sanar masaba kai, maza sanar masa kafin iska ta rigaka. Ina dai iyaka yace ya janye daga aurena ko, sai me? Nace sai me idan yayi hakan? Ko hakan sabon abu ne daga cikin rayuwata balle ya daman. Ba shi kaɗai ne namiji ba, dubu bayansa biye suke dani kuma in har na basu dama tamkar ƙyaftawar ido zasu amsa da rawar jiki har suna shelantama duniya samuna cike da murna da farin ciki. Balle nayi imanin ko ƴaƴa goma na haifa a duniya Rafeeq zai amsheni ni da su da hannu biyu ya godema ALLAH saboda soyayyar da yake min ta dabance, SO na yake, tsananin SO da wani mahaluki baitaɓa min kwatankwancinsa ba a wannan duniyar.....”       “Ƙarya kike yi!!! I said you are lying!!!!!”.      Ya faɗa cikin wani irin ƙaraji idanunsa da suka kaɗa jazur na firfitowa tamkar zai mareta. Matuƙar tsorata tayi, dan ta gama yarda marin nata zai yi kawai, sai da taji shiru sannan ta buɗe idanunta data rumtse. Suma sun kaɗa sunyi jazur kamar nashi. Cikin dakiya da sake tsatstsaresa da idanun ta ce, “Kai ka ɗauka ƙaryar ne, amma ni da yake nunama soyayyar zan bada labari. Zan kuma tabbatar maka da hakan nan da ƙanƙanin lokaci. Wata ɗaya kacal zuwa biyu zan zama MATARSA, MALLAKINSA ta har ABADA in sha ALLAHU”. Ta raɓashi tai wucewarta fuuuu.         Baiyi wani yunƙurin dakatar da ita ba a yanzu, dan bai ma motsa daga yanda yake tsayen ba harta gama ficewa. Sai lokacin yay wani irin kai hannu ya hankaɗar da flower base ɗin dake ata bayan kujerar mai tsananin ƙyau da ƙayatarwa. Jikake tatsatsa ya tarwatse a ƙasa komai ya zama pieces.        “I will teach you lesson”.    Ya faɗa da tsananin kaushin murya dake bayyana dukkan fushinsa. Daga haka ya juya zuwa cikin bedroom ɗinsa. Kayan jikinsa ya fara zarewa kawai yana wulli da su, kafin ya wuce cikin closet ɗinsa ya ratsa ya shige bathroom. Ƙaton gaske ne shima. An kuma tsarashi da kayayyakin toilet masu ƙawa tamkar ba banɗaki ba. Ƙarƙashin shower yaje kawai ya buɗe duka ukun ruwa suka fara saukar masa a jiki shaaaaa!! Tamkar irin ruwan samar nan mai zuwa babu zato. Hannayensa kawai ya dafe a jikin glass ɗin da aka zagaye wajen wankan da shi ruwan na cigaba da saukar masa. Yafi mintuna talatin a haka dan har numfashinsa ya fara fisga alamar ruwan ya masa yawa sannan ya kashe, a haka ya cigaba da tsaiwar ruwan daya saukar masa na kwararewa musamman na cikin sumarsa dake lashe kuɗaɗe da shi kansa bai san adadi ba. Ada shi ba ma'abocin tara suma bane, amma wasu dalilai suka sakashi fara tarawar harta zama ɗabi'arsa. Ba tara sumar kawai ba, abubuwa da yawa ya ɗabi'antu da su ne daga baya bisa wasu dalilai. Kuma a yanzu sun zama halittarsa kuma jinin jikinsa da shi kansa bai taɓa tunanin raba kansa da su ɗin ba...        Ya jima a hakan, dan sai da zuciyarsa ta koma ta kwanta cikin ƙirjinsa luf kafin yayi wanka kamar yanda ya saba da brush ya fito, idanun nan sunyi matuƙar juyewa da komawa jajaye. Gaban mirror ya tsaya yana goge jikinsa, kafin ya shafa mansa mara hayaniya ya feshe jikinsa da sprys ɗinsa masu ƙamshin tsiya da saka zuciya nutsuwa. Ya kuma gyara kansa da kwantaccen gashin dake lafe a kumatunsa, ya sama bakinsa ƙamshi. Tausasan kayan barci farare tas ya sanya, ya sake feshe jikinsa da turarurrukansa na barci tamkar ba kwanciya zaiyi ba sannan ya nufi katafaren bed ɗinsa dake a wani kalar dunƙule waje guda tamkar zero. Zama yay ya jingina da gadon tare da kai hannu ya rage fitulun ɗakin ya maida mai duhun haske sai bed side lamp kawai dake kunne itama ta gefensa. Sai da yaja lallausan duvet ɗinsa ya rufe ƙafafunsa zuwa ƙugu sannan ya ɗauki eyeglasses ɗinsa dake ajiye kusa da novel ɗinsa dake a bed side drawer ɗin ya saka, novel ɗin shima ya ɗauka. Alamar daya saka a inda ya tsaya ya sashi buɗewa kai tsaye ya fara karatu cike da son kauda komai dake cinkushe da zuciyarsa.....     ___________★         Kamar yanda ta saba damunsa a kowanne dare da sakwanni yau ma tsaf ta kammala shirin barcinta ta faɗa saman gado. Jinta take wani free yau ita kaɗai a ɗaki babu Maanal. Sai hakan ke sakata nishaɗi tun ɗazun. Yayinda tuni ta kaima uwarta gulmar fitar Maanal ɗin da saurayi da rashin dawowar tata. Nan sukasha gulmarsu da aibanta Maanal ɗin wai tana can an kaita hotel yawon fasiƙanci dai aka fake fa dubiya. Bayan sun kammala wayar ne tai abubuwan da malam ya bata tai shirin barci shine ta ɗauki waya. Kai tsaye data ɗin ta ta buɗe. First WhatsApp ta fara shiga, duk da ta fahimci kamar bai cika damuwa da WhatsApp ɗin ba sam. Amma tanan take saurin gane idan yana online. Koda yake da wahala ma kaga ya kashe data shi kam. Yanzun ma dai kamar yanda tai fata yana online ɗin, cike da farin ciki ta tura masa sallama da gaisuwa kamar yanda ta wajabtama kanta a yanzu. Ganin fin minti biyar babu amsa ta shiga masa WhatsApp call. Amma har ya kashe ba'a amsata ba. Fita tai ta koma ta tura masa ainahin massege, nan ma mintuna biyar shiru. Sai tai direct call kawai tana fatan ya ɗauka koda bazai ce mata komai ɗin ba kamar yanda ya yi mata. Dan data taki sa'a ya ɗauka har sau kusan uku data kira shi, sai dai daga sallama da amsa mata gaisuwa a cinkushe baya sake cewa komai zai barta taita surutunta harna tsahon mintinan data fahimci batasu yake daga haka a takaice yace goodnight ya yanke wayarsa. Kota sake kira kuma bazai amsa ba. Sau biyu yana mata haka, sakamakon roƙon wannan alfarmar datai a garesa jiya data bisa office, a lokacin bai tanka mata ba, amma data kira ɗin bayan ya gama bata wahala sai ya amsata a jiyan, hakama yau da safe. Shine ta samu hope ɗin sake kiransa yanzu ma da fatan ya ɗaga ɗin dan tanada yaƙinin aikin malam ya fara karɓuwa. A wajen bikin Yaseerah ko kallo bata ishesaba fa, amma a wannan karon gashi ya kulata har a office data samesa ya kuma bada mota aka maidata gida, ai dole tace aikin malam yayi.        A kasalance ta ajiye wayar ganin kira har uku babu amsa, amma sai zuciyarta sam bata gajiyaba, har yanzu tana jin zalama da fatan ya amsa ɗin. Sake tura masa text massage tayi har uku na roƙon ya ɗaga kiran, ta watsap ɗin ma ta tura masa, sannan ta sake kira. Sai dai yanzun ma babu alamar zai ɗaga mata. Idanunta na zubar da hawaye ta tura masa tsararren sabon saƙo masu kalamai masu armashi da kashe zuciya sannan ta kwanta badan taso hakan ba. Ta jima batai barci ba hawaye na bin fuskarta. Ita kanta bata san irin son da takema bawan ALLAHn nan ba. Amma tabbas mai zafi ne. Matuƙar zafin da ta tattabar idan bata mallakesa a matsayin miji ba akwai ƙura...... ___________★         Maanal bata koma sashen Oum ba sai da ta tabbatar ta daidaita kanta da nutsuwarta a waje. Dan sai da tasha kukanta sannan ta share hawayenta tsaf ta koma sashen Oum ɗin. A falo ta sameta mai aikinta na kwashe su Barrah da sukai barci za'a kaisu ɗaki ai musu shirin barci kamar yanda taji Oum ɗin na bada umarni. Komai batace ba, sai zama tai tana murmushi da faɗin, “Oum duk munzo mun sakaki wahala”.     Harararta Oum tayi cikin sigar wasa. “Oh haka kike ɗauka shiyyasa kika kasa sakin jiki dani. Gaba ɗaya kamar ba Lillyn babban yaya ba, kamar ba Autar Oum ba, kamar ba Bestien Auta ba. Maanal kin canja min, matuƙar canjawa da mamakin hakan ya kasa barina”.      Kai kawai Maanal ta duƙar tana murmushinta mai sanyi, sai kuma ta furta, “Nama manta banga Babban Yaya da matarsa da Mamy da Abbah ba?”.          “Uhm sai yanzu kika tuna da su? To suna nan abinsu. Mamy tana tare da Abbanku ne a ƙasar Oman, Amma ina ƙyautata zaton nan da kwana biyu suna hanya insha ALLAHU. Babban yaya kuma da matarsa da matar Fawzan da yara suna Kano ana bikin ƴar ƙanwar Mamy ɗin ne kin san kuma itama Saheeba kamar ƙanwa ce a wajenta. Shine matar Fawzan ta mata rakkiya shima yau Babban yaya ya wuce da yammar nan dan yana fita kuna shigowa. Ɗaurin auren safe ne shiyyasa yaje ya kwana sai ya dawo goben idan ALLAH ya kaimu. Su kuma sai biki ya tashi, Fawzan da Auta aiki ya hanasu zuwa, ni kuma jikin nawa ne sai a hankali”       Cikin gamsuwa Maanal ta jinjina mata kai batare data sake cewa komai ba, sai dai tayi mata addu'ar lafiya mai dorewa. Daga haka itama Oum ɗin ta zuba mata ido kawai. Sai kuma zuwa can ta katse shirun nasu da faɗin, “Rafeeq ɗin ya wuce kenan?”.        Batare data ɗago ba ta ce, “Eh wai ana jiransa a asibiti ne”.     “Uhm ai ya riga da ya ɗaurama kansa irin aikin Papa. Gashi nan gaba ɗaya nauyin ya koma kansa yanzu, dan ma Papan na ƙoƙarin rage masa wasu abubuwanne. Mu kuma so muke shi ya huta saboda tsufa, dan ma ALLAH ya bashi jiki mai ƙyau ne da kuma zuciyar taimakon al'ummar. Tun yaushe kuke tare da Rafeeq Maanal?”.         Matuƙar dukan zuciyarta tambayar tai, dan har sai da ta motsa mata a cikin ƙirji, maƙoshinta ya ɗan bushe saida ta haɗiyi yawu da ƙyar. Yanzun ma bata ɗago ba kanta a ƙasa tana wasa da yatsun hannunta ta bama Oum ɗin amsa cikin Muryar tan nan ƙasa-ƙasa.      “Shekara ɗaya kenan Oum, a Jos inda nayi sarvese”.     “Oh iko ALLAH, dama kece yaketa bani labarin ya samu a Jos ashe. ALLAH mai girma kenan. Ya jima yana faɗa mana ni da Majdiya, sai dai bamu maida hankali ba saboda sanin halinsa sarai. An jima ana fama da shi akan aure yana botsarewa da faɗin shi baiga wadda tai masa ba. Har Papa ya fusata zai haɗashi da wata yarinyar abokinsa sai gashi da zancen ki. Amma sai babu wanda ya ɗauka serious ne. Ko kwanciyar asibitin nan naƙi zuwa ne saboda ban wani yarda da gasken yake ba duk da Majdiya ta sake tabbatar min. Ashe nayi sake da tuni naga ɗiyata da ƴar uwata. Nayi kewar Asiya matuƙa Maanal. Haka ke da su Amaal, idan na tunaku a raina har hawaye nake wani lokacin. Bana fatan ALLAH ya sake maimaita min abinda ya faru a baya”.      Hawayen da suka cika idonta suka gangaro. Hannu tasa ta sharesu da sauri tana murmushi mai ciwo. Sai kuma ta miƙe tana faɗin, “Kinga tashi muje kiyi shirin barci ki kwanta. Dan Rafeeq ya jaddada min ki kwanta da wuri”. Ta ƙare maganar tana ƴar dariya da kama hannun Maanal ɗin da jikinta yay wani kalar sanyi ƙalau.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖3️⃣8️⃣ ______________ https://chat.whatsapp.com/KU8Mqd2Mo530Pc14hc7QOG *ROYAL JELLY* *(MAIDA TSOHUWA YARINYA)* 🔥💃💃 Wani kayan sai amale wannan supplement shi akecema maida tsohuwa yarinya ita Kuma yarinya ta koma jaririya😂💃 Ina kuke Mata masu aji waanda sukeso suga suna walwali kamar tauraro toh gafa dama tasamu kiyi washar washar abinki.....🔥⭐⭐👑 Royal jelly nasa jikin mace yayi glowing mace jikinta yayi Kamar tangaram😍😍 ⭐👑 Royal jelly natsoro da gashin mace yayi kyau ⭐👑 Royal jelly na gyara mace ciki da wajenta ⭐👑royal jelly na fidda shape din mace...💃💃⭐👑 Royal jelly na Hana fatar mace tamukewa , yasa tayi looking fresh ⭐👑 Yanasa mace yayi looking under age dinta💃💃💃kiji ana wacce ke kullun kamar wata budurwa🔥🔥 ⭐👑 Royal jelly nakara hasken Ido yakuma gyara gashin ido 🔥⭐👑 Royal jelly na tsirar da farce da kwarinshi... Idan kinji ana maganar glowing to kici birki a royal jelly 🔥🔥⭐👑💃🏼💃🏼 Haseer supplements ta kawo muku supplement kaloli sai wanda ranki keso hajiya a cikin farashi mai sauqi Phone: 08038796871 _________ ........A haɗaɗɗen bayin Oum Maanal tayi wanka. Ita dai sai bin ko'ina take da kallo. Tun can baya tasan su Oum nada kuɗi, amma komai nasu ya sake canjawa daga sanin datai masan. Ita kanta Oum ɗin ta sake gogewa ko tsufa batayi. Da waɗan nan tune-tunen ta fito a wankan. Rigar wanka ce dan haka bata ɗan ji takura ba sosai, koda yake Oum bata cikin mutanen daya kamata acema tana jin kunya, to mi zata ɓoye mata, matar da tun bata san kanta ba take mata wanka harda goyo. Tasha kwana a gadon Oum daga ita sai pant. Oum da Bestyn ta ne suka fara sanin jinin haila yazo mata. Kalmar (Besty) ta sake maimaita kanta a cikin zuciyarta, sai kawai taji zuciyar tata ta mata nauyi. Ture tunanin tayi da ƙarfi ta maida hankalinta ga bin ɗakin da kallo. Oum ta fita, sai kaya da aka ajiye a saman gado. Kayan ta matsa ta ɗaga. Wando da riga ne na barci, sunada yalwar da bazasu matseta ba ko kaɗan. Bata wani ɓata lokaci ba ta sanya, tana gama sanyawa Oum ta shigo ɗakin hannunta ɗauke da wani ɗan basket mai ƙyau golden. A gefen Maanal ta ajiye, Maanal ta kalleta tana mata sannu sannan ta kalla kayan. Mayukane da zasuyi dai-dai da fatarta, ba daidai da fatarta kawai ba ta jima da saninsu, dan dasu take amfani ada, bayan ita kuma mutum ɗaya tasan yana amfani da su a gidan....      Kamar Oum tasan mi take tunanin ta katseta da faɗin, “Nasan nawa bazasu ma skin ɗinki ba. Shiyyasa na kira Auta ya kawo miki nasa dan nasan fatanku yana ɗaukar mai iri ɗaya ne, sai kuma akai sa'a irin wanda ma kike amfani da su ne. Maza ki shafa kada jikinki ya bushe bara nima nai wankan”. Daga haka Oum ɗin ta miƙe batare da ta jira cewarta ba. Maanal ta jima bata motsa ba idanunta akan kayan shafar, wani abu ne mai nauyi ke tsikarar mata zuciya. Yayinda tunaninta ke kai kawo da tambayar kanta miyyasa ya cigaba da amfani da irin manta? Miyyasa wasu abubuwa nashi har yanzu suna a yanda ta sansu, waɗansu kuma a baya suke yawan faɗa akan tana so yayi su yaƙi yi. Amma a yanzu duk sai taga yana yin su.....       Knocking ƙofar da akayi ya sata ture tunaninta gefe ta kalla ƙofar, jin an ƙara na biyu yasa ta miƙewa ta ɗan gyarama su Barrah bargo sannan ta nufi ƙofar, duk zatonta cikin masu aikin Oum ne. Sai dai tana buɗewa taci karo da abinda bashi tai zato ba. Muƙut ta maida abinda tai niyyar faɗa ta haɗiye abinta tare da janye idanunta daga kansa taja jikinta baya ta koma tai zamanta a inda ta taso. Sai lokacin ya ƙarasa shigowa ɗakin hannayensa duka biyu zube cikin farin wandon kayan barcin sa. Tafiya yake cike da ƙasaita, ga mayataccen ƙamshinsa duk ya rikita ɗakin. Baiko kalleta ba ya wuce closet ɗin Oum kansa tsaye kuma hankalinsa kwance. Ƙasa-ƙasa Maanal ta bisa da kallo, tana mamakin mi kuma ya kawo shi yanzu. Bata da mai bata amsa, sai ma kira daya shigo wayarta a dai-dai lokacin. Wayar dake acan saman mirror ta ɗan zubama ido, sai ta tsinta kanta da jin nauyin jiki har kiran ya tsinke. Wani kiran ne ya sake shigowa, sai hakan yay dai-dai kuma da fitowar AA hannunsa ɗauke da wata bag ƙarama. Har ya wuce batare daya kalleta ba itama ta miƙe da nufin ɗaukar wayar sai ta hangesa agaban mirror ɗin kamar mai neman wani abu. Komawa tai ta zauna, sai kawai jin ƙarar wayarta tai a ƙasa. Da sauri ta ɗago, wayar tata ce kuwa, yayinda shi kuma yake duƙe yana duba abu a drawer ɗin jikin mirror ɗin tamkar ma baiga abinda ya faru ba. Oum dake fitowa ta ce, “Subahannahi kako yaddoma Auta waya Auta”.      Tsabar rainin hankali irin na AA sai ya juyo irin as bai lura ɗin nan ba ya ɗauki wayar yana jujjuyawa, ƙarasowa itama Oum ɗin tai inda yake ta amshi wayar ta duba. Gaba ɗaya tayi tatsa-tatsa. Screen ɗin yay wani irin zuuuuu alamar ya tashi aiki shima. Babbar waya ce, dan SS ce babba Daddy ya saya mata ita gift ɗin kammala karatun ta.        “Auta kayi ɓarna”. Oum ta faɗa tana sake jujjuya wayar. Fuskarsa dake a tsuke ya yamutsa babu alamar damuwa a tattare da shi ya ce, “Oum ban lura bane. Kawo zanba Ahmad da safe ya gyaro”. Yay maganar yana miƙama Oum hannu. Kanta kawai ta girgiza da ɗora masa wayar a hannunsa. Shi kuma batare daya ce komai ba ya ɗauka bag ɗinsa ya fice. Ajiyar zuciya Oum ta sauke tare da juyawa ta dubi Maanal. “Karki damu kinji Auta, nasan in sha ALLAHU zai bada a gyara kafin wucewar mu goben”.       Murmushin yaƙe kawai Maanal taima Oum. “Babu komai Oum”. Itama Oum ɗin sai tai murmushi tana jinjina mata kanta. Haka sukai shirin barci suka kwanta. Dan har Oum ɗin kwanciyarta tai a gadon tana faɗin, “ALLAH ya yarda yau zan sake kwanciya gado ɗaya da Babyna”.      Siririyar dariya Maanal ta saki, yayinda Oum ke tayata itama zuciyarta cike da nishaɗin yanayin.....     __________★         Washe gari da safe bayan sunyi wanka suna dining da shirin karyawa harda Ya Fawzan AA ya shigo. Da mamaki Oum daya fara gaidawa take kallonsa. Dan a shirye yake tsaf cikin baƙaƙen suit da suka sake fiddo ainahin cikar haibarsa da madarar ƙyau.       “Yau ba Saturday ba na ganka da shirin office?”. Oum ta faɗa cikin kasa haƙuri. Hannu ya miƙama Yaya Fawzan yana bata amsa da, “Oum project ɗin nan da nake gaya miki yau zamu fara aikinsa da Engineers ɗinmu”.       “Okay aina ma shafa'a, ALLAH yasa ayi cikin nasara ya kuma ɗaga darajarsa. Maza to zauna ka karya dan bazaka fita da yunwa ba”.             Agogon hannunsa mai matuƙar nauyin kuɗi da zama designer daba ako ina zakaje ka samesa ba sai ga wanda ya isa ya kalla. Cikin ɗan ɓata fuska ya ce, “Oum Please zansha coffee a office”.         “Ban yarda ba kuwa. Zauna in ba hakaba nasa Fawzan ya riƙe min kai na maka ɗura”.     Dariya sosai Fawzan yake yi, ya ce, “Tsaf kuwa zan danne miki shi Oum dan wannan girman jikin nasa da ƙarfuna suka bubbuɗe ba tsoro zai bani ba.”        Harararsa AA yayi, dan dole yakai hannu yaja kofin gaban Maanal da tunda ya shigo tai masa kallo ɗaya ta maida kanta bata sake ba, daga tsayen da yake ya kai shayin bakinsa, dai-dai Maanal ɗin tana ɗagowa ta kallesa da mamaki, hakama Fawzan da Oum duk kallonsa sukayi. Amma ya wani basar kamar bai gani ba. Sai Oum ce tai masa nuni da kujera. “Maza zauna tunda kadai san babu ƙyau shan abu daga tsaye”.     Baice komai ba ya zauna ɗin, sai faman kallon agogonsa yake yi alamar dai a ƙagare yake. Barrah da Haneeff ne suka fito daga kitchen tare da mai aiki. Dan sunce su noodles zasu ci shine taje dafa musu suka bita. Ganin AA ya sasu nufosa, cikin haɗa baki da ɗokin ganinsa sukace, “Uncle good morning”.        A mamakin kowa sai ya saki murmushin nan nasa na rowa tare da shafa kawunansu ya na amsawa. “Good morning Handsome & Oum na. Fatan kun tashi lafiya?”.       “Uncle Alhamdullah”. Suka faɗa cikin haɗa baki. Murmushi ya sake sakar musu da cewa, “Masha ALLAH”. Daga haka ya miƙe yana ajiye kofin da sauran shayi a inda ya ɗauka. Sai Maanal ta samu kanta da tsurama kofin ido kawai har yay sallama dasu Oum ya fita kafin ta farga. Yaya Fawzan ne ya katseta. Kayan shayin ya tura gabanta yana faɗin, “Haɗa wani shayin tunda ya shanye miki kinji Lilly”.       Ɗan murmushin yaƙe Maanal tayi, cikin muryar nan tata mai sanyi ta ce, “Yaya akwai a ciki ya isheni”.         “Kin tabbatar?”.    Kanta ta jinjina masa. Oum dai Murmushin ta take irin na manya batace komai ba. Sun kammala breakfast ɗin babu jimawa sai ga RK. Da gudu su Haneeff suka maƙalƙalesa suna murna. Hakan yasa Oum sake fahimtar akwai shaƙuwa sosai tsakaninsa da yaran. Fawzan ma har yanzu yana a sashen Oum ɗin suna hira, sai kawai RK ɗin ya baje aka dora da shi bayan mai aiki ta haɗo masa breakfast dan yace bai karya ba. Anan falon ya karya suna hirar, idonsa akan Maanal dake kwance kanta a cinyar Oum tana karatun novel ɗin nata na fama. Sai ƙara jinjina shaƙuwar Oum ɗin yake da Maanal ɗin, dan kuwa yanda Maanal ɗin ta saki jiki ya ishesa shaida. Musamman idan yay dubi da miskilancin tsiya irin na Maanal ɗin.... ____________       Da mamaki Shahidah ke sauraren Linda dake mata bayanin fitar Huznah tun 8. Ranta ne ya fara ɓaci da iskancin Huznah ɗin. Yaya tana a gidanta amma bata da mutuncin da zata dinga gaya mata zata fita. Kai ko gaisuwa tunda Huznah tazo gidan nan bata jin ta mata. Shi kansa Abbansu Barrah duk kawaicinsa yau da safe sai da yay magana. Shine ma dalilin da yasa yanzu da zasuyi zaman breakfast taima Linda magana akan ta tado Huznah ɗin su karya. Amma sai take sanar mata wai ta fita tun 8. Da alama kuma anguwa ta tafi dan taci gayu.      Komai batace da Linda ɗin ba ta juya tabar dining ɗin. Bedroom ɗin ta ta shiga ta ɗau waya tayi kiran Ammie. A lokacin Ammie na tare da Daddy dan yau itace da shi. Bata ɗaga kiran ba har ya tsinke. Cikin hikima tacema Daddy tana zuwa dan wayar tata dama a silent take. Sashenta ta koma sannan tai kiran Shahidah ɗin. Bayan ta amsa gaisuwar da Shahidahn ke mata ta ce, “Mike faruwa da safen nan kira Shahidah?”.        Cikin matuƙar ɗacin murya Shahidah ta ce, “Ammie akan yarinyar nan ne Huznah. Nifa gaskiya ina jin tsoro. Tunda tazo fa ba zama take ba, da mun fita aiki take shiryawa itama ta fice gidan nan wani lokacin ma sai mu rigata dawowa. Yau kuma da take weekend ma kinji tun 8 tabar gidan nan. Ammie ina jin tsoron kar wani abu ya faru ace a zamanta nan ne ban saka ido a kanta ba fa”.        Numfashi mai nauyi Ammie ta sauke. Cike da nazarin maganganun Shahidah ɗin ta ce, “Kenan akwai dai abinda tazo yi Abujan, saboda uban ya barta suka jinginata da zuwa gidanki ta zauna. Ki kwantar da hankalinki in sha ALLAHU babu abinda zai faru. Zuwa anjima zan kira Yazeed nai masa bayani ya sanya ido a kanta tunda yana Abujar.”        Ajiyar zuciya Shahidah ta sauke cike da gamsuwa tace, “Yauwa Ammie hakan dai yafi kam gaskiya. Dan shi kaɗai ne maganinta nikam bajin maganata zatai ba tana ganin shekarunmu ɗaya. Yasu Hameed da Aunty Sakina”.      “Lafiyarsu ƙalau gaba ɗaya. Ya batun dubiyar da su Auta sukaje jiyan?”.     Gaban Shahidah ne ya faɗi, amma sai cikin wayancewa ta ce, “Lafiya lau Ammie babu wata damuwa. Dan yanzu haka ma barci takeyi”.      “To Alhamdullah, dan inata tunanin kar taje gidan mutane ta nuna bata son yaronsu. Ni kuma harga ALLAH yaron ya shiga raina saboda nutsuwarsa da sanin darajar mutane. Tunda al'amarin Yazeed ya koma wani iri gara ta haƙura da Rafeeq ɗin ayi a wuce wajen zaman nan nata damuna yake yi”.      “Ammie adai cigaba da addu'a, in sha ALLAHU komai zai dai-daita, nawa ma Maanal ɗin take, rigimarta ce ta sata gama karatu da da wuri amma da yanzu ne fa ma ya kamata ta shiga jami'a. Rafeeq kam baida matsala mutumin kirki ne. Ya cancanta ai masa komai, kuma sun dace da Maanal ɗin. Sai dai nasan akwai rikici Ammie.....”     “Rikicin mi kuma? Wani abu ya faru ne?”.     “A'a babu abinda ya faru Ammie. Kawai nasan janyewar Yazeed akan Maanal bazai kasance mai sauƙi ba. Dan yana matuƙar sonta, auren nan dan baida yanda zai yi ne kawai uwarsa tafi ƙarfinsa ne. Yanzu haka kullum cikin roƙon Maanal yake akan ta bari a haɗa bikin ayi gaba ɗaya zaifi samun kwanciyar hankali. Ni wlhy duk sai ma tausayinsa ya fara damuna”.        “Nima ina jin tausayin nasa Shahidah. Sai dai su haƙura da junan sai yafi alkairi fiye da yin, dan nasan wacece Hajiya Sadiyya. Komai zata iya yi kamar yanda ta faɗa. ALLAH dai ya kawo mafita cikin sauƙi. Bari anjima mayi wayar na bar babanku shi kaɗai ina wajensa kika kira”.      “To Ammie ba damuwa sai anjima”...........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖3️⃣9️⃣ ______________ .........A ɓangaren Huznah tana can gidan Yaseerah. Dan dama sunyi da ita yau da wuri zataje gidan kasancewar tunda tazo sai dai tayi zuwan fisha. Ta samu ko barci basu tashi ba. Saboda weekend ne mijinta na gida. Sai kawai ta shige ɗayan bedroom ɗin Yaseerah ta kwanta itama ta ɗora barcin da bata samu yi ba a daren jiya isashe.       Sai wajen sha ɗaya Yaseerah da mijinta suka fito. Suna a d/table zasu fara breakfast mai aikinta ke sanar mata zuwan Huznah ɗin. Mijin nata ta kalla tana ɗan murmushi. “Baby Uncle ɗinka fa ya rikita min ƙawata. Munata binsa kuma yaƙi bamu muhimmanci. Yakamata ka shiga lamarin nan haka nan”.       Murmushi yay shima dakai kofin tea bakinsa. “Ai dama na faɗa mata tun farko, shi bana wasan yara bane. Dama Uncle Fawzan ne da sauƙi, amma Uncle AA tab ɗin, ina tausaya mata ALLAH. Da zata ji shawarata da ta jima da manta ta taɓama saninsa kawai.”         “Bazan iya haka ba Abdul-hakeem. Dan a yanzu bani da wani burin daya wuce mallakar Uncle ɗinka.”    Muryar Huznah da basu san da zuwanta wajen ba ta ratsa kunnunwansu. Gaba ɗayansu juyawa sukai suna kallonta, ganin yanda hawaye ke sauka mata da gudu a saman ƙyaƙyƙyawar fuskar ta ya sasu miƙewa. Hannunta Yaseerah ta kamo ta zaunar a kujerar kusa da ita, itama takai zaune tana riƙe hannunta alamar lallashi. Shima zama yay mijin Yaseerah ɗin, wani irin tausayin Huznah na ratsa shi. Tabbas yasan ta ɗaukarma kanta abinda yafi ƙarfinta, amma ko ya cigaba da gaya mata gaskiya yasan ba lallai ta fahimcesa ba. Gyaran murya yay a hankali, hakan ya sasu ɗagowa su duka suka kallesa..        “In sha ALLAHU zan taimakeki. Sai dai ki sani wlhy Uncle AA nada wahalar sha'ani. Amma akwai mafita ɗaya da nake miki hasashen idan kin gwada maybe ki dace....”     Jikin Huznah har rawa yake ta ce, “Wace irin mafita ce. Komai wahalarta ALLAH zan gwada, komai ƙalubalenta kuma zan jure”.     Kansa ya jinjina mata, sai kuma ya sauke numfashi. “Batun yanzu ba nasan Grandma suna fama da Uncle AA yay aure. Kuma a yanzu haka ma suna gab da masa auren ne amma bani da tabbacin sun sama masa matar ko basu sama masa ba, duk da dai akwai wata sister ɗin mu dake sonsa matuƙa kuma naga duk dangi nason a gaɗasu aure, shine dai bai maida hankali ba. To ina ganin mafita ɗaya ce na baki number ɗin grandma, ko kuma ki shirya na kaiku ke da Yaseerah kamar zaku gaisheta sai muce ai ke budurwar Uncle AA ɗin ce. Idan ALLAH ya taimaka aka dace sai kiga ya amsheki dole bisa umarninsu. Hakan yayi miki?”.        Cike da zumuɗi ta amsa masa, tana share hawayenta ga dariya. Shima murmushi yayi hakama Yaseerah. Ya ce, “Sai ki zama cikin shiri dan sai nan da kwana uku”.     “Miyasa ba yau ba?”. Ta faɗa cikin damuwa.    “Bata nan ne shiyyasa, amma ina saran dawowarta gobe ko jibi in sha ALLAHU”.        Ajiyar zuciya Huznah ta sauke. Badan taso hakan ba tace ALLAH ya kaimu. Dai-dai nan kira ya shigo wayarta. Koda ta duba sai taci karo da Yaya Yazeed. Mamaki ta kamata, dan hakan kan jima bai faru ba ganin kiran yayan nasu. Haka dai ta daure ta ɗaga dan tasan in har wayar ta tsinke bata ɗaya ba sai taci ubanta a hannunsa. Ko amsa sallamarta baiyi ba cikin kaushin murya ya ce, “Kina ina nazo gidan Shahidah baƙya nan?”.      Rawa jikinta ya fara, cikin karkarwar harshe tace, “Yaya wlhy bawani wajefa naje ba ina gidan Yaseerah ne nazo gaisheta”.        “Na baki mintuna ashirin kawai ki dawo gida. Idan ba haka ba hummmm!”. Ya yanke kiran. Kanta tai wani irin dafewa dan takaici, batama san ta fara antayama Yazeed ɗin zagi ba Yaseerah na tayata. Babu dai yanda zatai dole ta kimtsa mijin Yaseerah ɗin ya ɗauketa domin maidata da kansa. Dan hakan kawai zatai ta kuɓuta daga bala'in Yaya Yazeed. Dabarar tata kuwa ta taimaketa, dan ganin Abdul-hakeem ɗin ya sassauta tanadin da Yazeed ɗin yay mata. Sai dai duk da haka taci zagi da faɗa akan fitar sassafe babu kuma sanarwa. Ya kuma ja mata dogon gargaɗi akan in har ta kara fita a gidan wlhy sai ya mata dukan mutuwa.         Yana tafiya ta koma ɗaki tai kiran uwarta ta gaya mata tana kuka. Zage-zage itama Hajiya Basariyyar ta dinga yi da tsinar Yazeed ɗin. Sai da sukai san ransu ta koma lallashin Huznah da kwantar mata da hankali akan zatama Yazeed ɗin magana da kanta. Daga haka sukai sallama. Bata ko ƙara fita a ɗakin ba duk ɓuruntun da su Shahidahn keyi akan shirin tarbar baƙi su Oum. Sai ma nacin son samun AA take a waya amma hakan ya gagara. Da alama ma yayi blocking ɗin ta ne ita bata gane ba. Ai ko saita zauna tanata kuka. Sai da tayi mai isarta barci yay awon gaba da ita.....    ___________★         Ƙarfe huɗu da kusan rabi danƙareriyar motar Fawzan ta iso gidan. Yana gama parking Barrah da Haneeff suka fice zuwa cikin gida aguje suna ƙwala kiran mamansu. Dariya Fawzan ya dingayi, dan shi ALLAH ya ɗaura masa son yara matuƙa. Kodan har yanzu ALLAH bai bashi bane. Dan matarsa bata taɓa ko ɓatan wata ba shekara shida kenan. Oum ma dariya take ma yaran. Maanal dai komai batace ba, sai ma jagorantar su Oum tayi zuwa cikin gidan. Sun sami Shahidah na ƙoƙarin fitowa tarbar su Oum, dan haka sukaci karo a ƙofa. Cike da wani irin farin ciki Shahidah da Oum suka rungume juna. Sai kawai Shahidahn ta saki kuka. Harga ALLAH tana matuƙar son Oum, dan mace ce ƴar halak da bazasu taɓa mantawaba a tarihinsu. Ta matuƙar taka rawar gani a garesu da Ammien su ta yanda baki yayi kaɗan ya bada labari. Itama Oum ɗin hawaye take da murmushi duk a lokaci ɗaya, ta ɗago Shahidah tana mai share mata hawaye. “Uhm-uhm kefa yanzu kin girma Sheedan Oum, ke uwa ce babbar yaya kuma”.     Dariya Shahidah ta shigayi, hakama Fawzan dan tuno wani abu daya shuɗe. Maanal ma dai murmushi ne mai faɗi akan fuskarta. Abinda a yanzu yake da matuƙar tsada da wahala a gareta. Sai da Shahidah ta saki Oum sannan ta lura da Fawzan, cike da mamaki ta riƙe haɓa da faɗin, “Oh ni ALLAH wanake gani haka ya zama dattijo?”.        “A'a tsoho na zama ba dattijo ba”. Fawzan ya bata amsa yana hararta. Dariya duk suka sanya masa. Shahidah ta ce, “ALLAH kuwa ka yarda ka zama dattijo yanzu Yaya Fawzan”.     “Kema kin zama dattijuwar ai”.   Ya faɗa dai-dai suna kaiwa zaune a ƙayataccen falon nata. Dai-dai nan mijinta ya fito. Cike da mamaki idonsa akan Fawzan ya ce, “Kai kai wanake gani haka kamar Darma a gidana”.         “Ya arrahaman Busam!”.    Shima Fawzan ya ambaci sunansa yana miƙewa. A tare suka cafke alamar lallai sun san junan kuwa sani bana wasaba. Ai sai su Oum suka koma ƴan kallo. Sai da ƙyar Shahidah ta iya faɗin, “Nifa ban gane ba, wai dama kun san juna ne?”.       “Farin sani ma kuwa. Darma tare mukai degree master namu ai a Germany, sannan a yanzu haka akwai alaƙar aiki a tskaninmu. Kawai dai baya son zumuncine shiyyasa baki taɓa ganinsa a gidan nan ba.....”      “Wulaƙanci ai kai zumuncin kake so?”.     “Nadai fika tunda ni naje gidanka har sau biyu”. Cewar Abban su Barrah. Dariya Fawzan yay da faɗin, “Gori kenan. To yanzu ai gashi ALLAH ya kawoni, ashema ni ƙanwata kake aure kai wannan abin kunya da yawa yake”.      “Ato kaima dai ka faɗa”. Cike da girmamawa Abban Barrah ya gaida Oum. Itama ta amsa masa da kulawa cike da farin ciki. Nan fa aka ɓalle taɗi tsakanin Oum da Shahidah, Fawzan da Abban Barrah. Yayinda Linda tuni ta cika musu gabansu da kayan ciye-ciye Maanal na tayata. Duk wannan bidiri da ake Huznah na ɗaki tana shaƙar barci abinta. Sai da Maanal ta taje ɗakin ajiye kaya ta ganta baje a gado. Komai bataceba ta ajiye ta dawo wajen su Oum. Sai ga RK da dama yay musu alkawarin samunsu a gidan. Nan fa hirar ta ƙara armashi dan tuni Abban Barrah ya janyesu sun koma falon baƙi dan Oum ta sake itama suyi tasu hirar. Hakan yama Oum ɗin daɗi sosai, dan ta samu tattauna abubuwa da yawa da Shahidah wanda Maanal ta kasa sanar mata komai saboda zurfin ciki da miskilanci. Sai da akai magriba sun dawo Huznah ta fito. A ɗan yatsine ta gaishe su, sai dai saukar idanunta akan Fawzan yaso birkita mata lissafi. Sai da ta nutsu ta fahimci ashe ba AA ɗinta bane kammanni ne kawai. Dan suna kama sosai da AA ɗin, sai dai wasu abubuwa da suka ɗan babbanta su. Hakama kuma suna kamanni da Oum matuƙa. Hankalin Huznah ne ya tashi, dan haka kawai take ji a ranta wannan mutumin na kama da AA ɗin ta hakama matar, sai dai yanda ta gaishesu yasa daga amsa gaisuwar kowa ya watsar da ita musamman RK da kamar basu ƙaunar juna ita da shi.       Su Oum na gidan nan har tara, dan har sai da Autan ta ya kirata yana damunta shi dai ta dawo ya koma gida tun ɗazun duk basa nan gida babu daɗi kuma yana jin yunwa. Dariya Oum take masa da tsokanarsa akan wannan hali nasa na ɗafa, ya girma amma bai san ya girma ba koda yaushe yana laƙafe da ita. Idan tai masa aure yaya kenan. Shi dai roƙonta ya cigaba da yi akan su taho kawai. Tace shi bazai zo ya samesu anan ba yace ya gaji. Ƙyalesa tai tace gasu nan tahowa. Amma wayar Maanal fa ba'a gyara bane?. Sai cemata yay eh wai mai gyaran yace sai Monday ma.        “ALLAH ya kaimu” ta bashi amsa tare da sanar masa gasu nan dawowa. Sosai Shahidah ta haɗama Oum shata ta arziƙi, duk da tasan tafi ƙarfin duk abinda ta batan. Saboda suma su Maanal haka Oum ɗin ta haɗo musu abubuwa iri-iri na tsaraba. Da suka fito kuma sai da suka shiga super market ma aka ƙara wasu sayayyar. Huznah dai duk jikinta yayi sanyi da ganin waɗan nan ƴan gayun mutane gogaggu wayyayun ƴan boko da hutu da jin dadi ya gama ratsawa. Sai kuma gefe ɗaya na zuciyarta ya kasa samun nitsuwa akan kamannin Fawzan da AA ɗinta da kuma Oum. Jiki a sanyaye ta biyo su Maanal rakkiyar su Oum har mota. Maanal na manne da Oum ɗin sai shagwaɓa take mata cikin maganar nan tata ƙasa-ƙasa dake sake narkar da RK tana baƙanta ran Huznah da ganin tsantsar iskanci ne kawai da bariki kesa Maanal ɗin maida muryarta haka. Gefe kuma Fwazan na tsokanarta wai sun saka musu Oum ɗin su tsakkiya da shagwaɓar tsiya, ita tayi Auta yayi.      Dariya kawai Oum tayi da faɗin, “Babu ruwanka barni da kayana, suyi abinsu san ransu ko Auta?”.     Cike da jin kunaya Maanal ta ɓoye fuskarta a jikin Shahidah. Dariya suka sanya mata. Daga haka sukai sallama Oum na sanar mata wayarta zata taso mata ƙeyar AA ya kawo mata idan an gyara. Kai kawai ta iya ɗagama Oum tana ɗan murmushi, amma a ranta tasan bamai yiwuwa bane ya kawo da kansan. Shima kansa Fawzan murmushi yayi yaja mota suka fice. Sai RK dake tsaye jikin tasa. Ciki su Shahidah suka koma da yaran aka bar Maanal a wajensa zasuyi sallama, kamar zata sharesa. Sai dai ganin yanda Huznah ke wani binsu da kallon ƙwaf ya sata nufarsa....        “Humm dama haka kika iya shagwaɓa my queen?”.    RK ya faɗa yana binta da kallo ƙasa-ƙasa. Murmushi kawai tai masa mai sanyi kanta a ƙasa. Batare da tace komai ba. Shima sai ya saki murmushin da sake maida hannunsa ya harɗe a ƙirjinsa. “Koda yake ma ni fushi fa nake dake”.       Ɗan ɗagowa tai ta kallesa da faɗin, “Akan mi?”.    “Humm akan komai ma. Yanzu ace akwai alaƙa mai ƙarfi irin haka a tsakaninki da AA amma ban taɓa sani ba Maanal, ko'a fuska baki nuna min ba shima haka kuka wani rufeni a duhu. Zaman amana kenan?”.     Sosai gaban Maanal ya faɗi, ta zuba masa ido, ganin shima ya zuba mata nasa idanun tai saurin janye natan zuciyarta na duka. A ranta kuwa tunani take wace alaƙar a ciki yake magana kenan? Badai yaji komai ba? Badai yasan komai ba? Shi AA ɗin ne ya sanar masa kenan kamar yanda yace zai yi ko kuwa? Dan tanada yaƙinin Oum bazata faɗa masa ba duk da kasancewarsa jininta ƙani uwa ɗaya uba ɗaya. Cikin wani irin sanyi ta ce, “Mi kaji a kaina?”..........✍️ 😨😨😨😨😨🚶‍♀️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖4️⃣0️⃣ ______________ .......Da mamaki ya ce, “Abubuwa da yawan gaske”.    Harbawa zuciyarta ta sake yi, ta ce, “Wanne da wanne?”.       Sai da yay wani ɗan murmushi da gyara tsaiwarsa ya bata amsa da, “Ai bazasu ƙididdigu ba. Ashe ke ƴar gaban goshin Aunty Babba ce”.      “Bazaka faɗa min alaƙar da kaji ba kenan? Bayan kuma kai ne ka ɗakko maganar”.     “Miyasa kika damu da sai kin ji? Ko akwai wani abu da kike tsoron kada ace naji ne?”.         Harararsa ta ɗan yi, cikin rashin sakewarta da miskilanci ta ce, “Nikam mizan so ace kar kaji? Kawai dai naga ka ɗakko maganar ne da zurfi”.     Ƙaramar dariya yayi da faɗin, “My queen rikici. To kwantar da hankalinki banji komai ba bayan wanda kika san naji a gabanki. Amma dai zan koma Aunty ta bani labarin ƙuruciyarki kaf, idan ma da hotuna duk a haɗa min nasha kallo.”       “Kaji da shi dai”.    Ta faɗa tana ɗan yin murmushin da yake matuƙar son gani akan fuskarta. Sai dai bata yi masa sai idan taso. Sai da ya wani ɗan lumshe idanu da buɗewa sannan a kanta, ya ce, “Miya samu wayar taki ne wai? Inata kira ba'a ɗagaba daga baya kuma naji switch off. Na tambayeki ɗazun baki ce komai ba yanzu kuma naji Aunty na faɗin AA zai kawo idan an gyara”.        “Uhm faɗuwa tayi ne a jiyan lokacin da kake kira. Shine Oum ta bashi ya gyaro”.      “Ayya ALLAH ya kiyaye to, da gyaran nan ai da wata aka saya kawai. Ga wannan ki riƙe kafin asan abinyi dan zama ba waya babu daɗi”. Yay maganar yana miƙo mata iPhone 15 ɗinsa. Kanta ta girgiza tana kallon wayar, sai kuma ta ɗan kallesa. “Kabar wayar ka ai yace zuwa gobe za'a kammala gyaran”.       “Ni kuma gashi bazan iya cigaba da haƙurin rashin jinki ba. Please kar muyi jayayya”.      Komai bata sake cewa da shi ba ta amsa wayar. Daga haka tace masa sai da safe. Tsareta kawai yay da idanunsa bai amsa ba. Ta ɗan ƙibta masa nata, alamar yaya dai? Sai ya saki murmushi da ɗan ɗage mata gira shima. Harara kawai ta sakar masa da juyawa tana faɗin, “ALLAH ya kaika gida lafiya”. Tai gaba abinta. Har ta shige ciki yana binta da kallo. Sai da ta ɓace masa ya sauke ajiyar zuciya yana wani lumshe idanu ya buɗe. Sai kawai ganin Huznah yay a gabansa. Tsaf ya shanye murmushin dake saman fuskarsa kamar bashi ba. Yay kicin-kicin da fuska batare daya nuna yasan da ita ba ya buɗe motarsa zai shiga amma sai ta riƙe murfin caraf.        A ɗan fusace ya ce, “Lafiya?”. Dan shi tun randa ya fara ganin Huznah sam bata masa ba. Fuska ta ɗan marairaice kamar ba ita ba ta ce, “Kayi haƙuri dan ALLAH ina da tambaya ne”.      Kamar bazai tanka mata ba sai dai ya daure ya ce, “Tami?”.       “Wanda naji kana kira da Uncle Fawzan, da wannan matar. Dan ALLAH suma ƴan family ɗin Darma ne?”.      Wani kallon sama da ƙas ya mata a wulaƙance ya ce, “Kina da bussines da sune ko Darma Family ɗin?”.        Murmushi ta saki mai sanyi da ɗan duƙar da kai kamar mai jin kunya. Sai kuma ta ce, “Kusan hakan, ni ce wadda AA Darma zai aura”.          Gaba ɗaya RK ya wani wantsalo mata idanu waje da mamaki ya ce, “What AA fa?”.        “Yes”.     Ta bashi amsa cike da jin alfahari da kwarin gwiwa. Sai ya rasama abin faɗa dan aljabi. Shi dai yasan idan bai faɗama wani halin AA ba wani bazai kuwa bashi labari ba. To amma masu iya magana kance baka shaidar mutum akan mace. Sai dai sanin da yayma AA kai da kamar wahala. Mutumin da aketa fama da shi tsayin shekaru yay aure yaƙi. Tabbas Huznah mace ce ƙyaƙyƙyawa da duk inda kake son mace mai ƙyale-ƙyale za'a nunata. Amma miya ja AA nan wajen da babu kamun kai babu aji da akasan cikakkiyar mace data amsa mace da shi. Kai shifa zai iya rantsuwa yanda Maanal ke jansa a ƙasane ke ƙara masa soyayyarta. Dan yana son mace mai suna mace data san kimarta. Rasa abin faɗa ya sashi cewa, “Sai da safe nikam zan wuce”.      “A'a yayana ai baka gama amsa min tambayata ba Please”.     Sake juyowa yay daga haka kansa yunƙurin shiga mota da yake ya kalleta da mamaki, wai yau shi take kura Yaya, bayan duk ganinta da yake a gidan kusan kwana nawa baya jin tama taɓa ko gaidashi. Amma sai ya shanye mamakinsa ya furta, “Mi kike son ji kuma?”.       “Alaƙar matar nan da suka zo da Fawzan ɗin da kuma AA?”.      “Wannan ai shi AA ɗin ya kamata ki tambaya nake ga ko? Ko kuma su masu nan gidan tunda naga suma suna da alaƙa da su mai ƙarfi ma kuwa”.     Sosai gaban Huznah ya faɗi da jin kalaman RK. Sai dai kafin ta samu damar sake furta komai ya shige motarsa yay mata key. A gabanta ya fice a gidan aka maida gate da aka wangale aka zugesa. Rasama wane tunani Huznah zatai tayi, amma tai ƙoƙarin hana kanta kiran mahaifiyarta har sai ta bincika ainahin gaskiya sannan dai. Da wannan tunanin ta koma ciki itama...... ___________★        Washe gari lahadi Maanal ta tashi da burin fita gyaran jiki. Sai ga Yazeed yazo gidan. Jin inda take shirin zuwa yace tazo ya sauketa kawai. Haka badan taso ba suka wuce ita da Barrah da Huznah data maƙale akan zataje. Kasancewar Huznah a motar yasa Yazeed kama kansa. Dan shi fa agaban Maanal ne kawai dama zakaji muryarsa ko sauƙin kansa. Amma ƙannesa da sauran mutane shi mai matuƙar kamun kai ne da tsare gida. Ya dai tambayeta wayarta da yake kira baya samu ta sanar masa accident ɗin data samu, yayi addu'ar ALLAH ya kiyaye gaba daga haka ya kaisu wajen gyaran jikin. Yau ma kamar waccan ranar atm ɗinsa ya bata, ya kuma ce idan sun kammala ta kiranshi. Bataƙi amsa ba tai godiya kawai kodan idon Huznah ƴar saka ido.      Haka suka shiga wajen gyaran jikin. Sun sami mutane ba masu yawa ba, kasancewar sun fito da wuri sannan mai wajen ƙawar Shahidah ce. Ana tsaka da musu gyaran ita Maanal ana wanke mata kai, Huznah kuma wankin ƙafa da gyaran farce wata ƙyaƙyƙyawar mata ko budurwa za'a kirata ko bazawra ne ma oho ta shigo wajen ita da ƙawarta. A fuska dai kam akwai ruwan ƙyau, sai dai a jiki haka take slim babu gaba babu baya. Duk rashin jiki irin na Maanal sai ta ganta da ƙyan fasali akan matar. Dan Maanal rashin jikin ne dai kawai bata da, amma tanada cikar halittar jiki gwargwado duk da suma bawani na manyan mataba can. Amma dai duk inda mace zata kira kanta mace kam itama zata buɗe baki.       Yanda yarinyar ke yamutse-yamuste da shan ƙamshi ne yaja hankalin mafi yawan mutanen dake a wajen kanta. Tuni wasu suka ɗan fara mata magana tana amsawa da gyar, banda Maanal da ko kallon inda take batai ba. Ana gama ma wanke mata kai ta ɗauka novel ɗinta ta cigaba da karatu, yayinda Barrah da akema kitso ke gefenta tana game da wayar wajen RK. Ashe yarinyar nan hankalinta nakan Maanal data watsar da ƙurarsu. Sai hakan yay mata zafi ta shiga habaici da yaɓa magana ƙawarta na tayata da mata kirari da dariyar iskanci. A hakan ma Maanal bata ma nuna tasan bayan ita da wasu ma a shagon ba.        Cikin masu aikin wajen ce ta ce, “Oh ni, yau dai da alama da fitina kika fito gida Nurry, irin wannan takale-takale shin na miye? Dawa kike anan?”.        Sai da ta watsawa mai aikin harara sannan ta tauna chewing gum ɗin bakinta ya bada wani ƙas-ƙas ta ce, “Da ƙananun karuwan Abuja mana. Masu baro gidan ubale suzo nan su kama hotel suna girman kai da ɗaukar kansu wata tsiya. Ƴan iska ɗaya bayan ɗaya sai mun saitasu gidan iyayensu da ake cin masara sun bar mana garin mu shegu ƴaƴan talakawa”.        Dariya ƙawarta ta ƙyal-ƙyale da shi tana zuba mata wani kirari. “Sai dake tawajena, sa gabanki inda kike so. Kuɗi ya haifeki, cikinsu kika girma gidan su zaki zama matar aure. Kaga amarya a gidan tauraron matasan ƙasar nan kaf mai kiran kuɗi koda kwance suzo su masa bargo a gado. Yi yanda kike so kune Abuja dama ƙasar gaba ɗaya ai ko anƙi ko an so dai da ku”.       Wani yyyuuuuu Nurry ɗin tai da idanunta manya dake a juye kamar ƴar shaye-shaye. Cike da jin alfaharin Kirarin ƙawar tata ta wani watsama Maanal kallon banza. Hakan datai ya saka kowa fahimtar da Maanal ɗin take. Wani shegen murmushi Huznah ta saki na jin daɗi, sai kawai ta dubi Nurry ɗin fuska da murmushi ta ce, “Hy Mss”.      Da farko Nurry kallonta tai zata watsar, sai kuma dai taga itama Huznah ɗin ba daga baya ba. Jiki da suttura duk sun nuna ƴar wani ce. A ɗan yangance ta amsa da “Hy” itama tana watsama Huznah yatsu biyu. Tsam Huznah ta miƙe kasancewar an gama mata ta koma kusa da Nurry ɗin. Sai lokacin Maanal ta ɗan kallesu, kanta ta ɗan girgiza kawai ta miƙe tabar musu wajen ma gaba ɗaya ta koma sashen ƙunshi dan tana son a mata ɗan jan lalli a yatsunta da ɗan baƙi kaɗan a hannun kawai.        Ai hakan kamar yama Huznah daɗi ne. Tuni ta baje a tsakkiyar su Nurry aka ɗora hira harda musayar numbers. Haka dai akai musu gyaran jikin nan har bayan la'asar sannan suka fito domin komawa gida. Kasancewar Maanal bata kira Yazeed ba duk da yace ta kirashin sai ta tare taxi dan su tafi, sai kawai Huznah catai suje ita su Nurry zasu sauketa. Dan kusan tare suka fito da su Maanal ɗin suma. Ko ci kanki Maanal batace mata ba suka shige taxi ita da Barrah suka wuce abinsu. Ita kuma ta shiga jibgegiyar motar Nurry da take driving da kanta suka tafi..... _________★        Safiyar litinin safiya ce da duk wani ma'aikaci jininsa ke akan farcensa. Kamar dai anan gidan su Shahidah. Ita da yara da mijinta da Maanal duk sunyi shirin tafiya aiki. Kamar yanda suka saba tsaf dasu cikin kwalliya ta birgewa da tsarin addini. Huznah nacan ana shan barci dan jiya bata dawo gidan ba daga bin su Nurry sai bayan isha'i, haka kuma ta kusa raba dare tana charting dan groups su Nurryn suka sakata na WhatsApp kala-kala. Tana yi tana neman mutumin nata sai dai har yanzu bai cireta a black list ɗin daya Saka ta ba da alama. Haka ta haƙura tunda ta ɗau ɗamarar komawa office ɗinsa a yau litinin kawai.        Mai kai yara makaranta ya kwashesu Barrah. Abbansu ya wuce. Itama sai suka tafi da Shahidah. Har ƙofar gate ɗinsu ta kaita. Ta fito tana murmushi saboda maganar da Shahidahn tai mata dai-dai da isowar motar AA. Kamar ance ta kalla wajen sai ko idanunta a kansa. Yana zaune a bayan motar cikin ƙasaita da cikar kamala, kayansa dai na kullum ne suit a fagen aiki, sai dai na yau milk color ne, idan ka cire long sleeve shirt ɗin ciki data kasance coffee. Gajiyayyun idanunsa na cikin fari tas ɗin gilashinsa na ko yaushe dake ƙara cikar kamala da ƙyawun da ALLAH yay masa mai sanyi. Sumar nan da sajensa sun sha gyara luf-luf da su. A zahiri idanunsa a rissine yake da alama akwai abinda yake dubawa, sai dai kuma a kaikaice idanunsa akan Maanal suke. Amma bazaka taɓa fahimtar hakan ba akai mai kallonsa daga nesa ko kusa. Dan kallone irin na basarwa da iya taku. Kasancewar an sauke gilashin kaɗan tuni ƙamshin turarensa ya iso har inda su Maanal suke. Sai dai itama fa daga kallo ɗayan datai masa ta janye idanunta bata sake gigin kallon koda sashen da motar take ba. Sallama sukai da Shahidah da sam hankalinta bai kai ga AA ɗin ba ita. Ita kuma ta fara takawa a hankali cikin takunta na nutsuwa zuwa cikin Companyn........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖4️⃣1️⃣ ______________ *TALK WITH SIDDEEQAH* Operation Ciniki Dole 08149588205 Ni Olayyah na shiga uku na kwashe kudi na saro kaya domin in fara kasuwanci online, na gaji da zaman sai Yallaɓai ya bani kudin kashewa, kullum ni ce koma baya cikin danginsu, dukda yana kokarin sa, amma dai gwara in nemi na kaina kodan yan uwa da iyaye. Amma bari in kira Besty nah Huriyyah nasan zata samu maganin wannan damuwar tawa. Tunda na kira Huriyya na faɗa mata abunda ke hanani Bacci ta faɗa mun wani sirri da ya girgizani. Wato ashe itama da ta fara business online kuma bata ciniki amms tunda aka bata number din Coach Saddiqah komai ya fara tafiya daidai a kasuwancin ta ( Talk with Saddeeqah). Tunda ta shiga OPERATION CINIKI DOLE ONLINE BOOTHCAMP komai ya warware mata ciniki babu kama hannun yaro. https://wa.link/8al2f0 Ai ba shiri na nemi Coach Saddiqatu nima domin in shiga tsarinta na Saddeeqah Biz Growth Academy. Kuma Alhamdullilah ina shiga nafara ganin canji a business dina, har ma sabon online business na buɗe daga cikin abunda na koya a Operation Ciniki Dole Online Boothcamp. https://wa.link/8al2f0 Gaskiya wanda ya koya a wurin ƙwararriya ya huta domin ko dubu 100,000 akace in biya in shiga OPERATION CINIKI DOLE ONLINE zan biya domin amfanin da na samu cikin Boothcamp bazan iya faɗaba, gashi yanzu na samu na sayi machine din delivery na maida daki guda shago cikin gida na. Hurayyah ta taimaka da ta haɗa ni da Coach Saddiqah. OPERATION CINIKI DOLE ONLINE ya bani damar yin ciniki yadda ya kamata ba tare da wana damuwa ba. Indai kina business ko kina son ki fara Operation Ciniki Dole Online Boothcamp shine ajin farko da Coach Saddiqah zata rike hannun ki ta nuna miki duk wani sirri da dabaru na kasuwancin online. Daga rashin ciniki zaki koma sold out domin kuwa zaki dinga yin 6 figures monthly, in kin shiga OPERATION CINIKI DOLE ONLINE BOOTHCAMP baki ga sauyi mai kyau a business dinki ba za'a maida miki kudinki bayan 90days. Da Naira Dubu Goma kacal Pre-lunching Price zaki samu damar shiga OCD.( Kina biya zaki fara kwasar ilimi) Zakuma ki iya jira sai 20th January ki biya Naira Dubu Ashirin. ______________ .......Sanye take da doguwar riga ta atamfa da ɗinkin yay ƙyau sosai, tayi ɗaurin zara Buhari da yay matuƙar zauna mata kamar ta ɗauka ta ɗora a kanne ba hannu ya naɗa ba. Kasancewar kalar atamfar blue ne da fari ta ɗaura farin gyale ba wani ƙato ba sosai tun daga saman kanta sai ta baɗesa a kafaɗunta duka amma ya rufe mata ƙirji duka. Ta baya kuma rigar bata matseta ba shiyyasa sam babu ta inda jikinta ke nuna da wani zai ce ta fidda tsiraici. Kamar ko yaushe tana maƙale da sirrin farin gilashinta da ke ƙawata fuskarta da kwarjini na musamman. Yayinda sam fuskar babu alamar wasa da wani zai kawo mata wargi dan tsuke take tamau, ba wata kwalliya tayi ba a fuskar mai yawa, amma tayi ƙyau sosai. Ƙamshinta mai sanyi da saka zuciya nutsuwa. Yanda take takunta a nutse sai ka ɗauka yanga ce da tsatsar iyayi. Amma halitartace hakan sam bata da garaje ko gaggawa. Duk wanda ta haɗu da shi mace ko namiji takan gaisheshi batare da ko kallonka tayi ba ta wuce abinta. Idan kuma kai ne ka fara ambata sunanta ga ƴan wanda suka santa takan kallekan ta ɗan ɗaga maka hannu.      Isowarta ga ƙofar shiga dai-dai da tunkarowar AA shima assistant ɗinsa biye da shi da tarkacensa a hannunsa. Yayinda shi kuma waya manne a kunnensa yana magana cikin nutsuwar nan tasa kamar baya son magana.. dan ko assistant ɗin nasa bazaice ga abinda yake faɗa ba kai tsaye a wayar. Amma da yake da aka kira wayar tana a hannunsa shine ya ta miƙa masa yaga ansaka My D, Wato mahaifinsa. Yanda yake taku dake sake tabbatarwa shi ɗin tsayayyen namiji ne ingarman gaske. Mai lafiya da ji da ƙarfin ƙuruciya dana motsa jiki ya isa abin kallo ga masu kallon nasa. Balle azo ɓangaren iya ado da tsara shi. AA yasan sirrin gayu da ƙamshi, dan yana cikin manyan Handsome da duniya bazata taɓa takokin manna hotonsa ako ina ba ta faɗa da tabbatarwa. Yanda kowanne ma'aikaci sai ya ɗaura I'd card ɗinsa na aiki ƙofa ke bashi damar shigewa haka shima oga da kansa. Dan haka koda suka iso sai assistant nashi ya ɗora nasa id ɗin shi, dai-dai da itama Maanal data tsaya ciro nata a bag ɗinta ta ɗaura. Hannunta ɗaya riƙe da lunch box ɗinta, ɗayan kuma bag ɗin na'a kafaɗarta maƙale, dan mai irin kamar school bag ɗin nan ce amma ta gayu kuma ƙarama. Ɗan zubama lunch box ɗin idanunsa yayi sai kuma ya janye tare da shigewa yana magana a hankali da sai da ya ɗan gittata taji muryarsa acan ƙasan maƙoshi yana faɗin, “Yes Aba I hear you”.        Da kallo ta ɗan bisa sai kuma ta taɓe baki kaɗan tana yamutsa fuskar da ƙarasawa reception ta saka hannu kamar yanda dokar companyn take. Anan ne suka haɗu da Yaqub. Murmushi ya sakar mata da faɗin, “Good morning sister Maanal”. Kallonsa ta ɗan yi sai itama ta saki masa ɗan murmushi mai tsayawa iya motsin fuskar nan. Nutsuwar Yaqub ɗin da rashin hayaniya yasa take ganin mutuncinsa. Cikin ƴar siririyar muryarta ta ce, “Good morning ɗan uwa. Ya weekend?”.       “Alhamdullahi mun shata kam mun more”.     Malalacin Murmushin ta ɗan sake yi kawai. Batare da ta sake cemasa komai ba ta wuce. Binta yay suka jera. Duk da bawata magana suke ba sai da aka dinga binsu da kallo. Koda suka iso nasu ma office ɗin su Zaharadeen duk zuba musu ido sukai. Kallo ɗaya tai musu ta kauda kanta da faɗin, “Good morning”. A jimlace. Wasu sun amsa wasu kuma na binta da kallon dai. Ita kuma ta sake yin kicin-kicin da fuska ta gyara kujerarta bayan ta kakkaɓe ta zauna. Sai kuma ta warware tissue da ta ajiye a wajen ta fara goge abubuwanta duk da komai a tsaftace yake ƙal. Amma ita ƙa'idarta ne in har zata fara aiki saita sake goge komai nata har keyboard kafin ta fara. Batafi zaman mintuna arba'in ba ta samu kira daga office ɗin Design Director. Miƙewa tai kawai sai wayarta a hannu ta wuce. Su Zaharadeen suka bita da kallo cike da gulma. Sai dai ita bama tasan sunayi ba.         Cikin girmamawa da mutuntawa ta gaishe da Director Mustapha. Ya amsa mata da kulawa da binta da wani munafukin kallo. Kujera ya nuna mata alamar ta zauna. Bata musa ba ta zauna ɗin.      “Yauwa Sister Maanal zamuje can Workshop dan kin san aiki yayi nisa. Akwai abinda ake buƙatarki a wajen domin tattaunawa, tun jiya ma Watchmakers da horologists ɗin sukaso ganin ki sai CEO yace sai yau”.      Kai kawai Maanal ta jinjina masa a girmamame. Shima sai bai sake cewa komai ba ya miƙe yana sake jinjina girman kai da miskilancin yarinyar a ransa. Dan da yawansu a Company haka sukema yanayin maanal ɗin fassara yaransu da manyansu. A tare da shi suka isa Workshop ɗin. Wajene da yaji kayan aiki harda na tashin hankali. Dan ingantattun matchings ne da ko'a masu jajayen kunnuwan sai companyn da yaci ya ƙoshi ke dasu. Ga komai a tsare kuma a tsaftace. Cikin girmamawa suka gaisa da kowa. Tanata kallon abubuwa wani a cikin horologists ɗin na mata bayani oga kwata-kwata ya iso. Kamar dai ko yaushe AS ɗinsa biye da shi. Gaisheshi suka shiga yi cikin girmamawa. Ya amsa musu da kulawa shima. Sai lokacin Maanal da bata ko kalla sashen da yake ba ta furta, “Good morning Sir”.        A taƙaice kuma ciki-ciki ya amsa da, “Morning”. Yana maida hankalinsa ga Director Mustapha. Gaba yay suka bisa a baya har zuwa inda ake buƙatar ganninsu. Batare da Maanal ta farga ba sai ta tsinceta a kusa da shi tsaye gefensa na dama. Matsawa taso yi sai dai babu dama dan gabanta glass ne. Dole ta haƙura mayataccen ƙamshinsa na addabar hancinta. Lokacin da aka ajiye samfarin agogon data zana da hannunta sai taji notukan kanta na ƙoƙarin kwancewa. Yau mafarkinta ya zama gaskiya. ALLAH mai girma. Da ƙyar ta iya haɗiye hawayen da suka cika mata ido ta saita kanta tana al'ajabin komai da yaba ƙoƙarin Watchmakers ɗin harma da horologists ɗin, duk da kafin yau ta taɓa ganin aikinta a zahirance. Kai da ganin agogon kasan bana siye da ƙananun kuɗi bane. Bayan wanda aka haɗa ɗin sai pieces da suma aka ajiye nan fa suka shiga tattaunawa. Ɗan abinda Maanal ɗin ta ƙara musu bayani kadan ne ma, sai dai ta sake ƙayatar da su da fahimtar lallai za'aje da yarinyar a cikin Companyn dan tanada brain sosai......... __________★       Anan kaduna kam ALLAH ne yayma matafiya dawowa. Wato Hajiya Yaya da maƙarabbanta. Su dai su Ammie basu san da dawowar tasu ba ma. Sai da suka dawo ɗin tana zaune a falo Sakina na mata kitso Waleed ya shigo yake gaya mata. Duk da taji mamaki sai batace komai ba tace yaran suje su gaisheta.       Shiru Waleed yayi alamar bai son zuwa. Sai tayi murmushi tana miƙewa. Kitchen ta nufa ta haɗo abinci a cikin basket ta bashi tace suje dashi su kai. Nan ɗin ma amsa sukai jikinsu duk a sanyaye suka fita. Basu wani jimaba ko sai gasu sun dawo Hameed harda hawaye fuskarsa zane da sayin mari. Sam Ammie bata tambayesu miya faru ba, koda Waleed ma zai faɗa sai ta girgiza masa kai da nuna masa hanyar kitchen alamar yaje ya kai mata kayan abincin da suka dawo dasu ba'a taɓa komai ba.       “Amma aunty ai ya kamata kiji miyya faru? Jibafa fuskar Hameed harda sahun mari”.     Murmushi Ammien ta saki kamar bazatace komai ba, sai zuwa can tace, “Sakina kenan, to minene amfanin jin? Sakawa kai ɓacin rai ne fa kawai. Koma minene ya faru ai ya rigada ya faru ɗin, sai a barsa ya wuce kawai”.          “Hummm Aunty wlhy yanayin rayuwarki na birgeni, a ɗan zaman nan na kwanaki a gidan nan na ƙara samun ilimin zaman duniya. Zuwa yanzu na ɗaura ɗammarar ko sakina Salihu yayi na sake wani auren nima zan sake wasu abubuwa daga tawa rayuwar”.       “ALLAH sarki ƙanwata ALLAH ya zaɓa mana abinda yafi alkairi to”.      “Amin ya rabbi aunty”.   ★★      A sashen Hajiya Yaya kuwa tunda suka kora su Hameed da abincin da suka kawo bayan Basira ta falle fuskar Waleed da mari sakamakon maida mata magana da yayi sai suka bude sabon shafin zagin Ammie da ƴaƴanta musamman ma Maanal da tafi kowa tsaya musu a rai. Sunyi mai isarsu kafin su saki zancen su koma kan Hajiya Basariyya da taje wai gaishesu da musu sannu da zuwa.        A gabanta dai an amsa, dan a cewar Hajiya Yayan idan ma da gara gara Hajiya Basariyya ɗin duk da kuwa itama a baya ansha gwagwarmaya, amma zuwan Ammie yasa take ɗan jin sassaucin Hajiya Basariyya a yanzu. Ita kanta Hajiya Basariyya ɗin tana fitowa daga sashen ta wani taɓe baki da jan tsaki. Tana isa sashenta suka baje kolin yi da su Hajiya Yayan ita da ƴaƴanta itama.     Wannan rayuwar daga Hajiya Yaya har Hajiya Basariyya sun ɗabi'antar da yaransu a kanta tun suna ƙanana. Shiyyasa yaran sam basa ganin girman matan uban nasu idan ka cire Yazeed da Amrah da halinsu ya fita daban a cikin ƴaƴan Hajiya Yaya. Ita kam Hajiya Basariyya ma ai bata da zakkar na kirki har yanzu, ko sai nan gaba yaran sun ƙarasa kaiwa hankalin girma oho. Dan manyan su Huznah ne kawai masu shekaru.... ____________           Zaman cikin Workshop ɗin ya jasu lokaci mai ɗan tazara, dan sai da akai kiran azhar suka sami fitowa. Kasancewar itace ta fara fitowa kanta tsaye ga elevator ta nufa. Sai dai tana zuwa zata danna domin buɗewa ta figowa ta buɗe kanta alamar wani zai fito. Haka kawai ta samu kanta da maida hankali ga wajen. Sai ko idanunta akan Huznah data fito cikin matuƙar kwalliya data sakata yin ƙyau ainun. Hannunta ɗauke da basket alamar kayan abinci ne a ciki. Kallon kallo suka tsaya yima juna. Dan itama Huznah na fitowa idanunta akan Maanal ɗin suka sauka. Sunyi ma juna kallon fin minti ɗaya kafin Maanal ɗin ta fara janyewa cike da miskilancinta. Batare da tace da Huznah ɗin komai ba kuma tai shigewarta elevator ɗin tabar Huznah ɗin sake da baki tana kallonta. Gefe kuma masu shigi da fici ne da suka fassara al'amarin da wani abu daban can. Domin tuni sun gumtsa gulma.        Har Maanal ta koma ga wajen zamanta mamakin Huznah na mata kaikawo, shin wajen wa take zuwa ne ai a companyn nan? Wannan shine gani na biyu datai mata. Sai dai a wancan ganin ma bata san wajen wa tazo ba tunda tana shigowa ne ita kuma tana fita. Kasancewar lokacin salla ne abubuwan hannunta kawai ta ajiye inda ya kamata ta fita dan mafi yawa duk an fice salla. Sai wanda ba musulmai ba da kuma masu fashin salla kawai. Sai masu wasa da ita kuma dakan fifita aikinsu sama da tashi yin sallar akan lokaci. Duk da dokar mai kamfanin ce idan lokacin salla yayi dole ka ajiye kaje kayo in har kana cikin masu yinta kafin ka cigaba da aikinka. Amma hakan baya hana wasu tauye lokacin...     ★★   Cike da takun yanga da yauƙi Huznah ta nufi office ɗin AA. Sai dai tana isowa office ɗin Assistant nashi da ke farko kafin nasa acan ƙurya sukaci karo shi ya fito. Fuskarsa sai raɓar ruwa take yana ƙoƙarin gyara hannun long sleeve shirt ɗinsa, ya cire ta cikin sai ƴar ta saman shirt ɗin kawai data kasance milk itama. Shi baima lura da ita ba sam kasancewar hankalinsa yayi wajen sallar sai da tace da shi, “Hy my boss”. Sannan. Duk da a hakan ma da farko baiko kalla inda take ba yay shirin wucewa dan bai kawo da shi ɗin ake ba. Sannan bai riƙe muryarta ba balle yasan ita ɗin ce tunda ya tabbatar ma'aikatansa babu wanda keda ido da kwallin masa wannan kiran tsagerancin. Yanda ya kama girmansa haka suke tsantsar girmamashi ako ina daga samansu har ƙasa.        Ɗan saurin shan gabansa da tayi ne ya sakashi kallonta a karo na farko, murmushi ta sakar masa da ɗaga masa yatsunta biyu cike da iyayi ta ce, “Please boss da kai fa n.....”✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖4️⃣2️⃣ ______________ *TALK WITH SIDDEEQAH* Operation Ciniki Dole 08149588205 Ni Olayyah na shiga uku na kwashe kudi na saro kaya domin in fara kasuwanci online, na gaji da zaman sai Yallaɓai ya bani kudin kashewa, kullum ni ce koma baya cikin danginsu, dukda yana kokarin sa, amma dai gwara in nemi na kaina kodan yan uwa da iyaye. Amma bari in kira Besty nah Huriyyah nasan zata samu maganin wannan damuwar tawa. Tunda na kira Huriyya na faɗa mata abunda ke hanani Bacci ta faɗa mun wani sirri da ya girgizani. Wato ashe itama da ta fara business online kuma bata ciniki amms tunda aka bata number din Coach Saddiqah komai ya fara tafiya daidai a kasuwancin ta ( Talk with Saddeeqah). Tunda ta shiga OPERATION CINIKI DOLE ONLINE BOOTHCAMP komai ya warware mata ciniki babu kama hannun yaro. https://wa.link/8al2f0 Ai ba shiri na nemi Coach Saddiqatu nima domin in shiga tsarinta na Saddeeqah Biz Growth Academy. Kuma Alhamdullilah ina shiga nafara ganin canji a business dina, har ma sabon online business na buɗe daga cikin abunda na koya a Operation Ciniki Dole Online Boothcamp. https://wa.link/8al2f0 Gaskiya wanda ya koya a wurin ƙwararriya ya huta domin ko dubu 100,000 akace in biya in shiga OPERATION CINIKI DOLE ONLINE zan biya domin amfanin da na samu cikin Boothcamp bazan iya faɗaba, gashi yanzu na samu na sayi machine din delivery na maida daki guda shago cikin gida na. Hurayyah ta taimaka da ta haɗa ni da Coach Saddiqah. OPERATION CINIKI DOLE ONLINE ya bani damar yin ciniki yadda ya kamata ba tare da wana damuwa ba. Indai kina business ko kina son ki fara Operation Ciniki Dole Online Boothcamp shine ajin farko da Coach Saddiqah zata rike hannun ki ta nuna miki duk wani sirri da dabaru na kasuwancin online. Daga rashin ciniki zaki koma sold out domin kuwa zaki dinga yin 6 figures monthly, in kin shiga OPERATION CINIKI DOLE ONLINE BOOTHCAMP baki ga sauyi mai kyau a business dinki ba za'a maida miki kudinki bayan 90days. Da Naira Dubu Goma kacal Pre-lunching Price zaki samu damar shiga OCD.( Kina biya zaki fara kwasar ilimi) Zakuma ki iya jira sai 20th January ki biya Naira Dubu Ashirin. ____________ ........Yanda ya wani kalar zuba mata mayatattun idanunsa masu kaifi da cikar kamala yasa zuciyarta girgizawa. A take harshenta ya fara rawa, sauran abin faɗar tata ya kama gabansa. Sai ta koma in ina da rawar lips. Komai baice mata ba ya raɓata ya wuce abinsa. Da ƙyar AS ɗinsa dake kallon komai ya iya danne dariyarsa. Dan shi kam dariya ma Huznah ke bashi. Da tasan manyan matan da suka sha gwagwarmaya da faɗi tashi akan boss ɗin nan nasa da bata wahal da kanta ba. Amma dai zai cigaba da bin series ɗin domin ganin inda zai kasance the end. Shine ya bata wajen zama sannan ya wuce massalaci shima a gurguje dan har an tada salla. Maimakon itama tayi hankalin cewa zataje tai sallar saita gyara zama a lallausar kujerar dake a office ɗin AS ɗin. Ta ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya suna charting da sabuwar ƙawarta Nurry dake bata shawarwarin yanda zatai da AA ɗin yau, dan tun jiya ta juye mata komai sai dai bata sanar mata wanene shi ba. Gefe kuma tana yi da Yaseerah itama dake ƙara ƙarfafata...      ★ Kamar yanda ta saba ana idar da salla ƙoƙarin komawa kan aikinta tayi, ba kamar sauran daketa tururuwar wucewa cin abinci ba. Cikin ɗan sauri Yaqub ya cimmata, jin mutum a kusa da ita ya sata kallon gefen nata. Sai ta ɗan sauke ajiyar zuciya ganin Yaqub ne. Gaishe shi tayi kamar yanda al'adarta take ba in har tai kowacce salla zata gaida na kusa da ita. Shima sai ya amsa da kulawa yana murmushi tare da tambayarta miyyasa bata son zuwa cin abinci. Murmushi kawai tayi kaɗan, kamar bazata amsashi ba ta dai buɗe baki da ƙyar dan ƴan miskilancin na kusa ta amsashi da, “Ina zuwa da nawa”.       Murmushi kawai shima yayi, daga haka suka cigaba da tafiya a jere. Sai dai bawata magana ma suke ta kirki ba, amma duk wanda ya kallesu sai ya sake kallo, harda masu ƴar gulma akan ɗan kusancin nasu daya fara bayyana kansa ga kowa musamman a kwanaki biyun nan.        Sunzo gab da shiga akai kiran wayar hannun Maanal. Tsayawa tai tana kallon mai kiran, RK ɗin ne ba wani ba, dan haka ta koma gefe tana amsawa. Shima Yaqub sai ya tsaya jiranta. Cikin takunsa na ƙasaita yazo ya gitta su, sai dai kamar ance Maanal ta kalla sashen da yake kawai ta hango wata shegen harara daya zuba mata. Baki ta ɗan murguɗa da kauda kanta gefe ta cigaba da wayarta, dan zuwa yanzu tana ɗan jin nutsuwar tarayyarta da RK ɗin, duk da bata buƙatarsa a matsayin da shi yake kallon kansa a gareta, bama shi ba kowanne namiji ita bata buƙata. Basu wani jima a wayar ba sukai sallama dan shima zai shiga theater yace. Ƙarasa shiga sukai ita da Yaqub, sai dai tana zama ta samu kira daga office ɗin AS ɗin CEO wai ana nemanta. Rasama abin faɗa tayi, amma sai ta miƙe tana rufe ɗan bowl ɗin data zubo snacks da zataci. Koda ta iso tayi mamakin ganin Huznah zaune har yanzu, sai dai bata nuna ba ko'a fuska ta isa ga AS ɗin. Phone ɗin gabansa ya daddana tare da kaiwa kunne alamar kira, an ɗan jima ba'a ɗaga masa ba, ana ɗagawar kuma cikin girmamawa kamar yana gabansa ya furta, “Sir gata tazo”. Ɗan shiru yay alamar saurare, sai kuma ya gyaɗa kai yana faɗin, “Okay sir”. Yana ajiye kan wayar ya dubeta fuskarsa da murmushi.       “Sister Maanal ki ƙarasa ciki”. Kanta kawai ta gyaɗa masa. Yayinda Huznah ta miƙe ranta a ɓace. “Wane kalar rainin wayo ne ina zaune ina jira kace wata ta shiga kuma?”.      Cikin girmamawa ya ce, “Am sorry Mss. Ita ɗin staff ɗinmu ce, ganinta nada banbanci da ke. Sannan kiyi haƙuri boss baya son hayaniya sam. Musamman a irin wannan lokacin.”         Hararar sa ta ɗan yi, yay mata murmushi da faɗin, “Kiyi haƙuri idan ya bada umarnin ki shiga kema zaki shiga”.      Tsaki kawai taja masa ta koma ta zauna. A ranta tana jin zata iya kwana a wajen har sai ta samu izinin shiga wajensa yau. Dan ta bakin Nurry sai ta buɗe masa wuta da gaske kafin ta samu kan guy ɗin nan. Zafin kansa yayi yawa da faɗin rai.....        Kan Maanal a ƙasa ta shiga office ɗin, yana zaune a rukunin kujerun office ɗin masu laushi da ƙyawun kallo. A one sitter yake zaune ƙafa ɗaya kan ɗaya, sai novel dake hannunsa, gefensa akan coffee table glass bowl ne cike da fruits nau'i daban-daban masu tsafta da ƙyawun kallo. Sai bottle na ruwa an zuba wani a kofin. Har ta ƙaraso kusa da shi amma akwai tazara a tsakaninsu bai nuna yasan da shigowar kowa ba. Yayinda ita kuma idonta ke akan bangon book ɗin hannunsan. Dan ta jima tana neman novel ɗin amma ta gagara samu, har kuɗi ta biya dan a kawo mata shi amma har yanzu shiru. Sai kuma gashi yau ta gani a hannun wannan mutumin.      Duk abinda take yana kallonta ta gefen ido, amma bazaka fahimci hakan ba sai ma karatunsa da yake yi hankali kwance. Yawu taɗan haɗiye tare da gyara tsaiwarta ta ce, “Good Afternoon sir. Gani, ance kana buƙatar gani na”.        Shiru bashi da alamar tanka masa balle motsawa, sai da yaja fin mintuna biyu sannan ya ɗan ɗago yana mai kai hannu ya gyara zaman gilashinsa da ƙyau, sai ta samu kanta da kai hannu itama ta gyara nata. Zuba mata idanunsa kawai yayi, dai-dai ya ɗago suka haɗa ido. Da sauri ta janye natan tana wani duƙar da kai na girmamawa. Shi kam kallonta yake kawai daga sama har ƙasa, har ta fara jin gundura da kallon amma batace komai ba.        Sai da ya gama kalleta son ransa sannan ya ɗauke idanunsa, cikin muryar nan tasa ƙasa-ƙasa ya furta, “I need a drink”.      Karon farko ta zuba masa ido kai tsaye itama, sai kuma ta kalla bottle water ɗin gefensa fuskarta na ƙara tsukewa. Kamar zatai magana sai kuma mita tuna ta bar wajen. Kai tsaye fright ɗin office ɗin mai ƙyau sosai ta nufa. Koda ta buɗe sai tai kasare tana kallon komai. Cike yake da kayan drinks kala-kala. Sai fruits suma kala-kala kowanne anyi packaging ɗinsa. Haka kawai ta samu kanta da taɓe baki, batare data zauna tantancewa ba ta ɗauka ɗaya ta dawo inda yake. Sai dai me tana ajiyewa batare daya kalleta ba ya furta, “Bana shan wannan”. Komai batace ba ta juya ta ajiye ta ɗakko wani. Shima tana kaiwa zata ajiye ya sake furta, “Changes someone”. Nan ma batace komai ba ta juya ta ajiye ta sake ɗakko wani. Shima haka ya ce mata baya so. Cikin wani irin takaici da jin zafi ta juya, sai kuma ta tsaya cak batare data kallesa ba ta ce, “Which one do you need?”.     Shiru yay mata bai tanka ba, hakan ya sake ƙullar da ita. Fuuu ta nufi fright ɗin ta sake buɗewa. Wancan ta dangwarar a inda ta ɗauka, nacan sama ta zubama ido sai dai hannunta bazai kai ba. Ta gwada ɗauka da ɗiɗɗishe amma duk tsahonta hannunta bazai kai ba. Juyawa tai tana ɗan kallon office ɗin alamar neman abin takawa, sai ko idonta ya sauka akan wani ɗan glass table da aka ɗaura ƙyaƙyƙyawan flowers a samansa. Shiko ta nufa ta sauke flowers base ɗin ta ɗakkosa gaban fright ɗin ta ajiye. Da kallon mamaki kawai ya bita, sai da ta ɗakko yaga da gaske fright ɗin ta nufa ya ɗan waro oily luluu ayes ɗinsa dake cikin gilashi.      Itako hajjajun babu ko ɗar ta taka ta haye samansa ta shiga jido kalolin lemukan tana tarawa a ɗayan hannunta. Ba ita zai rainama hankali ba. Bari ta kai masa duk kalolin taga iyakar rainin wayonsa. Tana gamawa ta juyo da nufin sauka sai kawai tai wani irin yin baya sakamakon kasancewarsa tsaye a bayanta hannayensa duk a cikin aljihun ya wani zuba mata mayatattun idanunsa kawai. Kaɗan ya rage ta faɗi, da ƙyar ta iya daidaita tsaiwarta tana tura baki batare data cigaba da iya kallonsa ba. Shi kam nasa idanun ƙyam a kanta ko ƙyaftawa bayayi. Kasa jurewa kallon nasa tayi, kasancewar ta a saman table tsahonsu ya dai-daita a yanzu harma ta ɗan zartashi kaɗan. Tun tana jin zata iya daurewa har jikinta ya fara rawa. Ga sanyin fright ɗin da bata rufeba na busota, ta gaba kuma ya tareta tako ina dan tsaye yake gab da ita sosai. Ga kuma drinks data tara a hannu suma sanyinsu na shigarta. Wani irin cikowa idanunta sukai da ƙwalla, cike da sarewa ta saki drinks ɗin suka tarwatse a ƙasa har wasu na faɗa masa a kan ƙafa amma bai motsa ba.        Zarrrr hawaye suka fara gudu a ƙyaƙyƙyawar fuskar Maanal. Lips dinta na wani irin motsi na son yin magana amma kuma ta kasa. Karan farko ya ɗan lumshe gajiyayyun idanun nasa tare da taɓe baki kaɗan. Sai kuma ya kai hannu a hankali ya rufe fright ɗin, yaja jikinsa yabar wajen batare da yace mata komai ba. Sauka tayi itama jikinta na cigaba da rawa zuciyarta na mata wani irin zafafa mata jin zafisa. Ko kallon drinks ɗin data zubar batai ba ta nufi hanyar ƙofa tana share hawayenta. Sai dai koda taja handle ɗin domin buɗewa sai ta jita bam a rufe. Tsaye kawai tai jikinta na sake cigaba da rawa. Hawayenta na ƙara ƙarfin gudu. Ta ƙara kai hannu taja amma still dai. Ai bama tasan ta wani irin juyowa inda yake ba, sai kawai ganinta tai a gabansa.        Cikin matuƙar ƙunar zuciya da raɗaɗi ta ce, “Mikake buƙata da ni ne wai? What is your business with me? ”.     Idan office ɗin ya motsa to shima ya motsa. Nunama yasan da ita a gabansa baiyi ba, karatunsa kawai yake yi. Hannu tasa ta fisgi book ɗin tai wurgi da shi saman kujera, cikin matuƙar tsiwa da komawa ainahin Maanal data mutu (😂injita) ta sake matsosa a kausashe, cikin ƴar tsawa ta furta “Ajwaad!! Nace mi kake buƙata da ni? Kana min abubuwa ina ɗauke kai amma na kula kai ka kasa fahimtar karatun kurma. Dole ne sai ka kasance in to my life ne? Kasan dai ni ba shasha bace da zaka taka yanda kake so kamar yanda ka iya ko, kodan kaga nazo ina aiki ne a ƙarƙashin alfarmarka kake ɗaukata a ban san mi nake yi ba? To daga yau nabar aikin, na bari tunda dama ra'ayina ya sani jin zanyi bawai rasa tallafin rayuwane ba ko talaucin da da ake kallonmu a ciki....”     A karo na farko da tun isowarta wajen ya ɗago mayatattun idanunsa dake cikin gilashi, gently hankali kwance ya zuba mata su. Sake hayayyaƙo masa tai har tana nunashi da ɗan yatsarta manuniya tamkar zata tsokale masa ido. Idanunsa da yake ɗan ƙyaƙyƙyaftawa ya ɗan ja kamar zai lumshe sai kuma ya sake buɗesu warrr a kanta. Cigaba take da nunasa tana masifarta har baya ma fahimtar abinda take faɗa, tsabar yanda ta birkice tuni veil ɗinta datai rolling ya warware hakama ɗan kwalin ya zame dogon gashinta baƙi siɗik dake ɗaure a tsakkiya cikin ƙyaƙyƙyawan ribbon ya bayyana sai lilo yake. Sosai ya maida idanunsa ya zuba akan gashin yana masa wani irin kallo.       Ina Maanal bata san yana yi ba, masifarta kawai take tana kuka. “Na tsaneka, wlhy na tsaneka Ajwaad. Bana son ganin ko fuskarka, da nasan ƙaddara zata sake haɗamu a duniyar nan dana roƙa ALLAH mutuwata kafin hakan. Na cigaba da yin aikin nan ne dan kawai baka isa hanani yin abinda raina keso ba a duniyata a duk inda naso hakan koda kuwa wajen mallakinka ne......”       Duk da wani irin saukar aradu da kalamanta ke masa a cikin kunne a bazata, matuƙar bazata taji tattausan hannunsa ya sauka akan yatsar ta dake neman cokale masa ido. Fisgar hannunta tayi tana sake birkice masa. Sai dai riƙon da yayma yatsar bana wasan yara bane ba. Dan fisga ɗaya ya mata bama wani da ƙarfi ba sai gata a gabansa a zube. Biyota yay da kallo har lokacin ɗan yatsar nata dai na riƙe a hannunsa.        “Wlhy koka sakeni kona maka ihu”.     Karo na farko ya saki wani ɗan iskan murmushi yana ɗan ɗage girarsa ɗaya, sai kuma ya sauke ƙafarsa duka ya ajiye a ƙasan carpet ɗin da take zaune tare da duƙowa sosai kusa da ita gab har tana jin numfashinsa da ƙarfin turarensa sosai a cikin hancinta. Jikinta taso ja baya sai dai sam yaƙi bata damar haka. Cikin sake lumshe idanu da buɗesu a lokaci guda ya motsa laɓɓansa ƙasa-ƙasa ya furta, “Bismillah yi, ba ihu ba? Maza kiyi, ai bana yau ne farko ba daman”. Cusa kanta tayi cikin ƙafafunta ta dunƙule a waje ɗaya tana mai fashewa da kuka. Ga jikinta na matuƙar rawa. Tabbas komai dawo mata yake. Ta ƙarfin tsiya da tsiya-tsiya brain dinta da zuciyarta keson tilastata tuna baya. Bayan data jima da shafewa a tarihin rayuwarta. Bayan da bata fatan koda wata alama ta tuna shi, bayan da take kallo tamkar RAYUWA A BAYAN MUTUWA. Bayan data jima da tattarashi ta tura can bayan bayanta ta yanda bazata sake tunawaba har gaban abada. Miyyasa yake son tilastata ne? Miyyasa bazai mata adalci bane? miyasa yake son sake cuta mata da wannan DAFIN da yay ajalin ainahin Maanal. Miyyasa bazai gane komai ya canja bane, canjawa irin wadda ke shafe ƙarnuka da zamanoni tamkar ba'a yisu ba. Kaicon samuwar wannan aiki nata, kaicon amincewarta da yinsa. Ita da kanta ji take ma ta tsani kanta da kanta a wannan gaɓar.........✍️      _Hummm ni Balki, wai shin...🤔 To bara dai nayi shiru kada ace na cika takale-takale 🥱😌😩🏃_ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖4️⃣3️⃣ ______________ ........Shima da gaba ɗaya kansa ke juya masa, al'amura masu nauyi da suke lulluɓe a zuciyarsa na sake zaburowa, a hankali ya saki mata yatsan yana rumtse idanunsa da ƙarfi. Wani irin ratsa zuciyarsa da ɓargo kukan nata yake yi. Sai dai bazaka taɓa fahimtar hakan a fuskarsa ba idan ka cire idanunsa da sukai matuƙar kaɗawa. Tawani fannin kuma zai iya cewa kukan yake so tayi, dan zai rage mata nauyin zuciya dana zafinsa da yasan take ji. Fin mintuna biyar suna a haka kafin ya miƙe a wajen, veil ɗinta dake yashe a ƙasa ya ɗauka, ƙamshinsa na sake ratsa hancinsa, kanta ya ɗan rankwafo ya yafa mata veil ɗin a saman kanta batare da yace komai ba ya wuce ainahin office chair ɗinsa, batare daya zauna ba ya ciri ƙaramar pepper yay ɗan rubutu, sai kuma ya ɗauka shopping bag ƙarama dake a saman desk ɗin. Rigar suit ɗinsa dake a hanger ya cire itama tare da tattare wayoyinsa. Gabanta yaje ya ajiye shopping bag ɗin nan da shot note ɗin da yayi batare da yace mata komai ba ya nufi ƙofa. Sai da ya kai hannu zai danna maɓallin buɗe ƙofar batare daya jiyo ba ya furta, “Ki tabbatar kin shiga restroom kin gyara fuskarki”. Daga haka yay ficewarsa cike da takunsa na nutsuwa da ƙasaita.      Da wani irin sauri Huznah dake zaune cikin takaici da damuwa ta miƙe. Hakama AS ɗinsa daya san wannan ba lokacin fitowarsa bane miƙewa yayi. Baiko kalla inda Huznah take ba, sai Assistant ɗin nasa ya kalla. “Zanje airport ɗaukar su Mamy. Take care of everything”.      “Okay Sir ALLAH ya tsare”. Kansa kawai ya jinjina masa yay wucewarsa. Har kuma yayi taku uku sai ya tsaya cak jin ana binsa a baya. Ɗan waiwayowa yay tamkar mai jin ciwon wuya ya zuba mata ƙasaitattun idanunsa da gaba ɗaya suka sauya kala da launinsu. Dan farin gilashin fuskarsa bai zam ya ɓoye komai ba daga garesu. Kasa jure kallonsa Huznah tayi, sai ma jikinta dake neman fara rawa. Amma tai ƙoƙarin riƙe kanta da tsiya, sai dai muryarta na ɗan rawa ta ce, “A zahiri bakayi kama da mai wulaƙanta mutane ba, why ni nake neman zama ƙasƙantacciya a yayin zuwa ganinka? Please ka duba ni, ka bani dama muyi magana dan ALLAH”..          Karo na farko ya lumshe idanun nasa da buɗesu. Hakan tuni ya zame masa ɗabi'a musamman a yayin son yin magana. Cikin cool voice ɗinsa mai fidda ƙaramin amo da kasancewa ƙasa-ƙasa tamkar ba namiji ba ya furta, “Mi kike buƙata?”.       “Kai! Kai nake buƙata AA. Ina son yin magana da kai Please”. Lips ɗinsa ya ɗan ciza sai kuma ya janye idanunsa daga kanta. Ƙoƙarin wucewa yay batare daya tanka mata ba yana kallon Designer agogonsa da sai ka gama karaɗewa baka samo sa ba, dan shi duk wani agogon sakawarsa ana masa shi a companynsa kuma shi kaɗai, sai idan wani ne yace yana so ayi irinsa daga nan shi kuma yabar saka Design ɗin sai kuma wani. Da sauri ta bi bayansa suka shige cikin elevator daya buɗe. Anan ɗin ma dubansa tayi da son yin magana sai dai ta gagara sakamakon ganin fuskarsa babu alamun wasa. A haka suka fito tanata ƙoƙarin ganin ta daidaita tafiyarsu. Aiko hakan yaja hankalin ma'aikatansa matuƙa. Dan duk inda suka gitta idanu yuuu akansu. Masu ƙus-ƙus nayi masu jinjina kai nayi. Yayinda zukatan mafi yawansu suka sake yarda da eh lallai da gaske itace boss ɗin nasu zai aura kuwa. Dan abune da basu taɓa gani ba boss da mace kamar haka. Ina dai ka gansu da wata to lallai abokiyar kasuwanci ce, dan shi hatta a cikin family baya kula ƴar kowa, in dai kina sama da shi zai yi respecting ɗinki. Suna gama ficewa sai ƙus-ƙus ɗin ya ƙaru, yayinda wasu suka maida hankalinsu ga hotunan dake akowacce kusurwa ta Company ɗin na mace mai niƙab da hijjab. Wadda da yawansu sun gagara tantance hoto ne ko zane ne. So suke su tantance ko wadda suka fita taren ce. Sai dai sam babu wani alamu ko kamanni daya nuna hakan. Dan baka isa tantance ainahin wacece a hoton ba tako ina....         Yana fitowa drivern sa dake can wajen securitys suna hira ya miƙe da sauri. Sai dai koda ya iso garesa sai ya miƙa masa hannu murya ƙasa-ƙasa yana faɗin, “Don't worry, give me the key, I want to drive myself”.       Babu musu driver ya rissina ya miƙa masa key ɗin. Sai kuma ya buɗe masa motar da sauri.       “Ka sama mata taxi”. Ya sake faɗa yana ƙoƙarin shiga motar, kallon Huznah driver yayi, sai kuma ya amsa da sauri cike da girmamawa. Huznah kam dake tsaye kamar zata saki kuka kallonsu kawai takeyi, tana ji tana gani a gabanta ya birka motarsa ya fice cike da ƙwarewar iya tuƙi na nutsuwa da cikar kamala....        Lallai yau taga madarar wulaƙanci da babu ko gauraye a cikinta, wato mutumin nan cikin ruwan sanyi yake tsula maka tsiya babu hayaniya babu hargowa ko yawan magana. Dole ne ta koma Kaduna su sake shiri kam, amma zata fara bari ta haɗu da mahaifiyar tasa dan taga yaya nata takun itama, hakan zai sa susan irin shirin da zasu musu su duka.. da wannan tunanin ta ballama drivern harara ta fice da ƙafarta.....      ★★★   Maanal ta jima a wajen tana kuka, sai da ta fara jin zuciyarta na mata nauyi a cikin ƙirjinta kafin ta ɗago kanta da ƙyar, office chair ɗinsa ta zubama ido sosai tamkar shine a wajen, har yanzu hawayen na cigaba da ziraro mata. Tunanin dake neman tasiri a ranta ta ture da ƙarfin tsiya tare da miƙewa ta nufi restroom ɗin kamar yanda ya faɗa, dan itama tasan ko giyar wake tasha bazata fita a haka ba ai. Sosai restroom ɗin ya haɗu, gashi ƙal-ƙal sai ƙamshi yake zubawa kamar ba toilet ba. Ta jima tsaye tana kallon kanta a mirror ɗin bayin tana hawaye kafin ta wanke fuskar tata ta fito bayan ta gogeta da ƙaramin towel fari tas dake a bayin. Harta nufi ƙofa ta koma da baya, shopping bag ɗin daya ajiye a gabanta ta ɗauka kasancewar ganin abinda ya rubuta a takardar daya ajiye a sama, sai kuma ta maida ta ajiye. Nan ma ta juya zata tafi idonta suka sake sauka a novel ɗin nan nasa. Baki ta tura gaba sannan ta ɗauka shi dai ta ficewarta..       Koda ta fito bata kula kowa ba a wajen ta shiga haɗa ƴan tarkacen kayanta, kallonta kawai su Zaharadeen suke cike da gulma. Sai Yaqub ne daya miƙe tsaye yana kallonta tun shigowarta ya furta, “Sister Maanal are you okay?”.       Kanta kawai ta jinjina masa batare da dace komai ba. Kafin ya samu damar sake magana ta kwashi kayanta zata wuce. Cikin sauri ya bita yana faɗin, “Ina zaki je?”.     “Gida”. Ta bashi amsa a takaice. Cikin tashin hankali ya buɗe baki zai sake magana a fusace ta ce, “Please Yakub! Nace ba komai. Leave me alone”. Daga haka tai gaba abinta fuuuu. Shiru yay kawai yana kallonta, gaba ɗaya fuskarsa ta nuna tsantsar damuwa da tashin hankali. Shin mike faruwa? Mi akai mata? A office na CEO fa aka kirata! Miya faru acan ɗin?”. Rashin mai bashi amsa ya sashi juyawa jiki a sanyaye ya koma ciki. Sai kuma ya sake tadda wani abun takaicin, su Zaharadeen ne suke buɗe babin gulmar Maanal ɗin. Wai maybe ta faɗama CEO tana sonshi ne shine ya koreta a aiki, sai ALLAH ya ƙara suke mata da kiranta mai girman kai da faɗin rai. Takaicinsu ya saka Yakub ko kulasu baiyi ba......            ______________★       “Alhamdullahi ranka ya daɗe aiki ya kammala. Wannan shine cikakken bayani akan ainahin mahaifinta dama zuri'arta baki ɗaya”. Rabilu ne mai maganar fuskarsa washe da murmushi yana miƙama Sen.. Bukar bayani akan Maanaal daya binciko kamar yanda ya buƙata. Sosai fuskar sa ta washe da murmushi. Dan shi kaɗai yasan yanda yake azabtuwa da so da ƙaunar yarinyar nan data mamaye dukkan illahirin jinin jikinsa. Yanzu haka yau har gaban Mawaad company yasa drivern sa yaje ya faka mota har Maanal ta iso. Fitarta a motar Shahidah da dukkan abinda ya faru a wajen kan idonsa ne. Ji ya dingayi kamar ya sato ta saboda yanda tai matuƙar ƙyawu a cikin kwalliyar ta yau.        Rabilu ya cigaba da faɗin, “Su ɗin asalin su ƴan jihar Kebbi ne, ƙaramar hukumar suru a wani ƙauye da ake kira giro. Mahaifin nata ɗan sanda ne, dan har ya kai matakin DPO amma yanzu ya ajiye aiki sakamakon doguwar jiyyar da yayi. Ita kuma mahaifiyarta bata tare da shi a yanzu, dan sun rabu shekaru kusan takwas kenan, a yanzu haka tana auren wani Alhaji Usman Chalawa ne anan kaduna, yana riƙe da su kuma tamkar mahaifin nasu koma fiye da shi.”      Cike da zumuɗi ya furta, “Rabilu kaje wajen Oler ka amshi key ɗin motar ka sabuwa dal, zuwa dare zan nemeka idan na koma gida”.      Cikin matuƙar washe baki Rabilu ya shiga godiya harda ɗan zamowa daga visitors chair da yake zaune ta office ɗin Sen.. Aifa cike da zumuɗi ya bar office ɗin. Kai tsaye gidan Sen.. Bukar ya nufa domin amsar alƙawarinsa dan yasan baya magana biyu akan alkawari irin wannan daya shafi mata. Zai iya cewa dukan matan alhajin idan ka cire uwargidansa duk shine ya masa bincike akan sauran biyun. Ya kuma taka rawar gani akan samuwar auren fiye da zaton mai zato. Sai dai ya fahimci kamar Senator ɗin yafi sakin kuɗi da ɗoki akan wannan ƴar shilar. To ƴar shila mana. Akan matan Alhaji ai manaal ƴar shila ce. Dan ko jikansa na farko ya girmi Maanal sosai. Aiko ina sha ALLAHU zai yi iya ƙoƙarinsa dan ganin tako ina Alhaji bai samu matsala ba, ya kuma mallaki yarinyar da gaggawa. Dan yasan irin wannan kariɓujin arziƙin da ire-irensa sunta zuwa kenan. Zama kuwa ai ba nashi bane ba.... ____________★          Cike da nutsuwa Daddy ke kallon Yazeed. Yayinda shi kuma kansa ke duƙe a ƙasa rauninsa na sake bayyana akan fuskarsa. Karo na farko Daddy ya ɗan saki murmushi, yayinda tausayin yaron nasa ke ratsa masa zuciya. Ya jima da fahimtar tsananin so da Yazeed kema Maanal, sai dai bai sake tabbatarwa ba sai a ɗan tsakanin nan. Musamman yau da yazo masa da roƙo da magiyar janye batun sai nan da wata biyar ayi aurensa da Manaal. So yake a haɗesa gaba ɗaya anan da sati biyun daya rage shi da Nazeefa. Gyaran murya yay da gyara zamansa. Hakan yasa Yazeed ɗagowa ya ɗan kallesa.         “Yazeed kasan dai ina bayanka nima ɗari bisa ɗari akan zancenka da Maanal. Sai dai ina son kamar yanda su Baba Kalla suka faɗa wannan karon naje da kaina da baba nema maka aurenta ga mahaifinta. Hakan shine zai bada salama game da tujarar mahaifiyarka akan al'amarin”.      “Daddy nima na yarda da hakan, amma dan ALLAH ina sake neman alfarmar haɗewar gaba ɗaya. Nasan ko'a cikin satin nan zaku iya zuwa ga mahaifin nata, idan kuma ka amince min ni saina fara zuwa na ganshi”.     Ɗan jimmm Daddy yayi, sai kuma ya shiga jinjina kansa. “Shike nan na yarda da zancen naka in sha ALLAHU za'a haɗe bikin nan da sati biyun, zan samu Baba da batun shima sai mu saka ranar zuwa muga mahaifin nata, kai ka tsahirta sai bayan mun dawo ɗin. Kadai je ka cigaba da shirinka na zama angon mata biyu a rana ɗaya”.       Ƙasa Yazeed yay da idanunsa wani murmushi na suɓuce masa. Yayinda zuciyarsa ke wani irin washewa da farin ciki mara misaltawa. Ji yake kamar an masa gafarar zunubansa. Yana fitowa ya shiga neman layin Maanal dan yay mata albishir, sai dai bata shiga ba. Duk da yasan yanzu tana office kasa haƙuri yayi ya shiga neman Shahidah. Bayan sun gaisa yake tambayarta Maanal fa. Cikin girmamawa ta sanar masa har yau ba'a dawo mata da wayarta data samu matsala ba ne, amma tana ƙyautata zaton yau za'a kawo mata, sai dai idan ta tashi zata haɗasu..... ___________★        Shiru kawai Ammie tai tana kallo Daddy dake mata bayanin sabon hukuncin daya sake yankewa akan dawo da zancen bikin Maanal da Yazeed anan da sati uku. Za'a haɗe ɗaurin auren kawai idan ma bikin Maanal ɗin ne za'a ɗaga nan da zuwa ko wata ɗaya ne idan ita bata shirya ba to. Sai kuma batun zuwa ga dangin mahaifinta kamar yanda sukai alƙawari tun farko. A yanzu haka ma yana shirin zuwa su tattauna da baba ne. Ya sanar mata ne koda sun gama yanke hukunci shi da baban basai sannan taji ba.          Zuciyar Ammie kaikawo kawai take a cikin ƙirjinta, sai dai kamar yanda ta saba dannewa yanzun ma saita danne ta amsa masa da girmamawa tare da jera addu'ar fatan alkairi. Wannan halayyar nata ke ƙara masa jin sonta da ƙaunarta. Bayan ya wuce hawaye cike da idanunta tayi kiran Nene, ko gaisawa basuyi ba ta sanya mata kuka. Sosai hankalin Nenen ya tashi, ta shiga tambayarta abinda ke faruwa a rikice. Sosai Ammie tayi kuka kafin ta zayyanema Nene komai. Itama hankalin nata tashi yay, harma taji ta gagara furta komai.. ___________★        “Aunty Babba nifa ina son ku haɗu ke da Aunty Majdiya da Aunty Khaleesat kuyi magana da Baffah akan batun nan. ina so a cikin watan nan iyaye suyi magana, kuma wata biyu kawai nake so a saka, itama Maanal yau zanyi magana da ita”.         Baki Oum ta buɗe kamar a ɗan firgice zata bama RK amsa idanunta suka sauka akan AA dake kokarin shigowa, sai dai furucin RK ya sashi tsayawa cak shima..........✍️ _Wannan fa shine cakwakiya, tako ina kowa ya zaburo. Manaal akwai white blood kam🤣. Dangin AA wai mike damun Yayanku ne?🥱🏃_ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖4️⃣4️⃣ ______________ .......Kallonsa kawai Oum take yi zuciyarta na motsawa da bugawa da sauri-sauri, yayinda shima ya zuba mata gajiyayyun idanunsa da suka sake kaɗewa. A hankali ya ɗaga ƙafarsa zai juya ya fita ta kira sunansa a hankali.        “Ajwaad!”.   Cak ya tsaya batare daya juyo ba. Yayinda RK da bai lura da shigowar AA ɗin ba ya juya shima yana kallonsa. Cikin rashin fahimtar abinda ke faruwa ya saki murmushi da faɗin, “Ni dai ban more ɗa ba. Malam dawo bafa wata magana bace daban kaima ayi dakai batun son zuwa a nema min auren ƙanwarka Maanal mukeyi kawai”.      Da wani irin ƙarfi AA ya rumtse idanunsa jikinsa na wata irin tsuma. Da sassarfa ya nufi ƙofa murya a shaƙe ya furta, “Oum na ɗakko su Mamy” daga haka yay ficewarsa.       Da mamaki RK ya dubi Oum shima, “Aunty mike damun ɗanki?”. Murmushin yake Oum tayi kawai. Zuciyarta na ƙara raunana da mata nauyi. Cikin son danne komai ta ce, “Maybe aiki ne ko kuma an kunnosa daga waje. Kaga ka bari zamu tattauna anjima su Aban sun iso”.... ___________★        Kamar yanda Sen Bukar ya faɗa zuwa dare ya sake sabon zama da Rabilu. Sun sake tattaunawa sosai tare da tsaida ranar zuwa Giro domin ganawa da mahaifin Maanal. Yayinda tun a ranar ya sanarma uwargidansa shifa zai ƙara aure. Dan yau a gidanta yake. Kamar yanda ta saba cikin nuna rashin damuwa tai masa addu'a da fatan alheri. Sai da ta fito daga ɗakin nasa ta koma nata taci kuka. Ita kaɗai tasan yanda take matuƙar takaicin aure-auren nan na mijinta. Dan ita macece mai tsananin kishi. Shiyyasa a dukansu daya auro kowacce jinta take a sabuwar kishiya. A gareta bata yarda da zancen hausawa da kance kishiya ta biyu ita kaɗai ce kishiyar uwargida ba. Ita duk kishiya sunanta kishiya a wajenta. Sai dai irin matan nan ne ita masu ƙullata da shanye abu a cikinsu bazaka taɓa jin sun furta da baki ba. Shiyyasa ake mata kallon mai haƙuri. Amma sam ba haka bane ba, domin kuwa tana nan tana tara abubuwan a rai suna mata nauyi...       Shiko Sen.. Bukar ko'a kwalar rigarsa, dan tun a daren yama gama tsara komai. A gefe kuma ya saka babban yaronsa Oler yo shopping na garari zuwa gobe domin yin tsaraba kaikace ganin danginsa zaije ƙauye ba neman iznin neman auren ba......     _________           Tunda ya baro sashen Oum kulle kansa yay a bedroom ɗinsa. Wani irin ciwo kansa ke masa, ga sanyi na ratsa masa ɓargon jiki da ƙashi, bai ko iya cire takalman ƙafarsa ba ya faɗa saman gado tare da jan duvet ya ƙudundune kansa. Cikin ƙanƙanin lokaci kuwa zazzaɓi ya rufesa gaba ɗaya. _(Na tsaneka, wlhy na tsaneka Ajwaad. Bana son ganin ko fuskarka, da nasan ƙaddara zata sake haɗamu a duniyar nan dana roƙa ALLAH mutuwata kafin hakan. Na cigaba da yin aikin nan ne dan kawai baka isa hanani yin abinda raina keso ba a duniyata a duk inda naso hakan koda kuwa wajen ya kasance mallakinka ne.....”)_ wani irin sara masa kan nasa yayi sakamakon kalamanta da suke maimaita kansu a cikin kunnensa tamkar yanzu ne take ambatosu, ko a ɗazun ma dakewa kawai yake yi a gabanta. Ji yake tamkar yayta fasa ihu, ihu irin wanda sai ya janyo girgizar ƙasar da kaf gidajen duniya zasu narke cikin ƙasa. Sai dai ba zaiyi hakan ba, sai ma ambaton ALLAH da ya dingayi a zuciyarsa...       Dai-dai nan Oum da hankalinta ya kasa kwanciya ta iso sashen nasa. Dan har ta nufi sashen mahaifinsu ta fasa tayo nan. Ganin babu shi a main falo yasata haurawa sama da sassarfa. Nan ma babu kowa komai ma a kashe yake tamkar ƙasa. Bedroom ɗinsa ta nufa, tai nocking da kiran sunansa amma shiru. Handle ɗin ta kama zata buɗe dan zuciyarta na sake tabbatar mata babu lafiya amma sai taji gam. Sosai hankalinta ya sake tashi ta shiga kiran sunansa cikin damuwa da lallashi. Amma fin mintuna biyar baida alamar amsawa. Hawaye suka fara ziraro mata cikin rawar murya ta ce, “Haba sweetheart sokake na maka kuka. Ka buɗe naga halin da kake a ciki Please Autan Oum”.     Nan ɗin ma babu alamar motsinsa, hankalinta ne ya sake tashi, cikin sassarfa ta juya ta fita. Sashen Abah ta nufa, sallama kawai tayi batare da jiran amsa ba ta danna kai cikin bedroom ɗinsa. Dai-dai ya fito a wanka, batare da ya kalleta ba cikin barkwancinsa da Fawzan ya gada ya ce, “Ai ni da na cika fam saura kaɗan na fashe ganin matar gidan yau bata ɗokin dawowata kamar yanda shima ɗanta baiyi.....”        Jin tayi shiru sai ma kamar tana kuka ya sashi fasa nufar mirror da yay niyya ya juyo yana kallonta. Tsamm yayi sai kuma ya tako a hankali zuwa inda take cike da nutsuwarsa da cikar kamala. “Fateema miya faru?”. Ya tambaya hankali tashe. Idanunta dake zirar da hawaye ta zuba masa. Da ƙyar ta iya motsa lips ɗinta ta furta, “Ajwaad. Ya rufe kansa a ɗaki nayi kiran duniya bai amsa ba. Ina jin tsoro, tsoro nake ji Zaki na, kada yanayinsa na bayane ke son dawowa”.      Ɗan lumshe idanu Abah yay ya sake buɗewa a kanta (Sak ɗabi'ar AA da alama a wajensa ya gada rufe ido da buɗewa yayin magana😂👌🏃). Hannunsa yasa ya riƙo nata, cikin yanayin tashin hankalin shima ya ce, “Oh kenan akwai abinda ke damunsa? Dan a haka yaje ɗakkomu airport fuska kicin-kicin, daga gaisuwa ko bai sake kulamu ba har muka shigo gidan nan. Wani abu ya faru ne?”.         “Ni dai a sani na babu abinda ya faru a yau ɗin, duk da dai satittikan nan gaba ɗaya gashi nan dai tunda ya tashi daga zazzaɓin nan na gab da tafiyarku, yau kuma daga office ya wuce ɗaukanku dan da Fawzan ne zai je sai ya kirani akan akwai meeting na gaggawa da zai shiga dan ALLAH nama Auta magana yaje ɗaukanku ko Babban yaya. Shi kuma Fadeel ya tara aiki a office saboda zuwa Kanon nan da yay shiyyasa na turama Autan text akan shi yaje, ya kuma kirani a waya babu wani damuwa a tare da shi yace min zaije ɗin dan bashi da wani abu mai muhimmanci a lokacin, sai kuma gashi ya dawo yanzu a birkice.”       Cikin furzar da iska mai nauyi Dad ya ce, “It's okay ina zuwa.” closet ɗinsa ya nufa ya saka kaya tare da buɗe wata loka ya dudduba keys, ɗakko na sashen AA yayi yazo ya kama hannunta suka fito. Suna ƙoƙarin shiga sashen motar Fadeel da kowa ke kira babban Yaya a gidan ta shigo. Ganin yanda suka nufi sashen Auta kamar hankali a tashe ya sashi fitowa da sauri shima yabi bayansu ko rufe motar ma bai gama yi ba. Matarsa data fito daga flat ɗinsu domin tarbarsa ganin inda ya nufa ta ɓata fuska da binsa da harara, har zata juya a fusace sai kuma ta fasa itama ta nufi sashen AA ɗin dan son ganin mi mijin nata kema gudun zuwa yi sashen ƙanin nasa mai shegen girman kai.      Lokacin da suka iso su biyun Abah nata ƙoƙarin gwada key a ƙofar bedroom ɗin AA ɗin, yayinda Oum ke duba sauran bedrooms ɗin da ɗazun rikicewa ta mantar da ita dubawa. Dama bedrooms uku ne a saman, ƙasa ma uku. Ɗaya a main falo biyu a ɗayan falon.       “Abah lafiya kuwa?”.   Fadeel daya iso ya faɗa a rikice. Batare da Abah ya dubesa ba ya amsa masa da, “Ban san mike faruwa ba nima Fadeel. Oum ɗinku ce tazo hankali tashe tana sanar min Ajwaad ya kulle kansa a ɗaki”.       Kafin Babban yaya ya samu damar cewa wani abu ƙofar ya buɗe. Su duka afkawa sukai ciki har Oum da matar babban yaya data iso yanzun nan. Aiko tuni hankalinsu ya sake tashi dan ganinsa a bargo, yayinda tuni Oum da babban yaya sun haura saman katafaren gadon nasa dake a dunƙule kamar zero. Oum ce ta yaye bargon dan har fuskarsa ya rufe, hucin zafin zazzaɓinsa ne ya bugeta, sai kuma rawar sanyin da yake faman yi. Cikin fashewa da kuka Oum ta kamo hannunsa ta damƙe cikin nata tana kiran sunansa......       ________★       Kusan zamu iya cewa a position ɗaya AA da Maanal suke a ciki. Dan itama bama ta san a yanayin data iso gidan ba. Sai maigadi ne ya biya taxi drivern daya kawota. Itako tuni ta shige ciki tana layi saboda nauyin da ƙirjinta yay mata har numfashinta na seizing. Batama ko ƙarasa shiga cikin ainahin falon ba ta zube a ƙofa tana ƙoƙarin kiran sunan Shahidah sai dai muryarta sam bata fita. ALLAH ne ya taimaka Linda ta fito dan tana ƙoƙarin jera abincin su Barrah a d/table kasancewar suna gab da dawowa daga school. Idanu ta zaro tare da dangwarar da abinda ta ɗakko ɗin ta nufi Maanal da gudu. Ganin numfashinta na neman barin gangar jikin ta yasa Linda kwara ihu. Ai a guje baba magajiya ta fito daga kitchen tana tambayar Linda mike faruwa?. Ganin Maanal dake kakarin mutuwa yasa itama ta fasa ƙarar. Sai kuma ta runtuma waje a guje tana kiran maigadi. Cikin sa'a ta samesa tare da drivern yara da yazo ɗaukar mota zai tafi ɗakkosu. A guje suka koma ciki su ukun, Linda da Baba magajiya suka cicciɓi Maanal suka fito, a mota aka sakata, baba magajiya ta shiga itama driver yaja suka fice aka bar maigadi da Linda dan bazai yiwu subar gidan babu kowa ba kuma.         Maigadi ne ya tunatar da Linda cewar ya kamata ta kira Hajiya ta sanar mata. Sai yanzu itama ta farga da haka. Lokacin da ta kira Shahidah tana tsaka da aiki, amma haka ta wancakalar da komai cikin tashin hankali ta fice zuwa asibiti bayan ta kira RK. Cikin tashin hankali ya sanar mata isowar su Maanal ɗin a yanzu haka. Kana jin muryarsa kasan shima ya gama gigicewa, sai Shahidah ta ƙara ruɗewa itama.      ★ A wannan karon ma dai ansha matuƙar wahala kafin ceto numfashin Maanal, sai dai sam babu aman jini idan ka cire wanda ya ɗan ziraro mata ta hanci kamar haɓo. Shima kuma basuyi wahala wajen tsaidashi ba. Su Dr Ranjet basu samu nitsuwa ba sai bayan isha'i, dama shi RK wannan karon ma kasa komai yayi bakamar wancan karon da akai komai da shi ba. Sai dai yana a bakin ƙofar tare da Shahidah da mijinta da shima ya iso suna zaman jiran tsammani. Fitowar su Dr Ranjet ya saka su dukansu miƙewa. RK kamar ba likita ba ya nufesa da sassarfa yana tambayarsa yaya take?. Cike da kulawa Dr Ranjet ya dafa shi yana faɗin, “Calm down doctor, everything is fine”. Kusan su ukun a tare suka sauke ajiyar zuciya mai matuƙar nauyi. Yayinda Dr Ranjet ya sake kwantar musu da hankali..... __________★        A ruɗe Oum tacema Babban yaya yay mata kiran Uncle ɗinsu yana sashenta. Fita yay kuwa da sauri, sai dai yana fitowa motar RK na fita a gidan da gudu. Dan dai-dai ya nufo sashen AA da nufin jin damuwarsa saboda tunaninsa Oum na wajen mijinta kamar yanda tace masa zataje, sai dai yana gab da shiga sashen ne Dr Ranjet yay kiransa cewar gafa Maanal an kawo asibiti. Shine ya juya a guje ya faɗa mota ya fice. Fitar tasa dai-dai da shigowar motar Fawzan shima daga wajen aiki. Matarsa na a gefensa dan itama tana fita aikin, motarta ta samu matsala ne ta barta a office tai kiransa ya biya ya ɗakkota suka nufo gida. Ganin babban yaya ya sasu fitowa da sauri Fawzan na tambayar ko lafiya yaga Uncle Rafeeq ya fita a guje?.          “I don't know why! Na fito kiransa ne nima fa”.      “A da alama gaskiya babu lafiya, dan kamarma waya yake hankali tashe. Maybe asibitine suka kirashi kasan Uncle da patient ɗin nan nashi. Amma lafiya kuwa?”.       “Auta ne babu lafiya”.    Ai Fawzan ma bai samu damar sake cewa komai ba suka nufi sashen AA su duka ukun. Sai dai Babban Yaya na ƙoƙarin kiran layin family doctor ɗinsu a waya da shima ke aiki a KK HOSPITAL ɗin. Kafin doctor ya iso su duka sun rufu a kansa hankalinsu duk a tashe. Kallo ɗaya zakaima wannan taron kasan AA ɗin ɗan gatan dangi ne. Dan amaryar Abah ce kawai babu a wajen. Sai da matar babban yaya ta ɗaga waya tai kiranta sannan sai gata ta iso. Kusan tare suka shigo da doctor. Itama dai macece ƙyaƙyƙyawa, tana da ɗan jiki na ƙiba dan har tafi Oum ma. Sai dai Oum ta fita tsayi da haske dan ita fara ce kamar yanda Abah ke fari tas. Kai hasalima suna kama sosai da Abah ɗin tabbacin auren zuminci ne a tsakaninsu. Hakama duk yaran kama suke dasu, idan ka cire AA da yake da duhun fata sai dai kamanin fuskar Oum da Abah ɗin na tare da shi shima.        Duk fitowa sukai aka bar Oum da Doctor yana duba shi. Duk da cikin faɗa yake mitar shi abarsa kar doctor ɗin ya taɓasa. A barshi haka baya buƙatar kowane magani. Hawaye Oum take tana ƙoƙarin tausarsa da shafa lallausar sumarsa daya tara take cin kuɗaɗe. Yayinda idanunta ke zubar da hawayen tausayin yaron nata dan gaba ɗaya yanayinsa ya nuna alamomin tashin ciwonsa. Sam bata fatan hakan, bata son abinda ya shuɗe suke murna ya dawo. Sun azabtu matuƙar azabtuwa da halin da AA ya shiga a shekarun baya. Da ƙyar da addu'oi abubuwa suka sassauta. Sai tabon dake zuciyarsa da sun san har ya koma ga ALLAH bazai warke ba kamar yanda suma nasun yake zaune daram. Sai kuma gashi ƙaddara na neman sabunta abubuwa cike da ban al'ajabi da mamaki a duka ɓangarorin biyu.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖4️⃣5️⃣ ______________ .........Sai da Doctor yay masa allurai masu matuƙar ƙarfi a cikin drip ɗin da aka saka masa har kala uku a tare sannan barci ya ɗaukesa. Cikin kwantar ma su Oum da hankali yace musu karsu damu in sha ALLAHU komai zaiyi normal. Dan dama akwai malaria ne a jikinsa sai kuma damuwa data saka jininsa haurawa sama sosai, kuma da alama ya kwana biyu da damuwar a ransa amma ya cigaba da jigata kansa da sabgogi kuma.         Hankalinsu ya ɗan kwanta jin abun da sauƙi, sai dai a ƙasan ran kowa maganar damuwar da yake ciki ta damesu. Oum da Fawzan ne kawai da suka fahimci musabbabin damuwar zuciyarsu ke suya. Sai dai basuce komai ba akai dan ko Babban yaya daya dawo Kano basu gaya masa zuwan Maanal gidan ba. Bayan sun shiga sun gaggansa yana barci fuskar nan fayau sai dai a takure na rashin wal'wala tamkar yana ido biyu. Yayinda Oum ke zare masa takalman ƙafarsa a hankali. Amsa Babban yaya dake kusa da ita yay ya ajiye gefe, batare daya zare masa socks ɗin ba ya maida duvet ɗin ya rufe masa ƙafafun a yanda suke. Tie ɗinsa da tuni ya sassautoshi da kansa dama Oum ta ƙarasa zarewa shima. Sai ƴar rigar saman long sleeve shirt ɗinsa itama ta ɓalle botiran. Itama shirt ɗin ta rage botira uku na sama. Su dai sauran duk suna tsaye suna kallonta, musamman Abah dake mata kallo cike da so da ƙaunarta. Matarsa dabance a cikin mata, idan yace daban yana nufin daban ɗinne a cikin daban. Har yanzu bai iya samun abinda zai kwatanta Fateeman sa da shi ba. Murmushi ya saki mai sanyi sakamakon haɗa ido da sukai da babban yaya da shima ke murmushin, sai kuma duk suka janye ya ɗan kalla amaryarsa itama. Itama dai Oum ɗin take kallo fuskarta da ɗan murmushi. Jiyay itama so da ƙaunarta na sake dasuwa a ransa. Kai shi kam ya gode ALLAH da samun mata nagartattu na ƙwarai. Su ɗin aljannar duniyarsa ne.       Sallar magrib ce ta fita da su a sashen, amma Oum bata fitan ba sai ma umarni ta bama Fawzan akan ya kawo mata kayan sallarta nan. Da girmamawa ya amsa mata yana fita. Yayinda Abah dake kallonta cikin marairaice fuska ya furta, “Amma baiwar ALLAH tunda ɗan naki ya samu barci ai ƙyaji tausayina kizo ki bani abinci”.       Ɓata fuska Oum tayi tana girgiza masa kai, “Ni dai gaskiya babu inda zanje nabar yarona a wannan halin, in dai abinci ne ai na kammala Mamy ta shirya maka kuje ku ƙarata”.       Dad daya rasa ma abin cewa juyawa yay yana kallon Mamy, murmushi ta masa kawai da faɗin, “Kaima kasan ba kulamu za'ai ba ɗan gwal babu lafiya. Mu rufama kammu asiri muje muci abinci dan nikam har uku huɗu nake ganin mutane”.            Ɗan hararar wasa Oum tai musu tana murmushi. “Eh kwaji da gulmarku dai, dan kawai kanwa na kawo sai na bar yarona a halin ciwo na koma kanku”.       Dariya sosai Abah ya kwashe da shi, sai kuma ya nunama Mamy hanya yana faɗin, “Kinga Kamilah muje dan na kula itama uwar ɗan sai a hankali. Dama haka ɗan ya ɗakkomu a airport yana mana mazurai kamar sabon dan doka da mai laifi.”         “Kwaji dai da shi, ba kulaku zamuyi ba sai mun warke”. Oum ta faɗa tana murmushi. Ficewa sukai suma suna dariya. Dama tuni matan su Fawzan sun fice. Dai-dai nan Fawzan ɗin ya shigo da kayan sallar Oum. Ajiye mata yay shima ya fita dan kar ya rasa jami'a. __________★        Alhamdullah washe gari su dukansu jikin nasu da sauƙi. Musamman ma AA da Oum ke faman riritawa kamar wani ƙwai. A yanzu haka tana zaune ne bakin gado kusa da shi tana bashi breakfast, sai faman mata shagwaɓa yake ita ko tana lallaɓashi. Su Fawzan duk sun wuce aiki bayan sun shigo sun duba shi, hakama Abah tunda ya shigo ya gansa ya fita dan yana da uziri. Mamy ma ta shigo ita da matar babban yaya. Sai dai bata wani jimaba ta tafi tabar Oum da matar babban yayan dan ita bata aiki Bussines takeyi na kawo kaya daga Chaina tana rabama ma'aikata. A yanzu haka ma da Oum ke faman lallaɓa shi tana zaune tana faman musu dariya. Shi dai ba wani kulata yake ba dan tsakaninsa da matan yayyan nashi gaisuwar girmamawace da mutuntawa. Amma ka gansa yana hira dasu ko wani wasa da dariya abune mai wahalar gaske dan duk ƙanne suke a gunsa. Kai shifa mai ganin dariyarsa yanda ya kamata daga Oum sai ƴan uwansa, musamman Fawzan ma da suke kamar wasu friends ba brothers kawai ba. Dan shi Fawzan akwai barkwanci kamar Abah, saɓanin babban yaya da kusan halinsa ɗaya da AA ɗin.         “Oum Please ki bari haka zanyi amai”. AA yay maganar a hankali yana kwantar da kansa a kafaɗar Oum ɗin cike da shagwaɓa. Murmushi itama tayi da kai hannu ta shafa kwantaccen gashin kumatunsa dake luf-luf duk da yau ko gyara bai samu ba.      “To shike nan an barsa haka, ai kamayi ƙoƙari, kaida in baka da lafiya abinci ya zama maƙiyinka duk sonka da shi. Yanzu sai mi kake buƙata?”.       Cikin lumshe idanu da sake maida muryarsa can ƙasa ya ce, “Barci”.    “To Alhamdullah karɓa wannan ruwan addu'an kasha, Mamy ce tayo maka”.     Ɗan jim yay yana kallon kofin, sai kuma ya ɗauke kansa da faɗin, “Oum ga naki ma ban shanye ba. Ki bari saina gama da shi”.       “No naƙi wayon, shima kasha ai ba'asan inda za'a dace ba”.     Fuska yaso ɓatawa amma dai ya amsa yasa kofin a baki, bayan yayi bismillah ya shanye yana miƙa mata kofin. “Yauwa ko kaifa ɗan albarka. Shike nan kwanta abinka ka huta nima bara naje na idan abinda ya rage kafin ka tashi na nema maka lunch”.     Kansa kawai ya gyaɗa mata yana zamewa a gently ya kwanta. Dai-dai tana tattara kwanikan matar babban yaya mai suna Saheeba na tayata. Knocking akai tare da sallama, Oum ta amsa tana bada izinin shigowa dan su duka sun gane mai muryar. RK ne ya shigo cikin takunsa na nutsuwa, suna haɗa ido da AA ya saki murmushi cikin tsokana ya furta, “Ayya my son ashe an kusa a gangara”.     Harararsa AA ɗin yay yana ɗauke idanunsa a kansa. Yayinda Oum ke dariya Saheeba na tayata. Sai da ya kai zaune a bakin gadon ya gaida Oum, Saheeba ta gaisheshi da tambayarsa aiki ya amsa mata da kulawa da tambayarta ina yara. Amsa ta bashi da cewar suna Kano basu dawo ba sai gobe da sassafe zasu taho da mamanta. Ya jinjina mata kai kawai yana maida hankalinsa ga AA.          “Sorry my dear Son ai ban san abun haka ya kasance ba, sai ɗazun Fawzan ke sanar min ashe jiya ina ƙoƙarin fita ana kirana na dubaka. ALLAH ya ƙara sauƙi yasa ya zama kaffara”.       Batare da AA ya buɗe idanunsa ba ya jinjina masa kai kawai. Dai-dai nan Oum ke faɗin, “Ai na kira wayanka da dare ma bayan ya samu barci switch off, ALLAH yasa dai lafiya dan fitan naka a jiya duk sai da ya dame mu”.           “Wlhy tashin hankali yasa har cajin wayar ya kare ban kula ba Aunty, dama saura kaɗan sanda nazo nan jiya. Ƴarki ce babu lafiya sukai kirana gata an kawota asibiti, shine fa na tafi hankali tashe kin san ciwon nata nada haɗari”.      A rikice Oum ta ce, “Wai kana nufin Maanal?”.     Da wani irin mugun sauri AA ya buɗe idanunsa a karo na farko tun shigowar RK ɗin. Idanunsa masu kaifi da masifar haske kamar an watsa madara duk da halin ciwo da yake a ciki ya zubama bakin RK dake faɗin, “Yes ita Aunty, wai daga wajen aiki ta koma kawai ta yanke jiki ta faɗi”.         “Innalillahi wa'inna ilaihiraji'un yaya jikin nata?”. Oum ta faɗa tana kallon AA, suna haɗa ido yay wani saurin lumshe nashi ya juya musu baya.      “Da sauƙi Alhmdllh, dan yanzu haka ma na barta tana barci. Shiyyasa nace bara nazo naga Autan ki shima”.     Addu'a sosai Oum take ma Maanal, yayinda Saheeba ke amsawa zuciyarta na kai kawo da maimaita sunan Maanal ɗin. Can dai taga zata gaza ta tattare kayan data kwashe tana faɗin, “Oum bari naje dasu a wanke, ki huta zan masa lunch ɗin kawai”.      Kai Oum ta gyaɗa mata da sanya mata albarka. Daga haka ta fice da ɗan saurin da su Oum ɗin sam basu lura ba. Kai tsaye sashen Mamy ta nufa, shima dai komai ya haɗu ga wani ƙamshi na musamman na tashi, tana a falonta na biyu zaune da waya a hannunta alamar magana ta gama yi. Shigowar surukar tasu kuma ɗiya a wajenta dan Saheeba ƴar yayarta ce uwa ɗaya uba ɗaya, zama a iya cewa itace ta haɗa aurenta da Fadeel ɗin. Ɗan ɗagowa tai ta dubeta sai kuma ta maida ga wayar tata tana faɗin, “Saheeba lafiya kuwa?”.         Zama Saheeban tai kusa da ita gab fuskarta na nuna matuƙar ruɗani. “Mamy inafa lafiya. Kin san ina can wajen Yaya Ajwaad kamar yanda kikace naje na zauna komai ayi a gabana, sai ga ƙaninta yazo shine naji wata magana data ban mamaki.....” tsaf ta zayyane mata duka abinda aka tattauna a sashen AA ɗin. Cikin matuƙar mamaki Mamy ta sake maimaita sunan. “Maanal kuma Saheeba?”.       “Tabbas Mamy sunan nan naji, duk da nasan akwai Maanal da yawa a duniya zuciyata ta kasa yarda ba waccan yarinyar bace da Yaya Ajwaad ke ƙula fuci. Kin dai san makirci da munafuncin matar nan, musamman idan kika duba ƙaninta ne yazo da labarin da mai sunan”.      Wani ƙayataccen murmushi Mamy ta saki tare da gyara zamanta na ƙasaita. “Lallai lokaci yayi ashe, lokaci yayi da za'ai fito-na-fito na haƙiƙa tsakanina da Fateema akan ƳAƳANA. Saheeba! Ki ajiye wannan batun zamuyisa daga baya, amma ki tabbatar kin bibiyeta idan har zataje asibiti duba yarinyar kuje tare. Yanzu haka Abdull ne yay kirana zasuzo da matarsa da wata yarinya wai budurwar Ajwaad ɗin”.      Wani mugun faɗuwa gaban Saheeba yayi, har sai da ta waro idanunta waje sosai sannan ta furta, “Budurwar Ajwaad Mamy? Ajwaad ke da budurwa kuma?”.       “To nima abin dai ya ban mamaki gaskiya. Amma dai mu jirasu suzo ɗin. Kisa ai abinci daga ɓangarenki dan bana son ƴar tsirkun ta fahimci komai kin santa da bin ƙwaf. Yaya yasha ruwan rubutun?”.      Da ƙyar Saheeba da gaba ɗaya take a birkice ta amsa mata da, “Eh ya sha amma da ƙyar, dan sai da taita lallaɓashi wai shi nata kawai zai sha”.     Ƙwafa Mamy tayi ranta na ƙuna, sai dai batace komai ba akan haka. Itama Saheeban saita miƙe dan zuciyarta gaba ɗaya a ƙuntace take. Da haɗa hanya ta isa sashenta, kai tsaye bedroom ta afka tana rarumar wayarta dake a saman mirror. Bata ko damu da tarin miss calls data samu ba ta shiga laluben layin mahaifiyarta. Bugu biyu kuwa aka ɗaga. Ko gaisheta batai ba ta ce, “Mama akwai matsala fa, dole ki baro Kano a yau ɗin nan gaskiya. Sannan Nuratu ta taho Kanon ne?”.         “Ke lafiya kuwa kike min maganganu a gwame? Mike faruwa ko yake shirin faruwa?”.     “Abubuwane da yawa Mama, amma yanzu ina son sanin ina Nuratu take?”.        “Nuratu tana Keffi kema kin san shiyyasa batazo bikin nan na Kano ba, zasuyi bikin birthday ɗin ƙawarta”.     “Mtsoww wlhy wannan yarinyar gantalinta ya fara isata, tana can wataran zata ji an ɗaurama Ajwaad aure tunda ita bazata nutsu ba”.          “Aure?”.     “Sosai ma kuwa Mama. Tunda ita wawuyar yarinya ce. Ita tasan wlhy badan faɗi tashin da muke ni da ke akan batuntaba da tuni Mamy ta canjata da wata. Yanzu dai ki kirata idan taga da hali ta maza ta dawo Abuja dan Ajwaad baida lafiya tun jiya ko aiki bai fita ba yau. Ga Abdull nan kuma shida ƴar iskar matarsa ɗin nan mara kunya daya kawoma mutane cikin family bisa ra'ayinsa shi kaɗai wai zasuzo da wata budurwar Ajwaad ɗin ce, kin san kuma Mamy ita kaɗai ke goyon bayan auren nan nasa dama. Ga kuma wani batun a gefe da bamu gama tabbatar da shi ba”.      A matuƙar rikice Maman nata ta ce, “Na shiga uku ni Gambo, wane kuma batu ne haka Saheeba?”.    “Humm Mama ke dai kawai sai kin dawo”.          “Dawowa kam ta zama dole dan yanzun nan zan baro kano, yaranki ma sa biyo jirgi gobe dan ni ko ban samu jirgin ba zan biyo mota kawai”.........✍️     Humm, tofa🤔🥱🤨😌 ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖4️⃣6️⃣ ______________ .......Tunda Saheeba ta fita a sashen taketa faman kai-kawo. Wani irin watsal-watsal zuciyarta ke faman yimata. Tun tana jin zata iya daurewa harta kasa. Fitowa tai a sashen nata ta nufi sashen AA. Yanda ta shigo fuuu sai kuma tai laƙwas ganin doctor da RK da Oum a ɗakin. A take ta gyara yanayinta ta ƙawata fuskarta da murmushi. Sai kuma ta kalla Oum tana faɗin, “Na sake zuwa ne kar'a sakani a black list”.      Dariya Oum tayi itama, zuciyarta fes ta ce, “Kamar kin san na fara ayyana haka a raina, tun shigowar safe ban sake ganinki duba mu ba”.       “To ALLAH ya baku haƙuri na ɗan tsaya kan masu aikin nan ne kin sansu da aikin algus idan basu gadama ba. Yaya jikin naku?”.        Kallon AA Oum tayi da faɗin, “A jiki Alhamdullah”.      “To ALLAH ya ƙara afuwa”. Mamyn ta faɗa tana kallon AA itama da yay kamar bai ji shigowarta ba. Sai lokacin ya ɗan ɗago idonsa ya dubeta, da Muryar nan tasa ƙasa-ƙasa ya ce, “Ina kwana”.         Wani irin motsawa zuciyar ta tai na takaici, amma sai ta danne ta sakar masa murmushi da amsawa da, “Lafiya Lau, yaya jikin naka?”.       A hankali ya amsa da, “Alhamdullah”. Gaisheta RK yayi shima da girmamawa. Itama ta amsa da kulawa tana tsokanarsa wai shi da ɗan nasa ba'a san wazai riga wani aure ba. Ƴar dariya RK yay da kallon AA, sai kuma ya bata amsa da, “Karki damu Aunty muna tafe, dan gara ni na farayi kafin a fara kirana Baba na zaure”.       “Ato ya kamata dai, dan zaman ya isa haka Uncle tururu ɗansa tuzuru”.    Dariya kawai RK yake cike da jin nauyi, dan yana matuƙar girmama matar da ƙaunarta kamar yanda yasan ita da ƴar uwarsa suna ƙaunar juna. Dan in ba faɗa maka akai ba bazaka taɓa ɗauka kishiyoyi bane. Oum ma dai dariya take kawai doctor na tayata, gogan kuwa yama lumshe idanunsa dan ruwa doctor ya sake saka masa saboda sake samun ƙarfin jikinsa. Sallama tai musu ta juya ta fita tana sanarma Oum zataje taɗan kwanta ta huta. Oum tai mata godiya...       Bayan fitarta Doctor dake kallon AA ya ce, “Ranka ya daɗe BP naka har yanzu yana a sama sosai, dole zan ƙara maka allurar nan ka samu barci”.            A daƙile AA ya ce, “Bana buƙata doctor”.       “Ai dama ba dole sai kana buƙata ba ranka ya daɗe, jikinka ne ke buƙata. Dan rashin saukar tashi matsalane gaskiya”.     Baki ya sake buɗewa a ƙufile zaiyi magana Oum ta katseshi. “Kaga doctor yimasa kaji, kai kuma idan ka sake magana sai na cire maka kunne ɗaya”. Ta ƙare maganar tana hararar AA, baki ya tura gaba kamar wani yaro, dan shi in har yana gaban Oum jinsa yake ɗan yaronsa har yanzu. Dariya RK yake yi, tare da faɗin, “Taɓaran banza”. Hararar shi AA ɗin yayi, shima sai ya rama. Haka suke kamar wasu tom and jarry, sam AA baya Uncle da RK, dan shi sunansa ma yake kira sai idan yaso yake cema Uncle ɗin. To sun tashi ne tamkar friends, babu wani tazaran haihuwa a tsakaninsu sosai. Sai dai RK ne babba, amma idan yace ya girmesa to yanzu zasu hau sama kuwa su faɗo dan shi AA ya tsani RK yace ya girmesa. A ganinsa girman da bai wuce sati Uku ba har wani girma ne. Hanyar ƙofa RK ya nufa yana dariyarsa da faɗin, “Aunty kinga nayi nan tunda ɗan naki ya samu lafiya har yana min rashin kunya ina matsayin babansa. Na tafi wajen aiki inda ake son ganina bye”.       Cikin murmushi Oum ta ce, “Rafeeq kadai tasa min yaro dan kaga ba magana zai maka ba. Zuwa anjima in sha ALLAHU zan kiraka na shigo ba duba Auta ta itama”.          “To ALLAH ya kaimu muna zuba idon ganinki, idan kuma ɗan shagwaɓarki bai bari ba mun yafe zan kira a waya sai ku gaisa. Dan itama ina ƙyautata zaton zuwa anjima za'a sallameta, yau tunda safe take mitar ita a sallametan”.     Dariya kawai Oum tayi tana mai girgiza kai, tasan Maanal da ƙiriniyarta, damma taga yanzu kura tayi lafiya kamar ba Maanal ɗin ba..... ______________★        Jikin Maanal ma Alhamdullah, dan tama hana Shahidah sanarma su Ammie. Dama kuma Shahidahn ma batai niyyar sanarma Ammie ɗin ba kamar yanda mijinta ya fargar da ita cewar tunda da sauki karsu tayar musu da hankali.       Abinci Maanal ɗin keci RK ya shigo, sai da ya gaisa da su Shahidah kafin ya maida hankalinsa a kanta. Cikin tsokana ya ce, “Madam ba tayi”. Ai baima gama rufe baki ba ta miƙa masa plate ɗin. Mi mijin Shahidah zasuyi ba dariya ba. Uncle Sadeeq ya ce, “Doctor kai baka san dama neman kai take da abincin ba, an turketane tana ci dan dole”.      Fuskar RK da murmushi ya ce, “Ai naga alama Babban yaya. Irin wannan bani da sauri haka. Ni dai dan ALLAH kici abinci ki ɗan ƙara kumari”.     Hararar RK ɗin tayi, sai kuma ta tura baki gaba cike da shagwaɓa. Zama Shahidah tai kusa da ita cikin lallashi ta ce, “Kinga ƙyalesu Auta kinji, bari ma na baki da kaina”. Haka ta amsa ta cigaba da bata cike da kulawa da so. Sai RK ya samu kansa da shagala a kallonsu. Shi kaɗai yasan yanda yake jim ƙaunar yarinyar nan a ransa. Komai tayi birgesa yake. Yasan hakan daga ALLAH ne. Dan yana jin feeling akanta irin wanda zai rantse bai gaɓa ji ga sauran ƴamata ba. Kodan bai taɓa yin budurwa bane oho. Sam shi ada matsoracin mata ne, babu ruwansa da harkarsu, badan bai cika namiji bane, kawai dai karatunsa na likitanci daya ƙwallafa rai da aikin nan sun kwashe mafi yawan lokacinsa na rayuwa. Idan ka cire ibada da yake matuƙar bata hakkinta. Shifa ko irin ƴar soyayyar ƙuruciyar nan baiyi ba. Kuma a turai aka haifesa anan ya girma yay dukkanin karatittukansa. Gaba ɗaya bai wuce shekara huɗu da dawowa Nigeria gaba ɗaya ba. Amma ALLAH bai ɗora masa damuwa da mata ba. Shiyyasa shi da kansa yake sake yarda da son Maanal yake bana wasa ba. Hakama ƴan uwansa kowa murna yake da batun Maanal dan sun tabbatar da gaske son nata yake tunda shidai ba'a taba kamashi da case na mace ba.        Sosai Maanal ta matsa ita sai an sallameta ta warke. Amma Dr Ranjet ya dinga lallaɓata akan tayi haƙuri zuwa gobe. Dole badan taso ba ta haƙuran... ______________★        Kusan ƙarfe uku na yamma Abdul da amaryarsa Yaseerah sai Huznah suka iso katafaren family house ɗin na Ambassador Aliyu Darma. Dan a gidan su Yaseerah Huznah ta kwana. Daga Mawaad Company can ta wuce ranta a ɓace tana hawayen abinda AA ya mata. Shine Yaseerah taita lallashinta da tabbatar mata a yau zasuzo Darma's house. Hakan kuwa akai, tun a daren take lallaɓa Abdull akan suje har ya amice. Sai kuma gasu sun iso yanzu.         Sun sami tarba daga Mamy, ƙyaƙyƙyawar mace ƴar ƙwalisa data gama tafiya da zuciyar Huznah. Kai tun kafin ma Mamyn Darma's house ya gama tafiya da Huznah. Ta gama sallamawa da jinjina kuɗi irin na gidan su AA ɗin. Ta kuma yarda kuɗin ma hawa-hawane. Tasan mahaifinta nada kuɗi, tunda suka tashi suke jin ana sakashi a jerin masu kuɗin jihar Kaduna, kai bama Kaduna kawai ba a dattawan arewa masu kuɗi za'a iya sako mahaifinsu. Sai dai kuma Baba ma fa da babansa. Ta shaida hakan a yau kuma ta aminta.          Yanda take ta faman sinne kai da kaffa-kaffa da komai sai ya baka mamaki, ko gaishe da Mamy sai da ta duƙa har ƙasa. Sai Mamyn ce dake binta da kallo ta kamata ta tadata ta zaunar a kujera. Still dai Huznah ta kasa kallonta. Ita ma dai Yaseerah bata da wata sakewa, dan dangin mijin nata ƙalilan ke sonta, duk da dai ita Mamyn na sonta. Kawai dai dan Abdull ɗin ya dage sai ita ne yasa suka ƙyalesa. Hakan yasa su biyun duk suka nutsu, sai Mamy da Abdull ne ke hira. A haka Saheeba ta shigo suka gaisa tare da saka masu aikinta jere abincin da Mamyn tace tayo a sashenta na tarbar baƙin. Saheeba dai ta danne sun gaisa da su Yaseerah, sai dai hankalinta nakan duk motsin Huznah ne. Bisa umarnin Mamy sukaje d/table, anan ɗin ma dai Huznah bata sake ba ita adole mai kunya. Ita dai Mamy sai kallonta take tana murmushi. Dan haka kawai kuma sai taji son yarinyar a ranta saboda kunyarta da nutsuwa gefe ga ta ƙyaƙyƙyawa. Dan duk ƙyawun Nuratu da da take kallo dai-dai da AA sai taga ai Huznah ta takata ta shanye. Dama dai a ƴan kwanakin nan wasu abubuwa na Nuratu sunsa ta fara shakkar haɗa aurenta da AA ɗin, amma bata fito ta faɗama kowa ba. To tana ganin yarinyar nan itace zata zama raba gardama. Dan kodai ya aurenta ita kaɗai kota sakashi ya haɗa da Nuratun su biyu a masa auren gata auren huce takaice auren da tasan zai baƙanta ran Oum fiye da auren su Fawzan.       Bayan sun kammala cin abincin ta umarcesu da suzo su duba AA. Abdull ne ya tambayeta “Baida lafiya ne Uncle AA ɗin Grandma?” (dan haka yake kiranta kasancewarta ƙanwar kakarsa uwa ɗaya uba ɗaya). Amsa ta bashi da “Eh son, yau ko aiki ma bai fita ba yana kwance”.     Gaba ɗaya ji Huznah tayi hankalinta ya tashi, dan har fuskarta ta nuna hakan ɓaro-ɓaro, amma dai ta daure batai magana ba. Mamy dai na lure da ita. Hakama Saheeba dake jin kamar ta shaƙo Huznah ɗin. Sai faman tsine mata take a zuciya. Sashen Oum suka fara zuwa, Oum ta tarbesu da kulawa kamar yanda ta saba ma ƴan uwan Mamyn, dan haka cikin girmamawa Abdull ya gaisheta, hakama Yaseerah da Huznah data kusa zubewa a tsaye da mamaki tana satar kallon Oum. Tabbas bata manceta ba, itace ta gani a gidan Shahidah tare da namiji mai kama da AA ɗinta. Rashin sanin alaƙarsu da su Maanal ɗin kuma yasa har yanzu bata sanarma mahaifiyarta ba, gefe kuma ta ɗan shiga ruɗani, shin tsakanin Mamy ɗin da matar wacece mahaifiyar AA ɗin? A dai kamanni yafi tsananin kama da Oum, shin yaya take ne?. Da ƙyar ta iya dannewa dai suka baro sashen bayan Oum ta cika su da abin arziƙi, sai dai fa da alama ita Oum bata gane Huznah ba. Koda yake a gidan Shahidah da suka haɗu ita bawani ta maida hankali a kanta bane lokacin.       Daga nan sashen AA suka nufa kamar yanda Mamy ta sanarma Oum cewar zata kaisu su dubashi. Wani irin lumshe idanu Huznah tai lokacin da suka shigo main falo ɗin sashen da wani irin ƙamshi mai daɗi ke tashi. Suna isowa falo na biyu taji zuciyarta na wani kalar tsaitsinkewa saboda haɗuwarsa. Falo kamar bana tuzuru mara mata ba. Anan Abdul ya dogare, fuskarsa da murmushi ya ce, “Grandma bari mu dakata anan a masa magana idan zai iya sakkowa mu gaisa. In ba hakaba bara na haura ni kaɗai sai na dubashi kin san Uncle baya son wargi bakamar Uncle Fawzan ba”.      Murmushi Mamy tayi, dan itama dai tasan maganar Abdull ɗin gaskiya ne. Dan in har ta hau da su Yaseerah sai yaji haushi. Su Saheeba ma dake matsayin matan yayyansa kuma ƴan uwansa na ƙut sosai yake tujara idan suka shiga masa koda falon sama ne balle. Yanzu haka ko ɗazun tana jin yanama Fadeel mitan shi matansu su daina shigo masa har bedroom.           Mamy ce ta haura saman da kanta. Dai-dai AA daya farka daga barcin da Doctor ya sakashi dole ya fito wanka. Knocking ƙofar da akai ne ya sashi yamutsa fuska cikin yanayin mara lafiya, muryar shi ƙasa-ƙasa da kamar baya son buɗe baki ya furta, “Ina zuwa”. Daga haka ya ajiye towel ɗin hannunsa da yake goge sumarsa da ruwa ya jiƙa saboda ciwon da kansa ke masa har yanzu kaɗan-kaɗan ya sakarma kansa ruwan. Boxer ya saka tare da cire bathrobe ɗin ya saka jallabiya sannan ya nufi ƙofar dan duk zatonsa Oum ce. A hankali ya buɗe ƙofar, cikin ɗan shagwaɓa ya furta, “Oum sai yanzu, ni nayi fush.......”     Kasa ƙarasawa yay saboda yin tozali da Mamy ba Oum ba. Ta koyi kicin-kicin da fuska tana masa wani irin kallo, kansa ya duƙar ƙasa yana mai haɗiye busashen yawu ya furta, “Am sorry, nazata Oum ce”.         “Humm” kawai ta furta batare data kula zancensa ba ta juya tana faɗin, “Kasameni a ƙasa baƙi zasu gaisheka”.     Kallo ya bita da shi, harta fara taka stairs case ɗin. Kaɗan ya lumshe idanunsa ya buɗe, sai kuma ya ɗan furzar da iska ya koma cikin ɗakin..........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖4️⃣7️⃣ ______________ ........Fin mintuna goma bayan sakkowar Mamy sannan ya sakko. Duk da sanye yake da slippers masu taushi hakan bai hana bayyanar tahowarsa ba. Ga wani mayataccen ƙamshin turarensa mai ratsa zuciya na rige-rigen shiga hancinansu tun kan su fara ganinsa.        Ai tuni zuciyar Huznah ta fara gudu a ƙirjinta, yayinda take satar kallon hanyar ƙofar upstairs ɗin ta gefen ido. Bayan wasu ƴan sakanni ƙofar ta buɗe slowly, ya bayyana garesu. Sanye yake da wando da riga duk baƙaƙe masu kamar kayan sanyin nan dan harda hula a bayan rigar, sai dai bai saka ba ya saketa a dokin wuyansa ta kwanta. Sam babu wasa ko alamarsa a saman fuskarsa datai wani irin fayau ya ƙara haske. AA ba fari bane, amma yanada hasken fata da ko'a cikin baƙaƙen irin baƙin nan ne mai matuƙar ƙyau da shining ga wani glowing da yake tamkar jinin mutanen ƙasar Labanon. Yanada hanci dayay dai-dai da tsarin tsaka-tsakin fuskarsa daba doguwa can ba, ba kuma faffaɗa ba. Ga shi da cikar gashin gira dana ido da ko wata macen bazata nuna masa eyelashes ba. Kwantaccen gashin sajensa daya zagaye har matsaikaitan lips ɗinsa pink shine yafi komai sake ƙawatashi. Kamar koda yaushe idanunsa manne da eyeglasses ɗinsa fari ƙal da kamar ba'a amfani da shi na ƙara ƙarfin gani. Yanda oily idanun suka sake wani fita tar-tar kamar an watsa ruwan madara sabon tatsa dole kaji wani iri idan ya kalleka da su. Gashi dogo masha ALLAH.       Tunda ya gama sakkowa kallon kowa baiyi a cikinsu ba. Sai takowa da yay a hankali zuwa cikin falon sosai. A kujerar farko dake bangon daya fito ya zauna kawai, sai a lokacin ya ɗan dubi Abdull dake gaishesa cike da girmamawa. Cikin yanayin ɗan zuba masa ido batare daya amsa gaisuwar ba ya ce, “Ango ne a gidan namu”.     Murmushi Abdull ya saki mai ƙayatarwa tare da duƙar da kansa yana sosa ƙeya. Cike da jin nauyi ya sake gaida AA ɗin. AA ya girmi Abdull sosai, dan shi a yanzu bazai wuce 26+ ba gaskiya. Kawai dai an masa auren gata ne. Sai yanzu AA ɗin ya amsashi da tambayarsa iyalin. Sake duƙar da kai Abdull yay da faɗin, “Ai Uncle gata nan ma tare mukazo dubaka”.      Batare da AA ya kalli inda Abdull ɗin ya nuna ba ya furta, “Oh Masha ALLAH, Thanks”.      Gaisheshi Yaseerah ta shiga yi da tambayarsa yaya jiki, ya amsa mata a taƙaice still dai bai kalleta ba. Dan kowa yasan wannan kam ba ɗabi'arsa bace kallon mata ko'a sanda yake a ganiyar samartakar balaga balle yanzu da wasu dalilai suka saka shi sake kame kansa ga komai, dan AA akwai tsantsar kame girma, ko wanda suka girmesa sukanga ya cika musu guri balle wanda ya girma. Sai a lokacin Huznah data kasa numfashi mai ƙarfi ta fara gaisheshi itama, AA akwai iya haddace muryan mutane da riƙeta idan yaso, dan haka ya ɗan kalla sashen da suke a karo na farko, a mamakinsa kuwa wadda yay tsammanin ce. Wato budurwar yarinyar nan mai shegen naci da iyayi data takurama rayuwarsa a kwanakin nan. Ƙoƙarin janyewa yake suka haɗa ido da Mamy data kafesa da nata idanun. Sai kawai ya kautar da kan nasa cike da basarwa. Haka kawai Mamy ta saki murmushi. Dan ta tabbatar da abinda take son tabbatarwar, da gaske AA ɗin yasan Huznah ba ƙarya sukai masa ba. Saheeba ma dai sai faman raba idanu take a tsakanin Mamy da AA da Huznah. Itama kuma taga reaction ɗin AA ɗin a sanda Huznah tayi magana. Tuni hankalinta ya ƙara tashi, wani kalar tsanar Huznah na ratsa zuciyarta.       AA ne daya miƙe ya katsema kowa tunaninsa. Dan hankalinsa kwance ya nufi ƙofa, sai da ya kama handle ɗin batare da ya juyo ba ya furta, “Abdull thanks you ALLAH ya baku zaman lafiya”. Daga haka ya shige tare da maido ƙofar ya rufe. Kusan lokaci ɗaya Yaseerah da Huznah suka saki ajiyar zuciya. Dan ita kanta Yaseerah ɗin sai yau da take ganin AA ɗin da ƙyau. Rayawa take a ranta (Ashe haka guy ɗin ya haɗu, ya subahannallah mutum kamar shi ya zana kansa da ƙyawu. Ga aji ga kwarjini. Wannan shine irin mijin da take fatanma kanta, dan Abdull yana da ɗan irin qualities ɗin kaɗan shiyyasa ta aminta da shi. Ashe ga inda ake mazan nan na gaskiya. Ya ALLAH gaba ɗaya an wargaza mata dukkan lissafinta. Sai a yanzu ta sake tantance abinda ya haukatar da Huznah ashe). A ɓangaren Huznah ma sambatu kawai take zubawa a zuciya. Wani irin ƙyau da kwarjini AA ɗin ya sake mata. ALLAH badan kar ace tayi ƙarya ba daya kalleta da wannan idanun nasa mai kamar an watsa madara da oil a ciki kaɗan ya rage ta suma. Kai dole dole ne ma ta mallaki mutumin nan, idan ba hakaba zata iya rasa ranta.      Da ire-iren wannan tunanin suka koma sashen Mamy, kasancewar lokacin sallar Asr yayi Abdull ya wuce massallaci. Su kuma Mamy ta haura dasu sama a ɗaya daga cikin bedrooms ɗin ta tace suyi salla. Ita kuma ta nufi nata..... ____________★         Senator Bukar dai yaje Kebbi cikin garin Giro, bai kuma sha wahalar samun ainahin gidan kakannin su Maanal ba. Dan gidane sananne a cikin garin. Alhamdullah kuma ya samu tarba irin wadda bai mayi zato ba. Dan cike da farin ciki suka dawo garin Abuja dama jirgi yabi shi da Rabilu da Oler. Yanda yake ta famar washe baki da zumuɗi ya saka uwargidansa a tashin hankali, dan ta tabbatar ya samo abinda yake so. Batace da shi komai ba yay shiri ya wuce gidan matarsa ta biyu dan yau itace da shi...        Itama dai a yau ya zazzage mata batun ƙarin aurensa, a ɓangarenta mace ce mara haƙuri da iya shanye abu, dan haka tun a daren sukaci uwar watsi ƙarshe kowa a part ɗinsa yay barci. Dan ya tabbatar mata akan Maanal fa zai iya saita mata hanya ne shi ba damuwarsa bane. Dole taja bakinta ta kulle dan tasan kaɗan daga abinda zai iya aikatawar kuwa.....      _Ikon ALLAH miya faru a Giro🥱 to?._ _____________★        Yanayin da take jin jikinta Alhmdllh yasa ta ce Shahidah taje gida kawai ta huta yau zata kwana da nurse. Da har Shahidah ɗin taƙi Dr Ranjet yace karta damu taje ɗin. Dama asibitin bawai suna barin masu jiyya bane ba ai kawai dai sune oga ke bari. Zuwa yanzu Shahidah ta fahimci asibitin nan mallakin RK ne. Duk da yanata dojewa bai son su sani. Dan haka koda Dr Ranjet ya ce ogan ta fahimci RK ɗin yake nufi.         Mijinta ne yazo ya ɗauketa, basu tafi ba sai da ta tabbatar ta mata duk abinda take buƙata duk da jikin nata Alhmdllh sannan. Bayan tafiyar tasu Maanal ɗin na zaune tana karatun novel ɗin data ɗauka na AA ranar a office ɗinsa, dan yau ta matsama Shahidah ta kawo mata shi asibitin tare da glass ɗinta. Sosai take zumuɗin karatun book ɗin saboda labarinsa da aka bata. Tayi matuƙar zurfi a karatun dan tana jin daɗinsa, bata damu da shigewar lokaci ba dan kusan 11 ma da rabi. Sai can ƙasan zuciyarta dake ɗan kawo mata tunanin ina RK, rabonta da shi tun safe da ya shigo ya dubata a gaggauce ya fice. Tana son tambaya tana tsoron kar Didi tai mata wata fassara daban dan haka taja bakinta tayi shiru. Sai dai lokaci-lokaci yana zuwa mata a rai.       Kaɗan-kaɗan wani irin daddaɗan ƙamshin turare ke shigo mata hanci, tun tana fuskewa da cigaba da karatunta har dai yanda turaren ke sake ƙarfi a ɗakin ya addabeta. Cikin nutsuwarta da rashin rawar kai ta ɗago idanunta kaɗan tana bin ɗakin da kallo, dai-dai saukarsu inda ƙofa take ƙirjinta yay wani irin motsawa alamar zuciyarta tayi zallo. Sosai ta zuba masa ido tana masa kallo irin na  mamaki ko ruɗani zamuce oho. Sai dai fuskarta a dake babu alamar wani shock a kanta. Sai ma janye idanun tai a slowly ta maida ga littafin kamar bataga komai ba.          Gently shima ya lumshe nasa oily idanun da ke a ɗan kumbure kaɗan da kuma ɗan sirkin ja a cikinsu dan har yanzu basu komai dai-dai ba saboda ciwon kai yaƙi barinsa. Sai dai da ɗan haskensu fiye da jiya da yake a halin ciwo sosai. Sake buɗesu yay a kanta yana mata wani irin kallo mai wahalar fassara. Fin mintuna biyar suna a haka baka jin komai a ɗakin sai sanyin ac da aka saka mata kaɗan daya gauraya da ƙamshin mayataccen turarensa mai kashe garkuwar jiki. Gaba ɗaya kallon ya gundiri Maanal, dan jinsa take har cikin ɓargon jikinta da magudanan jini. Tuni ta daina karatun kallon rubutun kawai take, sai dai fuskarta ta sake tsukewa.           A cike da ƙasaita ya miƙe daga jinginar da yay a jikin ƙofar hannayensa duka zube cikin aljihun farin jeans ɗin sa, daga sama ma baƙar rigace mai hi neck data ɗame masa murɗaɗɗan jikinsa, sai dai ya kawo jacket mai ƙyau baƙa da adon fari kaɗan a jikinta ya ɗaura. Kasancewar zip ɗin gabanta a buɗe yake har ƙasa ne ya bayyana rigar cikin da faffaɗan ƙirjinsa zuwa lafaffen cikinsa. Yanda yake takowa takalman ƙafarsa masu ƙyau da ɗaukar hankali na bada ƙara haka zuciyarta ke motsawa a ƙirjinta da ƙarfi. Cike da izza ya tura kujerar gaban gadon gab da gadon sosai da ƙafa, kafin ya matsa gab da gadon har Maanal najin tamkar zai faɗo mata akai sannan ya kai zaune. Yanda ya ɗan rankwafo a kanta sanda zai kai zaunen yasa hucin numfashinsa dakar fuskarta, yayinda ƙamshinsa ya gama mamaye illahirin iskar da take shaƙa. Dole ta ambaci sunan ALLAH a zuciyarta.      Anan ɗin ma zaman ƙasaitar yayi, dan ya wani harɗe ƙafafu ɗaya kan ɗaya tare da kwantar da bayansa a jikin kujerar hannayensa duk biyu dafe da hannuwan kujerar. A har yanzu ɗin ma idanun nasa na'a kanta ne sai faman lumshesu yake da buɗewa daga cikin fari tas ɗin gilashinsa dake sake ƙawata masa fuska. Rumtse idanu Maanal tayi tana mai danne dukkan abinda ke yunƙuro mata. Batare data sake ko kallon sashen da yake ba a kausashe, a kuma tsiwace ta furta, “What are you looking for here?”.         Maimakon bata amsar data buƙata sai kawai ya zuba ma lips ɗinta idanunsa har adams apple ɗinsa na ɗan motsawa a maƙoshinsa. Wani irin takaici ne ya sake ratsa Maanal. Tai wani irin juyowa da rinannun idanunta da suka juye lokaci guda ta saukesu a kansa. Slowly shima yaja nashi dake kallon lips ɗinta ya daidaitasu a cikin natan. Kallon cikin tsakkiyar idanu sukema juna. A hankali a hankali na Maanal suka fara ƙyalli alamar taruwar hawaye. Wani ɗan iskan murmushin gefen baki ya saki yana sassauta girman idanunsa dake cikin nata. Tamkar wanda akama dole ya motsa lips da Muryar nan nasa can ƙasa-ƙasa kamar abin dole ya furta, “Because you need me”.        “Never! Har abada kai baka cikin abinda rayuwata take buƙata Ajwaad”.        Wani ɗan killer Smile ya saki yana mai janye idanunsa gefe, fin sakan biyar sannan ya sake juyo da idanun nasa a kanta. “Really! You don't need me in your life?”.      “Kana tantamar hakan ne?”.   Ta faɗa a zafafe. “Sosai ma kuwa? Inda har baƙya buƙatata in you life kuma da baki cigaba da ajiye wannan ba”. Ya ƙare maganar yana buɗe tafin hannunsa wani sliver agogo ya bayyana. Kallon agogon take zuciyarta na bugawa da ƙarfi a cikin ƙirjinta, agogonta ne fa, agogon da ta saka a randa zasuje Zaria ita da Ammie da Yaya Yazeed da Amrah. Tabbas tasan ta ciresa a hannunta, daga haka bata sake tuna ina yake ba. Kai hankalinta ma sam bai kai garesa ba sakamakon haɗuwa da RK da tai acan ya harmutso ta.....       “Hyy”.    Ya katse mata tunani cike da son tunzurata. Harararsa kuwa tayi ta ɗauke kanta gefe batare da ta ce komai ba. Murmushin sake samun nasara ya saki kaɗan yana wani ƙanƙance idanunsa a kanta.           “Wannan pretending ɗin naki ya isa haka. K Bestyn AA ce har yanzu, ko ki yarda ko karki yarda idanunki na nuna hakan ga kowa......”      Wani irin wurgar da littafin hannunta tayi, a bazata kawai ta ganta a gabansa ta dirgo daga gadon. Wani irin lumshe idanu yay ya sake buɗewa sakamakon shigar ƙamshinta mai daɗi cikin hancinsa. So yana matuƙar son traditional perfumes, zai iya cewa ma itace ta koya masa amfani da su ita da Oum..........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖4️⃣8️⃣ ______________ ........Akan ƙyawawan ƙafafunta da ƙumbunan ke a gyare fes-fes suna ƙyalli ya saukesu. Kafin ya tafi da kallonsa har saman baƙin wandon data saka irin mai manne jikin nan, yana gab da gwiwarta rigar asibitin ta bayyana, itace har zuwa sama fara da ɗigo-ɗigon jaa, tsabar neman magana da salon iskanci ya wani sauke a saman ƙirjinta ya kafe wajen da ido tare da ɗan datse lips ɗinsa. Da sauri ta koma saman gadon taja bargo ta lulluɓe jikinta gaba ɗaya tana furta, “ALLAH ya isa wlhy da mun kallon da musulunci ya haramta”.       Murmushi yay mai fidda ɗan sauti sai dai sam haƙwaransa basu bayyana ba. Sai kuma ya taɓe bakinsa cikin halin ko in kula ya furta, “Daga baya kenan. Idan kin manta bari na tuna miki na san komai A to Z tun kan ki zama abin kallo. Ko kin manta wannan hannun ya miki wanka, ya wanke miki pupu, ya share miki majina, ya wanke miki pants, ya wanke miki blood na period. Ya.....”      “That's enough malam. Kuma ka bar ɗakin nan tun kafin na maka ihu wlhy.”       Murmushi ya sake yi yana taɓe baki da wani ɗan ɗage gira. Babu alamar zai ma motsa balle yayi abinda tace ɗin. Saima cikin tsareta da idanunsa da suka kaɗe ga jijiyoyin kansa duk sun sake fitowa. Muryarsa can ƙasa ya ce, “Ke baki gajiya da faɗa? Why are you being stubborn ne?”.       Harara ta balla masa da faɗin, “Anyi faɗan da taurin kan, in baka son a maka ka fita rayuwata mana”. Sai da ya ɗan lumshe idanu ya buɗe akanta. Yanda yake mata wani shegen kallo tamkar idanunsa zasu narke a kanta ya saka tsigar jikinta tashi, kauda kanta tayi gefe da sauri, shi kuma ya ɗan ciza lips ɗinsa yana wani jan numfashi a hankali. “Nima ki fita tawa rayuwan mana. Kinbi duk kin hanani sukuni, kin hanani aure, kin sa duk nabi na tsani yaran mutane babu hujja”. Ai bama tasan sanda ta wara manyan idanunta a kansa ba tana harararsa, rasa abin cewa yasata faɗin, “ALLAH zai saka min sharrin nan da ka min”. Sai kuma ta sake sakkowa a gadon tare da fisgan hijjab ɗin sallarta ta saka. Ƙofa ta nufa fuuu dan gara dai ta bar masa ɗakin kawai sai yaci kansa yasha baƙin ruwa. Sai dai me ƙofar gam alamar saida ya rufe sannan. Ranta ne ya sake ɓaci, har takai hannu zata bubbuga sai kuma ta fasa saboda tunawa a asibiti suke kada ta shiga hakkin sauran majiyata. Dawowa tai inda yake cikin da tsantsar masifa da tsiwa ta balbalesa da masifa.        Yanzu kam gaba ɗaya dauriyarsa ƙwacewa tai, dole ya kai hannu saman kansa dake wani irin sara masa da masifar ƙarfi ya dafe, dama tuni dauriya kawai yake yi, shi kaɗai yasan azabar da kan nan ke masa, dan shi dama a ciwonsa ciwon kai yafi yawa. Sam masifa ta rufema Maanal ido, sai cigaba da zazzaga masa take, “Please Besty my head ki daina min ihu”.       “Anƙi a daina, tunda baka so ka fita mana, waya kawo ka nan ɗin?”.       “Ya ALLAH” ya faɗa da wata sassanyar murya yana kai ɗayan hannun ma ya tallafe kan gaba ɗaya. Dan da gaske ji yake kamar kwalwar ciki zata zazzago.       A karo na farko gaban Maanal ya faɗi, dan yanda ya kira sunan ALLAH ɗin da tallafe kan sai kuma hankalinta ya tashi. A hankali ta fara haɗiye masifar tata tana kallonsa. Yayinda shi kuma ke cigaba da jujuya kansa a cikin hannayensa yana cigaba da kiran sunan ALLAH, sai kuma ya koma faɗin, “Please Besty my head, kaina Besty zai fashe ki riƙe min, dan ALLAH ki riƙe min”.           Ai tsabar yanda jikin Maanal ke rawa batama san takai hannunta saman nashi ba, ta ture ta maye gurbinsa da nata tare da duƙawa a gabansa tana leƙen fuskarsa da faɗin, “Na shiga uku mike damunka? Miya samu kan naka? Ka tashi muje wajen likita na roƙeka”. Sai hawaye sharrr.        Bai iya ya motsa ba, sai hannunta dake a saman kan nasa da sanyinsa ke wani ratsashi ya sake dannewa da nasa da ƙyau. Yayinda ita kuma zafin kan da yanda jijiyoyin ke harbawa ke ratsata. Matuƙar firgici ta shiga, dan tun tana hawaye har kukan nata ya fara fidda sauti. Da ƙyar ya ɗaga idanunsa da suka gama kaɗewa ya kalleta, cikin motsa lips ɗin da ƙyar tare da ɗan jujjuya kai ya ce, “Stop crying, bafa da yawa bane”.             Kukan ta sake fashewa da shi da faɗin, “Hakanne bada yawa ba, kaga yanda idonka yay ja kanka yayi zafi? Nidai ka bari naje na kira maka Rafeeq...” tai maganar tana ƙoƙarin miƙewa da son cire hannunta dake a saman goshinsa. Da sauri ya riƙo ɗayan hannun nata yana jujjuya kai, sai kuma miya tuna ya saki hannun yana faɗin, “Am sorry”. Itama kamar wadda ya fargar sai tai saurin janye ɗayan dake a saman kansan, ta ɗan ja jikinta baya. Murmushi ya ɗan yi, sai kuma ya miƙe still dai hannunsa dafe da kan nasa ya ɗan raɓa ta gefenta ya zauna a gadon jiyyarta yana faɗin, “Help me naɗan kwanta anan ko zai sauka”.         Batace komai ba ta matsa masa, kwanciyar yay rigingine ya lumshe idanunsa hannunsa dafe da kan nasa. Tun tana kallonsa daga tsayen harta kai zaune a kujerar daya tashi dan itama sai taji kawai tana wani irin jin jiri, yayinda baya data shuɗe ke son maimaita mata kanta a zuciyarta. Haka suke ita da shi, da wahala ɗaya ya kwanta ciwo ɗayan bai kwanta ba shima. In ko ba haka ba dukkan hidimar mai ciwo ɗayan ne zai yi. Zata iya cewa fara kaiwar AA ɗin lokacin balaga ne yasa Oum ta fara saka idanu akan al'amuransu, harma takan kasance tare da su batare data barsu keɓewa su biyu kawai ba. Sai dai duk da haka ƙaddara bata barsu ba. (Ƙaddarah!) Zuciyarta ta maimaita kalmar da amsa kuwwa. Rimtse idanunta tayi da masifar ƙarfi sai kuma Zuciyarta ta fara zafi, (Eh tabbas batace ƙaddara kawai ba, harda ganganci da son zuciya daga AA ɗin, eh son zuciya, koma tace zalunci......) Hawaye suka shiga solalo mata masu shegen zafi. Zaram ta miƙe daga gaban nashi ta nufi window jikinta na rawa. Yanda ta tura kujerar da ƙarfi harta faɗi ya sanya AA buɗe idanunsa da ƙyar. Kallo ya bita da shi, sai kuma yay saurin rumtsewa jin abinda take faɗa cikin kuka mai tsanani daga inda take....         “Dan ALLAH ka tafi, ka tafi nesa dani bana son ganinka. Ka barni naci gaba da rayuwata cikin salama. Namaka alkawarin zan bar aiki a companyn ka. Bana son tuna komai, bana so, ka daina kusantoni, ka barni, dan ALLAH ka barni na roƙe ka Ajwaad....”        “Besty!” ya faɗa a can ƙasan maƙoshi daga bayanta batare data san sanda ya baro gadon yazo wajen ba. Kuka ta sake fashewa da shi tare da durƙushewa a wajen, “Ka daina kirana da wannan sunan, ka tafi kawai, ka tafi Ajwaad....”        “Zan tafi, amma ki saurareni kona minti biyar ne”.     “Bazan iya ba, baka da sauran space na lokacina, sam baka da shi.” sai kuma ta juyo tana daga durƙushen ta haɗe hannayenta waje guda alamar roƙo🙏. “Na roƙeka ka barni Ajwaad. Ka yi nesa dani, bana buƙatar jin komai daga gareka, bazan iya baka komai ƙanƙantar lokacina ba a yanzu”.         Da ƙyar ya iya haɗiye abinda ya riƙe masa maƙoshi, ya lumshe idanunsa da sukai mugun kaɗewa mai ban tsoro daban tashin hankali ya sake buɗewa a kanta. Cikin wani irin murya mai matuƙar laushi da sanyi ya ce, “Kin fi son mu cigaba da kasancewa a wannan matsayar kenan? Mu cigaba da ɓatama waɗanda ke bibiyar rayuwarmu lokacinsu. Yes muna ɓata musu lokaci ne kema kin sani, dan in har bani ne MIJINKI ba, wani bai isa ya zama ba!!.” ya ƙare furucin ƙarshe a kausashe. Ɗago kai tai da sauri tana kallonsa da jajayen idanunta. Shima ɗin kallonta yake da wani mugun kallon tabbatarwa. Amma ta dake a kausashe ta ce, “Mi kake nufi Ajwaad?!”. Shima a kausashen ya ce, “Abinda kikaji na faɗa shi nake nufi. In dai ni Ajwaad Aliyu Darma ina numfashi a doron wannan ƙasar, wani banza wofi bazai taɓa aurenki ba Maanal. Dan haka tun kafin dare yay musu ki sanar da su suje su nema matan aurensu. Ki kuma sani ko mutuwa nayi kika auri wani in sha ALLAHU sai na hanaku zaman lafiya da fatalwata. Idan kuma kinji wasa bismillah, ga fili gamai doki”. Ya ƙare maganar yana miƙewa da kaɗa mata yatsarsa manuniya a saitin fuska tamkar zai tsokale mata idanu. Miƙewa tai itama a gabansa tana huci ga hawaye na zirara mata da gudun tsiya. Cike da tsiwa ta riƙe ƙugu da duka hannayenta biyu tana kallonsa babu ko gezau. “A tunaninka kana da wani ƙarfin yin duk abinda ka faɗa? Ka lalata min rayuwa sannan kai tunanin hanani auren wani? Shike nan mu zuba, nace mu zuba ni da kai dan ALLAH ɗan halak ka fasa, ka saka a ranka ni kuma Maanal Habib Umar Giro zanyi aure, kuma zan auri wanda kake da kusanci da shi wato Rafeeq. Ka fara shiri nan da wata biyu kacal, wata biyu....” ta ƙare maganar tana karkaɗa masa yatsarta itama da raɓashi zata wuce. Ai a wani irin fusace a kuma bazata taji an damƙo hijjab ɗinta an fisgota baya. Babu zato ta jita manne a jikin bango, duk da ko kaɗan jikinsa bai taɓa nata ba yanda yay mata rumfa da ingarman jikinsa saboda ya fita tsaho da cikar jiki nesa ba kusa ba, babu ta inda zata shaƙi iska ya masifar sake hargitsata. A kausashe a kuma faɗace, dan gaba ɗaya taswirar ƙyaƙyƙyawar fuskar sa ta canja. Ga jijiyoyin kansa sun sake fitowa, idanunsa sun masifar kaɗewa irin mai ban tsoro ɗin nan tamkar an watsa jini a cikinsu. Da kakkausar muryar da bata taɓa tunanin ya mallaka ba ya ce, “Idan kikace zaki zuba WASAN da ni kema kin san kece zaki sha wahala wlhy. Amma bismillah mu zuba ɗin, sai dai ki sani wani ɗan iska bai isa shiga GONAR dana jima da shiga ba har abada, yanda na fara mallaka ni zan cigaba da mallaka har ƙarshen numfashi.” Daga haka bai sake cewa komai ba ya juya ya fita a fusace kamar wani mafaraucin soji a daji. Yana gama maida ƙofar ya rufe tai wani irin zubewa a wajen ta fashe da kuka jikinta na rawa. Kuka take sosai, kuka irin mai zuwa da dukkan ƙarfinka dana zuciya. Kuka mai ban tausayi. Ita wannan mutumin kema alfahari da abinda yay mata a baya, ita yake ma iƙirari akan abinda ya aikata mata. Ita Maanal. Wlhy dolene ta tabbatar masa shi ba kowa bane, bai kuma isa komai ba, tabbas zata tabbatar masa, dole ne ma ta bbatar masa, ta hanyar auren RAFEEQ ne kuma kawai zata tabbatar masan. Ta jima a wajen tanayi, sai shigowar nurse ɗin dake kula da ita ne ya kawo ƙarshen yanayin. Hankali tashe tazo ta tadata a wajen, da taimakonta ta maidata gadon tana jera mata tambayoyi akan ko jikin nata ne. Kanta kawai ta iya girgiza mata. Sai kawai nurse ta shiga lallashinta, dan AA ne ya turota dama. Daɗaɗan kalamai ta dinga faɗama Maanal masu kwantar da zuciya, a hankali a hankali ta fara tsagaita kukan har tai shiru. Hawayenta ta share tas tare da sake yin lamo a gadon. Nurse ɗin ma tayi tunanin ko tayi barci ne sai ta lallaɓa ta fita dan akwai abinda zata ƙarasa sannan ta dawo.       Kamar jira Nurse ɗin na fita RK na shigowa. Yayi sallama har fin sau uku da knocking amma shiru, sai ya ɗan kalla agogonsa da tunanin ko tayi barci. Ganin lokaci yaja sosai sai kawai ya yarda tayi barcin ne. Ƙofar ya ɗan tura ya leƙa, can ya hangota kwance a gado a lulluɓe, sai dai mi wani ƙamshin turare da ya san bai taɓa jinta da shi ba ne ya bugosa. Sai da gabansa ya faɗi, ai ba shiri ya shigo ɗakin da sauri. Tabbas ƙamshin turaren ne, turaren da in bai ƙarya ba a wajen AA kawai ya san shi.      (AA!) Zuciyarsa ta sake maimaita masa sunan da amsa kuwwa. Sai kuma ya shiga waige-waige a ɗakin kamar zaiga AA ɗin a ciki. Duk abinda yake Maanal na jinsa, amma ta dake tai likimo kamar mai barci, dan bata son ya ganta a yanayin da take sam. Jin ya fice da sauri yasa ta lumshe idanunta da ƙarfi sauran hawayen dake a ciki suka wani zubo shaaa..... ____________★ Da ƙyar ya iya fita a taxi ɗin ya nufi gate ɗin gidan nasu, dama satan fitar yayi. Daga fitowa sallar isha'i ya maƙale yaƙi komawa ciki. Sai da ya tabbatar Abah da yayunsa sun shige sannan ya fito a massallacin ya tari taxi ya nufi asibitin dan kawai ya ganta. Tun safen da RK yazo gidan da batun nata ciwon zuciyarsa ta kasa samun nutsuwa. Ji yake kamar ma nasa ciwon ya dawo sabo ne. Sai kuma gashi ya dawo a wannan bahagon halin yanzu.          Da mamaki security daya buɗe masa ƙofa ke kallonsa. Sai dai shi ko kallon nasa baiyi ba ya wuce flat ɗinsa. A hankali ya maida ƙofar ya rufe yana sauke ajiyar zuciya ganin kowa bai gansa ba. Sai kuma ya dafe kansa dake matuƙar sara masa har yanzu tamkar zai cire. Yana shigowa falo na biyu yay wani irin turus ganin Mamy zaune. Zuba mata ido yay sai kuma ya ɗan wawwaiga kamar mai neman abu. Dan wani irin tsarga zuciyarsa kallon da take masa yake yi. Amma sai ya dake kamar yanda ya saba. Idanunsa ya maido kanta cikin sautin muryarsa mai fita ƙasa-ƙasa ya ce, “Mamy kina buƙatar wani abu n....”      Hararar data wullo masa ta hanashi ƙarasawa. Sai ma duƙar da kansa da yay kawai.           “Daga ina kake?”.     Ta faɗa da kakkausar murya. Sam AA ya tsani ƙarya, baya sonta baya shiri da mai yinta. Gara idan bazai faɗi gaskiya akan abu ba ya gwammaci yin shiru kawai. Haushi ne ya turniƙe Mamy, cikin baƙin ciki da ƙunar zuciya ta wani daka masa tsawa. “Ajwaad bada kai nake ba ne?! Kasan dai bana son wannan banzan halin naka na iskanci ko? Nace daga ina ka fito??”.        “Mamy Please my head”   Ya faɗa yana kai hannu a saman kansa. Harara ta balla masa duk da zuciyarta ta motsa da yanda yayi ɗin. Amma sai a faɗace ta ce, “A'a your heart ba head ba. Ni zaka rainama wayo kama pretending ko. To wlhy bara kaji, idan ma wani abu kuke ƙullawa kai da ita to ka dawo cikin hankalinka, in ba hakaba wlhy kaine masha wuya. Dan har yanzu har gobe kai har ƙarshen rayuwa ina akan bakana. Yanda ƴan uwanka suka auri zaɓina kaima dole hakan zakayi. Dan haka ka sani na zaɓa maka yarinyar da sukazo tare da Abdulhakeem ɗazun a matsayin mata, a cikin satin nan za'aje nema maka aurenta. Kuma wata biyu kacal za'a saka...”      Ai da wani irin bala'in sauri ya kalli Mamyn, ta watsa masa harara cike da tabbatarwa........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖4️⃣9️⃣ ______________ ..........“Haka na faɗa kuma haka za'ai. Sannan wacece Maanal ɗin da wannan yaron Rafeeq ke magana ɗazun?”.      Wani irin sake bugawa zuciyarsa da ƙirjinsa da kansa sukai a lokaci guda. Ya tsatstsareta da kaifafan idanunsa da suka gama jirkicewa gaba ɗaya kamar zai haɗiyeta da su. (Maanal! Waya gaya mata zancen Maanal? Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un.....)       “Sai ka gama tunanin zaka faɗa min wacece ita?!”.     Ta sake faɗa a tsawace kamar zata falle fuskarsa da mari.. Da sauri ya kai duka hannayensa biyu ya dafe kansa. Sai kuma yay saurin zubewa a kujerar dake kusa da shi jin jiri na neman zubar da shi a wajen. Ɗan tsai tai tana kallonsa, kamar zata matsa garesa sai kuma, fuuu ta nufi hanyar kitchen tana faɗin, “Idan ka gama pretending ɗin iskancin kazo ka saman ka faɗa min wacece ita. In ba hakaba ni zan bincika, kuma ka bari har ya kaimu ga hakan wlhy sai ranka yay mummunan ɓaci a gidan nan. Zuwa safiya kuma idan ita uwar taka da uban naka suka tambayeka game da Nuratu da Huznah dan ALLAH kace baka so kaga yanda zan maka. Dan ko ka yarda ko baka yarda ba sai ka auresu dole su duka kuma a rana ɗaya”. Daga haka tai ficewarta ta kitchen ɗin dan dama tanan ta biyo....     ______★        “Jaan! wai ina kuma zaka naga ka ɗauka key?”.      “Zan ɗan duba Ajwaad ne, dan tun fita sallar isha'i yay wani wajen. Kin san Oum akan Ajwaad dai, na tabbatar tana can zaman jiransa hankalinta a tashe. Ballan tana baida lafiyar nan”.      Baki Nibras ta ɗan taɓe, tare da ballama Fawzan da yay gaba abinsa harara. Wani irin takaicin Oum na keta mata zuciya. Harta koma ta kwanta sai kuma ta miƙe zaram, sakkowa tai a gadon ta saka slippers ɗinta tabi bayansa batare data neman hijjab ta suturta jikinta ba duk da kasancewar kayan barci ne kuwa, dan ma dai sunada girma basa nuna mata ko'ina na jikinta. Tuni Fawzan har ya shige sashen AA, dan haka itama ta afka kawai. Isowarta dai-dai Fawzan ɗin na jijjiga AA cikin matuƙar tashin hankali da kiran sunansa. Sosai zuciyar Nibras ta motsa, tai mutsuwar tsaye tana kallon yanda mijin nata ya tallafi abin sonta da duka alamu suka nuna baya cikin ƙoshin lafiya. (A tabbas masoyi, dan kuwa da dukkan zuciyarta take jin ƙaunar ƙanin mijin nata kuma ɗan ƙawar mamanta. Mahaifiyarta da Mamy aminan juna ne shekaru masu yawa. Bata san komai daya faru ba wata rana mamanta ta bata umarnin shiryawa akan zatayi baƙo. Sam bata jayayya da ita, dan duk abinda take so itama tana so. Dan haka babu musu ta shirya tarba ta musamman ga wannan baƙo, duk da bata saka a ranta zata iya aminta da shi matsayin miji ba. Dan tana da nata tsarin itama akan mijin aurenta. Sai dai me, tana ganin Fawzan a matsayin baƙon nata duk ta rikice, dan guy ɗin it is hot kuma handsome. Bata wani ɓata lokaci ba ta miƙa wuya, kamar wasa soyayya ta ƙullu duk da ta fahimci shi ba wai hundred percent ya bata ammana bane. To amma mamanta ba Maman yara bace, tuni ta shirya mata duk ta yanda zata mallaki Fawzan ɗin har akai gagarumin biki na nunama tsara. Dan kowa yasan family na Ambassador Aliyu Darma ba gidan wasan yara bane. Bayan tashen dukiya da suna da yay Ƴaƴansa ma gwarazan kansu ne a fanin nema. Sai dai me, bayan aure da baifi wata ɗaya ba AA ya dawo Nigeria sakamakon jiyya da yay a ƙasar waje na tsawon shekaru biyu. Tun fa da Nibras ta ɗaura idonta akan AA taji komai ya ƙwace mata. Dan hundred percent shine irin zaɓin data jima tana ma kanta. Bawai dan Fawzan bashi da qualities ɗin AA bane. Kawai dai akwai abubuwa da yawa da suka bambanta su duk da a fuska suna kama da juna. Tayi iya bakin ƙoƙarin ta na ganin ta danne kwaɗayinta amma abu sai ƙara girma yake a zuciyar tata. Dan takai har siffanta kanta take tare da shi a lokacin da take tare da mijinta. Tabi hanyoyi da yawa akan AA amma ko kallo bata ishashi ba, dan yana da tsari akan mu'amularsa da matan yayyan nasa.......)          “Nibras! Nibras!”. Kiran sunanta da Oum ke ƙwalawa ya maidota hanyyacinta. Sam bata san lokacin da Oum ɗin ta shigo sashen ba. Oum ɗin ce ta ƙara katse mata gajeren tunanin da faɗin, “Nibras ɗakko bowl a kitchen ki sawo ruwa a ciki. Kai kuma Fawzan ɗakko towel ƙarami a toilet ɗinsa”.        Cikin rikicewa Fawzan ya amsa mata. Dan shi dama bai iya rikicewa ba. Har ya tafi Oum ta ƙwala masa kira. “Kaga dawo mu kamashi zuwa can sama ɗin zaifi”.       “Oum kin san bazamu iya ɗaga shi ba. Auta bana wasa bane. Bari na kira Babban Yaya dai”. Oum bata musa masa ba, ya shiga kiran Babban yaya. Cikin ƴan mintuna kuwa sai gashi. Shima hankalin nasa a tashe yake. Da ƙyar suka kama AA ɗin su biyu suka miƙar zuwa upstairs. Dan gaba ɗaya jikinsa ya wani irin saki sai numfashi yake da ƙyar da kiran sunan ALLAH dana Oum yana faɗin Kansa kansa dai. Sai da suka shinfiɗesa a gadon sannan Fawzan ya nufi ɗakko towel ɗin, dai-dai da dawowar Nibras. Sai faman hawaye take, dan ji take kamar ta maido ciwon kanta ko zata ji sassauci. Babban Yaya ne ya amshi ruwan da towel ɗin yana faɗin, “Oum kuje falo bari nai masa. Dan jikin nasa ma ya ɗau zafi duka yana buƙatar ruwan sanyin”.      Oum dake hawaye bata musa ba. Sai dai Nibras ba haka taso ba. Dan takaici har ɗan hararar babban yaya tayi ta gefen ido. Ganin yanda Oum ɗin ke hawaye Fawzan ya kama hannunta cike da lallashi, dole itama Nibras ɗin ta biyosu badan taso hakan ba. Sai dan tasan rijiya ba wajen wasa makaho bane ba. Shima babban yayan kamar AA yake baya ɗaukar raini..      Tsaf babban yaya ya gogema AA jiki yana tofa masa addu'a, a hankali jikin ya dinga hucewa shi kuma yana sauke ajiyar zuciya. Sai da ya koma sanyi ƙalau barci ya fara ɗaukarsa sannan ya barsa haka. Kaya marasa nauyi ya ɗakko a closet ɗinsa ya canja masa, dan ya zame waɗan can duka da boxer kawai ya barsa sanda yake goge masa jikin. Koda ya sanar ma su Oum suka shigo itama zama tai a ta ɗayan gefen tana tofa masa addu'a, hakama Fawzan na daga wajen ƙafafunsa yana tausa masa su da tofa masa addu'ar kamar yanda babban yaya da Oum keyi. (😀AA ɗan gata kenan). Tsahon lokaci suna a hakan kafin barci mai nauyi yay awon gaba da shi, wannan addu'ar da suke masa ce kawai mafita, dan in irin wannan ciwon kan ya bugesa sam maganin asibiti baya masa. Ba kuma dan ciwon bana asibitin bane, kawai dai ita addu'a dabance, maganin kowacce irin masifa ce.. Yanda yake sauke numfashi kaɗan-kaɗan ya sakasu dinga sauke ajiyar zuciya suma. Yayinda Nibras dake ta hawaye ta kasa haƙuri sai da ta tambayi Oum cikin dauriya, dan ji take kamar ta shaƙeta kota tureta daga zaman datai kan AA a saman cinyarta. Kishin matar take ji, tsananin kishinta mai zafi. Bama ita ba, duk wanda zai raɓar mata AA bata ƙaunarsa sam musamman mace. Kai hatta Mamyn ma haushinta take ji, dan ta jima da fahimtar daga Mamy har Oum ɗin dukkan soyayyarsu akan AA tafi ƙarfi. Dan kowa nayi ne bakin rai bakin fama duk da Mamy na ɓoye kurwanta wa kowa sai su da suka sani ita da Saheeba da ƙalilan ɗin mutane...... _____________★      WASHE GARI ba ƙaramin tashi hankalin RK yay da ganin yanda idanun Maanal suka kumbura ba. Gasu sunyi jazur. Amma koda ya tambayeta sai tace barci ne bata samu isashe ba sai gab da asuba. Badan ya yarda ba ya barta. Zama yay da kansa ya haɗa mata tea kamar yanda yay a kwana biyun nan, amma sai tace ta ƙoshi, ita so take dai su sallameta.         “Karki damu in dai sallama ce in sha ALLAHU yau za'a sallameki. Amma dan ALLAH ina son muyi magana Maanal”.     Yanda ya kira sunan nata in serious yasa ta kallesa. Sam kuwa babu wasan data sani akan fuskar tasa. Sai hakan ma yaso bata mamaki, kamar ba RK sarkin tsokana ba. Itama nutsuwar tayi yanda ya kamata. Kofin shayin ya miƙa mata, babu musu ta amsa. Tare da cema “Thanks” a hankali.        “Karki damu wannan aiki na ne. Maanal ina son muyi magana akan lafiyarki. Dan haka a matsayin likitanki nake tare dake anan.”      Kanta ta jinjina masa. Shi kuma ya sake gyara zama sosai da sake nutsuwa. Maanal kin yarda da ALLAH?”.      Nan ma kanta ta jinjina masa. Ya ce, “Alhamdullah, ina son yanda kika yarda da ALLAH shi kaɗai bashi da wani abokin tarayya ki yarda da cewar komai naki a hannunsa yake. Kuma shi mai iko ne akan komai. Maanal magana ta gaskiya ciwon dake tare dake baya buƙatar komai ƙanƙantar tashin hankali daga gareki, domin ciwo ne mai haɗarin gaske. Nasan rayuwa bata kasancewa sai da JARABAWOYI a cikinta, domin suna tafiya ƙafa da ƙafa ne da fitar numfashin mu. Amma duk sanda abu ya faru damu ya wuce yana da ƙyau mu manta da shi kamar ba'ayi ba. Tabbas ban san minene lulluɓe da rayuwarki ba, sannan ban san minene musabbabin ciwonki ba. Amma ina roƙonki ko sau ɗaya ki samu wani ki tattauna damuwarki da ita nauyin zuciyarki zai ragu. Sannan ki sake miƙa al'amuranki ga ALLAH, ki ƙara ruɓanya ibadarki da addu'oi muma in sha ALLAHU zamu tayaki kinji. Amma ki kwantar da hankalinki, ki daina barin damuwa na miki yawa akwai haɗari, dan ciwonki na neman kaiwa wani mataki musamman a tsakanin nan da yake yawan tashi. Dan ALLAH ki cire komai kinji. Ke mai haƙuri ce na sani, kuma jarumace dan a ɗan zamana dake na karanci ƙyawawan halaye daga gareki masu yawan gaske. Ƴan uwanki na sonki, ki daure ki bama kanki farin ciki, suma zasu samu farin ciki”.         Murmushi tayi a karo na farko, sai kuma ta kallesa wani abu mai nauyi na narkewa daga cikin ƙirjinta. Tabbas zuciyarta bata son kowane ɗa namiji da sunan soyayya. Amma abubuwa da yawa daga RK na birgeta. Mutum ne shi mai sauƙin kai, sam bai ɗauki rayuwa da girma ba. Komai nashi so simple, burinsa ya bama kowa farin ciki koda shi bazai yi farin cikin ba, ko a wajen ma'aikatan asibitin nan takan ji suna hirarsa da yabonsa akan tausasawa kowa duk da kasancewar asibitin MALLAKINSA....       “Nifa wannan kallon ALLAH narka ni yake yi Baby”. Ya faɗa yana wani karyar da kai. Murmushi ta saki a karo na farko, sai kuma ta kauda idanunta a hankali ta maida su ƙasa ta rissinar har lokacin da murmushi a kan fuskarta. Kusan minti ɗaya sannan tai magana batare data sake kallonsa ba.       “Nagode sosai Yaya Rafeeq. Nagode da irin kulawar da kake bani batare da gajiyawa ba. Nagode da irin haƙurin da kakeyi da ni duk da abubuwa da nake maka da dama....”     “No! no no please ni ban taɓa miki abu dan ki gode min ba. Dan haka kibar gode min. Kuma yaushe na zama Yayanki ne ma?”.     “Yanzu mana”.    Ta faɗa tana ɗan waro idanunta dake a kumbure sosai, gasu da ja har yanzu. Dariya sosai ya shiga yi, da sauran dariyar a fuskarsa ya ce, “A'a nagode a barni a matsayin da na kawo kaina dai. Ke duk tarin yayun nan naki. Ga Yazeed, ga Fadeel, Fawzan, AA, Uncle Sadeeq, Uncle Hamza haba ai sai daɗin ya miki yawa idan na ƙaru”.             “Kai dai kace baka son yin ƙanwar da ni kawai na haƙura”.       “Ni bance ba. Amma dai a barni a wancan matsayin, idan ma zan zama yayan a bari sai anan gaba kin shigo daga ciki”.        “Hummm”.     Kawai tace tana cigaba da juya spoon a cikin shayin daya bata. Fin minti ɗaya sai kuma ta ɗago ta ɗan kallesa. Ganin kallonta yake shima sai ta ɗan kauda idanun ta. “Yaya Rafeeq ka shirya yin aure yanzu?”.        Mugun faɗuwa gabansa yay dan abin yazo masa a bazatar da baiyi zaton ji daga gareta haka cikin sauƙi ba, duk da bai san ma'anar yimasa tambayar ba. Cikin nutsuwar ban mamaki ya ce, “Miyasa kika mun wannan tambayar Maanal?”.             Ƙasa ta ƙara yi da kanta, tana mai kokawar ƙarfafa kan nata da danne dukan abinda ke neman rinjayar shawarar data gama yanke ma kanta tun a daren jiya. Ajiyar zuciya taja mai nauyi kafin ta saki murmushi mai ciwo. “Ka amsa min kawai, ka shirya yin aure yanzu?”.      “Ban san miyyasa kika min wannan tambayar ba Maanal, amma tabbas na shirya yin aure, dan na isa yinsa, da ban shirya yin aure ba ALLAH bazan tunkareki da sunan soyayya ba. Saboda alƙawari naima kaina bazan taɓa ɓatama kowacce yarinya lokacinta ba in har ba aurenta zanyi ba. Na daɗe ina addu'ar a duk sanda zan so wata ɗiya mace ya kasance aurenta nake so zanyi”.        Sosai ta kafesa da ido, sai kuma ta wani lumshesu da sake buɗesu a kansa. Cikin son taushe muryarta dake neman fara yin rawa ta ce, “Ina son zuwa Kaduna a weekend ɗin nan. Kuma ina son na ɗan huta a can....” sai kuma ta ɗan yi shiru. Cikin zaƙuwa RK yace, “Uhumm ina jinki”.        Murmushi ta sake saki mai ciwo idanunta dai na kallon ƙasa. “Na baka dama kaje ku gana da Daddy akan batun auren mu”.       Ai ba zuciyar RK ba, hatta ɗakin ma ji yay yana masa girgiza. Yayinda wasu irin hawaye masu azabar zafi suka silalo da gudun tsiya a kumatun Maanal. Ƙarar tarwatsewar abu da basu san ko minene ba ta ratsa kunnunwansu. A tare duk suka dubi ƙofar, dan tanan ne abun yay ƙara. Plates ɗin abinci ne suka watse a ƙasa. Dubansu suka maida ga wanda alama ta nuna daga hannunsa plates ɗin suka suɓuto...........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖5️⃣0️⃣ ______________ .........“Subahanalillahi Naufal ya akai haka?”. Oum ta faɗa tana kallon Naufal first born ɗin babban Yaya kenan da a safiyar yau suka dawo daga Kano shi da sauran ƙannensa biyu ƴammata. Kafin Naufal da yay ƙwalƙwal da idanu alamar zai yi kuka ya bata amsa ta maida dubanta ga AA da yay tsaye a ƙofar duk ya tare ko'ina babu ma ta yanda zata iya shigowa. Sake leƙo fuskarsa tayi daga bayan san da take sai kuma ta kalla direction ɗin daya zubama idanun. Kallon cikin ido suka zubama juna shi da Maanal.. sai dai kafin ta iya yin wani yunƙuri RK da tuni ya baro inda yake yazo ya kama Naufal ya ɗaga gudun kar ya taka fasashshen plate ɗin daya tarwatse shi kaɗai ya katseta da faɗin, “Alhamdullahi ai babu ma abinda ya zube kamar plates ɗin ne suka suɓuto kawai daga basket ɗin, inaga tuntuɓe yayi ne”.      “Ai kasan Naufal da wautan tsiya. Tun da naga ya figo basket ɗin da gudu nasan komai zai iya faruwa. Baka dai ji ciwo ba ko?”. Tai maganar tana kallon Naufal ɗin dai. Kansa ya ɗaga mata cike da shagwaɓa ya ce, “Oum Uncle ne fa ya kusa sawa mu faɗi”.    Yanda yay maganar yana kallon AA yasa duk suka kallesa suma. Taɓa AA Oum tayi, dan gani tai ma kamar baya motsi, sai dai kuma tana taɓa shin ya juyo ya kalleta, hannunsa ta kama cikin nata ta rumtse da ƙyau, sai kuma ta juya ga Naufal da RK kema dariya da faɗin, “Ko kuma kai ka kusa sakawa ku faɗin ba. Aunty ai banyi zaton yanzu zaku ma taho ba.     “Rafeeq ai bana wasa da Baby na sam. Balle kace yau za'a sallameta shiyyasa nace in sha ALLAHU da wuri zanzo. Sai kuma Auta da nake son yaga likita yau shima”.     Karo na farko RK ya dubi AA sosai. Ganin yanda idanunsa sukai masifar kaɗewa ya ce, “Ya Salam badai kan nasa bane har yanzu?”.          “Shine kuwa wlhy yaƙi sauka, jiya haka ya kwana a wahale”. Ta bashi amsa tana jan hannun AA ɗin zuwa gaban gadon da Maanal take. A kwance take yanzu ta juyama ƙofa baya, hakan yasa Oum zama a bakin gadon kusa da ita. Shi kuma yay tsaya kawai daga gefen Oum yana kallon ƙofa dan yaƙi sake kallon Maanal. Kujera RK ya tura masa cike da kulawa ya ce, “Zauna anan bara na duba Doctor Rasheed ɗin muga. Ai da kun sanar min da gida yazo ya samesan”.          “Yayi ƙoƙari ne ai Rafeeq, kwana biyun nan yanata zaryar zuwa gidan, kuma dama yace idan bai sauka ba yau asibiti ya kamata yazo ya duba shi da ƙyau shiyyasa”.   Jajantawa RK ɗin ya sake yi kafin ya juya ya fita yana jaddadawa AA ya zauna. Sai dai ko kallonsa yaƙiyi balle ya zauna ɗin. Yana daga tsayensa duk da hajijiyar da yake ji na jujjuya masa kai. Oum kuwa data riƙo hannun Maanal a hankali ta shiga kiran sunanta. Hakan yasa cikin dauriya da jarumta Maanal da tuni ta goge hawayenta tas ta juyo ɗin. Suna haɗa ido da Oum ta sakar mata murmushi, sai kuma ta tashi zaune ta shige jikinta cike da shagwaɓa ta ce, “Oum ni nayi fushi sai yanzu”.          “Oh oh my baby kada kiyi fushi kinji, ayima Oum afuwa yaya jikin naki?”.       “Naji sauƙi Oum. Yaya Rafeeq ma yace zasu sallameni yau”.     “To Alhamdullah ALLAH ya ƙara afuwa. Tun jiya naso zuwa shima sai Auta ya kwanta shiyyasa”      “Hy Aunty”. Naufal ya faɗa yana ɗagama Maanal hannu fuskarsa da murmushi. Murmushin itama Maanal ɗin tai masa. Sai kuma ta ɗaga masa hannun itama ta ce, “Hy Handsome”.          Farin ciki ne ya kama Naufal jin an kirasa Handsome, dama Uncle AA ne kawai ke kiransa da sunan. Gaban gadon ya ƙaraso sosai. Ya ce, “Nagode Aunty da kika kirani Handsome. Kun zama biyu kenan ke da Uncle.” yay mata nuni da AA.     Batare data kalli AA ɗin ba taima Naufal murmushi kawai. Gaisheta yaron yay da tambayarta yaya jiki, ta amsa masa da kulawa tana zaunar da shi kusa da ita. Sai kuma ta kalla Oum tana faɗin, “Yana kama da babban Yaya sosai”.      Dariya Oum tayi a karo na farko, idonta akan Naufal ta ce, “Kodai Auta. Dan komai na Naufal Auta ne sak, duk da dai dama suna kama da Fadeel ne shima ɗin, amma Fadeel ai fari ne, shiko Naufal irin fatanku gareshi ke da Auta”.         Maimakon Maanal ta amsa zancen sai ta basar ta hanyar shagwaɓe fuska ta ce, “Oum mi kika dafo min?”.       Dai-dai Oum zata bata amsa RK ya shigo. Idonsa a kansu sai kuma ya kalla AA, da kulawa ya ƙarasa garesa yana faɗin, “Wai baka zauna ba. Ko duk ƙulafucin Oum ɗin kaka ne kazo ka tsaya mata a kai kamar zaka koma ciki kai da ɗayar Autar tata. Common malam zauna kada ka faɗi”. Yanda baiyi magana ba tunda ya shigo yanzun ma bai tanka ba, sai dai ya zauna ɗin dan shima yasan in ba hakan yay ba tabbas gab yaje da zubewa a ƙasa, sam kuma baya son cigaba da tada hankalin Oum, dan kwana biyun nan da baida lafiyar nan har rama tayi, ga shi itama tana fama da kanta..... ____________★        A Kaduna kam shirin kai lefe ake gidan su amarya. Shi ango ma baya nan yana Lagos kwana takwas kenan. Kaya ne na garari aka shirya na kuma fariyya. Jiya yini guda masu shiryasu na aikin nan. Akwatina set ashirin daa huɗu cif, kaloli daban-daban. Kuma kowane set zaka samu kusan akwati biyar ko uku harda masu goma sha biyu. Ga galleliyar mota new model a 2023 sabuwa dal a ledarta. Hajiya Basariyya dai tana nane dasu a gabanta ake komai duk da zuciyarta a ƙuntace take, amma yafi yarda data danne ayi komai akan idonta, Ammie ko yanda ba'a gayyaceta ba bata saka kanta a sabgar ba daga ita har Sakina da har yanzu take a gidan. A yau ɗin ma sai suka ƙirƙiri zuwa gyaran jiki abinsu. Duk bidirin shirin kayan da akai basa nan. Aiko Hajiya Yaya da ƴaƴanta suka samu na zaginsu wai Ammie tana hassada ne saboda ba ɗiyarta bace ba. Koda suka dawo gidan haka suka cigaba da habaice-habaicen su Ammie tayi kamar ma bata jisu ba...      Washe gari tun sassafe gidan ya fara tara dangin Hajiya Yaya. Sai wasu a dangin Daddy dake ɗan ɗasawa da Hajiya Yayan. Yanda gidan ya cika saika ɗauka bikin ne ma ya fara. Har lokacin kuma babu wanda ya zo ya cema Ammie tazo ga lefe kota shirya zuwa kai lefe, ita kuma tayi biris da kowa bata saka kanta ba. Bayan sallar azhar suka cika motoci goma cif sai ta amarya dake tsakkiya da toyota hilux da aka zuba kayan lefen a ciki. Haka suka tafi a jere gwanin sha'awa, duk inda suka gitta sai an tanka kuwa. Dama haka suke so, gari ya ɗauka ko'ina ayi zancen wannan aure. To ALLAH ya cika burinsu dan kuwa an fara, sakamakon ƙannen Yazeed kaf da wasu a dangi tun jiya sun gama watsa wannan lefe a kafafen yanar gizo tako ina.. A can gidan Aunty Sabuwa ma gida cike yake tanƙam da ƙawayenta ƴan duniya da dangin mijinta. Anyi abinci kala-kala domin tarbar baƙi duk da kuwa aurene na dangin juna. Cikin abinda baifi mintuna ashirin ba anguwar ta gama rikicewa, dan kuwa kiɗa suka saki sosai da dj ɗinsu da suka tanada. Kafin a ɗan sarara a shiga buɗe kaya, masu video nayi, masu hotuna nayi, masu guɗa nayi harda ƙawayen amarya. Dan babu kunya hatta amaryar ma tana a gidan abinta sai washare baki take da jin kanta sama ƙololuwa, dan tasan ita kam ta wuce tsara sai dai ta taya ƴan baya da addu'a kuma, amma 2025 kam tata ce...           Tukuyci na miliyan ashirin aka bama ƴan kawo lefe suma da tarin kayayyakin snacks da akai packaging, sai drinks da ruwa katon-katon, dambun kaji, danbun jan nama, soyayyu da gasassun raguna a ƙyafe guda biyar. Lallai wannan al'amari ya kai duniya tasan da shi. Dan kuwa ba garin Kaduna kawai ba duniya ce ta ɗauka sakamakon yanda komai ke yawo daki-daki a media tako ina. Dan hatta tarbar da suka samu da shagalin da akai a gidan Aunty Sabuwa shima anata ɗorawa. Hakama tukuyci da kayan alatun da aka maƙare musu motar da ta kawo kaya shima dai duk an ɗora. Hakan ya sakama jama'a kwaɗayi da shirin son ganin yanda wannan shagalin biki zai kasance na ƙwarya tabi ƙwarya. Wanda kuma suka san ainahin waye uban amaryar dan bai kai ko kwatar dukiyar uban ango Alhaji Usman Chalawa ba nata mamakin hidimar da su ma su Aunty sabuwar sukayi. To kowa dai na son yaga yanda za'a kwashe kam, dan in dai har kawo lefe kawai duk akama waɗan nan hidimomin ai taron biki kam dole ko mu ƴan kallo mu kasance a cikin shirin shan kallon (😂 lolz).... ______________★          Sosai kasancewar su Oum a asibitin ya ɗan ragema Maanal nauyin da zuciyarta tayi. Dan ma hankalin Oum ɗin ya rabu biyu saboda AA. Dan shi ma bayan Doctor ya dubashi sosai sun ɗan kwantar da shi amma yace na yini ɗayan ne kawai. A wannan yanayin Shahidah ta iso asibitin ta samesu. Tayi farin cikin ganin Oum sosai. Kasancewar an hana kowa zama a ɗakin da AA yake dan suna son ya samu barci sosai duk sai suka tare anan ɗakin Maanal ɗin. Sai bayan sallar azhar da AA ya farka Oum ta nufi can. A lokacin ita kuma Maanal ta samu sallama. Koda suka gama tattare kaya zuwa mota Shahidah tasa Maanal gaba tai domin duba AA. Bata so hakan ba, sai dai bazata iya musu da Didinta ɗin ba. Musamman daya kasance RK na tare da su ne.           RK ne ya fara shiga bayan yayi knocking an bashi izinin shiga. Sai Maanal, Shahidah a ƙarshe. Oum na zaune a kujera, shi kuma AA na kan gadon ya jingina da filo Oum zata fara bashi abinci a baki, sai faman ɓata fuska yake alamar baya son cin abincin ko kuma duk ciwon ne oho masa. Plate ɗin abincin Oum ta ajiye tana kamo hannun Maanal da faɗin, “Masha ALLAHU ƴan matana anyi sallamar dai?”.           Kai Maanal ɗin ta jinjina mata a ɗan shagwaɓe. Ita kuma tayi murmushi da faɗin, “To Alhamdullah, ALLAH ya ƙara lafiya yasa kaffara ne.”       Amin RK da Shahidah suka amsa da shi, kafin Shahidah ta maida hankalinta ga AA daketa kallonta. Duk da yasan dama zai iya ganin nata, amma sosai mamakinsa ya bayyana amma ya gagara iya cewa komai. Wannan ba komai bane daga halayensa, dan haka Shahidah bata damu ba, sai dai zafinsa da suke ji tun na shekarun baya akan ƴar uwarsu taji yana taso mata. Komai dawo mata yake kamar yanzu ne yake faruwa. Da ƙyar ta iya dannewa ta tambayesa jikinsa. Karan farko yay ɗan murmusa, irin guntun murmushin nan mai tabbatar da ƙunar zuciya. Tabbas yaga tsanarsa a bayyane akan fuskar Shahidah, hakan na nufi har yanzu suma basu mance komai ba, basu mance abinda ya faru ba suna riƙe da shi a ransu fiye ma da Maanal. Baiga laifinsu ba, dan ko shine hakan zai yi, amma inama zasu fahimcesa kamar yanda Oum ta fahimcesa bayan ya zauna da it.....         Maganar RK ce ta katse masa tunaninsa, ya ɗan kallesa sai kuma ya janye idanunsa yana jinjina masa kai. Baya son sakama ransa tsanar ɗan uwansa kodan daraja da kimar Oum, amma tabbas zafinsa yake ji, kishinsa yake ji mai tsanani akan Maanal. Ta yanda ya gwammaci ya dinga masa shiru akan abubuwa da dama fiye da yin magana.      Sai yanzu Maanal da tunda tai masa kallo ɗaya bata ƙara ba ta furta, “Ya jiki?”. Daga haka tai shiru. Shima sai bai amsa ba, ya dai ɗago idanunsa ya kalleta kawai. Yana ƙoƙarin janyewa akai knocking ƙofar. Shahidah ce ta amsa sannan ta bada izinin shigowa. A hankali aka turo ƙofar, yana sanye cikin lallausan farin yadi da yay masa matuƙar ƙyawu, sosai kamanninsa da AA ke a bayyane, ta fuska da ɗabi'u. Sai a shekaru ne kawai suka banbanta da hasken fata. Ɗan ja yay ya tsaya turus yana kallon Shahidah da itama take kallonsa, sai kuma tai saurin kauda idonta. Shima janyewa yay ya maida ga Oum, sai kuma ya sake waresu akan Maanal da itama take kallonsa. Cikin kasa daurewa ya ce, “Oum kinga mi nake gani?”.      Murmushi sosai Oum ta saki mai ciwo, sai kuma ta jinjina kanta da faɗin, “Na sani Fadeel. Shahidah ce da Lillyn ka”.      “Wai da gaske ne kenan?”.    Yanzu kam har sai da hakwaran Oum suka bayyana a waje, sai kuma hawaye suka ciko mata idanunta. Da ƙyar dai ta iya dannewa ta sake bashi amsa........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖5️⃣1️⃣ ______________ .......Matuƙar mamaki Babban Yaya ya shiga da jin komai daga bakin Oum da RK. Sai satar kallon Shahidah yake da jinjina mamakinsa akan canjawar Maanal. Ta ƙara tsaho duk rashin jin nan da rawar kai babu yanzun. Hakan ba abun mamaki bane ba, musamman idan aka tara yanda abubuwa suka kasance zama a iya ganin fiye da hakan daga Maanal. Nan fa ya tasa Maanal da tambayoyi har ma da Shahidah duk da shi ɗin ba gwanin yawan magana bane ba.         Maanal ce mai amsa masan, dan itama Shahidah tana amsa ɗai-ɗai ne. Itafa Family ɗin nan idan ta cire Oum a ciki da Fawzan da Abah da Mamy bata jin sauran a ranta yanzu. Sai ma wani kalar zafinsu da take ji, amma darajar Oum yasa taketa ƙoƙarin dannewa dan Oum ta cancanta. Ana cikin hakan sai ga Fawzan shima ya iso, bayansa matarsa ce Nibras, sai Saheeba matar babban Yaya hannunta riƙe da ƴar budurwar yarinya mai tsananin kama da su Babban yayan. Sai budurwar yarinya ƙyaƙyƙyawa a ƙarshe biye da su hannunta ɗauke da irin box ɗin nan da ake saka kayan abinci. Ambatar sunan Lilly da Shahidah da Fawzan yayi ya saka Saheeba kallon sashen da sauri. Kallon ido cikin ido sukaima juna da Shahidahn. A take fara'ar fuskar Saheeba ta ɓace ɓat. Itako Shahidah ta janye nata cike da basarwa tana bama Fawzan amsar maganarsa. Ita dai Nibras bata sansu ba a zahiri. Amma sunayen da aka ambacesu da shi ya sata tsatstsaresu da idanunta, dan ta ɗan san labarin dangantakar tasu da familyn Darma a wajen mahaifiyarta. Sai dai kuma bata da tabbacin waɗan can ɗin ne ko wasu daban.         Ita ko budurwar data shigo a ƙarshe gaba ɗaya hankalinta naga AA ne. Dan tuni ma ta kai gaban gadon babu ko kunya ta zauna a kusa da shi. Sai dai hararar daya jefa mata ta sata miƙewa tsaye zambar tana faɗin, “Sorry Yaya”.        Komai baice mata ba, ita kuma bata nuna damuwa ba ta ɗan rissina tana gaisheshi da tambayarsa jikin nasa. Sai kuma ta jawo kujera dake can jikin ɗayan gadon dake a ɗakin dan gado biyu ne Naufal na barci a wajen ta zauna kusa da shi sosai. Dai-dai nan Shahidah ta miƙe tana faɗin, “ALLAH ya ƙara lafiya bara mu wuce Maanal ta samu ta huta.”      Wani irin ɗagowa budurwar mai suna Nuratu tayi jin sunan Maanal a karo na farko. Sai a yanzu ta kalla Oum kasancewar Maanal ɗin na'a jikin Oum kamar ƴar mage. Tabbas bata san Maanal ba a zahiri itama a wancan lokacin na ƙuruciya dan ita ta rayune ba'a gidansu ba, yayar babansu ce ta riƙeta suna zaune a Lagos. Bayan rasuwar mijinta ne suka dawo Abuja, amma tasan komai na labari tsakanin yarinya mai suna Maanal da Yaya AA ɗinta. Burin ranta, da take fatan ya zama miji a gareta tun a randa ta fara tozali da shi a Lagos. Ƙoƙarin tuna inda tasan fuskar Maanal take yi, dan haka ta kafeta da idanu. Ƙirjinta ne yay masifar bugawa lokacin da suka haɗa ido da Maanal dake miƙewa Oum riƙe da ita. Sarai Maanal ta ganeta ita, hakan yasa ta janye idanunta cike da basarwa. Itako Nurry ta kasa janyewa dan ta gane Maanal itama, itace yarinyar da suka haɗu a wajen saloon ranar Sunday ɗin data gabata. Jitai jikinta kawai ya fara rawa, zuciyarta na bugawa da sauri-sauri saboda tsoron abinda take hasashe, cikin rawar murya da suɓutar baki ta furta, “Wai itace Manaal ɗin da nake jin labari a gidan su Mamy na Kano Aunty Saheeba?”.         Ba Saheeba data ambata ba, hatta su Babban yaya sai da suka dubeta, shi kansa AA wani kalar mugun kallo ya zuba mata ita da yayar tata Saheeba duk da matar yayansa ce. Sai kawai jikin Saheeba da Nurry ya kama tsuma. Cikin daburcewa Saheeba da kallon rashin mutuncin da Babban yaya ke jifanta da shi gana AA a gefe ya gama rikitata ta ce, “Wlhy ni ba wani bad abu na sanar mata akanta ba. ALLAH ma ne shaida bani na gaya matan ba. Nuratu ko'a bakina kika ji?”. Ta juya tana kallon Nuratu da zuciyarta ke mazari. Dan ta fahimci itama katoɓarar data nema yi. Sai dai kuma wani irin jin tsanar Maanal ke sake haɗa wutar guguwa a can ƙasan ranta. Kai ta girgiza ma Yayar tan, sai kuma ta ce, “No nima fa ba ina nufin wani bad abu bane ba wlhy ko aka sanar min a kanta. Kawai na faɗa ne ta yanda zan tabbatar da ita ɗin ce bawai dan wani abu ba.”        Fawzan ne ya girgiza kansa kawai da katse yanayin ta hanyar faɗin, “ALLAH ya ƙyauta to. Amma wannan maganar ma baida wani amfani. Ƙanwata muje na saukeku gida ko”. Ya ƙare maganar idonsa akan Shahidah. (Da ada ne catake ita ba ƙanwarsa bace). Suyita musu da jayayya, dan da gaske Fawzan ya girma Shahidah ɗin da kusan shekara uku, kusan ma za'ace AA ne sa'anta. Amma ta girmesa itama da wasu watanni. Alaƙar Shahidahn da babban Yaya yasa suke ƴar jayayyar da Fawzan ɗin sarkin barkwanci da tsokana.       Murmushi Shahidah tai masa da faɗin, “A'a mun hutasheka Yaya Fawzan. Da mota ma nazo shiyyasa nace shima Rafeeq ya huta abinsa.”          Sai a lokacin RK da komai ke masa kaikawo yay magana. Maanal da tuni tai gaba ya kalla. Dan ita ko kallon Nurry batai ba balle wani dake ɗakin akan maganganun. Hasalima bata nuna tasan anayi ba, tunda tabar jikin Oum tai hanyar ƙofa abinta. Kai kawai ta jinjinama RK da sakar masa ɗan murmushin daya sake tokare maƙoshin AA tai ficewarta. Itama Shahidah sai kawai ta bita tana wani jin sake tsanar wannan family.         Biyosu RK yay da sauri, hakama Oum. Dakatar da RK Oum tayi, kafin ta ƙarasa inda Shahidah ke ƙoƙarin buɗe motarta ta riƙo hannunta. Da sauri Shahidah ta juyo, sai kuma ganin Oum ya sakata sakin murmushi. “Lah Oum ko munyi mantuwa ne?”.       Fuskar Oum cike da damuwa ta ce, “Ba mantuwa kukai ba Shahidah, haƙuri zan baku. Dan ALLAH kada abinda yarinyar can Nuratu tayi ya dameku. Nasan koda wani abu taji ba wanda kuke tunani bane ba. Dan dukkan abinda ya faru sirrine da iya mu da ku muka sanshi. Ni......”       Da sauri Shahidah ta shiga girgiza mata kai, “No Oum dan ALLAH kar kice komai. Mu tsakaninmu dake sai addu'a da fatan alkairi. Kamar yanda tun farko muke miki kallon uwa yayar Ammie haka har gobe wannan matsayin naki bai goge ba a zukatanmu. Bamu taɓa riƙeki a ranmu ba. Kosu wlhy albarkacinki dana Abah da Mamy suke ci har muke jin komai ya wuce kamar bai faru ba. Abinda ya faru ƙaddararmu ce mu duka da ku, babu kuma wanda ya isa ya iya canjata ba gashi komai ya wuce kamar ma bai faru ba”        “Na sani Shahidah, amma idan na tuna nakan ji na tsani dukkan kaina wlhy. Kuma ina sha ALLAHU addu'ar da nake tsahon shekaru bazata taɓa tafiya a banza ba. Da izinin UBANGIJI sai Ajwaad ya gyara ɓarnar da yay da kansa. Gaskiya kuma saita bayyana. Abinda duk ke a ɓoye zai fito fili”. Kuka ya sarƙe Oum...     Rungumota Shahidah tayi, yayinda Maanal tai saurin shigewa mota hawaye na gudu akan fuskarta. Jikinta sai rawa yake yi. La'ilaha'illa antas-subahanaka inni kuntu minazzalumin ta dinga ambata. Tsohon lokaci har bata san mi Shahidah da Oum suka cigaba da tattaunawa ba Shahidah ta shigo mota. Komai basu cema juna ba sai murmushin da Maanal ta ɗan sakar ma Oum dake mata magana ta ɗaga mata hannu....     Komai dake faruwa a idanun RK ne dake tsaye daga can nesa da su. Shifa gaba ɗaya an ƙarasa kulle masa kai. Yau ya fahimci lallai akwai wani babban al'amari daya shiga tsakanin wannan zumuncin. Sai dai miyyasa kowa ke son ɓoyewa ne? Anya bai kamata ya sani ba? To idan ya sani amfanin mi sanin zai masa. Kawai yana son Maanal hakan ya wadatar da shi. Idan lokacin ya san komai a tarayyarta da Darma Family yayi yasan zata sanar masa duk da ƴan uwansa ne jininsa na kusa kuwa. Koda Oum ta iso inda yake bai tambayeta komai ba. Sai ma murmushi da yay mata yana mai nuna mata hanya alamar suje. Zuba masa idanu Oum tayi sosai, sai kuma a hankali ta furta, “Rafeeq! Da gaske kana son Maanal?”.       Idanunsa sosai ya waro a kanta, sai kuma ya narke fuska cike da nuna damuwa ya ce, “Haba Aunty, wane irin tambaya ce wannan mai tarwatsa zuciya. Kema shaida ce ban taɓa kawo wata yarinya gareku da sunan soyayya ba. Miyyasa kuke ganin komai na kamar ba serious ba?”.       “Sam ba haka bane ba Rafeeq. Nasan kai mutum mai son wasa ne. Amma ban taɓa kallon al'amuranka a matakin rashin serious ba. Itama tambayar na maka itane kawai.”              Kansa ya ɗan jinjina da faɗin, “In sha ALLAHU Aunty zan tabbatar muku da babu wasa akan batuna da Maanal. Dan yanzu haka ma ta bani damar zuwa Kaduna na gana da Daddynta a next week”.     Cak Ammie ta tsaya gabanta na faɗuwa. Dan lips ɗinta har ɗan rawa yaso farawa amma tai ƙoƙarin dai-daita kanta da ƙyar. Sai kuma ta sakar masa murmushi kawai da faɗin, “Masha ALLAH, idan mukaje gida zamuyi magana”....        Koda suka dawo ɗakin sun sami babban yaya nata zuba faɗa ma Nuratu. Ta inda yake shiga tata nan yake fita ba. Sai shigowar Oum datai masa magana ya tsagaita. Amma duk da haka a fusace yace su wuce su koma gida ba'a buƙatar sake ganinsu a asibitin ma. Haka Saheeba da Nibras da ita Nuratun suka fita ransu a ɓace suma. Sai dai babu damar magana dan tabbas babban yaya da AA basu san wargi ba. Koshi Fawzan dake da yawan barkwanci bawai ya saki kansa bane raini ya shiga tsakaninsa da Matarsa ma balle ita Nuratun. Hatta da ita Saheeba dake matsayin matar babban yayansu da suke matuƙar girmamawa babu raini a tsakaninsu dan matsayin ƙanwa take a wajensa.. Anan suka bar yaran, dan tuni Anum maƙalƙale take da jikin Fawzan dama tun fara faɗan Daddynta. Shi ko Naufal har yanzu yana barci ne....... ____________★       Koda suka iso gida daga Shahidah har Maanal basu sake tada maganar nan ba. Shahidah tayi hakan ne kawai dan gudun tadama Maanal hankali, sai da ta shiga ɗakinta tai kiran Amaal suka tattauna. Sun jima akan wayar suna magana har Maanal ta shigo sannan Shahidah ta yanke kiran dan bata son tasan da Amaal ɗin take waya. Itama Maanal bata damu da sanin dawa Shahidahn ke wayar ba. Sai ma zama da tai a bakin gadon nata.        “Har kinyi wankan?”.    Kai Maanal ta jinjina mata cike da ƙarfin hali. Sai kuma tai ɗan murmushin san kore damuwar nan ta ƙarfin tsiya sannan ta furta, “Naga mutiniyarki na haɗa kaya fa ko Kaduna zataje ne itama?”.         Da mamaki Shahidah ta ce, “Wai Huznah?”.     Kai Maanal ta jinjina mata. Ita kuma tace, “Humm to ita dai ta sani, ai garama ta koma ɗin dan nikam wannan gantalin nata na tayar min da hankali musamman a kwanakin nan data san Yazeed baya Abujan. Narasa mi yarinyar nan take yi a garin nan?”.          Murmushi kawai Maanal tayi amma taƙi gayama Shahidah gaskiyar abinda ta sani akan Huznah ɗin. Badan bata son ta sani ba sai dan bata son sako al'amarin mutumin (AA🤣) da Huznahr ke bibiya sam a al'amuranta. Sai ma kawai ta basar da zancen ta hanyar faɗin, “Didi nima ina son zuwa Kaduna a weekend ɗin nan”.         “Amma Auta kinfa san satin ne bikin Yazeed”.      “To minene a ciki Didi. Dan ana bikin yaya Yazeed kuma sai naƙi zuwa Kaduna?.”      “Baƙya gudun abinda zai iya zuwa ya dawo”.      “In sha ALLAHU babu komai Didi. Kawai ina kewar Ammie ne sosai wlhy. Sannan ina son Rafeeq yaje su gana da Daddy dan na bashi damar hakan”.      Da sauri Shahidah ta dubeta. Harshenta har harɗewa yake wajen furta, “Maanal akan mi kike son Rafeeq ya gana da Daddy?”.    Ɗan jimm Maanal ɗin tayi tana kokawar saita kanta da danne duk wani yinƙurin raunin da zuciyata ke son bayyanawa akan fuskarta, sai kuma ta saki murmushin karfin hali. Kanta tsaye ta ce, “Na bashi damar neman aurena”.       “What!! Neman aurenki fa kika ce Manaal? Rafeeq ɗin? Shifa ɗin ɗaya daga cikin zuri'ar su Ajwaad ne??”.      “Tabbas hakane Didi. Shiyyasa ma na bashi wannan damar. Sannan kin manta ne, alaƙar dake tsakanin Oum da Rafeeq tafi ƙarfi fiye da wadda ke tsakani da su. Dan haka na yarda na amince zan auri Rafeeq in sha ALLAHU”. Daga haka ta miƙe ta fice daga ɗakin ko waiwayen Shahidah data saki baki da hanci da ido tana kallonta batai ba.........✍️ _🥱🥱Nifa a wata gaɓar rasa abincewa nake 😆._ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖5️⃣2️⃣ ______________ .........Wani irin kalar zubewa Shahidah tayi a saman gadonta kamar wadda aka kwashema dukkan ƙarfi da zuciya a lokaci ɗaya. Kalaman Maanal na mata wani irin kai-kawo dai-dai da bugawar zuciyarta. Sai kuma kamar wadda aka zabura ta lalubo wayarta. Kira ta sake dannama Amaal. Aiko bugu ɗaya ta ɗaga dan dama tun ɗazun nemanta take itama amma ta gagara samunta....      “What! Rafeeq fa? Maanal kuwa nada hankali? Kota manta alaƙar dake tsakanin Rafeeq da Ajwaad ne?”.      “Nima na faɗa mata hakan wlhy Amaal. Amma ta nuna min ai alƙar dake tsakanin Oum da Rafeeq tafi ƙarfi akan wadda ke tsakanin Rafeeq da su Ajwaad. Ni wlhy nama rasa wane tunani zanyi. Dan tabbas akwai ƙura babba. Anzo gaɓar fa da dole Ammie tasan halin da ake ciki kin san dai Auta da taurin kai da kafiyar tsiya”.          “Amma kin san zamusha faɗa akan ɓoye matan da mukai. Sannan na faɗa miki jiya naje gidan na samu Daddy na shirin zuwa Kebbi domin ganawa da waɗan can mutanen na Giro. Na tabbatar kuma yau ɗin nan sun tafi ma shiyyasa nake ta nemanki tun safe. Yanzu haka can gidan zanje dan Hameed ya kirani ya sanar min Ammie na ciwon kai yau gaba ɗaya a kwance ta yini kuma yaga Daddy ya fita daga wajenta da safe kamar a fusace. Kinga ko ya tabbata akan zuwa Giro ɗin ne maybe ta nuna bata so ko”.        “Innalillahi wa'inna ilaihiraji'un Amaal komai zai iya faruwa kam. Wannan wace irin gaɓa ce mai rikitarwa da tada hankali. Aiko muma bamuga ta zama ba dole na ɗauka hutu Kona kwana huɗu ne muzo Kadunan gobe idan ALLAH ya kaimu. Daga nan kawai har biki”.      “To gaskiya hakan ne ya kamata kawai ku taho. Bara naje naga halin da Ammien ke ciki”.     Jiki a sanyaye Shahidah ta amsa ta da to kawai suka yanke kiran.      Bata leƙa Maanal ba sai bayan sallar magriba, ta sameta tana karatun Alkur'ani. Zama tai dan haka Maanal tana kaiwa inda ya kamata ta tsaya ta dakata. Duban Shahidah tayi da da faɗin, “Didi kina son wani abu ne?”.         “A'a Auta, ina Huznah take?”.     Sai da Maanal ta ɗan taɓe baki sannan tace, “Naga Yaseerah ta kiranta yanzun nan ta saka hijjab ɗina ta fita a rikice. Ban san mita gaya mata ba amma da alama Yaseerahn na wajen gidan nan ma dan naji tana cemata gata nan zuwa ba sai ta shigo ba”.       Kai kawai Shahidahn ta girgiza da faɗin, “To ALLAH ya ƙyauta. Dama zance miki ne inaga gobe in sha ALLAHU zamu wuce kadunan gaba ɗaya”.         “Didi aikinki fa? Wani abu ya faru ne?”.      “Babu damuwa zanma Abban Barrah magana ya nema min hutu na kwana huɗu tunda oga na abokinsa ne. Kinga idan biki ya tashi sai mu taho gaba ɗaya kawai”.        Magana Maanal taso yi, sai kuma ta ce, “Okay ALLAH ya kaimu to”...... _____________★             A ɓangaren AA kam shima bayan wucewar su Maanal ya matsa aka sallamesa. RK yaso ƙin yin hakan amma ina. Ganin yana neman birkice musu Oum tace yasa a sallame san kawai. Sun iso gida Mamy da Abah na shirin zuwa asibitin dubashi. Dan shi Abah yau yaje gidan gwamnati tunda safe sakamakon kiran daya samu daga mataimakin shugaban ƙasa. Ita kuma Mamy ta fita dan ko kai AA ɗin asibiti bata san anyi ba sai da ta dawo ko sashenta bata shiga ba taci karo da Abah ya fito zaije asibitin. Shine yace ta juya suje dan yasan halinta zata iya ƙin zuwa saboda kawaici. Bata ce masa komai ba suka nufi motarta data ajiye yanzu, dai-dai nan kuma sai ga ƴan asibitin ma. Sai kawai suka runguɗa zuwa sashen Oum dan AA yace shi can zaije baya son sashensa. Can ɗin kuwa aka nufa da shi har ɗakin Oum. Anan suka zagaye sa cike da kulawa da tsantsar soyayyar da kowa ke masa a gidan....         ★★★    Abdul-hakeem mijin Yaseerah yazo gidan kawoma Mamy saƙo data manto a wajen mamansa shi kuma yaje gidan ta bashi ya biyo Mamyn dashi ya samu batun ciwon AA ɗin bai sauka ba da har yau ya kaisa ga zuwa asibiti. Shine ya kira matarsa Yaseerah yace tazo itama ta duba shi sai su koma gidan tare. Ita kuma ta kira Huznah ta kuma biya ta ɗakkota a gidan Shahidah kamar yanda mijin nata ya bata umarni. Koda suka shigo kai tsaye sashen Oum suka nufa dan har lokacin itama Mamy na acan dama duka ƴan gidan har su Saheeba da Nibras da Nuratu. Mai aikin Oum Mamy ta saka shigowa da su Abdul ɗin har falon sama na Oum.        Duk suna a falo, idan ka cire AA dake can bedroom ɗin Oum da yay barci. Sai Babban Yaya da bai dawo gidan ba tun baro asibiti da yay ɗazun. Nibras da Nuratu na'a falon ƙasa suna girki. Nuratu ce ta fara cewa zata girka ma AA abinci kamar yanda uwarsu da suka kira suna gaya mata abinda ya faru a asibiti ta basu shawarar yi. Sai ita kuma Nibras ta ce itama zatayi dan wani irin tsanar Nuratu take ji tuni batun yanzu ba. Abinda ma ke ɗan sassauta mata ƙinta ganin yanda shi AA ɗin baya wani shiga sabgarta. Itama dai taci kuka bayan dawowar tasu daga koro sun da akayi daga asibiti. A hakan ma ba wani tarihin Maanal ta sani cikakke ba game da alaƙarta da AA, amma ta ɗauki aniyar bugar cikin  Fawzan ta sani yau dan tasan irin matakin da zata ɗauka akan Maanal ɗin da dukan ahalinta ma. Dan itafa a yanda take jin AA a ranta ALLAH ko mahaifansa da su Fawzan zata iya kawarwa ta mallakesa ita kaɗai.       Su Huznah sun hawo Nibras da Nuratu dake a kitchen basu sani ba. Sai da har su Abdull sun gama gaishe da Abah da Mamy da Oum Abah na tsokanar Abdull sannan suke haurowa da kayan abincin da suka shirya harda mai aikin Oum. Sannu Oum da Mamy ke musu, duk suka amsa tare da tambayar Mamy ina za'a kai masa abincin. D/table Mamy tace su ajiye. Dan haka duk suka ajiye a can ɗin. Juyowar nan da Nuratu zatai tana magana da Abdull sai idanunta ƙuru-ƙuru a cikin na Huznah da tun shigowar Nuratu falon mamaki da ruɗani suka baibayeta. Cikin kuwa ɗan waro ido na nuna mamaki Nuratu ta ce, “Kai wai wa nake gani kamar Huznah?”.       Murmushin ƙarfin hali Huznah ɗin tayi, sai kuma ta sinne kai ƙasa wai ita kunyar surukai na wajen ta ce, “Nice Nurry”.      Idanu Yaseerah da Abdul-hakeem suka haɗa. Yayinda Mamy ta saki wani murmushin jin daɗin ganin Nuratu da Huznah ma kenan sun san juna. Dan haka sai kawai ta miƙe tana faɗin, “Kunga muje can kafin Maman ɗan nan tace zamu hana mata shi barci”.       Dariya Oum tayi dan sanin da ita Mamy take. “Oh abun ma harda ƴar sharri. To shike nan kuje ɗin dai dan kuwa ban san a tada shin”.     Mamy ma dariyar ta sake yi. “Ai nasan gaskiya na faɗa”.       Shima Abah dariya yaketa musu. Haka Mamy ta fice tare da su Huznah. Nuratu ma tai wuff ta bi bayansu. Suna gama fitowa daga apartment ɗin Oum ɗin caraf Nuratu ta riƙo hannun Huznah dake kusan ƙarshe. Cak Huznah ta tsaya, sai kuma ta juyo tana kallon Nuratu. Murmushi ta sakar mata da faɗin, “Oh oh friend ashe kece? ALLAH duk kin saka mamaki yama rufe ni da ganinki gidan nan kodai gidanku ne?”.         Nuratu da zuciyarta keta watsal-watsal a ƙirji ta ce, “Eh gidanmu ne. Amma ba inda aka haifan ba. Gidan da zanyi aure kenan, kuma wanda zan aura ɗin ma kuka zo dubawa. A ina kika san Abdul-hakeem?”.      Tsabar yanda zuciyar Huznah tai wata girgiza har taurari ta dinga gani na mata yawo a cikin ido. Cikin rawar baki ta ce, “Waye zaki aura ɗin?”.      Cike da gadara da alfahari Nuratu ta bata amsa da, “Ajwaad Aliyu Abubakar Darma, wato AA Darma”.         Ai zabura gefe Huznah tayi tana mai fisge hannunta daga cikin na Nuratu, sai ko gata jikin bango kamar mage ta gamu da kare a kwanar da babu hanyar ɓillewa. Yanda tai ɗin ya saka Nuratu kafeta da ido itama zuciyarta na wantsalawa a karo na biyu. Sai kuma ta matsa gaban Huznah tana faɗin, “K jira-jira wai badai dama Yaya AA kike bibiya ba?. Babbar bala'i wai dama shine kika bamu labari?”. Bata jira amsar Huznah ba tai saurin fara danna wayarta ta latso hoton AA dake cikin wani lallausan farin yadi da yay masa shegen ƙyau ta nuna mata. “Shine wannan?”.        Jinjina mata kai Huznah tayi a mutuƙar harmutse.     “Kambu are you mad? Wai dama mijin aurena kike bibiya. Ehhhh ahhh lallai kin taro match yarinyar nan. Yau naga baƙar shegiya ubanwa ya aiko ki?”. Tai maganar da nufar Huznah gadan-gadan tana neman kai mata hannu ta shaƙota. Hannun nata Huznahr ta riƙe caraf, a dai-dai nan Fawzan ya iso wajen.       “Kai kai kai lafiya?!!”. Ya faɗa cikin daka tsawa. Dan shima abinda Nuratun tayi a asibiti har yanzu haushin bai bar ransa ba. Dakatawa Nuratu tai daga shirin shaƙe Huznah. Sai dai cikin wani irin ihu da hargowa ta ce, “Yaya Fawzan wai har wannan tsinanniyar ce zatace tana son Yaya AA. Son shi take amma tazo ta raɓu da jikina inata bata shawarar yanda zata sameshi. Ni wannan ƴar iskar zata maida bahuwa. Na rantse da ALLAH yau saina haɗa miki jini da majina ta yanda bazaki taɓa sake sha'awar yima kowa ƙwacen saurayi ba dan ........” ta ƙarasa da ashariya mai girman gaske tana sake zaburowa kan Huznah.            Cikin ƙanƙanin lokaci rikici ya harƙume a tsakaninsu da hayaniyar ta saka su Mamy fitowa. Hakama Oum sai gata da Abah harda masu aiki duk sun yo waje. Itama Nibras da Saheeba haka. Wani irin jan faratunnan ƙarin da Nuratu tayi a hannunta tai a saman fuskar Huznah,tun daga wajen kunnenta har zuwa bakinta. Ƙara Huznah ta saki na azaba tana mai dafe fuskarta da duka hannuwan biyu jikinta na rawa. Aiko cikin tashin hankali Mamy da Oum sukai kan Huznah ɗin, ita kuma Saheeba ta riƙe Nuratu. Mugun ciwo Nuratu taima Huznah , dan yanda kasan tsagar yarbawa irin na farkon ƙarnin nan haka suka kasance har sanda huɗu na yatsunta. Jini tuni ya jiƙe wajen abinka da farar fata jiki kuma babu wahala.        Ai Fawzan baima san ya kwashe fuskar Nuratu da mari ba. Yana ƙoƙarin sake kai mata wani Abah ya riƙe hannunsa yana mai girgiza masa kai. Kuka Huznah take sosai na azaba, hakama Nuratu kukan marin da Fawzan ya mata take yi. Sai dai bakinta bai mutu ba sai sake jadadadama Huznah take idan bata fita a sabgar AA ba ALLAH sai dai ta kasheta. AA nata ne ita kaɗai. Yanda taketa surutai yasa kowa ya fahimci akan AA suke faɗan, dan in ka cire Mamy da su Abdul-hakeem sai ita Saheeba babu wanda yasan alaƙar Huznah da zuwa gidan ma.           Dole Abdull da Yaseerah da jikinta duk ke faman rawa suka kama Huznah zuwa mota domin kaita asibiti. Ita kuma Saheeba taja Nuratu sashenta. Nibras da bayanin Nuratu ya sata jin wani irin ƙaiƙayin baƙin ciki a zuciya fuuuu ta wuce nasu sashen itama. Sai Mamy da Oum da Abah da Fawzan kawai aka bari. Cikin ɓacin rai Fawzan ya ce, “Wannan yarinyar sam bata dace da Ajwaad ba wlhy Abah. A haka kuke son aura masa ita tana abu kamar ƴar daba. Daga zuwan yarinya taji mata wannan mugun ciwon a fuska. Haka dama ɗazun a asibiti tayi akan Lilly, tana wani tambayar wai ba itace tasan labarinta ba, uwar mi ta sani to? Mi aka gaya matan akan su Shahidahn”.         Cike da mamaki Abah ya ce, “Wace Lilly da Shahidah?”.       “Lilly dai daka sani Manaal da Shahidah na Kano”.   Wani irin girgiza zuciyar Mamy tayi, haka Oum ma sai da ta ɗan rumtse ido. Yayinda Abah ya furta, “Fawzan kasan mi kake faɗa kuwa? Da gaske kake yi?”.      “Wlhy Abah da gaske nake yi. Itama an kwantar da ita a asibitin ne shine suka shigo duba Auta”.    Wani irin lumshe idanu Abah yayi zuciyarsa na masa nauyi a cikin ƙirji........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖5️⃣3️⃣ ______________ ........A ɓangaren Maanal kuwa bayan fitar Shahidah text ta turama RK dan tana son su ƙarasa maganar da suka fara. Ko minti biyu ba'a cikaba kuwa da tura saƙon sai ga kiransa ya shigo. Kamar bazata ɗauka ba ta dai daure ta ɗaga ɗin tare da saka hans free kawai. Sallama tai masa da sassanyar muryarta da a yau rauninta ya sake fita fili. Shima sai ya amsa mata da tashi sassanyar muryar. Tare da faɗin, “Gani a compound ɗin ku”.      Sosai mamaki ya kama Maanal, harta kasa ɓoyewa sai da ta furta, “Wasa kake amma?”.      Murmushi yayi mai sautin da har taji, “Da gaske nake my queen, dama ina gidan kusan minti goma kenan bana son takura miki ne kawai, harma ina shirin juyawa sai kuma ga saƙonki”.       Ajiyar zuciya Maanal ta sauke, zuciyarta na sake ƙarfafata akan RK ɗin. Tabbas bata buƙatar yin rayuwar aure da kowa. Hasalima bata da burin yin auren kwata-kwata. Amma tasan iyayenta da ƴan uwanta bazasu bari ba. Sai kuma Ajwaad, dole ne ta tabbatar masa da abinda yake ganin bazata iya ba. Zatai auren a cikin zuri'arsa kodan tabbatar masa da wannan Maanal ɗin ta yanzu tafa banbanta da wadda ya sani a baya. Miƙewa kawai tayi ta ɗan gyara hijjab ɗinta na salla da har yanzu bata cire ba, sai ɗan turare data ƙarama jikinta ta fita. Babu kowa a falon dan su Barrah na tare da Abbansu basu dawo gidan ba. Kitchen ta shiga ta ɗauka ruwa a tray da glass cup. A karo na farko ta nufi falon baƙi sannan ta fita compound inda RK yake. Iso tai masa zuwa falon baƙin, hakan sai ya sake bashi mamaki sai dai baice komai ba ya bita.           Koda suka shiga ita ta zuba masa ruwa da kanta sannan ta zauna. A karan farko da yaji ya kasa daurewa ya furta, “Gaba ɗaya sai mamaki kike bani. Gani nake kamar bake ba”.       Guntun murmushi kawai Maanal tai masa. Sai kuma ta kallesa. “Idan kiɗa ya canja itama rawar canjawa take yi ai. Ina son ka san yanzu muna akan gaɓar serious ne”.         “Hakane. Nima hakan nafi so mu kasance ɗin Maanal. Na kuma ji daɗi da godema ALLAH daya kawo mu wannan gaɓar ɗin.”       A hankali ta haɗiye ƴan kwallar data ciko idanunta. “Ɗazun mun fara magana sai dai bamu ƙarasa ba, shiyya nace kazo yanzu dan in sha ALLAHU kamar yanda na sanar maka gobe zan wuce Kaduna.” batare da jiran amsarsa ba ta miƙa masa diary ɗin data shigo da shi a cikin wata kyakkyawar bag. Amsa yay yana ciro sa daga jakan, sai kuma ya ɗan jujjuya shi a cikin hannunsa sannan ya ɗago ya kalleta. Itama shi take kallo, dan haka ta janye nata idanun.       “Na yarda da kai fiye da yanda kake zato. Badan komai ba sai dan wasu dalilai. Sannan kai ɗin koba komai jinin Oum ne. Wadda nake kallo uwa nagartacciya bayan mahaifiyata. Kaje da wannan zaka samu dukkan tarihin rayuwata data shuɗe a ciki, dan in har akwai abinda na rage ban rubuta ba to zai kasance ƙalilan ne, ko kuma baida muhimmanci. Bayan ka gama karantawa zaka iya sake tun-tuɓar Oum dan sake samun gamsuwa. Daga nan sai ka yanke dukkan hukuncin daya dace koyaya ne zan amshe shi. Dan ALLAH in har baka gama karanta shi har ƙarshe ba kada ka kirani a waya, kada kazo kaduna.” daga haka ta miƙe tsaye, shi dai kallonta kawai yace yama rasa abin cewa.        “Dare ya farayi sai da safe” A karo na farko ya ɗan ja numfashi ya fesar, sai kuma ya jinjina mata nasa kan yana miƙewar shima. Haka suka fito a tare kamar wasu kurame. Dai-dai nan motar Abdull ke shigowa gidan. Duk tsayawa sukai suna kallon motar har wanda ke ciki suka gama fitowa. Da mamaki RK ya furta, “Abdul-hakeem”. Sai kuma ya juya yana kallon Maanal. Itama shi ɗin ta kalla, tare da faɗin, “Ka sanshi ne?”.           Kafin ya bata amsa Yaseerah ta fito da Huznah, fuska duk facin bandage musamman ɓarinta na dama. Nufarsu RK yayi, dan haka badan taso ba itama tabi bayansa. Duk da Abdull yayi mamakin ganin RK a gidan sai ya danne, sai da suka gaisa RK yake tambayar abinda ke faruwa idonsa akan Huznah. Bayani Abdull yay masa a taƙaice. Kamar RK ɗin zai yi magana sai kuma ya fasa ya juya yana kallon Maanal.        “Inaga ni bara naje, ki musu iso ciki ko?”.    Kai kawai Maanal ta jinjina masa, sai kuma tai masa ALLAH ya kiyaye hanya tai gaba abinta batare da tace ma su Yaseerah komai ba.. Suma komai basu ce ɗin ba suka bita kawai, yayinda Abdull yake ta satan kallon Maanal ɗin. A ransa yana raya aji da nutsuwar yarinyar, gata ƙyaƙyƙyawa da wani skin nata mai ɗaukar hankali da yay ƙaranci ga matan wannan zamanin da suka maida kansu fararen dole da bleaching.....         Gaba ɗaya Shahidah kasa cewa komai tai da bayanin Abdull ɗin. Dan Yaseerah taso su ɓoye amma Abdull ya kware zance ga mijin Shahidah abinsa, dan shi dai namiji ne babu ruwansa. Godiya sukai musu, suma suka miƙe suna musu sallama dan dare ya fara. Dama ita Maanal bama ta tsaya a falon ba ganin kallon ƙurullar da Abdull ɗin ke mata a kaikaice duk da kuwa hijjab ne a jikinta har ƙasa. Ko bayan wucewarsu da Huznah ta shigo ɗakin Maanal bata kulata ba, tanata ma haɗa ƴan abubuwan da zata wuce da su Kaduna ne kawai. Itama Huznah ɗin bata kulata ba tai kiran mamanta a waya. Basu wani jimaba sukai sallama dan ta sanar mata ne kawai zata dawo Kaduna gobe....      _______________★    A Kaduna kam kamar yanda Daddy ya faɗa sunje Kebbi garin Giro asalin tushen su Maanal. Sai dai an samu saɓani tsakaninsu da manyan da ya kamata su gana da su. Dan kuwa an tabbatar musu kakarta da babanta da baffanta sunje Kaduna, wani kuma babban Senator ne ya aiko aka ɗaukesu a mota wai zasuje wajen Asiya daya tabbatar musu yasan a inda take.      Rasama abin faɗa Daddy yay, Dan ya rasa yanda zai fassara zancen musamman akan batun senator da suka ce. Haka dole suka baro garin gwiwa a sage. Basu iso gida ba sai dare, zuwa lokacin kuma kowa yay barci, sai dai hakan bai hanashi zuwa ya sami Ammie a sashensa ba tana jiransa. A kallo ɗaya da yay mata ya fahimci hankalinta a matuƙar tashe yake kuma....... ___________★        Washe gari Shahidah, Maanal, Huznah da yara suka tashi da shirin wucewa Kaduna. Dan yaran ma babansu yaje school ɗinsu ya daidaita komai. Jirgin ƙasa zasu bi, dan haka Uncle Sadeeq ɗin da kansa ya kaisu train station bayan sallar zuhur. Basuyi ko mintuna goma ba suka wuce. Koda suka iso Kaduna Amaal ce tazo ɗaukarsu. Dan ita kaɗai tasan da zuwan nasu sai Hajiya Basariyya. Itama saboda Huzna ne ta sani ɗin.     A dai-dai sashen Ammie Amaal tayi parking motarta. Bata ko gama kashewa ba Huznah tai ficewarta daga motar. Da kallo duk suka bita, sai kuma Amaal ta taɓe baki da faɗin, “Wawuya kawai”. Babu dai wanda yace komai tsakanin Maanal da Shahidah. Sai ma ficewa da sukai daga motar suma. Itama Maanal bata jira su ba tai sashen Ammie da sauri, dan kewarta take sosai, burinta kawai ta ganta a jikin Ammien. Da sallama ta buɗe ƙofar, sai kuma ta ɗan tsaya turus tana kallon yarinyar dake ƙoƙarin buɗe ƙofar itama alamar zata fito. Yarinyar Maanal ta zubama ido. Dan sam bata santa ba. Itama dai yarinyar kallonta take yi. Sai kuma ta nuna ƙofar dake da takalma kusan ƙafa goma tana faɗin, “Ki shigo mutanen gidan suna ciki. Muma baƙi ne yau muka zo”.          Kamar Maanal zatai magana sai kuma ta jinjina kai kawai tayi gaba, a ranta tana maimaita zancen yarinyar da daga gani zatai ɗan karen surutu. Sallama ta sake yi bayan yarinyar ta matsa ta bata hanya, batare da jiran amsa ba kawai ta shiga ɗauke da handbag nata tana faɗin, “Ammie, Hameed, Waleed wai duk kuna in......”. Turus ta haɗiye sauran maganar sakamakon saukar idanunta akan Ammie dake zaune kanta a sunkuye kamar ma tana kuka. Da sauri ta saki bag ɗin hannunta ta nufeta, a gabanta ta durƙusa tare da riƙo hannunta tana mai leƙa fuskarta. “Ammie miya sameki kamar kina kuk....?”.      Nan ma ta kasa ƙarasawa ganin fa da gaske kukan Amma keyi. Amma sai Ammie ɗin ta sakar mata murmushi da sake jimƙe hannunta cikin nata tana ƙoƙarin sharce hawayen da ɗayan hannun. Ina tuni Manaal da zuciyarta ta tsarga tai wata irin juyawa tana kallon wanda ke cikin falon. Nene ta fara kalla. Sai Daddy, sai wani dattijo daya sata ɗan sakin baki, tana kai dubanta ga wanda ke a gefensa ta miƙe zambar, jikinta har wani tsuma yake ta nuna tsohuwar dake a gefen mutumin da ta zuba mata idanu. Sai dai kuma ta kasa ma magana lips ɗinta ne kawai ke ɗan karkarwa. A hankali Ammie ta riƙo hannun nata cikin tsawatarwa ta ce, “Manaal minene haka kike yi. Ki zauna ki gaishe su”.        “Ammie never!!”.   Ta faɗa wani irin kuka dake zuwa maka batare daka shirya ba na kufce mata. Hannunta dake cikin na Ammie ta warce ganin mutumin ya yunƙura ya miƙe da alama wajenta zai nufo. Tuni tai ƙofar dake cikin falon da gudu abinta tana sakin wani irin kuka mai ban tausayi da taɓa zuciya. Duk kallo suka bita da shi. Yayinda mutumin ya furzar da zazzafar iskar bakinsa maƙoshinsa na wani irin kaikawo a wuyansa da sauri-sauri alamar shiga tsananin damuwa. Tsohuwar nan ya kalla, itama kallonsa take cike da damuwa. Kanta ta ɗan girgiza masa. Sai ya sake furzar da huci mai kauri yana komawa ya zauna a inda ya tashi saboda maganar da tsohon nan yay masa.        Nene ce ta katse shirun nasu da faɗin, “Kuyi haƙuri mu bata lokaci zata huce. Kunga ana saka ran sai ma gobe in ALLAH ya kaimu zata iya tazo gata ma tazo yau babu zat.......” Sauran maganar ta maƙale sakamakon shigowar Shahidah da Amaal dake dariya Barrah da Haneeff biye da su... Sororo Amaal da Shahidah sukai suma cikin wani yanayi, sai Shahidah ce tai ƙarfin halin juyawa ta ɗan kalla Ammie. Ganin kan Ammie a gefe ita bama kallon ta inda suke take ba ya sakata maida kallonta ga Amal da itama ta ɗago. Sai kuma duk suka maida kan suka duƙar ƙasa fuskokinsu na sake bayyanar da fushinsu. Nene ce tai ƙarfin halin musu sannu da zuwa. Sai kuma ta nuna musu wajen zama na kujerun dake kusa da su.      Wani irin tsuma jikin Babu dake tsaye kamar ma wanda ya daskare yake, gashi ya zubama Amal da Shahidah idanu kawai...       “Shahidah bakuga baƙi bane?”.   Nene ta faɗa cikin son katse musu yanayin. Kallonta duk sukayi, da ido tai musu nuni da mahaifin nasu. Wani irin taunar lips Amal tayi, sai kuma tai yunƙurin barin wajen tana hawaye. Ganin haka yasa itama Shahidah yunƙurawa zata bar wajen da sassarfa, amma sai carab Babu ya riƙo hannunta. Cak ta tsaya hawayen da take riƙewa na rige-rigen zubowa.      “Shahidah”.     Ya kirata cikin tsananin taushin murya da sanyi. Hawayenta ta share tare da juyowa cikin dakiya ta kallesa. Hannun nata ya saki, dan duk da ba kallon raini ta masa ba ko wulaƙanci har tsakkiyar ransa yaji nauyi da tasirin kallon. Batace masa komai ba itama tabar wajen tabi ƴar uwarta data shige ɗakin Ammie. Duk abinda ke faruwa a idon kowa ne harda Daddy dake a falon, hatta Ammie datai uwar watsi da su tana kallonsu ne ta gefe ido......     Tsohon nan ne yayi murmushi, da faɗin, “Masha ALLAHU girman ɗan mutum ba wuya. Shekara bakwai da wasu watanni kawai da bamu gansu ba sai duk suka canja mana kamar ba su ba”.      Murmushi Nene ta sake yi mai faɗi, “A sosai su Maanal duk sun canja musamman ma Maanal ɗin. Dan wannan gaba ɗaya ba waccan Maanal ɗin da kowa ya sani bace ba. Sai dai muyi fatan kuma yanzu ALLAH ya kawo miji na gari”.      A tare suka amsa da Amin. A hankali Ammie ta miƙe tana faɗin tana zuwa. Babu wanda ya dakatar da ita ta nufi ɗakin da Maanal ɗin ta shiga, dan tafi tsoron yanayinta fiye da na Amaal da Shahidah. Gashi taga su ɗakinta suka shiga, ita kuma Maanal nasu ta shiga.....       Fitowar ta daga bayi dai-dai da shigowar Ammie ɗakin. Juyawa tai da sauri zata koma cikin bayin Ammie ta dakatar da ita.       “Maanal!”.   Cak ta tsaya sai dai bata juyo ba. Sai ma hawaye dake rige-rigen zubowa daga idanunta wanda dama su takeyi tunda ta shiga wankan. Cikin ɗacin murya da fitar sautin kuka ta ce, “Ammie waya kawosu garemu? Mi sukazo yi mana? Mi suke buƙata kuma yanzu a garemu. Ko anan ɗin ma sun zo su koremu ne? Sun zo su sake tozartamu a idanun mutanen arziƙinmu na nan ne suma? Ko sunzo su sake shegantamu su aibanta ki.....” kuka yaci ƙarfinta ta kasa cigaba da maganar. Hannu Ammie takai ta share hawayen da suka wanke mata fuska itama. Tare da matsowa kusa da ita, hannunta ta riƙo tare da juyo da ita suna fuskantar juna...........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖5️⃣4️⃣ ______________ ......... “Maanal!”.     Ammie ta kira sunanta cikin rawar murya tana mai share mata hawaye da sakin murmushi mai ciwo. Da ƙyar ta sake ƙoƙarin yin magana amma ta kasa saboda muryarta dake neman sarƙewa. Sai kawai ta jawo Maanal ɗin jikinta ta rungumeta tsam-tsam. A tare suka saki kuka mai ƙarfi.       “Ammie kice su tafi, bana son ganinsu wlhy. Sam bana ƙaunar sake ganinsu a rayuwata. Ko tunasu nayi ƙara jin tsanarsu nakey.....” yanda take magana cikin kuka itama Ammien cikin kukan ta ce,       “Shiiiiii bana son irin wannan maganar sam Maanal. Shi ɗin mahaifinku ne. Ita ɗin kakarku ce. Sunada muhimmanci mai girma da hakki a kanku. Koma mi kike tunani ki bari kinji, wannan tsakanin ni da su ne. Kuma ai komai ya wuce ko”.     “Bai wuceba Ammie, bakuma zai wuce ba, har abada kuma bazai wuce ba. Ni dai kawai su tafi. Idan ba hakama zan bar musu gidan. Gara na wuce na koma Abujan. Idan sun wuce sai na dawo”.       “Babu inda zaki je Autana. Kin san yanda nayi kewarki kuwa. Wata nawa ban ganki ba sai video call da bai gamsar dani. cikin lallashi Ammie take maganar, tare da kama Maanal suka koma bakin gado. Sosai take matuƙar ƙaunar Autar ta, dan ita ta fuskanci jarabawa guda uku ne a lokaci ɗaya. Shiyyasa ta fisu jigata da galabaita. Ga babbar jarabawar ciwo mai haɗari da take tare da shi. ALLAH ma dai ya ƙaddara tana da sauran kwana da tuni ta zama tarihi a cikinsu. Shigowar Nene ya katse Ammie daga lallashin Maanal ɗin. Kofin hannunta ta miƙama Maanal ɗin da faɗin, “Ga masoyiyar taki tunda kun mamemu, muda ke muku shirin zuwa wani satin biki sai kawai ku diro mana yau babu notis ja'irai kawai”.       Hannu takai ta share hawayen da suka gagara tsaya mata. Fuskarta a ƙwaɓe ta ce, “Ni garin ya isheni Nene kuma ina kewarku sosai.”          Cike da dabara irin ta manya Nene ta sanya dariya da dungure kan Maanal. “Ja'ira baki son garin amma gaki nan kinyi ƙyau ai. Nifa har wani ɗan ƙiba naga kinyi ma, ji kumatu dan ALLAH ko Asiya?”. Ta ƙare maganar da kallon Ammie tana jan kumatun Maanal. Murmushi Ammie tayi cike da ƙara jin ƙaunar Nene dake tamkar mahaifiyarta a yanzu, ta matuƙar taka rawar gani akan lamarin Manaal musamman a sanda take a halin mutuwa da rayuwa. Ta jinjina kanta da share sauran hawayenta tana faɗin, “Sosai kuwa Nene. Autah tayi ƙiba ba kamar sanda ta dawo sarvese ɗin nan ba. Ga fatanta yay wani kwanciya luff abinta halan ma bata tunawa damu ne a can”.        Da sauri Maanal ta waro idanu akan Ammie, sai kuma ta shagwaɓe fuska da faɗin, “Kai Ammie kema kina biyema Nene ko?”.     Dariya Nene da Ammie sukayi a tare. Nan fa suka cigaba da tsokanar Maanal har sai da sukaga ta ɗan sake tasha kunun gyaɗar da Nene ta kawo matan. Ammie da kanta ta ɗakko mata kaya ta tashi ta shirya. Tana ƙoƙarin maida towel ɗin datai wankan cikin toilet Daddy yay sallama.... ___________★      A bala'in hargitse Hajiya Basariyya ke kallon Huznah. Hakama sauran ƴan uwanta. Sai kuma duk suka zaburo kanta suka baibayeta suna tambayarta accident tayi?. Babu wanda ta iya amsawa a cikinsu, hakan yasa Hajiya Basariyya ta kama hannunta kawai suka shiga bedroom. Kamar jira take suna shiga ta rungume mahaifiyar tasu tana mai fashewa da kuka. Ƙanƙameta itama Hajiya Basariyyar tayi hankalinta na ƙara tashi. Sai dai bata iya cewa komai ba har sai da Huznah tai kuka sosai sannan. Ruwa ta bata tasha kafin ta tambayeta abinda ke faruwa.        Huznah bata ɓoyemata komai ba daya faru tun daga zuwanta Abuja har yau da suke tahowa. Shiru tayi tana nazarin komai daki-daki. Ta jima shiru kafin ta miƙe tana cema Huznah, “Tashi kije kiyi wanka zan saka Afrah ta kawo miki abinci da magani, sai kisha ki kwanta ki huta zamuyi magana anjima”.      Kai kawai Huznahr ta jinjina mata itama....      Ɗaki Hajiya Basariyya ta shiga tare da ɗaukar waya tayi kiran aminiyarta. Bugu biyu kuwa ta ɗaga, ko gaisawa basuyi ba ta ce, “Aminiya akwai matsala fa?”.       “Matsala kuma Aminiya! Tami?”.    Tsaf ta zayyane mata komai da Huznah ta sanar mata. Cikin jinjina al'amarin Maman Yaseerah ta ce, “Eh lallai akwai matsala. Dan kuwa Darma family da su Majdiya jini ɗaya ne, auren zuminci ne tsakanin Aliyu Darma da babbar yayarsu Fateema. Amma Aminiya miyyasa tun farko baku sanar min cikakken sunan yaron ba?”.        “Wlhy nima iyakar abinda na faɗa miki shi na sani, itama kuma Huznahr na tabbatar shi kaɗai ɗin ta sani”.      Ajiyar zuciya Maman Yaseerah ta saki, sai kuma ta jinjina kanta da faɗin, “Aminiya wannan maganar tafi ƙarfin waya kizo kawai”.          “Okay in sha ALLAHU cikin satin nan kafin a fara bikin nan zanzo. Ai dole ma na shigo dan na fahimci al'amarin nan shiri yake so na haƙiƙa. Babu ruwana da wata alaƙar yaron da Majdiya, koma ya suke sai Huznah ta mallakesa tunda tana sonshi kuma yana da kuɗi”.     Dariya Maman Yaseerah tayi daga can, sai kuma ta ce, “Ina bayanki wlhy. Ni kin ma tuna min miya faru ne wai naga jiya Alhaji ya dawo da dare, yau kuma da safe naji suna waya da Alhaji Usman akan zai zo kadunar”.         “Wlhy bamu san abinda ke faruwa ba muma. Tashi mukai kawai muka ganshi a gidan. Ina shirin naje na bincika da safe sai kuma ga baƙi anyi ban san daga ina ba, naga dai ya shiga dasu sashen Asiya, yanzu kuma sai ga ƴaƴanta da Huznah”.     “To aiko kiyi azamar bincikawa. Dan al'amarin kamar ba ƙarami bane, ina kuma ƙyautata zaton wannan baƙin sun fito ne daga zuri'ar ita Asiya da yaran nata ne”.         “Iye! Ya akai kika sani?”.     “Ba tabbatarwa nayi ba nima. Amma ga Alhaji nan na shirin tahowa Kaduna ɗin ma, amma lallai akwai abinda ake ɓoye muku”.       “Tab ɗin cakwakiya kenan, a lallai dole ne na bincika, ko dama shiyyasa naga tun jiya Uwar ɗan ke cika da batsewa, ban san miya faɗa mata ba mai gidan, haka itama Asiyan duk tayi sukuku”.      “Humm munafukai, wannan gida naku ai sai ku, na tabbatar akan auren ƴayan nasu ne”.      “Wlhy fa sai mu. Kinga bara naje kozan samesa a sashen nasa zan kiraki daga baya. Amma ki farama Malam bayani akan al'amarin dai kafin na shigo, dan ƙilama zuwa gobe zan shigo kawai in sha ALLAHU”.      “To shike nan hakan ma yayi, sai na jiki”.     Daga haka sukai sallama kowa ya ajiye wayar. Shiru Hajiya Basariyya tayi zuciyarta cike da tambayoyi fal. Sai dai rashin makamar riƙewa yasa ta tattara komai ta ajiye gefe. Fitowa tai ta shiga ɗakin Huznah. Sai ta sameta ta fito wanka tana shafa mai. Zama tai har sai da ta kammala ta shirya ta taimaka mata taci abincin tasha magani ta kwanta sannan ta tashi ta fito. Sashen Daddy ta nufa, amma sai ta samu yana tare da baƙi. Haka dole ta fito bayan ta gaidasu dan ya haɗe fuska ta yanda bataga wajen wargi ba balle samun damar yin halin nata na munafunci..     Shima Daddyn ɗan girgiza kansa kawai yay yana mai kai ɗauke idanunsa daga kallonta. Dan yaji a ransa wani tsegumin ne kawai ya kawota......        ____________★         *_TUNA BAYA.._* Sautin kukanta a maimakon sallama daya karaɗe gidan ne ya saka mahaifiyarta da ƴan uwanta fitowa kusan a lokaci guda. Sai dai babu wanda yay magana sai ido da suka zubama ɗan saurayin yaron dake goye da ita a bayansa da ita kanta mai kukan.        Kallo ɗaya yay musu batare da yayi magana ba ya ƙarasa ga tabarmar dake a jingine jikin bango ya ɗauka ya shimfiɗa. Kafin ya sauketa a hankali tamkar mai tsoron yaddata ƙasa. Ita kam kamar wadda ta ɗosana a kan wuta. Yana direta a saman tabarmar ta wani sake ƙwallarewa da ihun kukan nata. Cikin ɗan nuna rikicewa da sake bayyana damuwarsa akan fuska ƙarara ya juyo gareta. Ƙafar da take ɗangalewa ya riƙe. “Banace kiyi shiru zan rama miki ba. Na rantse miki daga nan gida kawai zan shiga na ɗauka kekena har gidansu sai naje na rama miki. Sannan na masa dukan tsiya”.         “To ni ka tashi kaje”. Ta faɗa cikin taɓara da ƙara ƙarfin ihun kukanta. Bama ta gama rufe bakin ba ya miƙe. Fisha ya kalla matar dake tabbatar da mahaifiyar yarinyar ce saboda kamanninsu. “Ammie dan ALLAH ki saka min ruwan zafi a ruwa yanzu zanje na dawo zan gasa mata ƙafar”.       Cikin sauri Ammie tai ƙoƙarin dakatar da shi ta hanyar kiran sunansa. Sai dai ina har ya fice da mugun hanzari da sassarfa. Kanta ta ɗan dafe tare da maida dubanta ga ƴar budurwar da zata iya kai shekaru goma sha ɗaya. “Amaal! Kinga maza bisa gida kicema Oum-Fadeel karta barsa ya fita”.            “To Ammie!”. Yarinyar ta faɗa cikin hanzari itama tana fisgar hijjab. Dai-dai nan Ammie ta dawo da kallonta kan yarinyar data sake wani ƙwallara uban ƙara tana tittirza ƙafafu da faɗin, “Ni dai kar a hanashi. Sai ya ramomini....”     Tsawa Ammie ta daka mata. Tare da nunata da yatsa. “Idan baki min shiru ba na rantse da ALLAH zan tsantsama miki jiki da magribar nan. Ai dama tunda naga kun jima baku dawo ba nasan kina can ɗaukar maganar da kika saba. Shima Ajwaad ɗin sakarai dake biye miki, kin tashi kin cire uniform ɗin ko sai na ci ƙaniyarki....”           Kuka ta sake fashewa da shi amma bamai sauti ba yanzu dan tana tsoron Ammie. Sai kuma ta nuna ƙafar tana faɗin, “Ammie nafa karye ne a ƙafar...”     “Karyewa?”. Ɗayar yarinyar da zata kaiwa sa'an saurayin yaron, idan ma ta girmesa kaɗan ne dake tsaye tana kallonta ta faɗa kafin ma mahaifiyar tasu ta amsa.            “Eh wlhy Didi. Ba Najib ɗin gidan Maman Ayna bane ya bugeni da keke mun fito islamiyya. Kuma shine yaƙi tsayawa harda cema Besty wai in ya isa yazo ya rama min”.      Shigowar Amaal da wata ƙyaƙyƙyawar mata mai kama da yaron sosai yasa babu wanda ya tanka mata. Matar ta nufeta tana faɗin, “Subahanallahi Baby na miya faru?”.           Fuska ta taɓe tana satar kallon Ammie, sai kuma ta ɓarke da kuka tana nuna ƙafarta da shigewa jikin matar da takai kusa da ita zaune. “Oum ba Najib bane ya karyani a ƙafata. Kuma na kasa tafiya sai da Besty ya goyoni ma”.       Sosai Oum ta shiga faɗa tana dudduba ƙafar da faɗin in fa har taji ciwon da gaske bazasu yarda ba. Ammie da taga abin nasu bana ƙare bane ta katseta da faɗin, “Aunty ALLAH ki daina biyema iskancin Manaal. Ni yanzu ma sonake nasan baki dai bar Ajwaad ya fita ba ko?”.          Kafin Oum ta bata amsa Amaal ta ce, “Wlhy Ammie ya tafi, inata kiransa ko kallona baiyiba ma ya kwashi keke da gudu”.     “Innalillahi banga ta zama ba”. Ammie ta faɗa tana shiga ɗaki. Babu jimawa sai gata ta fito da hijjabi a hannu. Sai lokacin Oum ta dubeta tana dariya. “Wai ina zaki je?”.          “A binsa zan mana. Sai na bari a cutar min da yaro tunda ke naga kinama ɗaukar abun bada muhimmanci ba, in dai kika biye ta wannan yarinyar wataran sai ta saka har ke an kai station ɗin ƴan sanda” Bata jira amsar Oum ba ta fice abinta.      Fitowar Ammie a gidan dai-dai da isowar Ajwaad a kekensa rigarsa ta islamiyya a yage. Fuskar nan ciɗin-ciɗin ga goshinsa ya ɗan kumburo kaɗan, sai gefen lips ɗin da jini kaɗan shima. Da sauri ta nufesa tana riƙe keken da faɗin, “Innalillahi Ajwaad, yanzu faɗan kaje kayo saboda ALLAH. Anya wataran Manaal bazata saka a maka dukan da zaka kasa tashi ba a anguwar nan?”.            Cikin ɓacin ran da muryarsa dake fita can ƙasa-ƙasa ta kasa ɓoyewa ya ce, “Ammie ciwo fa yaji mata a ƙafa, sai na ƙyalesa yaci bulus? Ko yanzu ban ƙyalesa ba sai na jera sati ina masa duka”.     Ƙasa magana ma Ammie tayi ta zuba masa ido kawai. Har ya shige shi da keken gidan bata iya ta motsa ba. Wannan abota na bata mamaki tsakanin Manaal da Ajwaad. Wata irin abotace mai ban mamaki da tsayawa a zuciya. Basu kasance sa'anni ba dan ya girmeta sosai kusan shekara bakwai ne tsakaninsu ma, sannan basu kasance jinsi ɗaya ba. Amma akwai wata irin shaƙuwa a tsakaninsu da sam babu ita a tsakaninsu da ƴan uwansu na jini ma. Ita abun har tsoratata yake yi.........✍️       _Tofa wasa farin girki, 🥱🥱yanzu zamu koma tushe fa._ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖5️⃣5️⃣ ______________ .......Su ɗin ƴan asalin jihar Kebbi ne, a garin Giro dake ƙarƙashin Suru LG. Aiki ne ya kawo mijinta nan cikin Kano kasancewarsa jami'in ɗan sanda. Ba Kanon suka fara zama ba. Sun zauna jihohi kusan uku a tsahon shekarun aikinsa. Sai dai shekara biyu data wuce aka maidosu nan cikin Kano suke zaune a anguwar sharaɗa. Yaransu uku ne duk mata. Shahidah itace ta farko, sai Amaal. Sai Manaal. Lokacin da sukazo Kano shekarar Manaal huɗu kacal, amma sai baƙar fitina a cikinta da shegen surutu. Manaal irin yaran nan ne masu shegen wayon tsiya da ɗan karan surutu kamar an musu ƙauri da kan akku. Ga ɓarnar masifa da jan faɗan tsiya. Sam bata ragama ƴaƴan jama'a dan ko anfi ƙarfinta saita ƙwaci kanta da cizo da bula ƙasa ko jifa. Gata suke mata matuƙa kasancewar itace kamar auta a gidan yanzu. Kowa ya kwaso abunsa zai ce Maanal. Musamman ma mahaifinsu da suke kira Baabu.       Dawowarsu cikin Kano sun samu abubuwan cigaba da dama, ciki harda ƙarin girma da Baabu ya samu, ita kuma ta fara kasuwancin turarruka da gyaran jiki irin na mata. Inda suke sabon wajene da aketa gine-gine, dan ko gidan dake a jikin nasu ma ana kan gina shi ne ba'a kammala ba. Sai dai an kusa kammala aikin. Hakan yasa kusan kullum zakaga mai gidan yazo da yaransa maza uku musamman ma weekend. Jefi-jefi sukan ɗan gaisa da Baabu idan anyi sa'a yana gida ko ya dawo wajen aiki. A haka ranar wata asabar yana gida suka tashi da shirin yin alala da yace yana buƙatar ci. Ammie ta kammala gyara wake ita da Shahidah da zata kai markaɗe. Sai kawai Maanal ta sanya rigima itama zataje. Cikin haushi Shahidah ta ce, “Dama kin bar damun kanki dan babu inda zanje dake. Haka kawai muje kita jibgar yaran mutane a gidan markaɗen kamar ranar da kika fasama ƴar mai markaɗen kai”.     Ihu Maanal ta sake ƙwallarawa tare da zubewa ƙasa tana burgima akan ita wlhy sai taje fa. Dai-dai nan Ammie ta fito da bulala da nufin tsula mata amma sai Baabu ya hana ta hanyar amshe bulalar ya ɗaga Maanal daga ƙasan. Daga haka ya fita da ita a gidan yana lallashinta. A dai-dai lokacin motar makwafcin nan nasa ta iso anguwar. Baabu bai wani maida hankalinsa ba dan baima san shi bane kasancewar bawai ya wani riƙe motar tasa bane. Sai da yay parking a gaban gidan nasa ya fito tare da matasan samarin ƴaƴansa uku sannan Baabu ya maida hankalinsa kansa. Sun gaisa cikin mutunta juna, yayinda suma yaran suka gaida Baabu da girmamawa. Ya amsa musu da kulawa yana mai shafa kansu, yayinda shima babansu yakema Maanal wasa.        “Ƴan samari yaya sunanku?”. Cewar Baabu yana shafa kan ƙaramin su. Babban ne ya bashi amsa da. “Ni Fadeel. Wannan Fawzan. Sai Auta Ajwaad.”       “Masha ALLAH, ALLAH ya albarkaci rayuwarku manyan gobe.”.    A tare suka amsa da Amin. Yayinda mahaifinsu keta faman murmushi saboda surutun da Maanal ke zuba masa. Sai kuma can ta kalla Ajwaad dake ta faman cin chocolate ɗinsa, cikin ɗan tura baki ta ce, “Kai yaron nan bazaka tsammin alawanka bane. Inata haɗiyan yawu amma sai sha kakeyi rowa haramun dai”.        Ba ƙaramin dariya ta basu ba. Banda Ajwaad ɗan kimanin shekaru goma sha ɗaya daya wani yamutsa fuska ya harareta ya ɗauke kansa. Sai Baabu da ya ɗan harareta shima. Amma ita ko'a jikinta ta maida kallonta ga Babansu ta na sake faɗin, “Abbansu kace masa ya tsammin raina ya biya”.           “Kinga manta da shi Babyna. Muje na baki ina da ita da yawa. Daga yau kuma kema ni Abbanki ne ba nasu su kaɗai ba.”     Cike da murna tace, “Eh”. Gaba yay da ita zuwa motarsa. Ya fiddo chocolate uku ya bata biyu a hannu, tare da ɓare ɗaya ya sake miƙa mata. Cike da jin daɗi ta amsa. Tare da juyawa ta murguɗama Ajwaad baki da faɗin, “Mai rowa ɗan wuta. Nima kuma ga nawa”.         Harararta nan ma yayi. Yayinda su Fawzan sukayi dariya. Shiko Baabu duk kunya ta ishesa. Ƙarfin halin Maanal da banne a rayuwa. Shegen surutunta da wayonta da suka girmi shekarunta na tada masa da hankali. Duk inda ake neman fitinannen mutum aka samu Maanal an rufe littafi kawai. Sai dai yana mata fatan idan ta ƙara girma ta canja daga hakan.. ƙiri-ƙiri da zai shiga gida yace tazo suje taƙi. Dole babu yanda ya iya ya barta wajen Alhaji kamar yanda ya roƙa.       Yini guda Maanal na tare da Alhaji Aliyu Darma, Tare da yaransa uku da tuni ta saki jiki da su. Musamman Ajwaad da tunda ya fito da kayan wasansa ta naniƙe masa. Lokacin da rana tayi sai ga Shahidah da kula cike da alala an kawo musu. Sosai Alhaji Aliyu ya nuna jin daɗinsa tamkar ya ari baki dan godiya. Anan ma Shahidah tayi-tayi Maanal ta bita suje gida amma taƙi. Dole ta barta itama ta tafi. Sai da akai la'asar sazu tafi sanan su Fawzan suka rakata har gida da ledan kayan ciye-ciye da kulan da aka kawo musu alala sukai godiya. Yayinda ita kuma ta shiga kuka saita bisu, sai da Baabu ya mata tsawa sannan ta nutsu. Dan a duniya Maanal na tsoron hargagi musamman na Baabu..       Wannan rana itace sanadin tarayyar waɗan nan ahali guda biyu. Dan kuwa washe gari sai ga itama mahaifiyar su yaran ta biyosu domin yin godiya. Anan ne kuma ta tarar da Ammie nama wata amarya gyaran jiki, itama tace ai sai ai mata kuwa.. tunda tazo Maanal na manne da ita. Kasancewar yaranta ita duk maza ne tana masifar son ƴar budurwar yarinya, shiyyasa tana ganin Maanal da jiya tasha labarinta a wajen ƴaƴanta yarinyar ta shiga ranta. Ga wayonta da surutunta na sakata nishaɗi. Yau ɗin ma dai da ƙyar aka raba Maanal da su, musamman Ajwaad da wasansu na yau yafi na jiya armashi. Dan yau ya saki  jikinsa ba kamar jiyan ba. Haka yake bashi da saurin sabo sam, akanyi baƙi a gidansu kwana da kwanaki babu ruwansa da su, dan shi yarone mai irin shegen tsantsenin nan, ga zuciyar tsiya da ƙulafucin iyaye. Ammafa idan ya soka to yaso ka kenan. Idan kuwa baka masa ba to babu abinda zakai masa ka birgesa ko kaja ra'ayinsa da shi. Shiyyasa a yau ɗin ma mamakinsa ya kasa barin Oum ganin yanda ya saki jiki a gidan tamkar a gidansu. Dan duk inda kaga Ajwaad yaje yaci maka abinci kansa tsaye to lallai yanayi da masu gidan.... ★★★          Kafin Alhaji Aliyu ya kwaso iyalansa su tare a sabon gidan nasu daya haɗu matuƙa gaya shaƙuwa da zuminci mai ƙarfi ya shiga tsakaninsa da iyalan Baabu ta yanda har suna kallon kansu tamar wasu ƴan uwa na jini. Oum ba itace kawai matarsa ba, ashe tana da amarya ma, sai da suka tare su Ammie suka sani. Bayan tarewar tasu kuma sai al'amarin ya ƙara ƙarfi fiye da tunanin mai hasashe. Ba shaƙuwar ahalin biyu ne kawai abin mamaki ba. Wadda ke a tsakanin Ajwaad da Maanal tafi zama abin kallo ga kowa. Dan takai a yanzu ako ina ɗaya yake ɗaya na wajen, shiyyasa idan baka sani ba baka taɓa gane ainahin gidan kowannensu. Dan takai yanzu ma Maanal taƙi zama a makarantar da take yi da yan uwanta. Da safe anta dagama kenan tace ita Ajwaad zata bi tasu makarantar. Anyi lallashin, an daka, anyi kurarin duk a banza. Hakan yasa Alhaji Aliyu roƙar Baabu damar maida Maanal makarantar su Ajwaad ɗin, kasancewar itama tana tare da Nursery, primary harda da secondary ne a tare. Daƙyar Baabu ya yarda dan bashi da yanda ya iya, haka aka maida Maanal makarantar su Ajwaad amma a ɓangaren Nursery. Shiko yana a primary 3 ne. To ashe rigima bata ƙare ba, dan kuwa Maanal sam bata zama ajinsu saina su Ajwaad. Anyi-anyi amma taƙi, da malaman sukaga tanada ƙwalwar karatu matuƙa, dan duk abinda akayi kafin kace me ta ɗaukesa a kanta harma tafi wasu ƴan ajin sai kawai aka ƙyaleta. Dan koma an kaita can ɗin ba zama take yi ba, sai dai taita jibgar ƴaƴan jama'a tana kukan ita dai wajen AA zataje. (Dan itace ta saka masa AA daga ji Oum ta faɗa ta kama ta haye tana kiransa AA).        Hajiya Maanalu mai abin mamaki kenan. Dan daga Nursery 2 dai tuni tayi jumping zuwa primary 3 abinta. Hakama a islamiyya tuni ta koma ajin su Ajwaad. Dambe da rigima kuwa sai abinda ya ƙaru. Duk da tana a cikin waɗanda suka girmeta kullum cikin takalar tsiya take. Taimaka rashin kunya kace zaka daketa ka gamu da Ajwaad. Dan duk abinda zai taɓa Maanal a duniyar nan Ajwaad baya ƙaunarsa. Hatta Ammie idan ta daki Maanal sai taga fushi a fuskarsa. Idan ko su Shahidah ne duk da sun girmesa koda yake kusan sa'an Amaal ne yana girmeta kaɗan sai fa yarama mata. Idan kuwa yana gidan tai laifi Ammie tace zata daketa sai yaje yace shi a dakesa a maimakonta, idan kuma ta riga ta ritsata tana duka zaije ya kareta shi a dake san. Idan abu aka bama ɗaya ɗaya bazai taɓa cinsa ba sai ɗaya na nan. Hatta da kaya ya koma yanzu iri ɗaya ake musu, idan kuma ya banbanta na mace da namiji kamar atamfa, lass, yadi to dole a ɗakko kala guda. Ajwaad shine tsifar kan Maanal, shine rakata kitso, shine wankin ƙananun kayanta irinsu pant, hula, vest da sauransu. Haka shima nashi idan zai yi tare zasuyi tana jagwalgwalo. Tun ana ɗaukar abun nasu wasa har kowa ya fahimci ba wasan bane aka kawo ido aka zuba musu. Sai dai iyayen na matuƙar kulawa da duk wani motsinsu saboda tsoron bin wata hanya mara ma'ana da a yanzu har yaran akan samu a ciki....      Alhamdullah a yanzu dai haka Maanal nada shekara tara cif a duniya, yayinda Ajwaad keda goma sha biyar. Suna a ajin ƙarshe na primary. Kasancewar Ajwaad nada tsayi kamar ƴan uwansa tuni ya tserema Maanal a girman jiki fintinkau duk da dama can ya fitan. Itako tana tsaka tsaki a tsayi saboda bata gama girma ba, gata muguwar siririya kamar ka hureta ta zube a ƙasa. Zuwa yanzu shaƙuwarsu ta sake wuce inda ake tunanani, baka isa kaji kansu ba. Hatta abinci tare suke cin abinsu. A hakan ma dan ana tsaye a kansu wasu abubuwan da yawa ana ƙoƙarin hanasu da tunatar da su halacci da haramcin dake a tsakanin iyakar da alaƙarsu zata yiwu. Kuma Alhamdullah suna fahimta da kiyaye abubuwa da dama duk da bawai sun balaga bane ba. Garama shi Ajwaad alamomin hakan sun fara kusantoshi yanzu... __________________★           Yanda take tura baki gaba ya sashi tsayawa yana kallonta. Sai kuma ya ɗauke kansa ya maida ga agogon falon. Ganinfa idan ya biye mata makara zasuyi ya sashi duƙawa. Dariya ta saki da siririyar muryarta kafin ta ɗane bayan nasa. Lunch box ɗinta da school bag ɗin dake ajiye ya tattara ya ɗiba sannan ya miƙe. Dariyarta tasa Ammie dake kitchen leƙowa. Takaici ya sata tsayawa kawai tana kallonsu, sai da ya kai ƙofa yana ƙoƙarin fita ta dakatar da shi.      “Yanzu Ajwaad bazaka hutama ranka ba dai?. Ka sauketa ta taka da ƙafarta, dan ubanta ba tun jiya ta taka ƙafar ba”.          Cikin yanayinsa na sanyin murya ya ce, “Ayya Ammie ALLAH ƙafan bai sakin mataba har yanzu. Bari muje su yaya Fadeel na jiranmu a mota”. Kafin ma ta sake cewa wani abu harya fice. Kai kawai Ammie ta girgiza tana komawarta, dan babu abinda suke buƙata yaran nan sai addu'a. Idan ta tuna mutuwa zata iya ɗaukar wani a ciki tabar wani har tausayi suke bata. Idan kaga Ajwaad na farin ciki ko surutu to tare yake da Maanal. Dan duk rashin son maganarsa sai da ta sakashi ringa yi, idan ma baiyi ba addabarsa take har sai ya tanka zata barsa. Kokuma taje ta takalo masa faɗan da dole ya tafi ramo mata......✍️.      😀😂🤣Eh lalle su Maanal an tsula tsiya a nahiyar arewacin Najeriya 😆🏃 ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖5️⃣6️⃣ ______________ ........Tuni su Fawzan har sun shiga mota. Da sauri driver ya amshi kayan hannunsa, shi kuma ya ƙarasa gaba ya buɗe ya sakata dan nan ne wajen zamanta dama. Sai da ya gyara mata skirt ɗin ta sannan ya rufe ya zagaya kusa da ƴan uwansa ya zauna. Cikin tsokana da dariya Fawzan ya ce, “Oh oh Lilly bestyn Auta (Dan haka suke kiranta). Auta bestyn Lilly. Idan yaran nan kuka girma munada kallo a anguwar nan wlhy. ALLAH yasa dai kar ku haɗiye juna ko ku ƙone mu saboda eh......” ya ƙare maganar cikin shaƙiyanci. Banza Ajwaad ya masa, sai ma ƙoƙarin fiddo books ɗin Maanal yake yana dubawa. Yayinda Fadeel da suke kira (Babban yaya)  yay ƴar dariya, hakama driver. Tsagal Maanal ta ce, “Yaya F minene eh...? Kuma sai mu cinye kammu kamar mayu”.      Dariya Fawzan ɗin ya sake kwashewa da shi. Tare da faɗin, “Lilly ba yanzu zaki san eh.. ba. Sai nan gaba. Ke dai ALLAH yabar tare”.         Cikin rashin damuwa tace, “Amin”. Sai kuma tai kneeling a kan kujerar ta saitin Ajwaad da yay kamar baya a motar tana lekensa. Cike da shagwaɓa ta ce, “Besty!”.    Ɗagowa yay kawai ya kalleta batare daya amsa ba. Wuyansa ta nuna masa tare da faɗin, “Baka sa tie ɗinka ba fa”.      Kansa ya maida ya cigaba da gyara mata abinda batai dai-dai ba a assignment ɗin da aka basu da tayi, dan jiya fushin faɗan da yayo mata bai tsaya ya koya mata ba sai Amaal ce ta mata. Kafin a hankali ya ce, “Zan saka sai mun sauka”.           “Ohhh”.      Ta faɗa tana cigaba da kallonsa. Duk abinda taga zai gyara mata sai tayi tambaya. Shi kuma ya bata amsa. Har ya kammala ya maida books ɗin shima ya maida hankali a kanta. Gaba ɗaya ta addabesu da surutu. Baka jin muryar kowa sai tata. Sai ko dariyar driver da Fawzan masu tayata dan shima Babban Yaya halinsa kusan irin na Ajwaad ne. Baida yawan magana. A haka dai har suka iso makarantar dan akwai ɗan nisa. Kasancewar a tsohuwar anguwarsu makarantar take. Ƙyawunta da son da suke mata yasa iyayen basu canja musu ita ba. Kullum driver zai kawosu ya dawo ya ɗaukesu.      Yanzun ma dai shine ya goyata, Fawzan ya taya shi da ɗaukar bags ɗin su da lunch box ɗin abinci data kasance ɗaya. Sai da ya rakasu har aji da kayan sannan ya wuce sashensu na yan secondary inda baban yaya Fadeel ya nufa. Ajwaad kam na sauke Maanal a mazauninsu dan kujerarsu ɗaya ta jawo bag ɗinsa. Zip ɗin baya ta buɗe ta ciro gogaggen tie dan uniform ɗin nasu kamar suit suke. Sai dai na mata skirt ne na maza wando. Zama yay a kujera tana daga saman desk ya miƙo mata wuyansa. Tsaf ta ɗaura masa dan tuni ta iya. Idan ka gansu dolene su birgeka kamar ba ƙananan yara ba. Ta gama ta gyara masa rigar da faɗin, “Wai Besty mi akai maka kake ta fushi. Inma dan ƙafatace ba nace maka na daina jin zafin ba. Tun jiya fa ka daina dariya why?”.          Shiru yay baice mata komai ba. Hakan yasa takai hannu saman sumarsa daya gyara ta shiga harmutsata. Hannunta yay ƙoƙarin riƙewa amma taƙi ta bari. Dole sai da yay dariyar da take so sannan ta barshi. Cikin dariya ya ce, “Besty wannan wane kalar kuturun wulaƙanci ne”.        Itama cikin dariyar ta amsa masa da, “Kamafi ƙyau a haka ALLAH”.    Rankwashi ya kai mata, ta kauce. Yay ƴar ƙwafa da faɗin, “Zan rama ALLAH ya kaimu Friday”.      “Mi zakayi?”. Ta tambaya tana ƙoƙarin ɓare lollipop daga cikin ledanshi.     “Meyi baya faɗa ai”. Ya bata amsa yana fige alawar ya saka a baki. Hararsa tayi, shima ya rama. Sai kuma suka ƙyalƙyale da dariya. Saida sukayi mai isarsu sannan ta zare alawar daga bakinsa ta sha. Sake maida masa tayi a bakin. Haka sukaita yi har suka shanye kafin malami ya shigo musu su nutsu kamar basu ba.            Kowa yasan a ajin basa taɓuwa. Maanal rashin kunya da tsokanar masifa, gashi itace ƴar ƙaramar ajin dan duk sun girmeta tunda rigimarta ce ya kawota cikinsu ba shekarunta ba. Ka taɓata ka haɗu da AA. Yanada zuciya ga ƙarfi, dan in har ka taɓa Maanal ka taɓoma kanka kuwa. Gashi da shegen naci akan faɗa dan baya barin saita kwana. Surutun Maanal yasa kullum sai an sakata a cikin ƴan surutu na ajin. Idan kayi surutu naira ashirin, in sha ALLAHU kafin a tashi sai ta tara ɗari biyu. Idan ance ta bayar taƙi biya, idan shugaban ajin ya biye mata suyi faɗa AA ya kamashi ya daka. Dole class master ɗin su ya maida shugabancin ajin akan Maanal ɗin, aiko tunda ta samu damar nan take tsula tsiyarta. Ta cikama ƴan aji kunne da surutu su suyi ta maka sunanka. Azo biyan kuɗi kaƙi biya Ajwaad yay maganinka. Hakan yasa ake tsoronsu, ta gefen ƙoƙari kuwa sune masu zuwa na ɗaya dana biyu, basu taɓa tsallake wannan positions ɗin ba. Ada kafin Maanal tazo ajin AA ke ɗaukar na farko, wata yarinya na ɗaukar na biyu. Amma tunda Maanal tazo shikenan fa matdayin yarinyar ya rushe. Kullum sune dai su biyun nan, babu ƙoƙarin da wasu basuyi ba ganin an turesu amma abin ya gagara.       Ada saboda kalar fatarsu tazo ɗaya kowa ɗauka yake Maanal ƙanwar su AA ce ta jini. Duk da babu ta inda suke kamanni na halitta sai dai fatansu yana kama sosai. Sai da tafiya tai tafiya kowa ya fahimci yanda alaƙar take. Duk da su ɗin yara ne da yawan mutane kai tsaye suke fassara alaƙar zuwa wani abu daban. Duk da su dai yaran babu wani abu makamancin hakan a tattare da furucinsu na baki, mawuyacine ma ace su sun san minene wata soyayya, amma hatta iyayensu na ganin zuwa nan gaba Wannan shaƙuwar zata iya rikiɗewa ta koma hakan....      (To bari muga ko hakan zata kasance😀🏃.)       ★★★      Kamar kullum ƙarfe uku dai-dai aka tashe su. Suna ƴan farko-farkon fitowa. Dan sun san driver ɗin su baya wasa. Ƙarfe biyu da rabi yake isowa. Uku a gate take masa. Ilai kuwa sun samesa inda yakan jirasu kullum. Dan su Fadeel ma har sun rigasu fitowa. Cike da tsokana Fawzan dake kallonsu ya ce, “A'a ƴar gurguwar Besty an warke ne?”.     Ƙafar tata ta kalla sai kuma ta kalla Bestyn nata. Harararta yay itako ta ƙyalƙyale da dariya tare da matsawa kusa da Fawzan. Nuni ta masa daya duƙo dan ya fita tsayi nesa ba kusa ba. Haka suke dogaye dan iyayensu ma duk dogayene. Shiyasa ko shi AA ɗin dake 15 years ya shallaketa sosai. A cikin kunne ta gwargwaɗama Fawzan, “Dama fa dan ya goyani ne Yaya F. Dan yanzu idan nace yamin goyo sai yace wai na girma. Kaga yanzu ai na samo dabara”.      Mi Fawzan zaiyi ba dariya ba. Harda kwanciya jikin mota. Yayinda Maanal ta shige mota da sauri itama tana tata. Tsaf AA ya fahimci abinda ta faɗa dan yana kallon motsin bakinta. Dan haka baice komai ba ya saka bags ɗin su da lunch box ɗin cikin booth kawai shima ya buɗe motar ya shiga. Dai-dai nan Yaya Fadeel ya iso shi da abokinsa. Ta saitin da Maanal take abokin nasa ya ɗan leƙa yana tsokanarta dan mutuniyarsa ce. Kafin ya mika mata chocolate da in dai suka haɗu sai ya bata. Cike da ɗoki ta masa godiya tare da bye-bye. Ta buɗe chocolate ɗin ta, kamar yanda suka sabama juna duk abinda ɗaya ya samu sai ya raba da ɗaya ta raba biyu ta juya ta miƙama Ajwaad rabi duk da tasan ba lallai yasha wannan ba. Ilai kuwa maimakon ya amsa harararta yayi ma. Ta taɓe baki kamar zatai kuka da faɗin, “Wai miyasa baka son amsar abun hannun Ya Abdull ne Besty?”.      Banza ya mata bai tanka ba. Maimakon hakan ma sai ya ciro headphone ɗin daya saka a kunnesa. Dariya Fawzan yay da faɗin, “Kishi mana Alaji. Kinga Lilly bani nasha tunda shi na mazan ya motsa”.          Bata wani fahimci mi Fawzan ɗin ke nufi ba ta miƙa masa duka chocolate ɗin ta juya itama a dole tayi fushi. Shiko ya ce, “Uhhm gaba takaini, ban nasha faɗan masoya hutu”.       Harararsa Babban Yaya yayi. Cikin ɗan zaro ido ya ce, “Babban Yaya mi kuma na maka kai kuma?”.     “Kai bakinka bashi da linzami ko?”. Cewar Fadeel ɗin.    “To ayi haƙuri babban yaya na daina”.        Shiru motar tayi babu wanda ya sake magana har suka iso gida....      Fuuuu ta fice batare data kalla kowa a cikinsu ba ta shige gidansu. Shima motar ya buɗe batare da ya jira an shiga cikin gida ba kamar yanda aka saba ya shige da ƙafa. Oum na zaune a falo ya shigo. “Oum good afternoon ”. ya faɗa a taƙaice yana shigewa ɗakinsu, dan su duka su a ɗaki ɗaya suke amma kowa da gadonsa. Da kallo Oum ta bisa, sai kuma ta girgiza kai kawai dan tasan ɗayan biyu ne fushin Auta. Kodai wani ya taɓa Maanal, ko shi da ita sun samu saɓani. Shigowar su Yaya Fadeel ya katse tunaninta. Su duka ita suka nufa, cike da shawagwaɓa suka zauna a gefe da gefenta kowanne yasa kansa a kafaɗarta duk da sun fara zama samari, koma muce sun zama. Dan Fadeel yana shekarar ƙarshe ne a secondary, Fawzan na aji biyar. Fuskarta ɗauke da murmushi ta shafa kawunansu dake cike da suma. “Da alama yau sojin gidan nan sunyi laushi, dan fuskar baban Commondo ya nuna.”       Dariya Fawzan yay da faɗin, “Oum wancan Commondo ɗin naki ba gajiyace ta maisheshi haka ba. Saɓani ya samu da rabinsa, bakiga sun barmu da dakon kayansu ba”. Ya ƙare maganar yana nuna school bags ɗinsu da lunch box ɗaya da suke zuba abinci.         Cikin ƴar dariya Oum ta ce, “Ai zancen gizo baya wuce ƙoƙi. Tana ina ita to?”.      Yanzu kam Fadeel ne yay ɗan murmushi da bata amsa da, “Itama tayi gida. Wannan yaron naki da alama zaiyi kishin tsiya Oum. Shike nan shi babu wanda ya isa ya raɓu Maanal koda da wasa ne. Ki lura da ko mu dan baida yanda zaiyi ne kawai. ALLAH ki ringa masa addu'a ALLAH ya sassauta masa”.            Sosai Oum ta saki murmushi mai ƙayatarwa. Kafin ta miƙe tana faɗin, “Kuna sakama autana ido a gidan nan. Tunda baya so a raɓar masa half ɗinsa a bar masa kayarsa mana”.      Miƙewa sukai suna dariya suma. Kowa ya nufi ɗakinsa domin yin shirin islamiyya kuma....       ★★      A ɓangaren Maanal itama dai haka ta shiga gida a kumbure. Su Shahidah dake dawowa tun ƙarfe biyu daga tasu makarantar suna tsakar gida suna wankin uniform. Da kallo suka bita dan ita ko kulasu batai ba. Koda ta shiga ciki ma bata nema inda Ammie take ba duk da tana jin motsinta a kitchen. Ɗakin Ammien ta shige dan ita nan ne wajen zamanta. Ɗakinsu kullum cikin faɗa take da su Shahidah da neman fitina da su, su sakata abu taƙiyi, su daketa Ajwaad ya rufesu da azabar masifa kamar Shahidah bata girmesa ba. Ganin haka yasa Ammie maidota ɗakinta ita sai aka zauna lafiya. Duk da a hakan ma idan neman maganar ta ya tashi takan shiga ɗakin nasu tayi ɓarnarta son ranta ta fito. Suyi magana tace ita sharri sukai mata mi zatai a ɗakin nasu da babu komai sai tarkace.        Gado ta faɗa ta sanya kuka, tafi mintuna goma har sai da Ammie tazo tana mata magana. Da farko ƙin tashi tayi ma sai da ta daka mata tsawa sannan ta tashi a firguce dan tana tsoron tsawa matuƙa. Cikin haushi Ammie ta ce, “Wane kalar shashanci ne kuma wannan zakizo kinama mutane kuka daga dawowa. ALLAH Manaal ki maida hankalinki a gidan nan. Ke kullum girma kike amma kina sake maida kanki wawuya. Baki da lafiya ne?”.      Kanta ta girgiza alamar a'a. Sai kuma ta sake matso hawayen da suka taru mata a manyan idanunta da kai kasan idan ALLAH ya kai ta zama budurwa ba ƙaramar ƙyaƙyƙyawar yarinya za'ai ba. Dan ko yanzu mutane da yawa kance za'aga ƴammata a wajen nan. Maanal irin yaran nan ne masu shiga rai lokaci guda. Balle gata da baki da rawar kai kuma. Uwa uba tsiwar tsiya...      Tsaki Ammie taja da sake faɗin, “To uwar miye kika shigo kinama mutane kuka?”.       Fuska ta sake ƙwaɓewa da faɗin, “Ba Besty bane ba. Kawai dan Ya Abdull abokin Babban yaya ya bani chocolate na bashi yaƙi ya sha, shine kuma yake fushi da ni bayan ban masa laifin komai ba”.      Kasama magana Ammie tayi, ta zuba mata idanu kawai cikin wani yanayi. Bazata gaji da faɗa ba al'amarin yaran na bata tsoro, tun basu tafasa ba suna neman hanyar ƙonewa. Gefe ta ture tunanin batare da ta sake cewa komai akan batun ba ta juya zata fita. “Ki tashi kiyi wanka kizo ga abinci dan lokacin islamiyya ya kusa”.          Jitai kamar tace bazata je islamiyya ɗin ba. Amma tasan faɗar hakan na nufin Ammie yin tamaula da rayuwarta. Dan mace ce mai zafi sosai da sam bata ɗaukar wargi.......✍️ _To miya canja Ammie yanzu🤔?_        ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖5️⃣7️⃣ ______________ ........Tamkar haɗin baki ta ɓangarorin biyu su duka sun tasa abinci gaba sun kasa ci. Yanda Ajwaad ke can a gaban Oum yana faman juya ɗan abincin daya zuba a plate anan ma haka ne ga Maanal. Oum dai ta ɗan lallashi Ajwaad, harta amshi spoon ɗin ta shiga bashi da kanta. Sai dai laumarsa batafi huɗu ba yace mata ya ƙoshi a shagwaɓe. Lallaɓashinsa ta shiga yi amma yace shi fa ya ƙoshi kamar ma zaiyi amai yake ji. Babu yanda ta iya dole ta barsa ya miƙe yana goge baki bayan ya saɓi bag ɗin islamiyyarsa. Dan su duka ukun sanye suke cikin uniform. Da kallo yayun nasa suka bisa da Mamy da itama take a falon, sai dai sam hankalinta bama a kansu yake ba. Sai dai babu wanda yayi magana har ya shiga store dake jikin kitchen ya fito, da alama akwai abinda ya ɗakko. Oum kawai ya kalla cikin sanyinsa ya furta, “Oum kimin addu'a sai na dawo”.       Fuskarta da murmushi ta ce, “ALLAH ya tsare Autana. ALLAH ya bada ilimi mai albarka. ALLAH ya daidaita tsakani kai da Besty”.        Idanunsa masu haske ya ɗan waro waje, sai kuma ya juya da sauri zai fice abinsa. Ai ko Fawzan ya kwashe da dariya. Yayinda Fadeel yay murmushi shi da Oum, Mamy dai kamar ma bata san sunayi ba. Harya saka ƙafarsa ɗaya waje Oum ta kira sunansa. Juyowa yay batare daya amsa ba.       “Mamy fa?”.   Oum ta faɗa babu wasa a fuskarta. Juyawa yay shima ya kalla Mamyn, sai kuma cikin sanyinsa da magana ƙasa-ƙasa ya furta, “Mamy sai na dawo”.        Karan farko ta ɗan juyo ta kallesu su duka, sai kuma ta ɗauke kai a taƙaice ta ce, “ALLAH ya bada sa'a”. Daga haka ta maida hankalinta a kallonta. Murmushi Oum tayi, zuciyarta na sake cika da so da ƙaunar kishiyar tata da takema kallon ƴar uwa. Yayinda Ajwaad ya fice abinsa yana amsawa...     Da ƙafa ya fito dan makarantar tasu babu nisa. Hakan yay dai-dai da fitowar su Shahidah Maanal biye da su. Bai tanka musu ba suma basu tanka masa ba. Sai da suka ɗan gota shi sannan ya lura da Maanal dake binsu a baya kamar bata so. Kallon juna sukayi kusan na sakan goma. Sai kuma kowanne ya ɗauke idonsa. Shi ya fara yin gaba like baima ganta ba. Itama sai tai nata gefen, sai dai duk da hakan a jere suke tafiya cikin tazara a tsakkiyarsu ta yanda ba lallai ka yarda tafiyar tasu ɗaya bace.        A aji ma koda suka zauna babu wanda ya kula wani. Sai da kusan minti uku sannan ya ciro kwalin drink da babban biscuit ya ajiye gabanta bayan ya buɗe kowanne. Batare da yayi magana ba ya ɗauka Al-qur'ani ya hau bitar karatu. Itama sharesa tayi taƙi ɗauka taci. Sai ma ta ɗakko littafin koyon larabci mai ɗauke da hotuna na zane-zane ta hau zana color. Cikin haushi ya ƙwace littafin ya sake tura mata biscuit ɗin da lemo.        “Bana ci”.     Ta faɗa a kumbure tana kalmashe ƴan hannayenta a ƙirji ta da juyar da kanta gefe. Cikin haushin shima ya ce, “K kin iyama mutane laifi ki fisu zuciya. ALLAH idan baki ɗauka kin ci ba sai na bar ajin nan.”     Tasan zai yi abinda yafi hakan. Dan haka bayan ta gama harare-harare ta ɗauka ta fara ci. Ajiyar zuciya ya saki a hankali yana sake maida hankalinsa ga Alkur'anin. Yanda taci da yawa ya sake tabbatar masa bata ci abinci ba. Yasan wannan halinta ne. In har tana fushi komi za'a bata in dai ba shine ya bataba bazata ci ba. Sauran wanda ta rage ɗin ta miƙa masa, babu musu ya amsa shima ya fara ci, wani ɗan guntu daya gutsira ya rage a hannunsa ta kamo hannun nasa ta saka a baki. Sai ya dungure mata kai. Dariya ta ƙyalkyale da shi. Hakan shima ya saka shi sakin dariyar. Kamar basu ba kuma sai suka warware. Bayan ya gama sukai bitar Alkur'anin tare kafin malami ya shigo musu.....     Koda aka tashi suka fito a jere Shahidah da Amaal kallonsu kawai suka tsaya yi, hakama Fawzan daya fito kallonsu yake yana dariyar shaƙiyanci. Maanal ce kawai ta tura baki gaba, shiko gogan bai kulashi ba yay gaba riƙe da bags ɗinsu. Koda suka iso gida su duka gidan su AA ɗin suka shiga. Tun a ƙofar falo Maanal ke ƙwala kiran Oum. Sai dai Oum na ɗaki bata amsa ba. Haka ta shigo ta nufi hanyar ɗakinta. Sai dai kafin ta shige sukaci karo da Mamy dake fitowa daga kitchen. Dakatawa Maanal ɗin tayi, tare da faɗin, “Mamy ina yini”.      Amsa mata Mamyn tayi da kulawa, tare da tambayarta makaranta. Maanal ta ce, “Alhamdullah” tana wucewa ɗakin Oum. Shima Ajwaad dake biye da Maanal ya gaishe da Mamyn, batare data kallesa ba ta amsa kawai tana wucewa abinta. Ɗan Binta yay da kallo, ganin kamar zata juyo sai ya ɗauke kai ya shige ɗakin Oum abinsa.       Oum na sallar magriba Maanal baje a gadonta. Ya ajiye bags ɗin nasu yana kallon Maanal ɗin. “Malama sallan fa?”.      Ya faɗa yana hararanta. Baki ta tura gaba da faɗin, “Zan huta ne na gaji. An jima ba sai nayi ba”.     Harara ya sake zuba mata, batare da yayi magana ba ya wuce toilet ɗin Oum, alwala ya ɗauro ya fito, gadon ya nufa, inda Maanal ta sake bajewa tana lumshe ido alamar barci ma take son yi. Duka hannayensa biyu yasa ya jawo ƙafafunta ƙiyyyy har ƙarshen gadon, ita kuma ta buga ihu tana kai masa duka da faɗin, “Ni ka barni ba nace zanyi ba anjima”.     Ko kulata baiyi ba ya direta a tsaye, cike da tsiwa ta dubesa zatai magana ya ce, “ALLAH kika sake magana sai na ɓata miki rai. Wuce alwala konaje na haɗaki da Babban Yaya ko Ammie”.      A duniya Maanal na tsoron Babban Yaya da Ammie, dan sune ke cimata ƙaniya a zauna kafiya. Cikin jin haushi ta cire ɗan hijjab ɗinta ta jefa a gadon Oum sannan ta wuce bayi fuuu. Shima ficewarsa yay batare daya sake kulata ba. Koda tayo alwalar kusa da Oum tazo tayi sallar itama...      Koda aka idar da sallar shi da Fawzan suka dawo, direct ɗakin Oum suka shigo, sun samu Maanal a saman jikinta kwance tana mata surutu. Fawzan ya gaida Oum, shima Ajwaad haka. Amsawa tai fuskarta da murmushi tana kallon Ajwaad, sai kuma ta kalla Fawzan suka saki murmushi. Ajwaad ɗin na kallonsu, amma bai tanka ba ya zauna kusa da Oum ɗin shima yana ɗakko bag ɗin Maanal na islamiyya. Sai da ya gama fiddo books ɗin duka sannan ya kalla Maanal dake ta surutu wa Oum.        “Parrot tashi kiyi aikin islamiyya idan anyi isha'i mayi na boko”.      Cikin ɓata fuska alamar fushi take da shi har yanzu, “Tace ni kayi min barci naje ji”.        “Ko mutuwa ko?”.    Ya faɗa cike da gatse. Tashi Maanal tai zaune idanunta cike da ƙwalla tana kallonsa. Sai kuma ta kalla Oum da faɗin, “Oum kin gansa ko, so yake ma na mutu ya huta ban girma naga ya zama kamar Daddy da Baabu ba”.         Da ƙyar Oum ta danne dariyarta, “A'a in sha ALLAHU Auta bazaki mutu ba sai kinga girman Auta ya zama kamar Daddy da Baabu. Yo ina dalili Auta gaskiya ka bari. Ƙuruciya tare tsufa tare in sha ALLAHU”.       Dariya Fawzan ya sanya da faɗin, “Wato Oum soyayyar nan fa na tafiya da ni.....”         Harararsa Ajwaad yayi, sai kuma ya rufe books ɗin zai tashi Oum tai saurin kama hannunsa ta maida shi ta zaunar tana gumtse dariya. Sai kuma taima Maanal nuni data matsa suyi karatun. Ƙarfin dariya Fawzan ya ƙara tare da miƙewa ya fice yana faɗin, “In dai nine ma nayi nan. Bara dai naje mu daidaita da Amaal nima kozan samu Besty na”.     Filo Oum ta ɗauka ta jefa masa. Ai ko ya ƙarasa fita a guje. Shi dai Ajwaad bai kulashi ba. Sai aikin da suka fara shi da Maanal na islamiyya. Basu tashi ba kuma sai da aka kira magrib. Ana idarwa ya dawo suka ƙarasa suka fara na boko kuma anan falo. Dan Oum sam bata barinsu su biyu a ɗaki, shiyyasa ma aka saka camara a ɗakinsu duk da ba'a taɓa kama ko ɗayansu da wani halin rashin tarbiyya ba gaskiya....       Da ƙyar Maanal ta bari suka kammala homework ɗin nan. Abinci ma tace ta ƙoshi sai da Oum ta lallaɓata ta bata tea. Ai ko tana gamawa ta ɓingire a jikinta ta hau barci. Sai da barcin yay nisa Ajwaad yazo ya ɗauketa ya kai ɗakin Oum ya kwantar, dan yasan ta gaji ɗin kam, kuma yanda tayi barcin nan duk bala'in dama za'ayi ayi bazata yarda tayi wanka ba.        Dama haka take, kusan rayuwarta raba dai-dai ce a tsakanin nan gidan su Ajwaad da can gidansu. Dan ko kayanta a rarrabe suke saboda ko'ina a gidajen biyu tana zama. Wani lokacin sai tai sati bata leƙa gidansu ba sai kewarta ta ishi Baabu ne ya aiko a kirata sannan. Idan kuma ƴan arziƙin na kanta kullum sai taje ta gaida Ammie da Baabu ɗin. Idan kuma aljanun nata suka koma can gidansu kullum zata zo ta gaida Oum ne......       _________★       A kwana a tashi asarar mai rai. Yau ga su Maanal da yin graduation na gama primary. Zokaga rawar kai wajan mutuniyar. Balle da taji Oum ta shirya musu party ita da Bestyn nata. Duk da dai shi ya nuna baya so, amma Oum tace babu fashi sai tayi tunda Maanal naso. Babu yanda ya iya dole shima ya sakko aka hau shirye-shirye. Ammie kanta ba son fatin take ba, dan tasan hanyar kashe kuɗi kawai Oum ta ƙirƙiro ma kanta. Dan koda ta sanarma Babu ma kai tsaye yace shifa gaskiya bai da kuɗi. Cikin sanyin murya ta ce, “Aunty ce fa dama ta shirya musu bawai kuɗi zaka bayar ba. Naga ya kamata ka sani ne shiyyasa”.       “Oh to ALLAH ya taimaka. Dan nima ina da nawa uzirin ne ma shiyyasa. Tunda hutun nan mai tsayine ina son muje gida gaskiya. Gwaggo nata magana akan hakan”.     Wani irin faɗuwa gaban Ammie yayi, a take zufa ta shiga tsatstsafoma goshinta. Ganin ya juyo yana kallonta saboda jin tayi shiru tai saurin gyara yanayinta tayi ɗan murmushin yaƙe. “Kai amma nasan yaran nan zasuyi murna sosai. Musamman ma Maanal da tunda aka baro garin ba'a koma da ita ba shekara kusan shida.......”       “Oh ke baki murna kenan?”.    “A'a haba yazance bana murna ni da garinmu. Baka fahimceni bane ba dai”.    Komai bai sake cewa ba sai shigewa toilet ma da yayi dan dama shirin wanka yake yi. Jagwab Ammie takai zaune zuciyarta na wani irin farfashewa a ƙirjinta. Gaba ɗaya jikinta rawa yake. Tabbas ta cancanci tai kewar tushenta, sai dai rasa wani giɓi da babban ƙalubalen data baro yasa mata jin tsoro da rashin son zuwa garin. Sai dai tasan ko giyar wake tasha bata isa bijirewa umarnin mijin nata ba kuma ɗan uwanta. Jin motsin zai fito yasa ta miƙe da sauri ta fita a ɗakin, tana mai ƙoƙarin danne komai..........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖5️⃣8️⃣ ______________ .........Babu bai sake bi takan bikin su Maanal ba, yama maida hankali a shirya musu tafiya gida. Yayinda Ammie taketa ƙarfin halin yin nata shirye-shiryen itama batare da su yaran sun san mi ake ba. A haka ranar juma'a akai partyn da Oum ta shiryama Maanal da Ajwaad. Abin kamar wasa sai gashi ya ƙayatar. Anci ansha yara sun sha bidirinsu musamman Maanal da ko zama ta huta batayi. Shi kansa AA duk ta takurama rayuwarsa. Haka dai aka tashi gab da magriba, tsabar gajiyar da Maanal tayi a inda tai sallar magrib anan ta ɓingire barci. Kallonta kawai Oum tai tana murmushi, dan a tare sukai sallar a ɗakinta. Ɗaukarta tai cak ta maida saman gadonta ta kwanar, ita kuma ta cigaba da lazimin ta.      Bayan idar da sallar isha'i su Ajwaad suka shigo harda Aban su. Kai tsaye ɗakin Oum Abah ya shigo. Yakai zaune bakin gado fuskarsa da murmushi yana kallon Maanal ya ce, “A'a anan surukar taki tai barci?”.        Dariya Oum tayi tare da faɗin, “Kaji Aban su da wata magana suruka kuma?”.      Murmushin sa ya sake faɗaɗawa shima da faɗin, “Eh mana. Ai abunne na Maanal da autanki akwai ban mamaki. Zan so wannan abotar tasu ƙarshenta ya kasance hakan”.       “To ALLAH ya zaɓa abinda yafi alkairi. Idan hakan ta kasance zanfi kowa farin ciki Gandanga. Dan har cikin raina nake jin matuƙar ƙaunar yarinyar nan wlhy”.            “Nima haka yarinyar ta shiga raina sosai. Badan kar ace ma na cika zumuɗi ba nifa da a yanzu zan ɗaura musu aure kawai”.    Dariya sosai Oum keyi. Shima Aba na tayata. Sai da sukai mai isarsu Oum tace, “Ayi haƙuri dai a barsu sukai hankalin kansu. Kar a tauyesu musamman ita da take mace. Gara shi namiji ne yana da damar auren fiye da ita”.     “Hakane kuma kema kinyi magana. Kinga nama shafa'a ɗazun Baban nasu ke sanar min zasuje gida hutun nan ma, dan mahaifiyarsa tana kewarsa sosai.”         “Kai masha ALLAH, ai ni har ƙoƙarin su nake gani ma. Musamman Ammien Shahidah. Garama shi tace yaje kusan sau uku. Amma ita tunda suka dawo Kano bataje ba hakama yara”.      “Abin ne sai a hankali ai. Kin san idan iyali sukai nauyi tafiya ma wahala take yi. Balle wannan aikin nasu na ƴan sanda sai a hankali. Kwanaki ma kamar zasu masa transfer ALLAH dai ya taimakesa aka samu canji. Hankalinsa ya tashi sosai dan yace baya son yawon da yake da yaran musamman a yanzu da suka fara girma”.              “Yana da gaskiya. Ita kanta takance ALLAH yasa ko ya samu canjin wajen aiki ya barsu su anan Kano dan tana jin daɗin zaman garin......”      Sallamar Ajwaad ta katse Oum. A tare suka amsa masa da bashi izinin shigowa.    “Lafiya Autana?”. Oum ta faɗa tana kallonsa. Fuska ya ɗan yamutse kamar zai saki kuka ya ce, “Oum kaina ke ciwo. Kuma ina jin yunwa”.       “Ya rabba. Autana badai duk kai kawon nan baka ci abinci ba?”.    Kansa ya ɗaga mata alamar “eh”. Da sauri ta kama hannunsa suka fice tana jan salati. Aba ya mike yana musu dariya....    ___________★          Sosai su Ammie suka shirya wannan tafiya. Yayinda su Shahidah keta zumuɗi banda Maanal da tace idan fa bada Ajwaad ba babu inda zataje ita kam. Babu wanda ya tanka mata dai akan batun. Su dai sun cigaba da shirinsu kawai.     A ɓangaren Ajwaad ɗin ma tunda yaji batun tafiya jikinsa yay sanyi. Da farko shima ya nuna son binsu. Har ya samu Oum da maganar tace ita dai babu ruwanta ya sanarma Aba. Bai Musa ba ya samu Aban da batun. Amma sai ya kwaɓesa akan maganar. Kai tsaye ya sanar masa bazai iyu ba. Suma zasuyi tasu tafiyar zuwa Adamawa suga gida...           Tafiya ta tabbata, amma ansha fama da badaƙala kafin Maanal ta yarda. Sun tafi tana kuka kashirɓan kamar zata shiɗe. Shima uban gayyar da taurin kansa yasa baiyi kukan ba da farko yana ganin sun wuce ya shige ɗaki ya kwanta a gadonsa sai ga hawaye. Daga ƙarshe da zazzaɓi ya yini ranar. Har washe gari sai da aka sanya masa ƙarin ruwa.     A ɓangaren Maanal ma kuka taci sosai har sai da Babu ya mata buyagi, itama ƙarshe zazzaɓi ya rufeta. Taita kwara musu amai a mota. Haka suka isa Kebbi tayi ligiff a wahale. Anan suka ɗan tsaya aka dubata. Washe gari suka ɗauki hanyar Suru da shima keda ɗan nisa daga nan cikin birnin Kebbi ɗin. Dan a ranar ɗin ma basu isa ba sai da zuhur..     Gari ne tsaka tsaki a komai. ba ƙato bane can sosai. Ba kuma ƙarami bane ba. Suna da wutar lantarki sannan akwai titi har a cikin garin. Kusan zaka iya samun duk abinda kake so naci ana saidawa musamman wanda ake mu'amala da shi ako ina kamar su kayan sanyi, kayan marmari, nama, da ire-iren hakan. Mutanen garin na neman ilimi gwargwadon iko, dan suna da manyan mutane sosai a ƙasar da ake damawa da su a gwamnatin jahar dana tarayya. Daga Suru hanyar Giro suka ɗauka, nan kam basu isa ba sai yamma sosai. Giro dai ƙaramin garine, amma ƙauyene mai ƙyau da ƙayatarwa. Tun kafin motar Babu ta isa labari ya iso gidansu. Lokacin da motarsa ta tsaya tuni yara sun zagayeta cike da zumuɗi musamman ganin harda baƙin fuska da basu sani ba. Dan duk sanda aka haifesu wasu kuma sukai wayo Ammi bata garin.      Tun daga waje zaka san gidan ƙaton gaske ne. Dan ƙofa ce wangamemiya ƙwarai da gaske. Sai ƙatuwar bishiyar ceɗiya da kufan wutar makarantar allo irin ta tsangaya an zagayeta da dutsuna. Gefenta kaɗan massalaci ne da ɗakuna a jere kusan guda goma ko muce shaguna da jikin bangonsu duk alluna ne. Jiki a sanyaye Ammie ta fito fuskar ta ɗauke da murmushin ƙarfin hali. Yayinda su Shahidah keta kalle-kalle suna son tuno abinda suka manta musamman ma ita da aka tafi da ita da ɗan wayonta. Tuni yaran sun fara kwasar kayayyakin suna shiga dasu, yayinda su kuma suka bisu a baya Babu biye da su. Ɗakuna ne guda biyu masu kallon juna a farkon shiga. Ana hannun dama ke buɗe wani dattijo mai farin gashi fatt zaune kan buzu yanata rubutu a wani ƙatoton allo. A hanli Ammi ta cire takalman ƙafarta zuciyarta na mata ɗan sanyi, ganin haka yasa suma su Shahidah cirewa, yayinda Maanal ta dogara tana kallonsu...       “Barka da hutawa Baffah”.   Ammie ta faɗa a hankali kanta a duƙe dai-dai tana shiga cikin ɗakin. Sai lokacin tsohon ya ɗago ya ɗan kallesu fuskarsa da murmushi. Cikin kamala da tausa harshe ya furta, “Lale da mutanen garin dabo”.    Murmushi Ammie ta sake yi hakama Babu da ya shigo riƙe da hannun Maanal data dogare a ƙofa. Sai da suka kai zaune tsohon ya sake faɗin, “Ashe zaka cika alƙawari Habibu ka kawo min iyalanka na sake gani kafin na koma ga ALLAH?”.     Sosai Babu ya sake sunkiyar da kansa cike da girmamawa ya furta, “Ai min afuwa Baba, ai min afuwa”.    Murmushi tsohon yay mai faɗin gaske. Sai kuma ya miƙama Maanal dake ta faman kallonsa cikin zare ido hannu alamar tazo gareshi. Da sauri ta matsa jikin babanta tana maƙe kafaɗa alamar bazata je ba. Turata Babu yay yana mai daka mata tsawa. Cikin harshen turanci ya ce, “Wuce kije mana ban son raini”.        Duk da tsohon bajin abinda Babu ya faɗa yay ba sai yay murmushi. Dan ya fahimta ganin yanda Maanal ta zabura jiki na karkarwa ta matso inda yake sai dai duk a ɗarare. Bai ƙiba ya kama hannunta ya zaunar a gabansa. Cikin tausasa harshe ya furta, “Wannan shi ake gudu dama ai Habibu. Shiyyasa muke kwaɗayin ku ringa matso da iyalan naku gab damu koda lokaci-lokaci ne”.        “ALLAH ya huci zuciyarku Baba”.    Babu ya sake faɗa da sauri. Cikin sanyin murya itama Ammie ta nema afuwa. Kafin ta ɗora da gaishesa cikin girmamawa. Ya amsa mata da kulawa tare da tambayarta bayan rabuwa. Hakama su Shahidah duk suka shiga gaishesa. Hannu duka ya miƙa musu alamar suzo garesa. Babu musu duk suka matsa. Sai da duk ya taɓa kawunansu sannan ya tambaye su sun ganesa?. Kai tsaye Shahidah tace ta ganesa. Amma Amaal na ɗan inda-inda. Ta dai san ta sanshi sama-sama. Sai dai a wancan lokacin bai kai haka tsufa ba. Gashinsa kuma bai furace kamar yanzu ba. Murmushi yay da akazo kan Maanal da yana tambayarta kawai ta fashe da kuka. Itafa harga ALLAH tsoronsa take ji. Musamman wannan farin gashin nashi dogo sosai daya zagaye ƴar ramammiyar fuskarsa. Ga farin rawani ya naɗa akan nashi. Lallashinta ya shigayi tare da bata farar alewa dake cike da wata ƙwarya a gefensa. Badai ta sha ba amma ta daina kukan.....       Sun jima a wajensa dan har duhu na neman rufawa kafin su shiga cikin gidan. Lallai ƙaton gaske ne da sassa daban-daban. Tarin manyan turamen daka dake a ƙarƙashin bishiyar dalbejiya a farkon shigowa gidan zai tabbatar maka da hakan. Sai runbuna da ake ajiye abinci da aƙalla sun kai kusan ashirin. Yara ne sosai a haka ma dan mangariba ta rufa ne wasu basa gida. Sai mata da akalla sun kai goma sha biyar dake tsaitsaye wasu ma daga su sai karin ƙirji. A hakan kuma ƙalilanne a matan gidan, waɗan nan wanda bazasu iya haƙuri bane saboda zumuɗin son ganin Ammie da yaranta.     Itama Ammien ganinsu yasa tuni ta manta da fargabarta. Fuskarta da murmushi ta nufesu. To suma dai bakunan nasu a washen suke. Duk da dai wasu fara'ar tasu bata kai ciki ba. Su dai su Maanal na raɓe jikin Babu da matan nan keta faman yima sannu da zuwa. Garama Shahidah da Amaal na ƙoƙarin gaishesu da kalmar “Ina yini”. Lallai shekara shida ba kwana shida bace. Suma sai kallon yaran suke da mamakin canjawarsu. Sun yi girma kuma sosai musamman ma Maanal da aka tafi da ita daga garin tana ƴar shekara biyu. Yanzu ko gashi tana ƴar budurwa shekara takwas ai ba wasaba su a wajensu. Dan yara sun ma fara kula samari. Kamar Shahidah kuwa masu sha biyar ai sun haihu ta biyu kota farko dana biyu a ciki. Kamar Amaal mai sha uku sune amaren wannan shekarar..          Har sashen gwaggo akai musu rakkiya. Inda anan ne ɗakin da Ammie tai rayuwa a ciki yake. Wajene aka dan katange da ɗakuna guda uku. Ɗaya na Gwaggo mahaifiyar Babu ɗaya nata. Sai ɗayan na kishiyarta da bata wuce wata biyar a gidan ba ta fita. Fitar tata ce kuma ya ƙara mata baƙin jini a gidan da ma wajen surukar tata da bata samu sassauci ba sai da suka bar garin da zama. Gwaggon na saman wani ɗan dutse daga ƙofarta tana alwala. Sau ɗaya ta ɗago ta kallesu ta maida kanta. Amma haka Babu ya nufeta fuskarsa da fara'a yana faɗin, “Barkanki da wannan lokaci Gwaggona”.      Ganin haka itama Ammi da sauri ta matsa ta tsugunna tana faɗin, “Sannu Gwaggo! Mun sameku lafiya?”.   Maimakon ta amsa su su duka a daƙile ta jefama Ammie wani kallo ta maida idanunta akan su Shahidah dake tsaye suna kallonsu sannan ta maida ga Babu ta sakar masa murmushi. “Babana kasha hanya”.    Murmushin ƙarfin hali yayi dan abinda taima Ammin ya ɗan sokesa. Sai dai bai nuna ba ya danne abinsa ya maida mata da murmushin yana faɗin, “Aiko dai Gwaggo. Bara na je salla gashi har za'a shiga damma ina da alwala”.     Kanta kawai ta jinjina masa. Ya miƙe yana kallon su Shahidah dake rakuɓe suna kallon Ammie dake duƙe kanta a ƙasa har yanzu. “Ku kuma kukai tsaye anan. Ku shigo mana”.       Jikinsu a sanyaye suka ɗaga kawuna. Shi kuma ya fice batare daya waiwayesu ba zuciyarsa duk babu daɗi. Yasan dole sai haƙuri, dan hutun nan sam bazai zame musu na farin ciki ba sai abinda suka gani. Tsakaninsa da mahaifiyarsa babu wata damuwa. Amma yanda takema matarsa da yaransa abun na damunsa matuƙa. A ganinsa matarsa bata cancanci hakanba kodan hallacin iyayenta a garesa ya kamata Gwaggo ta rangwanta mata. Amma ina, ya rasa wace irin ƙiyayyace wannan mai zafi........✍️     ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖5️⃣9️⃣ ______________ Follow this link to join my WhatsApp community: https://chat.whatsapp.com/F7aIYP99bGn9mIqLhjUWKR GOLDEN COLLECTIONS TA TANADAR MUKU KAYAN ADO N FITA KUNYA KAMAR SU ATAMFA,LACES ABAYA SHOES AND BAGS DA KAYAN DECORATIONS D FURNITURES A FARASHI ME SAUKI __________ .........*_SU WAYE SU AMMIE?:-_* Alhaji Umar da mutane sukafi sani da Alhaji Umar Giro ɗan asalin jihar Kebbi ne a garin Giro dake ƙarƙashin Suru LG. An haifesa a babban gida da yay suna matuƙa a cikin garin Giro saboda kasancewarsu manyan mutane masu ƙarfin ilimin addini. Su kusan ashirin da bakwai mahaifinsu ya haifa, maza sunfi yawa, dan mata huɗu ne kawai a cikinsu, sauran su ashirin da uku duk maza ne. Malam Ibrahim shine mahaifinsu, sai iyayensu mata su uku. Ta tsakkiyar itace mahaifiyar Alhaji Umar, shi kaɗai kuma ta haifa a duniya, sauran ƴaƴa ashirin da shida duk na matan biyu ne. Dan matarsa ta farko haihuwarta goma sha ɗaya amma ƴaƴa goma sha shida duk nata ne. Sai amarya nada goma cif duk da itama dai wasu sun rasu a ciki.      Kishi sosai ake zubawa a gidan Malam Ibrahim, hakan yasa ƴaƴansa suka tashi da zafin ƴan ubanci. Kowa ɗan ɗakinsu kawai yake so. Wannan aƙidar tafi wahalar da Umar, dan shi kaɗai shi mahaifiyarsa ta haifa shiyyasa sam baya wani jin daɗin zaman. Yasha wahala ƙwarai da gaske a hannun ƴan uwansa, har takai karatun ma baya fuskanta dan anan cikin gidansu suke ɗaukar karatu wajen mahaifinsu, ƴan uwansa manya kuma sune gardawa a yanzu.        Ganin yanda Umar ɗin ke cikin tsangwama da ƙyara yasa mahaifinsu ɗaukarsa ya bama wani amininsa shima malami ne amma a can cikin birni, yanada tarin almajirai kuma Alhamdullah ana karatu. Mahaifiyarsa tasha kuka, amma hakan yafi mata kwanciyar hankali akan zamansa a gidan. Umar ya koma cikin birnin kebbi, kuma Alhamdullah yana samun ilimi, ya kuma kwantar da hankalinsa sosai dan Malam Khamisu ya saka shi cikin ƴaƴansa babu banbanci. Ƴaƴan malam Khamisu su suna karatun boko, hakan yasa shima Umar aka saka shi a boko.      Zamu iya cewa Umar ya fara karatunsa cikin nasara, kasancewarsa yaro mai basira cikin ƙanƙanin lokaci yay zarra. Ga kuma ilimin addini shima alhmdllh. Umar na zuwa Giro akai-akai saboda mahaifiyarsa, dan haka canjin da rayuwarsa ta samu a bayyane yake ga kowa. Cigabansa na saka ƴan uwansa sake jin tsanarsa da hassadarsa su da iyayensu, sai dai babu yanda zasuyi. A haka ya gama secondary school ya fara jami'a, yana level 2 ALLAH yay ma mahaifiyarsa rasuwa. Ya shiga tashin hankali matuƙa daga shi har mahaifinsu, sai dai babu yanda aka iya da hukuncin UBANGIJI. Bayan rasuwar mahaifiyarsa ya sama ransa dangana ya maida hankalinsa ga karatunsa, har ALLAH yasa ya kammala jami'a. A kuma wannan lokacin ALLAH yay ma uban riƙonsa Malam Khamisu rasuwa shima. Umar ya sake shiga ruɗani, dan komai ya fice masa a rai. Dan haka ya tafi yin sarvese ɗinsa nesa da Kebbi. A jihar Niger cikin garin Minna Umar ya fara Sarvese, inda anan kuma ALLAH ya haɗashi da matar aure. Lubabatu yarinya ƙyaƙyƙyawa mai ilimin addini da nutsuwa. Gata da haƙuri da tarbiyya. Cikin ƙanƙanin lokaci soyayya ta ƙullu tsakaninta da Umar da hidimar ƙasa ta kawosa garin Minna. Lubabatu su biyu ne a wajen mahaifinsu, daga ita dai ƙanwarta Shamsiyya. Suma ALLAH yayma mahaifiyarsu rasuwa matar uba ke riƙonsu, suna matuƙar shan wahala a hannunta. Hakan yasa Umar na nuna yana son Lubabatu mahaifinta ya bashi.      Cikin ƙanƙanin lokaci aka gama komai, dan kafin ya gama sarvese har ranar aure an saka musu. Yana kammalawa akasha biki. Nan Giro aka kawo amarya family house ɗinsu, dan ba auren nasu kaɗai akai ba harda wasu a cikin ƴan uwansa da suma akayi duk a ranar. Sai da aka gama shan biki, bikin da aka nuna matuƙar banbanci dan sam Umar baida wani gata a cikinsu, gashi itama Lubabatun duk sai a hankali tunda basu da wani gata suma sakamakon rashin uwa. Haka dai akayi biki aka gama, amare suka tare da mazajensu. Umar baya son zama a Giro, amma saboda kunyar mahaifinsa ya kasa magana. Ga aiki ya samu a Kebbi, sai ya zam dole ya koma Kebbin sai weekend yake zuwa. Sam Lubabatu bata jin daɗin zama a cikin waɗan nan ahali, dan kishi da ƴan ubancin da ƴan uwansa ke nuna masa duk sai ya tattaru ya koma kanta a yanzu. Ga matan ƴan uwansa suma sun sakata a gaba, facalanci mai muni ake zubawa a tsakaninsu. Musamman ma da Matar yayansu na biyar wanda Umar ke bimawa a wajen mahaifinsu mai suna Talle. Talle irin matan nan ne masu mugun hali da hassada da ƙyashi, duk wani cigaba tafi son ace itace da shi. Yaranta biyu a gidan, Habibu da mace, sai ƙaramin ciki da take laulayi. Tayi matuƙar tsanar Lubabatu a gidan, dan tafisu wayewa da cigaba. Ita tayi karatun boko har zuwa secondary kuma gana addini dan tayi sauka. Suko mafi yawansu musamman ma Talle kota allon bata nutsu tayi ba sai talla. Sosai matsi yayma Lubabatu yawa, dan matan ƴan uwan mijin nata sun haɗe mata kai bisa jagorancin Talle. Koda yaushe tana a ɗaki babu sakewa, idan kaga farin cikinta sai idan Umar na gidan. Ba kuma wai zaman nasa na hana ai mata abu bane, a'a farin cikin da yake bata a gidan ne kawai ke sauƙaƙa mata baƙin cikinsu. Ana haka ta samu ciki, haka taita rainonsa har lokacin haihuwa, sai dai ALLAH baiyi mai rayuwa bane wajen haihuwa ya rasu. Itama tasha wahala, wahalar data saka Umar roƙon mahaifinsu ɗaukarta su koma cikin Kebbi, dan kuwa tana naƙuda matan gidan babu wanda ya kulata wai ai bata gaya musu ba. Wannan yaja tasha wahala har ɗan ma ya rasu. Sai da Malam ya shigo gidan ne yake ji a wajen yara ransa ya ɓaci yasa aka kira wata unguwar zoma dake anan kusa da su. Ɗari bisa ɗari Malam Ibrahim ya basa goyon baya. Aiko ya tattara matarsa suka wucewarsu. Wannan abu ya baƙantama mutanen gidan rai sosai musamman irin su Gambo, sai dai basu da yanda zasuyi sai haƙuri.       Komawa Kebbi tama Lubabatu daɗi matuƙa, dan hayar gida madaidaici Umar ya kama musu. Ya kuma nema mata admission ta koma makaranta. Alhamdullah komai Lubabatu na samu yanzu, bata da wata damuwa. Ga Umar abubuwa nata zama masa. Dan ya shiga harkar kasuwanci tako ina kuɗi ke shigo masa. Sosai yake ƙoƙarin taimakama mahaifinsa dama ƴan uwansa duk da basu taɓa nuna jin daɗin abinda yake musu ba, sai dai Haruna mijin Talle shi da yake dama tun can yana son Umar, kasancewar sun tashi ne a tare. Matarsa ce da mahaifiyarsu da ƴan uwansa kan canja masa tunani wasu lokutan. Amma a yanzu sai yake ƙin biye musu suka ƙulle da Umar ɗin har ya fara jan ra'ayinsa ya fara kasuwanci shima anan dai Giro ɗin. Abinda Haruna ɗin yayi ya ƙona ran matarsa da ƴan uwansa, amma ya nuna musu shifa babu abinda Umar yay masa dan haka babu ruwansa da ɗaukar ma kansa hakkin ƙuntata masa. Wannan abu da Harunan yayi yasaka mahaifinsu farin ciki, ya dinga saka masa albarka kuwa.      Shaƙuwar Haruna da Umar tasa Umar ɗin cewa Haruna ya bashi Habibu ya saka shi a makaranta, babu musu kuwa Haruna ya bashi yana faman godiya. Sai dai rigima ta ɓarke dan Talle tace bata yarda ɗanta ya koma hannun maƙiyinta ba. Shi ko yace bata isa ba dan ya bashi kuma babu yanda zatai. Rigima tai rigima har Haruna yama Talle saki ɗaya, ya kuma ɗauki Habibu ya bama Umar. Sai da akaita roƙonsa Talle ta ma kusa gama idda sannan ya maidota.       Rayuwar Habibu ta inganta, dan Lubabatu da zuciya ɗaya ta riƙe Habibu kamar ba uwarsa ce ba ta gallaza mata. Habibu ya fara boko da islamiyya, kuma Alhmdllh yana fahimtar komai Dan yaro ne mai ƙwazo. Yana son Lubabatu da Umar, dan yanda suke tattalin rayuwarsa har ji yake sunfi masa iyayensa, saboda Talle masifaffiyace har su ƴaƴan nata ba daɗi suke ji ba. Sai da Habibu ya kammala primary sannan ya fara zuwa Giro, dan malam ne ya saka wannan dokar saboda sanin halin uwarsa. Duk da cigaban da Habibu ya samo bai hana Talle nuna tashin hankali da son ganin ɗanta ya dawo gareta ba. Sai dai kuma babu yanda ta iya, dan Haruna ya tabbatar mata idan tai masa hauka sauran matan huɗu ma da take dasu zai kwashe ya bama su Umar ita kuma ya saketa. Wannan furuci ya tada mata da hankali dole tai shiru, amma ta koma yima Lubabatu habaici da gorin haihuwa dan ita tun wancan haihuwar bata sake ba har yanzu. Yanda take mata gorin haihuwa haka sauran matan gidan suma suka fara, sai ya zam sam kwanakin da sukai a Giro bai mata daɗi ba, bama su gama cika kwanakin ba tace ita dai zata koma. Haƙuri malam Ibrahim ya dinga bata kamar ba surukarsa ba. Ita kuma tace ba komai baba. Haka dai suka dawo Giro harda Habibu. Ashe ALLAH mai rahama mai jinƙai tana maƙale da ciki harna wata biyu.       Ta raini cikinta cikin aminci da yarjewar UBANGIJI, babu kuma wanda yasan da shi sai da ya shiga wata takwas Baba Haruna yazo Kebbi ya ganta da shi. Ya taya ɗan uwansa murna matuƙa, yana dawowa Giro kuwa ya fasa zance. Ashe shi Baba yasan da cikin, dan Umar ya sanar masa amma yay shiru dan ya fahimci yanda Umar yake rayuwa a cikin yan uwansa da matansa, da yanda itama matarsa ke fuskantar ƙyara da hantara wajen surukansa. Aiko wannan batun ciki sai da ya ɗaga musu hankali, musamman Talle, dan da farko ma saida ta jefa cikin da mummunar kalmar data saka Haruna marinta. To babu dai yanda suka iya, haka ALLAH ya sauki Lubabatu lafiya, ta haifo ƴarta mace. Habib yafi kowa farin ciki dan ya samu ƙanwa. Giro baba yace su dawo ai suna, haka kuwa akayi duk da Lubabatu bata so ba, amma darajar baba zata iya yin komai. Shagalin suna akai na garari na faɗa aji, dan Umar ya kashe kuɗi batuƙa, ta yanda a lokacin kowama ya fahimci lallai ya kama ƙasa, dan lokacin tabbas kuɗi na shigo masa Alhamdullah. Sosai mahassada su kuma suka zuba hassadarsu, dan su Talle dai habaici suke. Wai ai ta banza, idan ana son nuna musu anyi kuɗin miyyasa bata haifi namiji Magaji ba. Babu wanda ya kulasu, dan sune jahilai. Bayan suna da sati ɗaya suka shirya komawa Sokoto saboda makarantar Lubabatu data Habib, amma sai Talle tai tsalle ta dire Habib bazai koma ba. Nan ma ubansa Haruna yace bata isa ba tayi kaɗan. Haka tana ji tana gani suka tattara suka wuce suka barsu da ƙunar zuciya...       Bayan haihuwar Asiya Lubabatu bata sake ko samun ciki ba, dan haka ta maida hankalinta akan yaranta biyu, wato Habib da Asiya. Gata suke musu matuƙa daga ita har Umar ɗin. Ga tarbiyya suna samu mai inganci. Sosai Habib ke son Asiya, dan ita yake kallo a matsayin ƙanwarsa uwa ɗaya uba ɗaya ba ƙannansa na Giro ba. Yakan je Giro ɗin, wani lokacin ma harda Asiya. Amma sam babu mai nunama Asiya soyayya sai baba kawai da Baba Haruna. Sai ko shi Habib ɗin dake zama yayta kaffa-kaffa da ita duk da kuwa hakan baya hana Talle dukanta da hantararta. Dan gaba ɗaya ƙiyayyar da takema Lubabatu da Umar ta koma kan Asiya yanzu. A haka Umar ya kammala karatunsa. Ya nuna yana sha'awar aikin ƴan sanda. Aiko babu musu Baba Umar ya sama masa. Ya fara aikin babu jimawa Asiya ta kammala secondary ta fara jami'a itama. Sai kawai Baba Umar ya yanke shawarar haɗasu aure, koda ya tuntuɓi Lubabatu murna tayi sosai, dan acewarta wa suke da shi bayan Habib ɗin dazai riƙe musu yarinya, Habib tarbiyyarsu ne hakama Asiya, suna ƙyautata musu zaton alkairi. Wannan magana tata ta ƙara masa ƙwarin gwiwa ya nufi Giro da batun. Anan ma Baba yayi matuƙar murna da sanya masa albarka, hakama baba Haruna. Amma sai Baba yace suyi shiru da zancen kawai sai ranar ɗaurin aure. To dama akwai bikin jikokin gidan da za'ayi har su bakwai, saboda yawan family ɗin da wahala kaga an tashi auren yara an aurar da ɗaya ko biyu. Hakan kuwa akayi, aka fara taron biki batare da kowa yasan dana Habib da Asiya ba. Har ita Asiya da Habib ɗin kuma. To dama yanzu indai za'a aurar da yara a gidan Baba Umar shike yin komai na hidimar batare da gajiyawa ba, duk da ƴan uwansa basu taɓa gode masa ba sai ma zaginsa akan kullum baya musu. Baba Haruna ne kawai mahaifin Habib ke ganin ƙyautatawarsa.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖6️⃣0️⃣ ______________ ........Ba ƙaramin tashi hankalin kowa yayi ba lokacin da akaji a ɗaure-ɗauren aure harda Asiya da Habib, tab ɗin jan inji mata. Ai a ranar kowa yaga ainahin Talle a wannan gida. Tayi tujara ta fitar hankali, tai tsalle ta dire akan bata yarda ba kuwa. Aiko Baba Haruna yace idan bata yardaba kuwa sai dai itama ta koma gidansu da zama. Ansha rikici kam bana wasa ba, harma wanda basu san ainahin matsalar gidan ba da takurar da Umar ke fuskanta da iyalansa kowa ya sani yanzu. Baba ne dai yasa Baba Umar da Lubabatu da tsirarun danginta da sukazo biki, dan ƙanwartace ma kawai Shamsiyya da itama yanzu tayi aure a Kaduna harda yaranta biyu. Sai dai mijinta yana tafiya da ita Lagos shiyyasa sukan daɗe basu haɗu ba.        Dama dai an tsara ma amarya da ango gidan zamansu anan Kebbi, dan haka can suka tare su. Sudai suna musu addu'a da fatan zaman lafiya da zuri'a mai albarka. Alhamdullah Habib na nunama Asiya kulawa, duk da kuwa a yanayin nasu kamar dai babu wanda ke son ɗan uwansa da kalmar soyayya sai dai ƴan uwantaka, kawai iyayensu sun musu shigar sauri ne tunda basu tambayesu ba. Amma kuma bazasu taɓa iya musu da su ba dan haka suka haƙura suka amshi juna kamar babu komai. A farkon zaman tarbiyya da ilimi ne kawai ke jagorantar zaman auren, amma a hankali sai Asiya ta fara son Habib, so kuwa mai tsananin gaske, tun bai fahimci ƙanwarsa ta faɗa soyayyarsa ba har ya fahimta. Dan haka ya sake ninka kulawar da yake bata. Bawai shima Habib baya son Asiya bane ba, yana sonta shima sosai, sai dai shi Talle mahaifiyarsa itace matsalarsa. Dan yana samun matsi a gurinta a duk sanda yaje Giro akan sai ya saki Asiya komai daren daɗewa. Irin wannan abubuwan yasa yake jin bai son zuwa Giro ɗin ma, Asiya kuwa tunda sukai aure bai yarda taje ba. Sai ya fake da karatun da take yi. Baba ne kakansu idan ya samu lokaci yana shigowa Kebbi, shima Baba Haruna haka, dama ko zasuso zuwa sai dai domin su. Itama dai Asiya ta mayi mahaifiyarta Lubabatu, dan sai da tai shekara biyar harta kammala karatunta ma da service sannan ALLAH ya bata ciki, babu irin tujarar da Talle batayi ba akan wannan rashin haihuwa amma kowa yay uwar watsi da ita har shi ɗan nata Habib. Dan yanzu ma ba'a Kebbi suke ba an maida shi aiki Zamfara can suke da Asiya. Sosai Baba Umar da Mama Lubabatu sukai farin ciki da samuwar cikin ƴar tasu, hakama kakansu Baba Ibrahim da Baba Haruna mahaifin Habib. Gambo kuwa sai taita aibanta cikin har sai da Baba ya tsawar mata.     Ciki ya girma suka dawo Kebbi haihuwa, inda ALLAH ya sauki Asiya lafiya ta haifo ƴarta mace mai kama da ita da kakarta Lubabatu. Babu ta inda yarinya ke kama da Habib gaskiya. Oho hakan bai damu Habib ba, farin ciki yake shima ya samu ɗiya jininsa. Hakama Lubabatu da Baba Umar da Baba Haruna suna farin ciki da samun jika. Giro aka koma akai suna saboda Baba, sunan daya haɗa hargitsi da farin ciki duk a lokaci ɗaya, dan kuwa Talle ana kai mata ƴa ko taɓawa batai ba sai cewa tai ba ƴar Habib bace, dan babu ta inda tai kamanni da shi. Wannan magana ta tada ƙura matuƙa, ƙura irin wadda a karo na farko Baba Umar ya zuba tsiya irin wadda ba'ayi zaton ya iya ba. Dan sai da Talle ta raina kanta kuwa. Murmushi Baba yay tayi dan shi kansa daya haifi Baba Umar bai san ya iya faɗa haka ba, saboda bayayi, shi mutum ne mai sanyi da nutsuwa. Wannan tujara da Baba Umar yayi tasa aka samu sassaucin ƙarasa taron gagarumin sunan lafiya.       Ana kammala taron suna suka tattara suka koma, Habib ya wuce Zamfara yabar Asiya anan tana wankan jego ita da jinjirarta mai suna *_Shahidah_*, sai ya koma zuwa musu weekend har suka kammala wankan ta koma can Zamfarar wajensa. Bayan komawar tata ne ALLAH yay ma mahaifin mama Lubabatu rasuwa. Hankali tashe suka wuce Minna ita da Baba Umar. Wannan tafiya itace ta canja komai daga rayuwar Asiya Umar Ibrahim Giro (Ammie) itace ta canjata daga sarauniya ƴar gata zuwa baiwa da ƙaddarorin rayuwa suka zagaye, dan kuwa a hanya Baba Umar da Mama Lubabatu suma sukai haɗari, babu kuma wanda ya shura a cikinsu tun a wajen dan gawawwakinsu aka kawo Giro. Kamanta irin tashin hankalin da Baba da Baba Haruna da Habib da Asiya suka shiga ma ɓata lokaci ne. Dan Asiya komawa tai kamar ta zare ma. Sauran jama'ar gidan kuwa bazaka iya cewa ga abinda ke cikin zukatansu ba akan wannan rashi. Bayan rasuwar su Baba Umar da sati biyu shima Baba ALLAH yay masa rasuwa. Dan tun da yaga gawar Baba Umar da Lubabatu a kwance jikinsa ya rikice, abinka da dama ga tsufa. Asiya tayi kuka har ta rasa hawayen zubarwa. Dan tasan ta rasa dukkan gatanta a family ɗin su sai Baba Haruna kawai ya rage mata sai kuma Habib da ƴar ɗiyarta. Haka dai aka sha alhini komai ya lafa. Habib ya ɗauka Asiya dan su koma Talle tace bai isa ba, ai kuma Asiya ta dawo Giro da zama kenan. Hankalinsa yay matuƙar tashi hakama na Asiya. Gashi ta kafa matsa tsaurara dokoki ciki harda in Baba Haruna ya tambaya yace shine yace zai barta ta ɗan huta. Idan ba hakaba ALLAH sai ta tsine masa. Wannan kalma ta girgiza Asiya Ammie tace zata zauna kawai. Ta dinga lallashin mijin nata. Haka badan yaso ba ya shirya ya koma Zamfara ya barta a Giro.         Rayuwa a Giro ga Ammie rayuwace mai tsanani da takura da damuwa. Tasha wahala matuƙa a hannun Talle da suke kira Gwaggo. Gaba ɗaya Ammie ta fita a hanyyacinta kamar bata taɓa shiga ajin makaranta ba. Ga Baba Haruna baya iya magana a yanzu saboda Talle ta danne masa kai a gidan teacher. Habib na zuwa weekend, amma bai isa sauka ɗakin Asiya ba. Ko da dare idan ya shiga domin kwanciya babu kunya Gwaggo ke zuwa ta buga musu tace ya taso ya koma ɗakin soro ya kwanta, inda ɗakin Baba kakansu yake. Haka babu yanda zai yi zai fito. Tom dai kuma UBANGIJI ya nuna mata ita bata isa hana abinda ya hukunta ba. Dan kuwa sai ga Asiya Ammie da ciki, gashi bata yaye Shahidah ba. Ta shiga tashin hankali, dan mutanen gidan ƴaƴa da iyaye sun tasata a gaba da zagi da habaici wai mayyar miji jarababbiya tayi gwanne. Abin kuma tsoro da firgici Gwaggo tace ai ciki bana Habib bane tunda ba kwana yake a ɗakin ba, dama ai Shahidah ma ba ƴarsa bace. Magana kamar wasa ta nema zama babba. Dan har gari ya ɗauki wannan zance. ALLAH gafurin rahimun sai ga Baba Haruna ya dawo hankalinsa a lokacin, dan kuwa asirin Gwaggo ya sakesa. Shine ya bama Asiya kariya har ya sake yina Gwaggo saki ɗaya. Ya rage saura igiya ɗaya a tsakaninsu kenan. Wannan saki shine fa ya sake haddasa wutar ƙiyayya tsakanin Gwaggo da Ammie. Da ƙyar dai Mahaifiyar Baba Haruna tasa ya dawo da Gwaggon dan ƴar ƙanwarta ce dama auren zumunci akai musu. Gwaggo ta dawo amma ta ƙara ninka ƙiyayyarta ga Ammie, sai dai a yanzu Baba Haruna na tsaye akan al'amarin Asiyar, dan ya ma fara shirin Asiya tabar giro tabi mijinta. Amma sai ta haihu kodan yanayin samun cikin.       Haka Asiya taita rainon ciki cikin matsi da takurar surukarta. Ga Shahidah dake ta fama da ciwo. Babu mai taimaka mata a gidan har tsoffin gidan saboda Gwaggo ta zama boss ga kowa. ALLAH ya sauki Asiya lafiya ta sake samun mace mai kama da ita itama kamar Shahidah. Aiko Gwaggo ma ta sake aibanta jinjira tace ba ɗiyar Habib bace. Sai da Baba Haruna yay mata tas. Baba Haruna shine ya tsaya akan komai akai suna yarinya taci suna Lubabatu, amma sai suke kiranta Amaal koma ace Asiya da Habib ke kiranta. Dan su dai ƴan gidan Lubabatu suke cewa. Zuwa lokacin an ma Habib transfer zuwa Maiduguri. Dan haka ana gama bikin suna ya sake shirya komawa. Sai Baba Haruna yace ya ɗauki matarsa su tafi.  Hankalin Gwaggo ya tashi akan hakan amma Baba Haruna yace bata isa ba kuwa Habib kamar ya tafi da iyalinsa ya gama. Hakan yama Habib daɗi, ya ɗauka Asiya da yaransa biyu suka wuce abinsu, suka bar Gwaggo na tujara.       Wannan tafiya ita ce ta samawa Ammie sauƙi, suka koma Maiduguri da zama ta samu damar rainon yaranta cikin aminci, anan ta koya gyaran jiki da haɗin turarruka. Shekararsu biyu a Maiduguri aka sake masa transfer zuwa jihar Nasarawa. Nan ma ya kwashesu suka koma. Anan ɗin ma shekararsu uku aka sake maida shi Sokoto, zuwa lokacin kuma bata sake haihuwa ba. Yaransu Shahidah da Amaal sunyi ƙyau abinsu yara kamar ka lashe, dan Ammie ma ƙyaƙyƙyawa ce kamar mahaifiyarta. Dole kaga yaran nan sai ka tanka, dan kamar wasu ɗiyan hamshaƙin mai kuɗi bana ɗan sanda mai ƙaramin muƙami ba. Shima Habib yana son yaransa, sai dai irin mutanen nan ne shi da bai cika jan yaro a jiki ba, komai dai na buƙatar rayuwa yana tsaye a kansu. Dan ko ita Ammie bazata ce ga wata soyayya a bayyane da yake nuna mata ba. Baya dai takura rayuwarta ko hanata duk abinda take so, ba kuma ya nuna mata tsantsar soyayya a zahirance. Ga wanda ma bai sansu da ƙyau ba idan yaga rayuwar zamansu sai ya ɗauka tana a cikin matsin rayuwa ne. Sun tattaro sun dawo Sokoto, a lokacin Shahida nada shekara bakwai, Amaal nada shekara biyar da wasu watanni dan tsiransu da Shahidah kaɗanne. Saida sukai sati biyu a Sokoto sannan suka je Giro. Babu wanda bai firgita da canjawar Asiya da yaranta ba. Dan ta koma ƴar gayunta kamar batai rayuwar Giro ba. Tuni kishinta da hassada ya shiga zukatan jama'ar gidan kamar yanda suka dingama mahaifiyarta Lubabatu.  A ɓangaren Gwaggo ma babu abinda ya canja, dan ƙiyayyar Asiya sai wacce tai gaba. Haka su Shahidah ko kallo basu isheta ba dan tace ita ba jikokinta bane ba uwarsu dai tasan inda ta samo su. Hakan na ma Habib ciwo amma baya cewa komai. A wannan zuwa kuma Gwaggo ta tsira sai Habib ya ƙara aure, dan a haifa masa namiji. Kai tsaye ya nuna mata bashi da wannan ƙarfin, dan shi dai bamai kuɗi bane, dukiyar da yake juyawa kuwa kowa yasan ta Asiya ce da iyayenta suka bar mata duk da ma dangin nasu sun kusa cinye rabi da kwata. Aiko ta tujaresa da masifa da bala'in daya sashi tattara matarsa da ƴaƴansa suka koma abinsu. Sai kuma suna komawar sai ga Asiya da ciki. Yayi farin ciki matuƙa, ya kuma shiga addu'a da fatan ALLAH yasa Asiya ta haifa namiji dan shima fa yana son a haifa masa namijin, ga maganar mahaifiyarsa ta sake kwaɗaita masa abun a rai. Kawai dan bashi da ƙarfin aure ne. Amma tabbas a ransa yana son ƙara auren ma. Dan yana ɗan neman mata batare da Asiya ta sani ba, tun kafin yay aure yake yi, bayan aurensu ya rage sosai sai dai kuma ita dama zina masifa ce. Faratane mara wuya, amma indai ka fara sai ALLAH ya soka da rahama kake dainawa.        Ammie tayi rainon cikinta cikin aminci da kulawa, har ALLAH ya kai cikin watan haihuwa ta haihu lafiya. Ta samu ƴa mace ma a wannan karon. Sai da Habib yaji wani iri a ransa, sai dai kuma yana ɗaura idonsa akan yarinya yaji ƙaunarta ta shigesa. Dan ita kam tayo kamannin mahaifiyarta da ƴan uwansa, ta kuma yo kammaninsa ta bangarori da dama da suke a bayyane........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖6️⃣1️⃣ ______________ .........Wannan karon ma dai Giro suka koma suna, sai dai babu wanda ya nuna murna da wannan haihuwa kamar ta Amaal daga Baba Haruna sai uban jegon sai kuma su Shahidah dake murna an haifa musu ƙanwa. Wannan karon dai Gwaggo babu damar aibanta yarinya tunda tana kama da ubanta a abubuwa da dama. Amma hakan bai hana sako batun haihuwar ɗa namiji ba data fahimci yana tasiri a zuciyar ɗan nata. Haka dai akai bikin sunan babu wani armashi sosai sukai shirin komawa Sokoto amma sai Gwaggo ta hana wai su zauna anan suyi wankan jego. Ganin yanda bata kawo tashin hankali ba a sunan yada baba Haruna tunanin ta sauya ne. Dan yanzu ta ɗan rage wasu abubuwan a zahirance saboda tsoron kada ta tsinke ƴar sauran igiyar ɗaya dake a tsakaninsu. Ta koma zuba rashin mutuncinta ta ƙasa, dan Habib ta koma takuramawa akan sai ya ƙara aure, ita kuma Asiya ana mata a kaikaice.      Shima dai Habib wannan karon bai damu ba ya barsu anan ya kuma yarda da batun ƙara aure, dan ya samu damar sheƙe ayarsa da sabuwar karuwarsa da suka haɗu anan Sokoto ɗin kwanan nan. Zama kamar wasa ya nema zama gaske. Dan bayan gama wankan jegon Maanal Habib bashi da niyyar cewa su shirya komawa Sokoto, sai dai yana zuwa duk ƙarshen wata yay musu weekend ya koma. A haka aka tado batun aurensa. Auren daya bama kowa mamaki ya kuma saka Ammie a tashin hankali. Amma sai Baba Haruna ya dinga kwantar mata da hankali da nasiha ta sakama kanta dangana kuwa ta rungumi ƴaƴanta. Cikin ƙanƙanin lokaci akasha biki kuwa, yarinya ƙarama da bata wuce shekara sha bakwai ba. Inda Ammie ta burge kowa shine tattara komai ta watsar kamar ma ba ita akama kishiyar ba. Sai shima kansa Habib ɗin ya dinga kiyaye duk wani abu da zai taɓa mata zuciya ba kamar yanda Gwaggo taso ba. Itama yarinya da aka ɗoro akan rashin kunya da zata dinga yima Ammie sai ta dinga jin shakkarta. Abinda ya ragema amarya armashi samunta ba'a cikakkiyar mace da Habib yayi ba, dan tun a daren farko sai da tasha maruka a wajensa a ɗaki batare da sanin kowa ba. Ko sati kuma bai cika ba na amarci ya tattara ya koma wajen aiki. Aiko akaita gutsiri tsoma wai Ammie ce tayi wani abu, dan Gwaggo har ɗaki ta sameta ta mata wankin babban bargo. Ita dai batace komai ba. Habib bai zo gida ba sai da yay wata guda kamar yanda ya saba, ya kuma murje idonsa ya sauka ɗakin Ammie, itako tanata roƙonsa bai kulata ba, ana cikin haka sai ga Gwaggo har ɗaki, tas taima Ammie da zaginta akan muna fuka ta tasa ɗanta gaba har ɗakin amarya Sailu. Ai ko ranar ma maimakon ta samu kulawa a wajensa sai duka taci a banza, dan ya fahimci bata da kunya, Habib kuwa irin mazan nan ne da basa ɗaukar raini, shi hatta macen bariki tai masa hauka duka take ci a wajensa, Ammie ce kaɗai ta tsira da irin wannan halin nasa, duk da yana shan marinta itama a wasu lokutan. To ataƙaice dai wannan aure bai rufa wata biyar ba a wani zuwa ya saki Sailuba saki har uku. Nan fa gari ta ɗauka Ammie ce ta koreta. Babu kalar abunda Ammie bata gani ba akan wannan rabuwar auren amarya da mijinta, ƴan gidan suka kara tsananta, na Gwaggo kam ai ba'a magana. Ga Habib bashi da niyyar cewa su shirya subar garin har sai da Maanal ta shiga shekara ɗaya da rabi sannan akaima Habib transfer zuwa Kano. Aiko Baba Haruna da'a yanzu ya fahimci Habib na neman matan banza yace ya tattara matarsa da iyalansa su wuce tare. Gwaggo ta nuna bata yarda ba, Baba Haruna ya nuna mata shima bata isa ba. Kamar Habib baya so haka ya wuce da su Ammie Kano, dan yasan an rage masa jin daɗinsa ne kawai. Anan ya samu gida ya kama musu haya, daga baya kuma ya saye shi da kuɗin Ammie na gado, shine dalilin komawarsu da zama garin Kano. Tunda suka koma kuma basu sake zuwa Giro ba sai dai shi yazo sau uku sai yanzu shekara kusan shidda kenan dan tun Maanal nada shekara ɗaya da wasu watanni da kaɗan ya rage sukai biyu. Ita dam bata san Giro ba bata san ƴan Giro ba.... ________★★★         Babu wanda ya sake bi takan su Ammie a gidan duk da wasu suna son kawo musu abinci suna jin tsoro ne. Anan ƙofar ɗakin sukai sallar magrib da isha'i. Sai kusan tara saura Babu ya shigo tare da Baba Haruna. Ganinsu a inda ya barsu su da kayansu ya sosa masa zuciya sosai. Baba Haruna kam a fusace ya shiga ɗakin Gwaggon. Sosai ya mata tas da abinda tayi ɗin, ya kuma tabbatar mata wlhy a wannan karon idan tace zatai wani abu to ta tabbatar shi bazai ɗauka ba ƙofa a buɗe take gareta. Wannan kalmar na tayar mata da hankali akan mijin nata. Dan tasan igiyar nan ɗaya tak ke riƙe da aurensu yanzu. Bakuma zata so ace ya tsinketa a yanzu da suke a shekarun tsufa surukai cike da gari ba. Shi da kansa ya fito ya shiga dakin dake a mallakin Ammien, ɗakin duk tarkace ne ma a ciki, dan haka ya fita babu jimawa sai gashi da almajirai kusan biyar, su ya saka gyaran ɗakin, shi kuma Babu ga fita nema musu abinci da maganin da Maanal zata sha dan zazzaɓin ya dawo. Dandanan aka gama gyara ɗakin, aka kawo katifa da tabarmi aka saka musu. Harda turaren wuta na tsinke baba Haruna ya ɗakko a ɗakinsa aka kunna, dan yanzu shine ya mayi mahaifinsu a gidan, shine ke da almajirai yake koyarwa, dan haka ya koma ɗakin zaure inda suka samesa na mahaifinsu da zama kenan. To da yake tunda yaga Gwaggo na niyyar kashe katifar dakin Ammien sai ya saka aka ɗauketa ya maidata can ɗakin nasa aka lulluɓeta, sai idan Babu yazo ake kawo masa, daya tafi kuma yasa a maidata can.      Gajiyar tafiya tasa basu ma wani iya cin abincin kirki ba dan ma harda shayi, suna son yin wanka basu san yaya zasuyi ba, dole suka hakura suka kwanta a haka. Dama ita Maanal tuni tayi barci abinta, duk da barcin nata bana daɗi bane ba. Washe gari dai sun ɗan samu kulawar mutanen gidan sakamakon ganin Baba Haruna tsaye akan al'amarin su. Dan har koko an kakkawo musu a wasu sassan. Duk da ma dai su yaran sun kasa sha sai Ammie ce tasha. Kosan da Baba Haruna da bread ya saya musu kawai suka iya ci, sai naman jiya da Babu ɗin ya saya musu basu ci ba. Yanda Maanal ta tashi da zazzaɓi sosai dole Babu ya ɗauketa zuwa asibiti. Ƙarin ruwa suka saka mata dan jikinta duk babu ƙarfi, hakan yasa suka jima can har sai bayan zuhur ya dawo da ita. Anan ne yake sanarma Ammien Abban Fadeel ya kira shi sun gaisa, itama Oum nata nemanta wayar a kashe.      Sai lokacin Ammie tama tuna da wayar tata, ta bincikota a bag sai taga ashe ta mutu ma babu caji. Dole ta bama su Shahidah tace suje waje su nema yara su rakasu inda ake caji sukai mata. Badan sun so ba suka fita, dan basa ƙaunar ganin hararar da Gwaggo ke musu da kallon tsana. Sai zuwa yamma suka amso mata tai kiran Oum, lokacin Maanal ta tashi a barci amma sai ƙunci take taƙi kula kowa abinci ma sai da Ammie tace zata zaneta sannan taci sa kaɗan. Amma yanzu tana jin ance Oum tai wata irin zabura tazo ta nanuƙe Ammie. Dole Ammie ta taƙaita gaisuwar da suke da Oum ɗin ta bata wayar, dan yi take ma kamar zata warceta. Oum na jin muryar Maanal itama ta saki murmushi...       “Oh oh! My Baby I miss you”.   Cike da zumuɗi Maanal ta ce, “I miss you too Oum. Oum ina Besty?”.     Dariya Oum tayi tana mai jinjina kanta idonta akan Ajwaad dake kwance a gadonta, tunda yaji ta ambaci sunan Maanal shima ta kafeta da idanunsa. Wayar ta miƙa masa tana faɗin, “Gashi nan kin barsa da ciwon kewa”.     Baki Maanal ta tura gaba, cike da shagwaɓa ta ce, “Oum ai nima banda lafiya ina ciwon kewarsa”.      Dariya Oum ta sanya, hakama Shahidah da Amaal. Ammie kama sai ta girgiza kanta kawai. Ganin su Shahidah na mata dariya ta tashi tana harararsu da murguɗa musu baki ta fice a ɗakin. Ammie na kiranta akan ta kawo mata wayarta kar tai mata ɓarna bata dawo ɗin ba. Gwaggo na tsakar wajen nasu tana haɗama dabbobinta dusa, suna haɗa ido da Maanal ta harareta, itama ko ta rama da murguɗa mata baki ta ɗauke kanta. Ai sai Gwaggo tai mutuwar tsaye da mamakin wannan fitsararriyar yarinya. Ita zata harara ta rama wannan jaririyar ƴar?.      Oho ko'a jikin Maanal, dan kujerar Gwaggo dake a ƙofar ɗakinta ta zauna abinta. Sai kuma cikin shagwaɓa ta ce, “Besty!”.      Wata irin ajiyar zuciya Ajwaad ya sauke yana lumshe ido da ya zame masa ɗabi'a duk da ƙarancin shekarunsa. Sai kuma a cikin muryarsa mai sanyi da zurfi ya amsa da, “Oummyim!”.       “Haushina kake ji dan na tafi na barka? Banfa da lafiya nima, yau har asibiti Babu ya kaini akamin karin ruwa”. Ta ƙare maganar muryarta na rawa alamar son yin kuka. Tashi zaune Ajwaad yayi sosai, cikin damuwa ya ce, “To kar kiyi kuka, nima banda lafiyan ai, jiya saida aka min ƙarin ruwan”.      Kukan ta sakar masa kuwa, da faɗin, “Besty nidai kace Babu ya dawo dani wajenka. Ni bana son nan. Akwai muguwar mata a garin. Yanzu ma ka ganta sai hararata take...” kuka sosai yaci ƙarfinta        Sosai hankalin Ajwaad ya sake tashi daga can, sai ƙoƙarin lallashinta yake yi amma tana ƙara ƙarfin kukan harda tutturza ƙafafu. Ga Gwaggo ta zuba mata wani shegen kallo. Kukanta yasa Shahidah fitowa. Sai dai suna haɗa ido da Gwaggo ta koma ciki da sauri. Dama a tunaninsu ko wani abu akama Maanal ɗin tunda sun san halin muguwar kakar tasu sai a hankali ce. Sosai Maanal take kuka har sai da Oum ta amsa wayar daga hannun Ajwaad da duk ya rikice da kukan nata itama tana lallashinta da tabbatar mata Bestien nata zaizo ya sameta. Da ƙyar tai shiru sannan Oum ta maida ma Ajwaad waya suka cigaba da hirarsu mai cike da shirme da shiririta musamman ga Maanal dan ko yaya shi Ajwaad ya ɗan tasa ya fara hankali....           Sam rayuwa a Giro batama Ammie da yaranta daɗi. Maanal ce ma dai babu ruwanta, tashin hankalinta kawai ace ta yini batai waya da Ajwaad ba. Anan ne zaka ganta kamar mara lafiya. Amma da sunyi waya sai ka walwalarta ta dawo. Sai ma ta fice wasa cikin gida abinta. Maanal dai dama jaruma ce a fagen iya faɗa da tsokala, anan ɗin ma duk da matsin da suke a ciki bata canja ba. Dan kuwa jibgar ƴaƴan mutane take yi, idan kafi ƙarfinta kasha ƙasa a cikin ido. Gwaggo kuwa idan ta harareta itama ta rama. Ɗakinta kuwa kai tsaye take shiga tace tana son abu kaza. Idan Gwaggon ta korota da zagi taƙi fitowa. Kota warto abinda take so ɗin ta fito a guje. Wannan hatsabibancin nata yasa Gwaggo tafi tsanarta fiye da kowa. Kullum cikin aibantata take da zaginta. Abin na damun Babu da Ammie sai dai babu yanda zasuyi, dan Ammie tama Maanal faɗa akan shiga harkar Gwaggon amma yarinyar nan data faki idon Ammie sai tasan abinda taima Gwaggo. A haka dai sukai sati uku a Giro, duk sun fita hayyacinsu sunyi baƙi sun rame saboda rashin abinci mai inganci. Suna a kwana na ashirin da biyar Babu yazo ma Ammie da batun wai zai yi aure. Sannan suma kawunan sa sunyi magana akan Shahidah da Amaal ya kamata a musu aure dan sun isa, musamman ma Shahidah data fara zama uwar mata. Dan haka sun yanke hukuncin ita Shahidah ta auri Lado ɗan wajen Badaru. Ita kuma Maanal Ƙasimu ɗan wajen Sagiru. Wani irin tashin hankali ne ya ziyarci Ammie. Ita ba auren Babu ɗin ne damuwarta ba, batun Shahidah da Amaal.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖6️⃣2️⃣ ______________ .......Kuka sosai Ammie ta sanya ma Babu da roƙo da magiya, amma sai ya nuna mata shima bada son ransa bane. Dan bazai so yaransa suyi rayuwar garin ba, ba kuma zai so a yanke musu karatunsu ba. To amma bazai iya jayayya da ƴan uwan mahaifinsa da ƴan uwansa ba. Ina sam wannan batu bai shigi Ammie ba. Dan tasan wannan ba umarnin kowa bane sai Gwaggo. Hankali tashe taje ta samu Gwaggo da kuka da roƙo, sai Gwaggon ta rufeta da zagi ta kuma juya maganar. Dan kuka ta sanya da kururuwa wai Ammie ta sameta har ɗaki tana mata gargaɗi idan bata saka Babu ya janye batun ƙara aurensa ba sai tabi dare ta kasheta. Dandanan wajen ya cika da mutanen gidan harda makwafta. Kasancewar Ammie nada tabon fitar kishiya yasa kowa ya yarda da batun Gwaggo. Nanfa akaita cancana magana da zagin Ammie har saida Baba Haruna ya shigo gidan ya tsawatar.     Sam Ammie bata san miya rufema Babu ido ba, yana dawowa gidan Gwaggo ta faɗa masa ƙarya da gaskiya sai ya hau ya zauna. Aiko ya birkice mata yayta tujara a tsakar gida mutane naji, shi bazai yarda a raina masa mahaifiya ba. Ai ba a kanta aka fara kishiya ba. Shi ya gaji da baƙin halinta. Idan bata gode masa ba bata tsine masa ba. Shekara nawa yana zaune da ita zaman haƙuri badan ya taɓa jin sonta a zuciyarsa ba ko sau ɗaya. Sai dan kawai kar ace yama iyayenta rashin halacci ya kasa riƙeta. Shima namiji ne, yana son ya auri wacce yake so, yana son haihuwar ɗa namiji.. kai tujara dai kala-kala data sanya Shahidah da Amaal kuka sosai. Ita dai hajiya Maanal hidima bata san ma anai ba. Tana can tare da Baba Haruna daya fita da ita gaisuwa gidan wani abokinsa. Ammie tayi kuka har ta godema ALLAH, taji inama iyayenta na raye, ashe duk zaman da take da Babu ba soyayyarta a ransa har zuwa yanzu...       Anyi haka da kwana huɗu Babu baya kulata hakama ƴan gidan kowa ya ƙara ɗauke mata wuta ita da ƴaƴanta sai ga batun yima Shahidah da Amaal wai baiko. Ranar ji Ammie tai kamar tabar duniya ta huta. Karon farko ta sami Baba Haruna da roƙo. Yayi mamakin jin bada son ranta ake shirin auren yaran ba. Dan shi Babu ya nuna masa komai da amincewarta ne. Lallashinta yayi akan hakan, yace taje zai zauna da ƴan uwansa akan al'amurin. Wannan ya sakata ɗan jin sanyi a ranta. Sai dai me, koda Baba Haruna ya zauna da ƴan uwansa duk sai suka kasa fahimtarsa, ƙarshe ma mahaifiyarsa da har yanzu tana a raye duk da ta tsufa sosai ko tafiya bata iyayi sai tace idan bai bari amma yaran nan aure ba bata yafe ba. Hauka ake yara sunyi zagada-zagada ace an barsu babu aure. Ko so yake suna a musu irin yanda Umaru yay ma ita Asiya ɗin kamar ƴar arna sai da ta shekara ashirin a gida. Wannan yasa dole Baba Haruna ya bar maganar, ya kuma dinga lallashin Ammie. Ina hankalin Ammie ya kasa kwanciya, dan ko maƙiyinta bazata so ya kasance cikin wannan zuri'ar ba balle ɗiyanta. Balle kuma yara ƙanana kamar su Shahidah. Inama ƙudan yake ballantana romonsa.      Komai yama Ammie tsanani, dan sun tabbatar mata bazata koma da su Shahidah ba. Maanal ma za'ayi mata miji da lokaci yayi su dawo da ita gida. Ranar da aka saka ranar auren daya kasance sati huɗu kacal Ammie batai kwanan lafiya ba. Dan jininta hawa yayi ƙololuwa sai a asibiti ta kwana. Duk da wannan halin da take ciki sai zaginta mutane keyi wai kishi ne. Tana kishi dan mijinta zai ƙara aure. Babu wanda yay mata uzuri akan ƴaƴanta da ake shirin musu auren fin ƙarfi. Washe gari ta ɗan samu dai-daito, iya tunaninta ta rasa wazata tunkara ya taimaketa ya kuɓutar mata da yaranta, ƙanwar mahaifiyarta Shamsiyya kawai ta sani, itama a yanzu bata san duniyar da take ba. Dan tun bayan rasuwar iyayenta bata sake ganinta ba. Minna kuwa dama ba zuwa take ba tunda babu wanda ta sani sai kakanta ko'a lokacin, sai matarsa mara mutunci, yanzu kuma babu shi wajen wa zataje?. Wannan mutanen sune dangin mahaifinta, su kawai ta sani. Sai su Oum da suka zame musu ƴan uwa yanzu a garin Kano. A wannan karon kam sai kawai ta yanke shawarar kiran Oum ɗin, dan itace kawai mafitar data rage mata.       Bayan ta gama zayyanema Oum komai tana kuka itama Oum ɗin kukan take. Da ƙyar suka lallashi juna Oum tace ta saurareta zatai magana da Aban Fadeel in sha ALLAHU za'a kuɓutar da su Shahidahn daga wannan auren. Wannan waya itace ta sanya Ammie jin ɗan sanyi a ranta, har jininta ya ɗan sauka aka sallameta daga asibitin a ranar....      Washe gari kusan azhar saiga Amaal data fita sayo mata fura ta dawo cike da ɗoki. Kallonta Ammie da Shahidah keyi, sai kuma Shahidah ta ce, “Ke kuma ina furan? Kin san fa Ammie bataci komai ba ga magani zata sha”.       Zama Amal tayi da faɗin, “Yanzu zan koma na sayo, Abah na gani a waje tare da Ajwaad”.      Da mamaki Shahidah ta ce, “Aban Kano wai?”.    Cike da zumuɗi Amal ta amsa mata da “Eh”.     Ba ƙaramin waro ido Shahidah tayi ba. Yayinda Ammie ta saki murmushi mai faɗi tana rufe idonta sai ga hawaye sharrr. Da sauri tasa hannu ta goge kafin yaran su gani, wata irin ƙaunar Oum na ratsa mata zuciya da ruhi. Kallon Maanal dake barci sukai, Shahidah ta ce, “Lallai yau da bidiri a gidan nan ga Bestyn Maanal a Giro”. Dariya Amal tayi tana matsawa kusa da Maanal ɗin ta shiga tadata. Da faɗa kuwa ta tashi, dan dama faɗan sukai da wata yarinya a gidan ta fasama yarinyar baki shine Ammie ta daketa tai barcin dole. Dan uwar yarinyar har sashen tazo tana faɗin bazata yarda ba sai ta daki Maanal, yarinya duk tabi ta addabar musu yara. Haƙuri Ammie taita bata amma matar nan sai da ta gama cima Ammie mutunci da gori sannan tabar sashen. Hakkanne ma ya saka Ammie kasa cin abinci dan kanta wani irin ciwo yake mata mai zafin gaske......                 A cikin gidan ma tuni labari ya kai musu daga bakin yaransu. Kasancewar duk suna a ainahin babban tsakar gidan kowa na ayyukansa. Masu surfe, masu sakar mahucin kaba, bamu hira, masu sana'oinsu. Sun ɗauki ƙus-ƙus ɗin zance sai ga wani almajiri ya shigo hannunsa niƙi-niƙi da kaya wani matashin yaro biye da shi. A zahirance dai yaro ne, dan dudu bai wuce shekaru goma sha ba. Sanye yake cikin ƙananun kaya na jeans daga wandon har jacket ɗin saman duk sky blue. Sai rigar ciki data kasance red haka ma belt ɗinsa da boot ɗin takalmansa. Ƙyaƙyƙyawar fuskarsa sakaye da farin siririn gilashi mai shegen ƙyau da a kallo ɗaya zaka fahimci mai tsada ne duk da kuwa na ƙarin gani ne. Tafiya yake a nutse babu hayaniya balle garaje, kallo ɗaya kuma yayma tarin matan dake cike da tsakar gidan ya kauda nasa idon ganin yanda suka zuba masa idanunsu har yana jin tsigar jikinsa na tashi.       Cikin muryarsa mara ƙarfi da hayaniya ya gaishesu a jimlace batare da ya damu da sunji ko basu jin ba, shi dai yana biye da almajirin nan da kai tsaye ya nufi sashen Gwaggo. Suna gab da shiga sai ga Maanal a guje ta fito har tana ture almajirin. Kanta tsaye Ajwaad tanufa, shima da ya jiyo ihunta tuni ya tsaya cak yana kallonta. Ko damuwa da yanda jikinta yay buɗu-buɗu da ƙasar danben da sukai kafin tayi barci ma baiyi ba. Tuni ya buɗe mata hannayensa tazo ta shige jikinsa. Yako ɗagata camak sama yana juyi da ita illahirin fuskarsa na washewa da wani irin sassanyar murmushi daya bama ƴan gidan mamaki. Dan daya shigo sam babu alamar fara'a a tattare da shi. Sai da yay juyi sosai da Maanal dake ƙyalƙyala dariya kafin ya sauketa, sai kuma ta sakar masa kuka. Zuru yay yana kallonta, sai kuma ya kai duƙe a gabanta dan ya fita tsoho sosai, duk da kasancewarsa yaro shi ɗin dogo ne kamar sauran yayunsa da mahaifinsu. Tuni fuskarsa ta koma ta tsuke daga murmushin da yake, idanunsa farare tas da kamar an watsa madara sun fara canja launi.         “Is something bothering you?”. Ya tambaya kamar wani babba yana tsatstsareta da idanunsa. Ƙara ɓarkewa Maanal tayi da kukan iskanci, tare da faɗin, “Ni tare dakai zan koma. Bana son nan mugaye sunyi yawa. Kullum su Safare sai sun dakan, Ammie ma haka, su Didi ma suyita zaluntata. Wicked old woman ɗin can taita min harara da zagina tana cemin shaiɗaniya. Kowa cutata yake anan ƙauyen Baffa ne kawai ke sona da saya min kayan daɗi. Kuma dama na faɗama su Lami duk randa kazo saika rama min duk abinda suke min.”          Sosai ɓacin rai ya bayyana a fuskar Ajwaad. Har yama ji ya kasa magana. Dan shi fa idan kana son kaga ainahin fushinsa to kuwa ka taɓa Maanal. Ko Ammie da Babu dan baida yanda zayi ne kawai....      “Ajwaad!”.     Sassanyar muryar Ammie ta saka shi janye idanunsa daga kallon Maanal ya maida ga Ammien. Murmushi ta sakar masa da faɗin, “Kaga tashi kaji karka biyema wannan ibilishiyar. Kadai san halin mutuniyar taka maza taso”.         Dan Ammie ce kawai ya tashi, hannunsa riƙe dana Maanal suka shiga. Su Shahidah na masa sannu da zuwa yana faman balla musu harara. Amaal daba barin saita kwana take ba itama tai saurin faɗin oh har an kai maka munafuncinmu kenan?”.       Caraf Maanal dake naniƙe da shi ta murguɗa mata baki da faɗin, “E ɗin an faɗa, kuma duk abinda kuka min sai ya rama min har ma Ammie ko Besty?”. Tai maganar tana kallon AA. A hankali ya jinjina mata kansa, sai kuma ya ce, “Amma banda Ammie”. Fuska ta ɓata sai kuma ta sanya kuka tana turza ƙafafu. “Ni dai harda ita Besty, kullum fa sai ta dakan, yanzu ma ta daken ta sani barcin dole.....”         “An dake kin, oh ni Asiya nima ƙarar tawa kika kawo wajen Ajwaad ɗin?”. Ammie ce tai maganar tana ajiyewa Ajwaad ruwa a gabansa. Sai kuma ta zauna idonta na harar Maanal ta ce, “Karma ka bari ta ɓata maka rai kaji Ajwaad. Yarinyar nan tabi ta fitini ƴaƴan mutane a gidan nan, kullum babu ranar banza saita fasa kan wani ɗan kota jawo min magana. Fitinar Maanal ta isheni wlhy. Kuma ALLAH in baki min shiru ba zan miki duka agaban Ajwaad ɗin”.       Sarai Maanal ta san halin Ammie, tanada zafi akansu, sanyinta akan Babu ne kawai da mutanen gidan nan nasu. Muƙut ta haɗiye kukan tana mai lafewa a jikin Ajwaad. Cikin maganar nan tasa sanyi-sanyi ya ce, “Ammie kiyi hakuri, amma idan bata ramawa ai sai suyita dukanta. Yanzu ma jiba duk yanda ta rame tai baƙi”.     Baki Ammie ta saki tana kallonsa. Yayinda Shahidah da Amaal ke kwasar dariya. In dai Ajwaad ne zai yi fiye da haka akan Maanal, dan haka Ammie ta ce, “Shike nan ai dama kai ke ɗaure mata ƙugu, amma dai kubi a hankali, dan ina tsoratar muku randa hajar mai gari zata tsinke”.     Babu dai abinda Ajwaad yace, amma Maanal sai tura baki take yi. Koda aka kawo masa abinci bai iya ya nutsu yaci ba sai da ya dinga bama Maanal a baki. Itama sai ta dinga amsar spoon ɗin tana bashi. A haka Baabu da Aba suka shigo. Suma dai tsayawa sukai kawai suna kallonsu, sai kuma suka kalli juna suna murmushi. Al'amarin yaran na ƙara tasiri a zukatansu. Cike da farin ciki Maanal ta tafi ta rungume Aba. Shima ya ɗauketa yana dariya da faɗin, “Oh oh my Baby, Autar Oum kuma Bestyn Auta”.      Dariya Maanal ta sanya da jin wannan kirari na Aba, hakama Ammie da Baabu. Zama Aba yay da ita a jikinsa tana masa surutu, shiko yana biye mata dan harga ALLAH yana ƙaunar yarinyar, yanama ɗansa sha'awa da fatan wannan kusancin da shaƙuwar ya kasance musu har girma su kasance ma'aurata, duk da shi fa ko'a yanzu da su Baabu zasu amince wlhy baiƙi a ɗaurama yaran aure ba kawai. Yana dannewa ne kar ace ya cika azarɓaɓi, ba kuma asan mi gobe zata zo da shi ba.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖6️⃣3️⃣ ______________ .........Sai da Aba yasha furar da Ammie ta kawo masa sannan suka zauna tattaunawa. Gently Ajwaad ya miƙe idonsa akan Maanal dake tama Aba surutun Giro har yanzu. Nuni ya mata data tashi, ta maƙe masa kafaɗa bakinta a sama. “A'a ni ban gama ba Aba labari ba. Ka zauna na ƙarasa masa sai muje na nuna maka su Hanne dake dukana ɗaya bayan ɗaya ka musu duka har ɗakunan uwayensu”.       Harararta Ajwaad yayi, sai kuma ya sake tsuke fuska. “Idan baki taso ba ALLAH nan zan barki mu wuce ni da Aba”.     Ai baima gama rufe baki ba ta miƙe zaram, sai kuma ta kalla Aba kamar zatai kuka. “Aba ai dai dani zaku tafi ko?”.         Da ƙyar Aba ya gumtse dariyarsa da faɗin, “Sosai kuwa. Ai ƙafar bestynki ƙafarki har Kano. Oum ɗinku ma tace karna sake na baroki”. Sosai ta shiga dirga tsallen farin ciki, sai kuma ta nufi Ajwaad ta kama hannunsa. “Besty muje kafin Aba ya gama kama yaran can su Hanne jina-jina. Dan bazan tafi ban bar fuskokinsu da tabon da zasu dinga tunawa da ni ba, dole kuma asan Bestyna mai ƙarfin ILIYA ƊAN MAI ƘARFI YAZO”.       Komai bai ce ba ya riƙe hannun nata shima suka fice. Kai kawai Baabu ya girgiza, yayinda Abah ya fashe da dariya. Ammie ma murmusawa kawai tai da jerama Maanal ɗin addu'ar shiriya a zuciyarta. Bayan sun tsagaita da zancen su Maanal Aba ya gyara zama yana fuskantar Ammie.      “Ammien Amal ki kwantar da hankalinki, dan mun tattauna da su kuma ga shi Habib ya fahimta. Duk da dai an kai ruwa rana akan batun su Shahidahn gaskiya. Dan sai da nai katoɓarar nuna musu ai su Shahidahn nada mazaje a hannu, ba kuma su kowa bane sai yarana Fadeel da Fawzan sannan suka amince, amma da sharaɗin nan da wata shekarar za'ayi biki”.        Cikin matuƙar mamaki da ruɗani Ammie ke kallon Aba da Baabu. Muryarta har harɗewa take wajen faɗin, “Amma Yaya sufa su Fadeel ba'asan ra'ayinsu ba”.     “Ai basu ya dace asan ra'ayinsu ba Ammien Amaal. Su su Shahidah sune ya dace asan nasu ra'ayin saboda sune mata sune zasu zauna da su. Suko maza ne ai, sannan ni nasan daga Fadeel har Fawzan basu da bakin ƙin yarana zuƙa-zuƙa masha ALLAH, sai ma godiya ya kamata suma ALLAH da samun su a cikin sauƙi dan Shahidah da Amaal duk matan manya ne”. Ya ƙare maganar cike da barkwanci. Ammie zata sake magana Aba ya katseta. “Aifa magana ta ƙare Ammien Amaal, fatanmu ki saka albarka kawai dan ALLAH. Sai kuma batun shi Habib, ina son ki kwantar da hankalinki kiyi hakuri kiyi koyi da ƴar uwarki Fateema, zai ƙara aure bawai yana nufin ya bar sonki bane ba. Mu maza ALLAH ya saka mana son ku ku mata kuma fiye da ɗaya a zukatanmu. Wani lokacin ba gazawarku bace ba, daɗin zama da kune ke kawo hakan. Kiyi haƙuri kinji, in sha ALLAHU sai kinci ribar haƙurinki kuma na tabbatar miki bazan taɓa bari Habib ya wulaƙantaki ba. Shima kuma nasan bazai ko kwatanta hakan ba koda da wasa ma.”        Ajiyar zuciya Ammie ta sauke a hankali, dan ta fahimci dai shi nashi auren na nan daram. Fuskarta da murmushi ta ce, “Wlhy babu komai yaya. Ni dama ba nashi bane damuwata. Karatun yaran nan ne da kuma banbanci wannan rayuwar da basu tashi a ciki ba. ALLAH ya sanya albarka ya bamu zaman lafiya baki ɗaya. Baga Aunty ba ita da Mamy ai kosu ababen koyine a gareni idan ma ban tashi naga mhaifiyata da abokiyar zama ba. Dan haka ku daina tausata ma dan bashine dalilin son kuzo ɗin ba”.       “Na sani Asiya, ko shi Habib ya yabi ƙyawawan halayenki yanzu a gaban iyayenku, in sha ALLAHU kuma zakiyi nasara a rayuwarki”.     Murmushi Ammie tayi, hakama Baabu. Sai kuma Aba ya haɗasu ya cigaba da musu nasiha su duka biyun. Daga ƙarshe yace shi zai wuce dan zasu kwana a Sokoto da safe su kama hanyar Kano in sha ALLAHU. Idan kuma sun sami jirgi a daren nan ma zasu wuce. Sai dai kuma da Maanal fa zasu koma bazai bar Auta a cigaba da dukar musu ita ba.      Dariya sosai Ammie da Baabu suka sanya. Baabu ya ce, “Humm kaima kasan rigimar ƴar taka ai, ALLAH ta addabi kowa a gidan nan. Hatta da Gwaggo bata bari ba. Dan bata tsoron kurarin Gwaggo sam, shiyyasa kullum sai sunyi faɗa.”     Sosai Abba ke dariya. Yana mai sake jinjina rashin jin Maanal. Dan shi dai a ƴar fahimtar da yayma Gwaggon a iya yau kawai yaga kamar tana da zafi sosai. Sannan rashin ƙaunar da takema Ammie da yaran nasu a bayyane suke. Dan da ƙyar fa aka tankwarata akan batun su Shahidah ɗin nan. Shiko batun auren Baabu cewa tai idan yace zai bijire sai ta tsine masa wlhy. Dan haka da sauri Abban yace ai bama za'ayi hakan ba wannan kam sun karɓa. Shi yana ɗauki alƙawarin yin komai. Shine fa aka rabu lafiya, koda yake ko yanzu da suka shigo sashen nan yana kallonta tana harararsa, dan suna yin sallama ta shige ɗaki abinta kamar bata gansu ba. Amma a hakan Aban yace zai shiga ya sake gaisheta. Badan Baabu yaso ba ya masa rakkiya har cikin ɗakin, anan ɗin ma sama-sama ta amsa musu duk da kuwa Aban na janta da hira tana basar da shi.....       ★★    Maanal da Ajwaad kam koda suka fito haka ta dinga nuna masa yara abokan faɗanta, har cikin ransa yaso rama matan amma baba Haruna da ALLAH yakai idonsa ya janyesu su duka biyun zuwa ɗakinsa. Shi yayta jansu da labari bayan ya basu zuma da magani a cikin a wani ɗan ƙoƙo yace su sha duk da su basu fahimta ba sun ɗauka zumarce kawai. Daga Maanal har Ajwaad na matuƙar son zuma, dan wajen shi ma za'ace Maanal ta koya. Aiko hankali kwance suka hau sha, ko nace Ajwaad na sha yana bama Maanal Baba Haruna na musu labari. A haka Aba da Babu suka fito suka samesu. Maanal na jin zasu tafi ta fara kuka itafa sai tabi Besty. Babu kalar lallashin da Baba Haruna bai mata ba tace ina itafa sai Kano. Haka dole suka sake komawa cikin gidan aka shiryata tai sallama da mutanen gidan hannunta maƙale a cikin na Ajwaad. Dan ko shirin ma shine yay mata da kansa, su Amal ma dai da basu san yanda aka canja komai ba yanzu idanunsu duk sunyi ƙwal-ƙwal, ji suke kamar suyi ta Maanal ɗin amma babu dama. Zuma da dabino da mazarkwaila mai yawa Baba Haruna ya haɗama Ajwaad da Maanal na tsaraba. Haka aka musu rakkiya har cikin mota. Ko'a kwalar rigar Maanal bata damu da barin su Ammie da Babu da sauran ƴan uwanta ba, tana baya a tsakkiyar Aba da Ajwaad suka wuce tanata ɗagama ƙawayen faɗanta hannu dan tace sun shirya ta yafe musu😆..      __________★         Bayan wucewar su Maanal sabuwar tujara Gwaggo ta kafa a gidan, dan sai da taima Ammie zagin ƙare dangi na fitar hankali. Daga ƙarshe tace an sake matso da bikin Baabu nan da kwana huɗu juma'a kenan. Duk da abin na dukan Ammie haka ta dinga dannewa. Sai ta shiga ɗaki tai kuka. Dan ma yaranta na tausarta da lallashi dan Baabu kam ma dai takan yini bata sakashi a ido ba. Ba'a nan yake kwana ba. Tunda sukazo Giro bai kwana tare da ita ba. Ita da yaranta suke kwana, sai dai ya ɗan shigo musu a tsaitsaye saboda tsoron Gwaggo ma baya jimawa yake ficewa. Sai dai in suna buƙatar abu tai kiransa a waya. Idan kuma ya sayo sai dai a shigo da shi a ɓoye kosu Shahidah suje su amso su ɓoyo a hijjab. Maanal ce kawai ba'a ƴar haka da ita. Dan itafa bata tsoron Gwaggo. Idan tai mata tsawa ta murguɗa baki da ƙugu tai gaba abinta, haka Gwaggo zataita rantsuwar sai ta dake ta, sai ta sumar da ita. Duk kuma yanda zatai lambon kamata bata yarda, dan tsaf take cajama Gwaggo kai. Duk da taji haushin tafiya da akai da ita taji daɗi ta wani fannin, dan ta hutama da fitsararta...       Yau ɗin ma dai kuka sosai Ammie taci kafin ta dake zuciyarta, dan Babu tun daga rakkiyar su Aba har yau bai dawo gidan ba. Da alama ma Sokoto ɗin zai kwana.... _________★        Alhamdullah su Aba sun iso Kano lafiya. Duk da a lokacin anata shirin shiga sallar isha'i ne. Dan basu baro Sokoto ba sai da akai magrib. ALLAH ne ya taimake su suka samu jirgi mai zuwa Kano a daidai lokacin. Tuni Maanal tayi barci a jirgi, dole Ajwaad ya goyota suka fito tana a bayansa, sai Aba riƙe da ledar tsarabarsu dan ma sunƙi ɗakko kayan da yawa. Dan dama jirgi suka bi da zasu je. A sokoton ne abokinsa kuma ɗan uwansa ƙanin Oum amma cousin da suka fara sauka a gidansa ya bada mota driver ya kaisu Giro dan shi anan Sokoto yake zaune da iyalinsa. Aiki ne ya cillarosa nan kuma.      Alhamdullah nan ma sun samu babban yaya (Fadeel) da drivern dake kaisu school na jiransu a airport ɗin.  Yana hangosu yay saurin nufosu, shima baida yawan fara'a, dan halinsu kusan ɗaya da Ajwaad. A fuska ma sunfi kamanni, duk da dai su duka ukun suna tsananin kamanni da Abba da Oum, kasancewar su ɗin iyayen nasu aurene na zuminci, zumuncin ma na kusa kusa sosai, shiyyasa suke kamanni ɗaya, dan duk family ɗinsu haka suke da wannan kamannin. Su har alfahari suke indai ɗa na tsatsonsu ne koda an auro uwarsa bare baya ɗakko kamanninta sai nasu saboda ƙarfin jininsu. Koda Babban yaya ya gaishe da Aba ya maida hankalinsa akan Ajwaad da son taimaka masa ya amshi Maanal ɗin dake bayansa kansa ya girgiza alamar ya barta.     Hakan ya saka Babban yaya da Aban yin murmushi kawai. A haka suka ɗinguma zuwa ga mota. Driver ya gaida Abba cike da girmamawa sannan suka shiga, Abba da Ajwaad da Maanal dake barci a kusan jikinsu su biyun na baya. Shi kuma babban Yaya ya shiga gaba kusa da driver. Cikin ƙanƙanin lokaci suka iso gida, inda suka samu tarba daga Oum da Mamy da Fawzan. Sai dai Oum tayi mamakin ganin harda Maanal, dan batai tunanin zasu bari a taho da itan ba kamar yanda Ajwaad ke faɗin da ita zai dawo gida. Mamy dai bata tanka ba, dama kuma babu wanda yay tunanin tankawar tata dan dama haka take ita shiru-shiru. Ba komai ne zakaji bakinta a gidan ba. Garama idan suna hira da Oum ko Aba zaka jita cike da nishaɗi kamar ba ita ba. Amma akan yaran babu ruwanta da sabgarsu. Sosai take nuna kawaici da kara bama zaka taɓa tunanin tana da wata alaƙa da su ba...        Ɗakin Oum Ajwaad ya kai Maanal, Oum ta taimaka masa ya kwantar da ita bisa gado. Kwanciya ta gyara mata da rufa mata duvet dan ɗakin akwai ac. Batare daya zauna ba ya ce, “Oum naje wanka, jikina duk babu daɗi”.     Murmushi Oum ta masa, dan kowa yasan Ajwaad da tsaftar tsiya dama a gidan. Idan yana wani ƙalƙalin saika rantse ba yaro bane ƙarami ɗan shekara sha... Komai nashi zaka samesa kwaf-kwaf da kulawa kamar wani babban saurayi maji ƙarfi. Idan Ajwaad yay ado dole ka tsaya kallonsa. Sam bai damu da manyan kaya irin namu na malam bahaushe ba. Dan duk juma'a ma sai ankai ruwa rana da shi yake yarda ya saka. Garama idan Maanal ta saka masa rigima ta ɗakko da kanta tace ya saka sai ya saka. Dan duk da baya so Aba bai taɓa tsamesa a ɗinkin manyan kaya ba. Yanda akema su Fawzan da Babban yaya haka shima ake masa su, shiyyasa ya tarasu tab wadrobe yana ado dasu.        Yana shiga ɗakin nasu Fawzan Sarkin tsokala ya fara tsokanarsa da dariya. “Ah-ah kaga baban soyayya, kaga Auta na Auta, Besty kuma na Besty. Wai yanzu nan dan ALLAH ko kunya baka ji ba Auta kaje gidan surukai ka ɗakko Lilly? Oh kai wannan wane kalar abin kunya ne haka?”.      Harara ya ballama Fawzan ɗin yana wucewarsa bayi batare da ya tanka masa ba. Aiko Fawzan ya shiga kwasar dariya har sai da Babban yaya ya shigo ya tsagaita. Koda ya maimaita na Babban yaya dalilin dariyar daya tambaya murmushi kawai yayi shima, dan shi kansa soyayyar autan nasu da Bestynsa na ƙayatar da shi, da. Haka yana musu fata da addu'ar ɗorewa a haka har girma su kuma kasance ma'aurata kamar yanda kowa ke tofa albarkacin bakinsa akan dangantakar tasu.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖6️⃣4️⃣ ______________ .........Duk suna a d/table suna dinner Maanal ta fito tana faman murzar ido alamar yanzu ta tashi. Fawzan ne ya fara ganinta. Dan haka cike da shaƙiyanci ya furta, “Oyoyo Bestyn Auta, bada kanki a sare kije gida kice ya faɗi. Kaga surukar Oum da Abah”.      Daina susan idon Maanal tayi ta tsaya tana kallon sa da farko kamar mai mamakin ganin kanta a nan ɗin. Yayinda suma duk suka zubo mata ido suna kallonta musamman Ajwaad. Oum kuwa da Abah murmushi suke yi, hakama babban yaya. Mamy kuwa kamar bata a wajen abincinta kawai take famar ci. Hannu Oum ɗin ta miƙo mata alamar tazo gareta. Da gudu kuwa ta iso ta shige jikin Oum ɗin, sai kuma ta saki kukan shagwaɓa.         Shi ko Fawzan ya wani tuntsure da dariya yana faɗin, “Oh oh yau naga ikon rabbu surukar Oum shagwaɓaɓɓiya kenan, an dawo zakuma a ɗaura daga inda aka tsaya ko”.       Rankwashi Oum ta kai masa sakamakon ɗagowar da Maanal tayi cike da taɓara da tsiwa ta ce, “Oum kinga Yaya F ko, kice ya daina ni Babynki ce ya bar cewa suruka bana son sunan”. Yanda tayi ɗin sai da ya bama kowa dariya. Dan shi kansa Bestien nata wani guntun murmushi ya saki kawai ya cigaba da kallonta. Ita ko ta cika tayi fam dan duk zatonta ma surukar wani mugun sunane da ake gudu. Gwalo Fawzan ya mata da faɗin, “Anƙi a daina ɗin, da wani bakinta kamar na tsuntsu”.       Kuka sosai ta buɗe baki zata sanya, Abah ya saka hannu ya ɗauketa cak yana hararar Fawzan. “Kinga ƙyalesa kinji babyn Oum ɗinta. Kin san dama shi bashi da aiki sai neman faɗa da mutane in dai Fawzan ne. Shiyyasa ma bazanje da shi saudia ba sai ke da bestyn ki kawai”.     Cike da farin ciki Maanal taima Fawzan gwalo da harara. Sai kuma ta hau murna za'aje dasu saudia ita da Bestyn ta. Da wannan lallashin Abah ya kashe rigimar, ya saka mata spoon a abincinsa sukaci tare...      Bayan sun kammala cin abincin ta gama tsiyaya musu surutunta Oum tajata zuwa ɗakinta tai mata wanka. Kaya gareta fal a gidan, anan ɗakin Oum da ɗakin su AA a cikin kayansa. Tana cikin shiryata Ajwaad ɗin ya shigo hannunsa riƙe da kayan tsifa. Tana ko kallon hannunsa ta ɓata rai dan bata ƙaunar kitso sam. Fuska a marairaice kamar zatai kuka ta ce, “Besty kaina na ciwo”.        Harararta ya ɗan yi yana kaiwa zaune a bakin gadon Oum da faɗin, “Idan an gama zaki sha magani”. Sosai ta tura baki gaba, sai kuma ta kalla Oum dake gumtse dariya. “Oum dan ALLAH kaina bada zafi ba? Taɓa kiji ma”. Dariya sosai Oum ta fashe da shi tana taɓa kan, “Gaskiya Babyn Oum babu wani zafi, kanki yayi datti ki daure a tsefe kinji, jibi ƙasa a cikinsa tule. Ko baki son kuje Saudian da Abah yace?”. Jiki a sanyaye ta ce, “Ina so Oum”.      “Yauwa ton daure kinji ƴar albarka. Ai Auta bazai miki da zafi ba kin sani ko? Gama chocolates bari na baki kije anayi kina ci baza kiji ma anayi ba har a gama”.      Da wannan lallashin ta yarda badan taso ba. Haka suka fito hannunta ɗauke da ɗan bowl da Oum ta haɗa mata kayan kwaɗayi, ɗayan kuma Ajwaad ya riƙe mata. Tsakar gida suka fito tacan baya inda garden ɗin gidan yake, wajen akwai ni'ima sosai dan an gyara shi yanda ya kamata. Ga kujeru an shirya domin hutawa harda na yara, sai lilo da dai kayan wasan yara. Koda suka zauna sai da ya ɓare mata chocolate ɗin ya bata wayarsa sannan ya fara mata tsifar. A hakan ma yana farawa ta ɓata fuska zatai masa kuka. Sai da shima ya ɓata fuskar da faɗin, “Oh nacema Abah ɗin  mu wuce mu barki?”.      Da sauri ta girgiza masa kai. Ya ce, “To oya malama nutsu”. Baki ta tura gaba da faɗin, “Niba sunana malama ba”.     Murmushi yay a karo na farko, tare da jan hancinta ya ce, “To Bestyn bestyn ta ko?”.       Cike da jin daɗi ta ce, “Yes”.   Ƙaramar dariya yayi, sai kuma ya buɗe baki alamar ta bashi chocolate ɗin. Cirowa kuwa tai ta saka masa a bakinsa, ganin ya ɗan ɓata mata yatsun yasa shi kama hannun nata ya lashe wadda ta maƙale. Murmushi tai da faɗin, “Kwaɗayi”.       “Ai ke kika koya min”. Ya bata amsa yana murmushin shima. Sannan ya fara mata tsifan. Tana kallon cartoon ɗin daya sanya mata tana masa surutu da juyowa ta bashi chocolate ɗin da sauran kayan ciye-ciyen. Shi ko yana biye mata. Dama in kaga Ajwaad na zuba surutu da murmushi to lallai Maanal na a wajen kuwa tabbas. Baya wasa da al'amarinta ko kaɗan. Idan ka gansu dole su birgeka kamar ba yara ba. Haka dai aka gama tsifan, wajen taja kuma aka hau faɗa, sai da ya riƙeta da ƙyau sannan ya iya taje mata, ita ko tana kuka da faɗin babu ruwanta da shi kada ya sake kulata. Dariya ya dinga yi shi dai bai kulata ba sai da ya gama ya ɗaure mata da ribbon duk da yayi datti. Dan cikinsa uban ƙasa ne na faɗan data dinga kwasa a Giro, a hakan ma wai kusan kitso na fin biyar ne akan nata a zuwansu. Koda suka dawo cikin gidan fushi ta dinga masa, sai ta koma kula Fawzan shiko Ajwaad ɗin ya sharesu. Hakan da yake yi idan tana tare da wani a cikinsu yake sa suke faɗin suma yana kishi da su akanta.. _____________★          Washe gari suna gama breakfast Ajwaad ya tasa Maanal gaba zuwa wajen kitso. Ita ko tana faman kuka da faɗin bafa zataje ba. Sai da ƙyar Oum ta lallaɓata ta yarda bayan ta mata alƙawura. Koda suka fito tsakar gida inda ɗan kekensa yake sai da ya hau itama ta hau daga gabansa tanata cika baki da iska. Shi dai bai kulata ba yaja keken suka fito. Ai tun daga gida har zuwa shagon Aunty Saloon duk inda suka gitta sai an musu magana. Dan Maanal fa cele ce a anguwar tasu saboda tsabar fitinarta da neman faɗa. Yara ɗai-ɗai ne batai rigimar da taja Ajwaad ya jibgesu ba.             Da farin ciki Aunty Saloon ta tarbesu tanama Maanal oyoyo da dawowa. Itako ta ɓata fuska taje jikin Ajwaad ta maƙure idanunta cike da ƙwalla. Dariya Auntyn ta fara yi da faɗin, “Maanal ke baki girma da ƙin kitso? Haba ƴar gatan Ajwaad Bestyn ta. Shi gashi yana son yaga ana gyara masa ke da kitso ke kuma baƙya so”.      Baki Maanal ta sake turawa gaba da kallon Ajwaad, shima kallon nata yake yi. Sai ta sake ɓata fuska zatai kuka. A hankali ya kai durƙushe gabanta ya dai-dai tsahonsu hannayensa duka akan kafaɗarta cike da lallashi ya ce, “Ba kin min alƙawari bazakiyi kuka ba? Ko kina son yaran anguwar nan su ganki su samu abin raina ki da tsokana”.     Kanta ta girgiza masa hawayen dake cike a idonta na gangarowa. Hannu yasa ya share mata, “To kada na ƙara ganin hawayen nan. Inba hakaba kuma na fasa shiga secondary ɗin tare dake”.       Da sauri ta haɗiye kukan, cikin rawar murya ta ce, “To bana bari ba”.     “Yauwa my sweet Besty. Faɗa min mi kike so naje na saya miki? Ko awaran can?”. Ya nuna mata waje can tsallaken titi da mai awara ke ta soyawa. Kanta ta jinjiina masa. Shima sai ya miƙe tare da kama hannunta ya kaita saman kujerar wanke kan ya zaunar, fita yayi tana kallonsa daga nan. Bai wani jima ba ya dawo da awaran a leda. Lokacin har Auntyn Saloon tayi shirinta na fara wankema Maanal ɗin kai. Dan duk ta fito da kayan shampoo ɗinta da suka zo dasu a cikin ƴar bag. Haka komai na Maanal a tattale yake ga Ajwaad. Sam bai yarda a mata amfani da kayan wankin kan wajen saloon ɗin ba, duk abinda yasan ana buƙata idan sukaje shopping da Abah ke kaisu duk ƙarshen wata zai ɗakkosa. Dan shi dama ko a wajen shopping ɗin zakaga duk abubuwan da yake ɗakkowa na Maanal ne. Ƙalilan zaka samu nashi. Kujera ya jawo gabanta sosai ya zauna, dan yasan bazata yarda ba sai anyi darun. Bai bata awaran ba ya ajiye gefe yacema auntyn Saloon ta fara. Kuka Maanal ta fara ƙoƙarin farawa ya girgiza mata kansa, sai tai shiru. Haka dai aka wanke kan yana riƙe da hannunta da lallashi kamar wata ƴar mitsilar yariya can ba ƴar shekara kusan takwas ba. Koda aka gama shi da kansa ya goge mata kan da towel ɗin da sukazo da shi ya ɗaure mata shi, sannan ya dinga bata awaran a baki ana busar da kan. Da aka zo kitso kam daru aka sha na haƙiƙa, dan dole sai da ya riƙeta, amma a hakan yasha cizo a hannu da bibbigewa. Kitson ma ba wani mai yawa ba dan shikku ne. Sosai ya mata ƙyau aka saka mata bet. Maanal akwai gashi Masha ALLAH, dan sun biyo Ammie ne cikar gashi da tsaho kamar ba nasu ba.          Sai faman sauke ajiyar zuciya take idanu sun yi jazur saboda kuka ta kama hannunsa tana dubawa, dan duk sayin ƙananun haƙwaranta. Sake fashewa tai da kuka tana shafa cizon da kallonsa, shima idon nasa duk ya kaɗa saboda kukan nata. A hankali ya ce, “Minene kuma? Ba'an gama ba?”.       Hannunta na bin wajen cizon ta ce, “Da zafi ko? Muje na amshi magani wajen Oum na baka”.      Murmushi yay mata da girgiza kansa, sai kuma ya shafa kitson nata da yay ƙyau sosai ya ce, “Babu zafi fa. Jiba yanda kanki yay ƙyau. Ya kamata ki daina kukan kitso Besty kin girma.”          “To ai Oum ta ce idan na girma zan daina ”.     “Wane girma kuma ya rage Besty. Secondary fa zamu shiga ai kin girma ko. Ba kiga ni idan kika rakani wajen aski bana kuka ba”.          A sanyaye ta ce, “Zan bari. Besty muje gida zanyi barci”.    Kansa ya jinjina mata tare da miƙewa. Cikin girmamawa ya kalla Auntyn Saloon dake kallonsu cike da sha'awa da mamakin irin wannan al'amari tamkar ba yara ƙanana ba. Godiya ya mata ya ɗauka bag ɗin sannan ya duƙa Maanal dake faman lumshe ido ta hau bayansa. Kekensa ya kalla sai kuma ya kalla Auntyn Saloon ɗin. “Aunty zanje na kaita sai na dawo na ɗauka”.        “To babu damuwa Ajwaad sai ka dawo. Ka gaishe da Hajiya. Maanal daru sai kuma next”.    Maanal dai bata kulata ba, sai ma sake lafewa da tai a bayansa dan barci take ji sosai. Tana fita wanda ke a cikin shagon suka fara gulma. Aunty Saloon dai dariya take yi da sake basu labarin wannan shaƙuwa ta Maanal da Ajwaad dake birge kowa a layin tamkar ba yara ba...      Kafin su iso gida har tayi barcin. Oum da Mamy na falo suka shigo. Muskar Oum da murmushi ta miƙe tana faɗin, “Ai na sani dama da barci zaku dawo gidan nan. An sha darun ma yau kenan?”.       Fuskar Ajwaad da murmushi shima ya ce, “Tab Oum miza'a fasa. Duk na sha cizo”.     Dariya Oum ɗin tayi da faɗin, “In ba Bestien taka ba wazai cijeka a zauna lafiya Auta. Maza jeka ka kwantar da ita to”.      Ɗakin Oum ya kaita ya kwantar, sai da ya rage acn ɗakin ya cire mata ɗab hijjabinta sannan ya fito. Oum na tambayarsa ina kuma zaije yace zai ɗakko kekensa ne. Daga haka ya fice. Mamy dai bata saka musu baki ba. Yana kuma fita suka ɗora da hirarsu da suke yi ita da Mamyn hankali kwance cike da farin ciki kuma kamar ba kishiyoyi ba. A haka Ajwaad ya sake dawowa ya samesu. Ɗakinsu ya wuce yana tambayar ina su Fawzan. Oum tace sunje aikan datai musu ne. Daga nan zasu duba malaminsu na islamiyya suji yaushe zasu koma. Dan tun wancan satin ya kamata su koma matar ya sayyadin ta haihu, haihuwar kuma tazo da matsala shine ya ƙara hutun, sai dai bai sanar da ranar komawar ba taka maimai. Ciki ya shige suma su Oum ɗin suka miƙe dan lokacin salla yayi.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖6️⃣5️⃣ ______________ .......Abah bai samu zama da su Oum ba sai daren yau akan batun daya faru a Giro. Komai bai ɓoye musu ba daya faru A to Z har hukuncin daya yanke akan Fadeel da Fawzan. Sosai tausayin Ammie ya sake baibaye Oum. Dan tamkar ƙanwa uwa ɗaya take jin Ammie a ranta ba maƙwafciya kawai ba. Ɗari bisa ɗari kuma ta bada goyon baya ga hukuncin mijin nasu. Ta kuma yabama dattakonsa. Itama dai Mamy ta jimanta al'amarin ƙwarai da gaske. Akan batun yara kuwa ta nuna kawaici kamar yanda ta saba. Daga ƙarshe ma miƙewa tai tana faɗin, “Wannan maganarku ce Oum, mu ƴan ALLAH ya sanya alkairi ne”. Daga haka ta fice tabar falon.        Da kallo duk suka bita. Kowanne na sake jin ƙaunarta a cikin ransa daga Oum ɗin har Abah. Mamy abar alfahari ce a garesu, dan suna matuƙar alfaharin shigo da ita cikinsu. Tana da wasu irin nagartattun halaye masu matuƙar ƙayatarwa a zahiri. Oum da Abah sun cigaba da tattaunawa, kafin suma su miƙe bayan sun gama yanke yanda zasu fahimtar da yaran nasu batare da sunga an ƙasƙantar da su Shahidah a idanunsu ba.         A ɓagaren Mamy kuwa koda ta shiga ɗakinta kasa tsaye da zaune tayi. Ta jima a haka kafin ta ɗauka waya tayi kira. Ba'a wani jimaba kuwa aka ɗaga. Sallama tayi tana kaiwa zaune. Sai kuma ta ɗora da gaisuwa.        “Yaya mutanen nan ban san mi suke so dani ba. Shike nan ni bani da wani ƙarfin iko akan ƴaƴana ma. Daga mijin har matar kamar tare suka auro ni? Nifa na fara kaiwa gaɓar da zan nuna ma matar nan ina buƙatar ƴaƴana nima. Sai dai ya sakan ko itama tayi zuciya ta haifi nata.......” kuka ya sarƙeta.      Numfashi aka sauke mai nauyi daga can, kafin cikin isa a furta, “Kamila! Dama wannan shine abinda aka dinga guje miki tun farko. Amma kika kasa fahimta soyayyar mutumin nan ta rufe miki idanu. Daga baya aka sake nusar dake illar sakar mata yaran nan tun suna zanin goyo nan ma kika kasa fahimta ke wai neman soyayyar miji. Ai gashi nan, ƴaƴan da mijin duk suna a hannunta ke baki amfanu da komai ba sai baƙin ciki da damuwa. Kin san wacece Hajiya Fateema kuwa akan mijin nan nata? Dukkan fa bincike sai da nayi a kansu. Akwai matsananciyar soyayya da shaƙuwa a tsakaninsu tun ta ƙuruciya. Tun fa tana ƴar shekara goma sha a duniya aka aura masa ita. Shi ya raineta, gida ɗaya suka tashi, shi ya koya mata komai taya dama kike tunanin zaki shiga wannan gidan ki samu farin ciki? Haihuwa da kike ganin bazatayi ba? Humm irin su Alhaji Aliyu Darma da kike gani ba wannan bane a gabansu....”         “Yaya ni dai naji. Koma minene dai ya riga ya faru ai. Kawai yanzu ina buƙatar dawo da yarana hannuna kota ƙarfin tsiya. Musamman Ajwaad. Wlhy yaron nan yi yake tamkar ma bai san muna da alaƙa ba. Har tayata kishi yake fa. Dan ALLAH ki taimkeni”.        “Hummm ai wannan yaron taƙadari ne daga gani. Kuma ba kowa ya busar masa da zuciya ba sai ita. Ga shegiyar yarinyar nan da suke ƙalatar juna ƴar maƙwaftanku, kai na tsani yarinyar nan da uwarta wlhy saboda aminiyar Fateema ce”.       “Wlhy Yaya na fiki tsanar Asiya. Dan haka koma mi za'ayi sai dai ayin wannan haɗin auren bazai yiyu ba. Sai kace ma ita na haifamin ƴaƴan kenan”.       “A da'alama kam ita ɗin kika haifamawa. Ba kuma makircin kowa bane sai na Hajiya Fateeman. Kinga idan yaran sun auri ƴaƴan Asiyar ai itace zata cigaba da juyasu ko. Ke wannan fa ƙulline babba wlhy. Amma karki damu zamuyi maganinsu. Kizo ki sameni gobe”.       “Aunty sai dai weekend. Dan yanzu ina cemasa zan fita zai iya zargin wani abu kin dai sanshi da kaifin tunani. Amma weekend zan tambayesa zuwa kitso sai na zo”.         “To hakan ma yayi ALLAH ya kaimu. Kidai kwantar da hankalinki”.     “Humm Yaya kenan, amma in sha ALLAHU zan yi ƙoƙari sai anjima”.... ___________★        SU WAYE SU OUM?.    Abah da Oum jini ɗaya ne. Makusanta sosai dan kuwa da mahaifiyarta da mahaifinsa uwa ɗaya uba ɗaya suke. Kunga kenan su cousins ne. Asalinsu ƴan jihar Adamawa ne, a wata ruga da ake kira RIGAR DARMA. Baffa Ishaq Darma da Gwaggo Halima sune tushen zuri'ar. ALLAH yayma Baffah Ishaq Darma arziƙin kiwo da noma matuƙa gaya. Dan yana da shanaye, tumaki, awaki, raƙuma, harma da dokuna da shi kansa bai san adadinsu ba. Sannan yana noma da ake kira noma ba wasan yara ba tun duniya na kwance. Yaransu huɗu. Mata biyu maza biyu. Abubakar shine babba, suna kiransa da suna Sardauna. Sai Umar, sai Maryam, sai auta Khadijah. Baffah Ishaq baiyi karatun boko ba daga shi har matarsa. Amma hakan bai saka ya tauye yaransa ba daga yi. Su duka sunyi karatun boko mai zurfi har matan. Kafin Sardauna ya fara aure bayan kammala degree ɗinsa na farko. Ya auri ƴar aminin Baffa Ishaq da yakema kallon tamkar ɗan uwa. Ansha shagali matuƙa irin na nunama tsara a wancan lokacin, amarya da ango suka tare acan cikin garin Adamawa. Bayan auren Sardauna da kusan shekara huɗu sannan Umar shima yayi tare da Maryam a rana ɗaya. Shima Umar ya auro ne daga ɗiyar dangi anan cikin Rigar Darma, ita kuma Maryam aka aura mata wani ɗan Alhaji da suke huɗɗa da baffah tsahon shekaru. Yana zuwa ya sayi dabbobi masu yawan gaske a duk ƙarshen shekara, a hankali zuminci ya ƙulle tsakaninsa da Baffan har suna kallon kansu tamkar ƴan uwa (mutanen da kenan masu girmama alkairi). Shi wannan Alhaji dai yana zuwa daga jihar Kano ne, asalinsa kuma ɗan garin Kura ne. Ɗansa ɗaya tal a duniya mai suna Kasheem. Yana karatu a turai. Yazo wani hutu gida Nigeria ya biyo babansa nan Adamawa shine ya ga Maryam itama a lokacin tazo hutun makaranta daga Yola. Aifa yace yaga mata, Baffa kuma yace ya bashi halak malak. Ansha biki nan ma na nunama tsara, Umar ya tare da matarsa anan Rigar Darma, ita kuma Maryam aka wuto da ita Kano. UBANGIJI mai hikima shakara ɗaya tak ALLAH ya sauki matar Umar lafiya, har kuma lokacin yayan su Sardauna ALLAH bai bashi haihuwa ba shi. Dan matarsa ko ɓatan wata ma bata taɓa yi ba. Kaf family sunyi murna, sun kumayi farin ciki, an sha shagalin suna shanaye sun sha wuƙa da ƙananun dabbobi yaro yaci suna Aliyu (Abah kenan😂👍).         UBANGIJI mai rahama matar Abubakar bata yaye Aliyu ba sai ga wani cikin. Dole aka cire Aliyu daga nn, sai kawai matar Sardauna ta amshesa ta yaye. Daga wannan yaye ne kuma bai sake dawowa wajen iyayensa ba su Baba Sardauna suka cigaba da riƙo tunda su har lokacin ALLAH bai kawo iyaka ba. Matar Umar ta sake haihuwar namiji yaci sunan Hamza, shima bata yaye ba ta kuma samun wani cikin. A taƙaice dai sai da ta jera yara huɗu duk maza sannan itama Maryam ALLAH ya kawo ciki. A kusan tare kuma suka sake haihuwa da matar Umar da tai mace a wannan karon. Itama dai Maryam ɗiya mace ta haifa da taci suna Fateema (Oum kenan😂👍).         Itama Maryam matar Babban Yaya wato Sardauna suka kawoma yayen Fateema. Bakuma su sake waigawa ba dan a lokacin ne ma suka bar ƙasar. Hakan da sukai na nufin suma sun barma Sardauna Fateema har abadan. Wannan abu ya saka Sardauna da matarsa kukan farin ciki da sake jin ƙauna da soyayyar ƴan uwansu. Basu haihu ba amma gashi suma sun mallaki ƴaƴa. Bayan nan itama Auta Khadijah tayi aure anan cikin garin Adamawa. Itama kuma babu jimawa ta fara haihuwar. Itama kuma ɗanta na fari haka ta mallakama Sardauna shi kamar yanda sauran ƴan uwanta biyu sukayi. Sai kuma cikin hukuncin ALLAH fin shekara goma sha sai ga matar Sardauna da ciki. Zamu iya cewa wannan zuri'a basu taɓa tsintar kansu a irin farin cikin da suka samu kansu ba na wannan tsakanin. Dan tuni Maryam ta baro ƙasar waje tazo gida Nigeria. A lokacin yaranta biyu da Kasheem Kura bayan Fateema da sukai ƙyauta. Majdiya, Sulaiman. Itama Khadijah nada biyu bayan Sa'eed da sukai ƙauta ma Sardauna. Sai matar Umar nada biyar bayan Aliyu da sukaima Sardauna ƙyauta suma. Ansha matuƙar shagali da bidiri na wannan ciki har ALLAH ya kaishi haihuwa aka haifo ƴan biyu duk maza. Kwantata muku irin shagalin da akai ai bashi misaltawa. Musamman Aliyu da Fateema da Sa'eed da akai ƙanne.        Zuwa yanzu Aliyu ya fara zama saurayi, dan yana da shekara kusan goma sha bakwai a duniya. Yayinda Fateema keda goma sha ɗaya cif. Akwai wata irin shaƙuwa da ƙaunar juna a tsakanin Fateema da Aliyu mai ban mamaki. Sun tashi tamkar wasu tagwaye duk da Aliyu ya bata shekaru sosai. Soyayyar ce mai ƙarfi irin wadda zaman rubutata ma jan lokaci ne. Gashi suna matsanancin kamanni dan ita Fateema ta ɗebo dangin mahaifiyarta ne gaba ɗaya. Sauran yaran Maryam kuwa sun biyo mahaifinsu Kasheem Kura sosai. Hakama yaran Umar ƙannen Aliyu kaf ɗinsu sun ɗebo gida ne, babu wanda ya biyo mahaifiyarsu, suma yaran Khadijah duk suna kamanni da danginta. Sai su ƴan biyu. Wannan yasa suke jin alfahari akan su jininsu nada ƙarfin da suke ɗebo kamannin gida ne. Yanda su iyaye ke kamanni da juna haka suma ƴaƴan duk suka ɗebo. Hatta da yaran Maryam dake kamanni da mahaifinsu sun ɗebo wasu abubuwan nasu, ita dama Fateema gaba ɗayanta sune.        Soyayya da shaƙuwar Aliyu da Fateema yasa Baffah Ishaq bama ƴaƴansa shawarar haɗe yaran aure saboda gudun shaiɗan a tsakaninsu, dan shaƙuwar tayi yawa matuƙa komai zai iya faruwa. Babu kuwa wanda yayi musu akayi hakan. Fateema nada shekara goma sha biyu da wasu watanni, Aliyu nada goma sha tara da wasu watanni aka ɗaura musu aure. Akai kuma shagalin biki irin na gata sai dai sun tare anan gidan Baba Sardauna ɗin dan yace yaransa bazasuyi nesa da shi ba. Balle kuma gasu yara ƙanana basu kai ƙwarin da za'a barsu su kaɗai ba tukkuna. Soyayya ta ƙara ƙarfi a tsakanin Fateema da Aliyu, yayinda a gefe suke ta karatunsu ga kuma kulawar iyaye. Aurensu nada shekara uku ALLAH yayma gwaggo Halima rasuwa. Kaf wannan zuri'a ta Darma sunji wannan mutuwa matuƙa, sunyi kuka har sun rasa hawaye musamman ma Baffa Ishaq Darma daya rasa mata ƴar uwa uwar ƴaƴansa. Bayan rasuwar tata kuma shima duk sai lafiya tai masa ƙaranci. Shekara biyu tsakaninsu shima yace ga garinku nan. Matuƙar ruɗani wannan family sun sake shiga, har takai Baba Sardauna da Baba Umar sun kasa jin daɗin zaman garin Adamawa sukayo hijira zuwa Kano. A lokacin shekarun auren su Aliyu biyar cif a duniya. Fateema nada sha shida, Aliyu nada ashirin da uku. Ya kammala karatunsa na jami'a, ita kuma zata shiga ss a sakandire.         Shekarar da Fateema ta kammala sakandare a shekarar ALLAH ya bata ciki. Murna da farin ciki ba'a magana. Dan wannan zuri'a na matuƙar son haihuwa. Sosai cikin ke bata wahala, kullum tana nane da Ummanta. (Matar Sardauna) Dan soyayya take musu ta haƙiƙa da sam bama su san ainahin ba itace mahaifiyarsu ba sai lokacin da akai musu aure. Hakan kuma bai sa sun canja daga soyayya da ƙaunar da suke mata ba. Itama kuma haihuwar da tai baisa ta sassauta soyayyar da take musu ba a matsayin ƴaƴa har gobe. Haka dai akai wannan rainon ciki Fateema kullum na sashen iyayensu. Har abun na damun Aliyu dan idan yana son ya kasance da ita sai yayi mata wayo da ƙyar tazo nasu sashen da aka ware musu a gidan. A haka ALLAH ya kai wannan ciki lokacin haihuwa. Sai dai yazo da doguwar naƙuda. Tun ana hasashen haihuwa a kusa har al'amarin ya fara bama kowa tsoro aka yanke shawarar yimata theater. A wancan lokacin matuƙar tsoron theater akeyi dan kodai a rasa ɗa ko a rasa uwa. Dole da wahala cikin biyun nan ɗaya bai kasance ba sai idan duk suna da tsohon kwanan ne uwar da ɗan. Aliyu kuka ya sanya akan bai amince ba, sai da likita yayta lallashinsa da su Baba Sardauna sannan da ƙyar ya amince aka shiga theater da Fateema.......✍️    _(Ina fatan dai kuna gane kan labarin😆. Fateema itace OUM a yanzu, Aliyu ne ABAH a yanzu😂👍)._ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖6️⃣6️⃣ ______________ .........Alhamdullah bayan dogon zaman jira da fargaba da kasancewa a tashin hankali an samu nasarar ciro yara ƴan biyu a jikin Fateema duk maza. Sai dai ɗaya bashi da rai, rabin jikinsa ma har ya ɗan fara ruɓewa. Wannan yanayi ya saka farin ciki da alhini a wannan zuri'a duk a lokaci guda. Sai babbar damuwarsu sanin halin da Fateema ke a ciki kuma. Dan Doctors ɗin dai since su basu lokaci. Haka suka sake koma a yanayin damuwa da taraddadi musamman ga Aliyu har zuwa washe garin safiyar ranar. Dan wajen ƙarshe sha biyu aka samu nasarar farfaɗowar Fateema. Dama wannan shine tsaikon da likitocin suka samu na zahiri. Zuwa yanzu kam kowa ya warware, farin cikin kowa ya fito a bayyane, anatama juna barga da addu'a ga jaririn da ya rage, wanda ma bai zo da ran ba ana masa addu'a.....        Watan Fateema ɗaya cif a asibiti aka sallesu, jikinta da sauƙi sosai, sai dai yanayin cs na wancan lokacin ba dai-dai yake dana yanzu na zamani ba. Sai ya kasance wasu tsarabe-tsarabe kan biyo baya da har mutum kan iya ɗaukar dogon lokaci yana mafa da jiyya sama-sama har komai ya zama normal. Zuwa lokacin tuni an raɗa sunan jariri da aka barsa da sunansa wato Hussain. Dan Hassan ɗinne baizo da rai ba kasancewar shi aka fara cirowa. Raɗin suna kawai akai, sai bayan sallama aka shirya taron suna. Ansha shagalin kam mai birgewa da nunama tsara, sai dai maijego na dauriyane kawai dan sam bata jinta cikin isashiyar lafiya har lokacin. Sai dai bata son ɗagama mijinta da ƴan uwanta da iyayenta hankali, shiyyasa ta cigaba da daurewa har taro ya tashi lafiya ta cigaba da wankan jegon da Umma ke mata da kanta. Wato matar baba Sardauna. Sun gama wankan jego lafiya, dan kusan ma arba'in biyu sukayi, ta ɗan zaga dangi harda Saudiya ita da Aliyu sukayo sati uku sannan suka dawo. Abin ƙaddara satinsu biyu da dawowa Hussain ya fara wata mura mai ban tausayi, murar fa ko numfashinsa da ƙyar yake fisga. Hankali tashe suka wuce asibiti da yaron, sai dai UBANGIJI shi mai hikima ne, a daren shima yabi ɗan uwansa. Kuka rurus Aliyu ya dinga yi, amma a mamakin kowa Fateema ko ɗigon hawaye, sai ma ta koma itace ke lallashin mijin nata kuma ɗan uwanta. Bayan rasuwar Hussain da kusan wata biyar sai ga Fateema ta fara laulayin sabon ciki. Murna a wajen Aliyu ba'a magana ko kwatantawa. Hakama sauran ahalinsu kowa na fatan alkairi da addu'ar ALLAH ya inganta. Sosai wannan ciki yazo ma Fateema da tsanani fiye dana ƴan biyu, dan bata sati guda a gida sai a asibiti, ƙarshe dai suka riƙeta a asibitin domin samun bedrest. Dan haka kawai saita dinga bleeding, doctors sunyi iya ƙoƙarin ganin sun shawo kan matsalar amma al'amarin ya gagara, har takai mahaifin ta dake matsayin babban likita a saudia wato Kasheem Kura ya nufo Nigeria da kansa. Shine ya tsaya akan matsalar, inda ya fahimci ƴar tasa tana fuskantar babbar ƙaddarane mai girma. Ya shiga tashin hankali amma haka ya daure ya jure ya fito fili yama uban riƙonta da uwar riƙon ta da mijinta bayani akan dole ne fa a raba Fateema da wannan ciki, dan sam mahaifarta bazata iya riƙeshi ba. Hasalima sai an rabata da mahaifar kanta sakamakon ciwo mai haɗari data kamu dashi, in ba hakaba kuma ciwon zai fara girma wataran a wayi gari ya harbi dukkan illahirin jikinta. Amma idan sunyi ƙoƙarin cirewa yanzu in sha ALLAHU an rabu kenan.       Wannan al'amari ya matuƙar ɗagama kowa hankali, musamman ma Aliyu. Amma lafiyar matarsa tafi masa duniya da abinda ke cikinta. Dan haka babu wani ja'inja ya amsama Abbu cewar kawai a cire ɗin. Haka kuwa akayi, aka cirema Fateema cikin da dama bai wani zauna da ƙyau ba, aka kuma cire mata mahaifa. Wannan shine ya kawo mata sanadin yin doguwar jinya ta kusan watanni takwas, kafin ALLAH ya bata lafiya komai ya daidaita tamkar ma ba'a taɓa yi ba. Har kuma lokacin bata taɓa sanin an cire mata mahaifa ba. Bayan samun lafiyarta abu na farko shine nema mata gurbin shiga jami'a da Baba Sardauna yayi ana BUK. Dan danan kuwa ta fara karatunta. Dan Fateema yarinya ce mai hazaƙa matuƙa da son karatu.        A randa ta fara shiga makarantar ɗaukar darasi a ranar suka fara haɗuwa da matashiyar budurwa da bazata wuce sa'arta ba, in ma ta girmeta baifi da shekaru uku zuwa huɗu ba. Kamila Shu'aibu ƙyaƙyƙyawar yarinya, baƙace amma baƙinta mai ƙyau ne. Tana da matuƙar sanyin hali da rashin son yawan magana. Wajen zama ya fara haɗa su da Fateema a ranar farko, Fateeman ce kuma ta samu Kalima. Bayan ta mata sallama fuskarta da murmushi tai nuni da kusa da ita tana faɗin, “Sis... Kozan iya zama?”.      Murmushi mai sanyi Kamila tai mata itama, tare da nuna mata wajen ta ce, “Bismillah mana ki zauna”.    Murmushi Fateeman ta sake mata sannan takai zaune da faɗin, “Thanks you”. Daga haka babu wanda ya sake shiga sabgar ɗan uwansa suka maida hankalinsu ga malamin. Tun daga wannan ranar sai ya zam duk wanda ya riga wani zuwa a cikinsu sai ya tanadarma ɗan uwansa waje a kusa da shi. Tun abin na musu kamar wasa har shaƙuwa ta fara tasiri a tsakaninsu. Sai dai babu wanda yasan komai daga rayuwar ɗan uwansa, karatun kawai suke yi har tsawon watanni. A hutun farko da suka farayi har aka dawo akaci kusan sati biyu babu Kamila, hankalin Fateema ya fara tashi ta fara bincike a wajen ƴan ajinsu, sai dai kowa kance shi bai san inda Kamila take ba ba tare ake ganinsu ba. Kamar wasa Kamila ta shafe watanni har biyu bata dawo school ba. Har Aliyu ya fahimci matsalar Fateema ya tambaye ta. Bata ɓoye masa komai ba ta sanar masa, shiko dama yasan labarin Kamila a wajenta tun farko. Haka domin farin cikinta yazo har makarantar ya tayata bincike har ALLAH yasa suka samu wanda yasan gidan su Kamila ɗin. Shine yay musu rakkiya.         Sosai Kamila ta shiga matuƙar mamaki tare da jin ƙaunar Fateema a ranta. Suka rungume juna suna kuka. Aliyu ne ya shiga basu baki, inda sai a lokacin Kamila ta ganshi. Mutuwar tsaye tayi dan lallai bawan ALLAHn ya haɗu, ya kuma daki zuciyarta da nashi tsarin, amma sai ta danne. Da farko tayi zaton yayan Fateema ne kawai saboda tsananin kamanni da sukayi, dan haka ta gaisheshi da girmamawa da kiransa da sunan Yaya. Shima ya amsa mata kadaran kadahan dan babu wata mace dake birge Aliyu sai Fateemansa. Hatta sauran yara matan family ɗinsu sam baya sakar musu fuska. Anan soro aka masa shimfiɗa, su kuma suka shiga daga ciki.       Su Kamila talakawane sosai, sannan tana rayuwane a hannun kakarta Iyale. Ashe ciwone ya kwantar da Iyalen ita kuma Kamilar ke jiyyarta shiyyasa bata koma makaranta ba. Ta wani gefen kuma babu kuɗin da zataje tai buƙatun makarantar ma. Dan mahaifinsu kaɗai Iyale ta haifa, su uku kuma suka haifa duk mata. Mahaifiyarsu ta rabu da babansu tuni saboda tsananin rayuwar talauci da suke a ciki. Yayi yunƙurin ƙwacesu a hannunta amma sai ALLAH ya bata nasarar guduwa da yayarta da ƙanwarta. Ita kuma a lokacin tana hannun Iyale dan tun yaye dama take anan. To a yanzu hakan dai ance Maman nasu na Saudia tana tukari, suma ƴan uwanta biyu na'a tare da ita. Babansu na son karatu shiyyasa ya tsaya mata cewar zatayi, dan baya son nan gaba ƴan uwanta dake a wajen mahaifiyarta su fita cigaban rayuwa. To da ƙyar da ya ALLAHU aka haɗa kuɗin makarantar ta fara saboda takardunta sunyi ƙyau, sai kuma gashi tunkan aje ko'ina karatun na neman fara tangal-tangal, dama Sakandire ɗin ma dayaya aka gama, mahaifiyarta ce ke turo kuɗi. Ɗan tsakanin nan kuma ta ɗauke musu wuta saboda roƙon da Iyale ke mata akan ta dawo garesu kodan ƴaƴan dake tsakani.       Zuwan Fateema da Aliyu gidan shine ya zamewa Kamila rahama da tarin alkairi, dan kaɗan daga tarihinta da Fateema taji ya ɗaga mata hankali, suna dawowa gida ta sanarma Aliyu komai tare da roƙonsa ya taimakawa Kamila ta koma makaranta. Baiyi musu ba kuwa ya taimaka da iya nasa ƙarfi Baba Sardauna ya ƙarasa sauran shi kuma. Hakan ya zama sanadin komawar Kamila makaranta, aka kai Iyale asibiti, aka kuma bama mahaifinta jari ya fara sana'a tare da tsaya masa ya ƙara aure. Wannan hidima mai ban mamaki daga ahalin Fateema shine ya sake dunƙule Fateema da Kamila waje ɗaya, wadda zuwa yanzu ta fahimci Aliyu mijin Fateema ne Kuma yan uwane na jini. Tayi kuka sosai dan harga ALLAH Aliyu ya shiga ranta sosai, amma ta dannema zuciyarta tare da ƙoƙarin ciresa a ranta duk da tasan abu ne mai matuƙar wahala.      Haka wannan abota ta cigaba da tafiya, shaƙuwa da zumunta mai ƙarfi na ƙara tasiri a tsakanin Kamila da Fateema. Har takai Kamila kanzo gidan Sardauna tai kwanaki a wajen Fateema. Babu wanda ya taɓa ƙyamatarta ko ƙyararta balle kallon banza. Ƙyautata mata suke da iya iyawarsu har ma da iyayenta. Suna da shekara biyu sun shiga farkon ta uku a jami'a hankalin Fateema ya fara tashi da ganin bata sake samun ciki ba. Ta fara takurama Aliyu suje asibiti amma sai yay biris da ita. Ta cigaba da masa naci daga ƙarshe yace babu inda zaije. Haihuwa ta ALLAH ce kuma lokaci ce. Idan sukai hakuri lokaci yayi zai basu. Shi ba haihuwar yake so ba ita yake so. Sam kalamansa basu gamsar da ita ba, dan haka ta samu Kamila da ƙorafin. Amma itama Kamilar kasancewar bata san komai ba sai ta lallasheta da bata shawarar ta bisa a hankali ta kuma cigaba da yin addu'a. Hakan kuwa akayi, Fateema ta sake yin haƙuri, sai dai kuma ta kasa daurewa dan sosai take son haihuwa. Musamman daya kasance ta ɗanɗana haihuwar da daɗin ɗa a hannu taji. A wata ranar juma'a ta zagaye taje asibiti batare da sanin Aliyu ba. Acan ne fa ta jiyo abinda ya sakata yanke jiki ta faɗi dan tashin hankali, dan sai nemo ahalinta akai suka sameta a nan.          Hankalin Aliyu da Baba Sardauna da Umma ya tashi jin abinda Fateema tazo ta binciko, dan haka suka rufeta da faɗa musamman ma Aliyu, yayinda ita kuma take kuka mai ban tashin hankali da tsuma zuciya. Dole suka koma lallashinta kuma. Kwananta biyar a asibitin aka sallameta, ta koma gida da sabuwar jiyyar zuciya. Sai dai mijinta da iyayenta na tsaye a kanta da lallashi daban baki da nasiha. Dan har malami sukutum Aliyu ya ɗakko mata yay mata doguwar nasihar yarda da ƙaddara ga bawa. Alhamdullah hakan yayi tasiri zamuce, dan ta rage damuwa sosai. Gefe kuma ga Kamila itama tana sake tausar zuciyarta. Yin haka babu jimawa mutanen Saudia sukazo hutu gida, a lokacin kuma aiki ya maida Dr Kasheem Kura Paris dan haka sukazo hutu gida daga nan kuma can zasu wuce. A wannan ɗan zama ne Maryam (Mahaifiyar Fateema kenan ta asali) ta nutsu wajen yima ƴarta Fateema nasiha da nusar da ita karta sake saboda ƙaddaratta ta tauye ɗan uwanta kuma mijinta daga samun ƴaƴa daga wata matar, ta barshi ya ƙara aure duk wadda ta zo ta haifa kamar nasu ne su duka. Tun wannan nasiha na tada hankalin Fateema saboda dunbin soyayyar da takema mijinta harta fara tasiri saboda tausayi da ƙaunar da take masa ta haƙiƙa ce. Bayan tasha fama da yaƙi da kanta da tsananta addu'a bayan wucewar iyayenta da ƙannenta biyu ta tunkari Aliyu da batun ƙara aure. Wayyo ai ranar Fateema taga ainahin abinda ake kira tujara. Dan rufe ido Aliyu yay ƴamata tas, ya kuma tabbatar mata idan ta sake tunkararsa da wani batun ƙara aure sai ya ɓata mata rai fiye da haka. Shi yace mata yanada sha'awar zama da mace fiye da ɗaya ne. Koya sanar mata rashin haihuwarta matsala ce ga rayuwarsa. Ita yake so ai, zai kuma cigaba da rayuwa da ita a haka har ƙarshen rayuwa........✍️       _🥲Tofa rikitata_ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖6️⃣7️⃣ ______________ .........Bayan yin hakan kamar Fateema ta haƙura tabar Aliyu, zuwa wani lokaci kuma saita dawo da zancen. A wannan gaɓar ma sunyi rikici sosai da har ya kaisa ga kai ƙararta ga Baba Sardauna da Ummu. Dole sukai zama dasu domin sasanta rikicin. Sai dai a wannan sasanci ma bawai Fateema tabar wannan rikici bane, dan ko'a gaban su Baba Sardauna tace tana akan bakanta. Shima yace yana akan bakansa. Fateema ta cigaba da naci da takurama Aliyu akan batun aure da yaƙin son fahimtar da su Baba Sardauna dalilinta. Tun kowa bai fahimceta ba har aka fara goya mata baya. Musamman da taga su Baba Sardauna kamar basa so sai ta shirya tai tafiyarta gidan Kakanninta wato Alhaji Lawan mahaifin Kasheem Kura. Sai da ta bari hankalin Aliyu yay masifar tashi sannan ta bayyana kanta bisa tasota gaba da Baba Lawan ɗin yay suka zo gidan Baba Sardauna. A wannan zamane suka tattauna sosai Baba Lawan ya nuna musu Fateema ta fisu gaskiya, ya kuma kawo hujjoji da dole suka amsa kodan kasancewarsa Uba ga harsu su Baba Sardauna ɗin.        Duk da haka har a lokacin shifa Aliyu bai gamsu ba. Amma baice komai ba. Sanin halinsa yasa anan Fateema tace ayita ta ƙare dan karma yace ya fasa. Ya zaɓa a ƴaƴan dangi duk wadda tai masa in ma a gefe ne ma duk taji ta gani. Ai ko a fusace Aliyu ya balbaleta da cewar shi bai son kowa. Ita da tace taji ta gani sai ta kawo matar tunda ita zai aurowa dan ita ta damu. Dariya kawai su Baba Sardauna sukayi, dan sun tabbatar fa Aliyu bai ƙaunar batun ƙara auren nan sam. Aiko Fateema bata gusa ba tace to ga ƙawarta aminiyarta Kamila, tasan halinta tasan tushenta ta kuma yarda da tarbiyyarta. Wani mugun kallo Aliyu ya watsa mata kuwa. Itama ta murguɗa masa baki ta ɗauke kanta dan zuciyata ta gama rufewa ita dai kawai Aliyu yay aure su samu yara ace nasu ne.        Anan ma Aliyu yaso tirjewa. Amma sai su Baba Sardauna sukaita lallashinsa da ƙarfafashi. Badan yaso ba ya amsa kawai. Ammafa suna komawa sashensu ya balbale Fateema da faɗa itako ta masa banza. Ita dai tunda burinta ya cika yaje yayta yi. Anyi haka da sati ɗaya Fateema ta shirya taje har gida ta tunkari Kamila da zancen. Ruɗewa Kamilar tayi.      “Haba Fateema wace irin maganace wannan. Shin kina zargin ina son MIJINKI ne komi?.....”      Hannu Fateema tai saurin ɗaga mata. “Kinga Kamila kada ki sauya min magana. Ni ban taɓa zarginki da koda kwatankwacin hakan ba. Hakama mijina nasan wanene shi, dalilin ƙara auren ne kawai ya taso masa. Kamila da'aje a auro wadda ban san halinta ba tazo ta rabani da shi ba gwara wadda na sani nasan halinta tasan nawa ba. Ina sonshi Kamila so mai tsanani, bazan so wadda zata zo ta cutar damu ba, domin maganar aure fa ake ba hutu ko zaman wucin gadi ba. A gaba ɗaya na hanga na hango kece kawai halayenki sukai min dai-dai da rayuwar mijina. Na kuma tabbatar miki zai soki kamar yanda yake sona in sha ALLAHU in har kin cigaba da zama akan ƙyawawan halayenki. Ba tallarki nai masa ba, haka kema ba tallarsa nake miki ba. Cancantar kasancewar mu a inuwa guda mu uku kawai na hango. Ki taimaken Kamila kada kice a'a, dan cewar a'a ɗinki na nufin wata da ban sani ba zata shigo min gida. Bai zama lallai ta kasance mai ƙyawun zuciya irinki ba. Maybe ta rabani da shi, maybe ta maidani gefe maimakon farina ya koma ganin baƙina da kasawata. Amma ke fa. A tsahon shekaru uku da muke tare ina jinki tamkar jinina, tamkar wata twin sister ɗina da muka tashi tare muka girma tare. Dan ALLAH ki tausaya min, ki auresa kizo ki haifa mana yara mu haɗu mu rungumesu tare. Mu rainesu tare, mu basu tarbiyya tare, su tashi a tskaninmu tare. Ba'a auro wadda kota haifi ƴaƴan zasufi ƙarfina ba, su ringa min kallon matar uba ba uwa ba. Please na roƙeki”. Kuka ya sarƙe Fateema. Itama Kamila kukan takeyi, sun jima a haka kafin Fateema ta miƙe ta tafi, tare da bata damar yanke hukunci....      To bayan dai kai ruwa rana da faɗi tashi, da kace nace da ƙyar dai Kamila ta amince bisa tsayawar ƴan uwanta biyu da suka dawo Nigeria a lokacin tare da mahaifiyarsu. Sosai farin ciki Fateema ta nuna da amincewar Kamila, taje har gida tai godiya. Anan ne suka fara sanin juna da sauran ƴan uwan Kamila da kuma mahaifiyarta da a yanzu itama take ƴakin neman komawarta ga mahaifin su Kamila ɗin.           An fara shigi da fici akan auren Aliyu da Kamila, sai dai shi ango ya tare gabas ya tare yamma akan shi babu ruwansa. Da ƙyar ma ya amince yaje yaga Kamila a gidansu sau biyu. Dai-dai da lefe da sadaki duk Fateema ta biya. Dan kaf Family ɗin Baffa Ishaq Darma nada kuɗaɗensu a asusun bankuna tun daga manya har yara. Kamar yanda Fateema ta buƙata babu wanda ya saka mata hannu a hidimar wannan aure itace tai komai da kuɗaɗen asusun bankinta. Sai abincin taron biki ne da abubuwan da suka biyo baya Baba Sardauna ya sauke mata akan dole ba dan taso ba. Haka dai aka ɗaura Auren Aliyu da Kamila. A kuma lokacin ne Baba Sardauna ya bama Aliyu gidan zama, dan yace yakamata shima ya koma nashi da iyalinsa yabar gidan gandu. Hakan baima Aliyu ba, amma baya iya musu dole ya amsa. A sabon gida aka kai amarya Kamila, ita kuma Fateema tace sai bayan kamar wata guda zata tare. Da kanta taima ango rakkiya gidan amarya. Sai kuma bayan ta koma gida taci kuka harta godema ALLAH. Daga baya kuma ta maida komai ga ALLAH taita sallolinta harta samu natsuwa zuciyata tai fayau kamar ba ita ba. Sai ma walwalarta ta ninku a safiyar ranar. Har Aliyu da yazo gidan ya nuna jin haishin yanda ya ganta cikin farin cikinta. Wai ai bata kishinsa ta masa auren dole. Bayan dariya kawai bata kulashi ba ita dai. Tunda dai taci nasara sai fatan kuma ALLAH ya azurtasu da abinda ake nema...       To da farko dai zaman Aliyu da Kamila babu wani armashi. Dan bai taɓa kulata a shimfiɗa ba. Baya sakar mata fuska. Baya zama suyi hira. Takurar Fateema ma ke sakashi zaman gidan amaryar da cin abincinta dan yasan idan yaje can wajenta ba bashi zatai ba. Gashi ta saka masa takunkumin bayan sati ɗaya ta ƙara masa sati uku wata guda zai yi a wajen amarya. Su Umma kuma sun goya mata baya. Hakan kuwa dole ya cika wata gudan nan a wajen Kamila sannan Fateema ta tare a gidan, har lokacin kuma bai taɓa kusantar Kamila ba. Itako Kamila hankalinta a tashe yake, dan bata tabbatar tana son Aliyu so mai tsananin gaske ba sai a yanzu da suka zama ma'aurata. Yanda yake mata, ko duk motsinsa Fateema dai yasa ta fara jin kishin Fateema mai tsananin gaske a zuciyarta. A ganinta ba'ai mata adalci ba. Idan ance Fateema tasa aka aurota to ai dama bawa baya wuce ƙaddarasa. Tun ran gini tun dan zane. Koda sawar Fateema koda rashin sawa dama ALLAH ya ƙaddara sai Aliyu ya ta zama mijinta. Wannan zafin kishi daya fara taso mata yasa ta tunkari mahaifiyarta da ƴan uwanta da batun, maimakon su tausheta su lallasheta su kuma sai suka fara ɗorata a hanya mara ɓillewa. Aiko ta mitsithtsike ido ta nunama Aliyu bafa zata yarda ba. Dan yanzu matsayinta ɗaya da Fateemar da yake damun mutane da batunta. Tofa wannan abu ya tayar ma Aliyu da hankali, yo tunkan aje ko'ina kenan ma. Tab ɗin jan inji mata, ai dole yayma tufƙar hanci. Nan fa ya zauna ya warware Kamila tsaf da rashin mutunci, yo har a gayama bafillace zuciya da baƙar magana. Uwar watsi sukai yace taje gida za taga aike. Hankalinta ya tashi sai kuma duk ta gigice. Ita ina taga ƙafar tafiya gida tabar wannan daular da kowa ke mata barka da arziƙin shigowa. Sannan ma auren sati uku kawai ai wannan abun kunya ne da ko'a mafarki bata fatansa. Dole fa ta zubar da makaman yaƙi ta shiga neman afuwa da rusar kuka da ban haƙuri tana tabbatar da sharrin shaiɗan ne. Hakan ma bai saurareta ba, yace saifa ta tafi. Haka kuwa dole ta tafi gida batare da kowa ya sani a dangin Aliyu ba. Amma sai dai me, a ranar iyayenta suka maidota, suka kuma duƙufa bama Aliyu haƙuri suma da tabbatar masa ƙuriciyace ke damun Kamilar kawai. Amma yay mata afuwa ko Fateema kada ya bari tasan wannan al'amarin dan ALLAH. Suka kuma masa alƙawarin canjawar Kamilar fiye da yanda yake buƙata.      Badan dai Aliyu yaso ba wannan wuta ta mutu a haka. Sai dai kuma ya sharɗanta ma Kamila sharuɗai masu tsauri game da Fateema in har tana son cigaba da rayuwa a cikinsu. dole kuwa ta amsa da hannu bibbiyu tayi biyya. Sai dai kuma acan ƙasa ta ɗauke karatun uwarta da ƴan uwanta tsaf. A haka Fateema ta tare gidan itama. Da gaske Kamila ta kwantar da kai fiye da zaton Aliyu. Tana bin shariɗɗansa sau da ƙafa. Bawai shariɗɗansa kawai ba, da gaske Fateema mugun kwarjini take mata, dan matar nada wata irin baiwa da nagarta mai ban mamaki. Ga ƙyaƙyƙyawar zuciyar zama da kowa da gaskiya. Sai dai bata son raini, bata son munafunci da wulaƙanci. Wannan abinda Kamila ta sani ne tuni, dan haka ta shirya yaƙar Fateema da su har ma da Aliyu. Sannu a hankali kuwa suka fara tasiri, dan duk wata hanya ta gwaji Aliyu yabi akan Kamila game da zamansu bai kamata da kowane laifi ba. Sai ma yanda take bin Fateeman ya fara saka masa jin nutsuwar zama da ita. A gefe kuma ga Fateema kullum damuwarta da fatanta taga Kamila da ciki.       To tsakanin mace da namiji kwance a ɗaki ɗaya sai ALLAH, yau da gobe kuma bata bar kowa ba. Dan sannu a hankali dai Kamila taci nasara akan Aliyu cikin dabaru da kissa irin na mata ya maidata cikakkaiyar mace. UBANGIJI kuma mai hikima da yin yanda yaso a lokacin da yaso ba'a rufa wata biyu da Kasancewar tasu a ƙarƙashin inuwa ɗaya ba sai ga Kamila ta fara laulayin ciki. Ya rabba zokuga murna ga Fateema. Sai ma ka ɗauka itace da cikin. Gaba ɗaya ta kwashe kulawarta kacokan ta maida kan Kamila. Hatta shi kansa Aliyun yanzu ba wani yana samun lokacinta bane, har ya fara kishi da hakan sai da ta zauna ta lallashesa. Bawai baya farin ciki da cikin da Kamila ta samu bane, a'a yana dannewa saboda baya son ko yaya zuciyar Fateemansa ta sosu. Dan haka ya barma zuciyarsa nasa farin ciki ita ya bari take nata a bayyane dama zuciya. A haka kwanci tashi ALLAH ya sauko Kamila lafiya, ta haifo ɗanta namiji mai tsananin kamanni da Aliyu da Fateema tamkar sunyi kaki, dan in baka sani ba kazo saika ma ɗauka Fateeman ce ta haifi yaron. Wannan shine ƙalubale na biyu daya sake girgiza Kamila da ahalinta, sai dai sun shanye a cikinsu suma sunata fatan alkairi. Sai ma ɗaukar jinjiri da Kamila tayi domin sake samun fada ga Aliyu tun a randa ta haifesa ta damƙawa Fateema tare da alƙawarin mallaka mata shi na har abada. Ta kuma sake maimaitawa a gaban Baba Sardauna da Umma da dukkan ahalin Aliyu da nata ahalin. Ranar kuka sosai Fateema tayi da sake jin ƙaunar Kamila. Tana ji a ranta lallai batayi zaɓen tumun dare ba. Hakama Aliyu wata sabuwar soyayyar Kamila ce yaji ta soki ƙahon zuciyarsa tayi tasiri a ciki tare da mamaye komai. Duk wanda zai so Fateeman sa to har abada zai dawwama shima kam yana sonshi da ƙaunarsa ne.         Haka dangin Aliyu da Fateema ma suka zo aka haɗu akasha shagalin suna yaro yaci suna Fadeel (Babban yaya 😂👍).       Bayan shan shagalin suna aka bar masu ɗansu. Gaba ɗaya Fadeel a ƙarƙashin kulawar Fateema yake. In dai ka ganshi a hannun Kamila to lallai za'a bashi abincinsa ne. Sai ko dare yayin yin barci. Amma dukkan wahalhalu na raino da kulawa Fateema ce. Kai hatta daren ma yana fara kai watanni shida ya koma kwana hannun Fateeman. Dan ALLAH yayisa bamai fitina ba. Tama kai ba wani ya damu da shan nn bane ba.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖6️⃣8️⃣ ______________ .........Fadeel da kansa ya yaye kansa. Dan wata irin shaƙuwace a tsakaninsa da Fateema da ita yakema kallon uwa ta haƙiƙa ba mahaifiyarsa ba. Yayinda Fateema ke nuna masa wata irin soyayya mai girma da ko ɗan data haifa a cikinta iyaka kenan. Son Fadeel take da zuciya ɗaya, so irin wanda koda wasa bata taɓa kawoma ranta ba itace mahaifiyarsa ba balle tunanin cuta masa. A haka suka kammala karatunsu. A lokacin Fadeel nada shekara uku, har lokacin kuma Kamila bata sake samun wani cikin ba. Sai kuma ta ɗan shiga damuwa. Idan Aliyu yayi magana saita nuna masa tana son haihuwar domin cikama Fateema burinta. Sotake ta cikama Fateema ɗaki da ƴaƴa ta yanda zata kwaranye mata ƙishirwar su. Idan ta faɗi hakan na saka Aliyu sake jin ƙaunarta mai yawan gaske. Sai dai kuma a zuciyar Kamila sam wannan ba shine gaskiya ba, tana faɗar ne domin sake farautar zuciyar Aliyu kawai, so take ya sota fiye da soyayyar da yake iƙirarin yima Fateema, so kuma take ta haihun ta yanda zata mallake komai daga garesa, dan ta san dai komansa nata ne tunda itace mai haihuwa.      To  ALLAH bai sake kawo haihuwar nan ba sai da Fadeel ya shiga shekara ta huɗu sai ga wani cikin. Zo kafa murna da farin ciki a wajen Fateema (Oum) kamar yanda Fadeel ke kiranta yanzu. Kamila kuma (Mamy) Aliyu (Abah). Hakama dangi nata mata fatan alheri musamman ta ɓangarenta. Fatansu shine ta sake haihuwar namiji, haka itama kanta wannan shine fatan nata. Ga Oum da Abah kuwa basu da wani zaɓi, duk abinda ALLAH ya bada so suke yi. A haka dai ciki ya shiga watan haihuwa, ranar na zuwa ALLAH ya sauketa lafiya ta haifo ɗanta namiji again. Ya ALLAH burin Mamy da zuri'arta ya cika, dan sun san ta kuma gama kama gida da mai gida. Ga Abah yayi murna ya kumayi kukan tausayin Oum a ɓoye kamar yanda yake yi a ɓoye tun haihuwar Fadeel. Ga Oum kuwa ko'a jikinta, dan ko sau ɗaya bata taɓa jin hassadar Mamy ba akan tazo ta haihu a gidan ita bazata haihu ba. Ita tun bayan kukan samuwar ƙaddararta bata sake zama ta damu kanta da tunanin shike nan bazata haihu ba, balle saka kanta a damuwa. Tuni ta fawwalama UBANGIJI komai, ta kuma amshi jarabawarta da hannu biyu, kullum cikin godema ALLAH take. Tayi imanin maybe haihuwar ba alkairi bace a gareta shiyyasa UBANGIJI ya jarabceta da yankewarta da wuri. Kuma ai ba sai ka haifi ƴaƴa da cikinka bane suke zame maka ƴaƴa, ɗa na kowa ne, maybe ma bazaka amfani wanda ka haifa ba sai na wani, nakan kuma wani ya amfana. Wannan yasa bata taɓa jin wani ƙaiƙayin hassada ga haihuwar Mamy ba. Dan zuciyarta duk ɗaya take ɗauka...       Kwana biyu da wannan haihuwa Mamy ta fahimci kamar Abah bai murna da haihuwar ba, sai hankalinta ya fara tashi, da dare ya shigo mata sai da safe ta daure cikin damuwa take masa tambaya. Ya jima shiru kafin ya kai zaune tare da ɗaukar jaririn ya rungume a jikinsa. Cikin kulawa ya ce, “Kamila ba farin cikine bana yi ba. Nama fi kowa farin ciki kuma ina cikin godiyar UBANGIJI daya bani abinda arziƙina ko ilimina baya badawa balle tarin dangi da nasabarsu. Zuciyata ce kawai, zuciyata ce ke tsananin tausayin Fateema. Kamila Fateema MATAR ƘWARAI CE RABIN ADDINI, ke shaida ce akan ta da ƙyawawan halayenta a ɗan rayuwar da kikai da ita ta ƙawance har zuwa ta zaman gidan nan. Munci buruka da yawa tsakanina da Fateema akan ƴaƴanmu, sai dai ashe ba haka UBANGIJI ya ƙaddara mana ba. ALLAH sarki Fateema baiwar ALLAH, koda wasa koda ganganci ban taɓa ganin damuwa ko jin ƙyashin samuwar haihuwa daga wata ba ita ba a gidan nan......”        Takaici da zafin da zuciyar Mamy keyi akan kalamansa na yabo ga Oum ya sata saurin katsesa ta hanyar faɗin, “Dan ALLAH ka daina faɗin Fateema bata haihu ba, ka daina raba ɗayan biyu akan yaran nan da Fateema. Tabbas ni ce nai rainon cikinsu da naƙudar su kawai, amma tun kafin suzo duniya mallakin Fateema ne. Ka shaida ni Kamila kamar yanda na mallaka ma Fateema Fadeel da alƙawarin bazan taɓa canja hakan ba koda a kan fuskata shima wannan jinjiri ɗan kwana biyu na mallakashi ga Fateema har abada. Da zarar na yayesa ta ɗauka nata ne, kai in ma zata sha wani abu ne ta shayar da shi da kanta ni tama amshesa yau ikonta ne”. Hawayen ɗaci da tiririn fitar kalamanta da iyakar bakinta suke banda zuciyarta suka shiga silalo mata....        Tabbas kamalanta ratsa ɓargo da zuciyar Abah suka dinga yi, har bai san ya jawota jikinsa ya rungume taba, sai jera mata addu'oi yake hawaye na zuba masa shima. Sosai ƙaunarta mai yawa take sake samun gurbi a dukkanin jinin jikinsa bawai a tsokar zuciyarsa kawai ba. Baiyi ƙwairon baki ba ya shiga jera mata kalamai masu nauyin gaske da ta jima tana ƙishirwar jinsu da buƙatar saurare daga garesa. Shi ɗin dai shi Aliyu da tun a haɗuwar farko ta kamu da soyayyarsa. Duk da so da ƙaunar da takema ƴaƴanta guda biyu masu tsananin kamanni da shi ta gwammace ta sadaukar koda na wuccin gadi ne domin samunsa shi da zuciyarsa gaba ɗaya. Daga baya sai tayi haƙin ƙwatar ƴaƴanta a tsakaninta da Fateema. Dan tabbas wannan ƙyautar duk biyu a iya fatar bakinta take bawai a zuciyarta ba. Amma ta fahimci dolen dole sai ta yita kafin ta samu zuciyar mijinta da dukkan kulawarsa fiye da wadda yakema Fateema. Dan haka zatai dauriya da juriya na wani lokaci...      Haka kuwa akayi, shima jinjiri da yaci sunan Fawzan Mamy ta tabbatar a gaban kowa ta mallakawa Oum har abada. A wannan gaɓar kam Oum kukan da tai har sai da ta dinga bama kowa tausayi, dan kuka ne na farin ciki da dukkan jin ƙauna dake fita tun daga zuciya. Ita kanta batama san inda zata ajiye martaba da kimar Mamy ba zuciyarta. Ƴan uwan Mamy kam da mahaifiyarta sun balbaleta da masifa da nuna mata kuskurenta. Amma sai tayi murmushi kawai tana mai kallonsu...       “Ku daina min kallon wawuya sarai nasan abinda nake yi. Amma bazaku gane ba sai a nan gaba kaɗan. Domin kuwa fatsa na jefa a kogi tare da ƙananun kifaye a jikin fatsar dan samun damar shaƙo manyan kifaye mamiyo. Har yanzu baku san wanene Aliyu akan Fateema ba....”        “Oh ke a naki haukan kina nufin duk kinyi hakan ne dan samunsa da matarsa?”.     “Tabbas hakane Mama, dan ta hakan ne kawai zan mallaki Aliyu da komai nasa, ta hakanne Aliyu zai bani dukkan yarda da aminci. Ta hakanne zan saka Fateema a kwalba na rufe rufewa ta har abada. Daga ƙarshe na dawo da ƴaƴana hannuna cikin sauƙi. Shiyyasa ma na sake tabbatar mata a gabanku a gaban Aliyu, a gaban dangisa haihuwata ma ta gaba mallakar Fateema ce. Zan bata ƴaƴa uku kafin wanda zasu biyo bawa su amsa sunan nawa....”        “To idan kuma haihuwar ta tsaya miki daga ukun kuma fa Yaya?”.    Autar su ce tai tambayar. Kallonta Kamila tayi da murmushi. Sai kuma ta dafata da faɗin, “Humm Gambo kenan, ina ji a jikina sai nayi haihuwa ɗai-ɗai har goma anan gidan, dan na sadaukar da uku kuwa ai ba komai bane, bama sadaukarwa bace ba ajiyar ce. AJIYA A DUHUn da FATEEMA bata sani ba. Dan komai daran daɗewa sai ƴaƴana sun dawo gareni a gabar da Fateema ke murna da jin alfaharin zata amfana. Zan bata fili ne a yanzu ta gama min wahala da su iya iyawarta, ni kuma na mora kayana a lokacin girmansu”.        Murmushi kawai Gambo tayi dan ita kam ta gamsu da bayanin Kamila, yayinda yayarta da mahaifiyarsu kawai suka girgiza kawuna, dan suna ji a ransu lallai Kamila ta tafka babban kuskure. Kuskuren da bazata fahimci kuskure tayi ba sai anan gaba....        To koma dai yaya ne Mamy ta cigaba da shayar da Fawzan shima, yayinda komai nashi ke'a hannun Oum, shan nn kawai ke kawosa tamkar yanda akai da Fadeel. Shi Fawzan ba kamar Fadeel ba, ba yaye kansa yay ba, yana da shekara ɗaya Mamy ta sake samun ciki, wannan shine dalilin yayesa gudun samun matsala. Nan ma Abah da Oum suka cigaba da kula da ita da kaffa-kaffa, dan wannan cikin ma sai yafi bata wahala fiye da na Fadeel da Fawzan. Ga cikin da tsirfar tsiya, yana son wancan baya son wannan. Tun yana watanni biyar yay wani irin girma na tsiya kai kace tagwaye ko ƴan uku ta ɗauka, dan Oum da Abah har tsokanarta suke akan wannan karan kodai ƴan uku ne ko twins. Murmushi kawai take yi akan batun, amma a can cikin ranta tana ma kanta fatan hakan itama. A lokacin da cikin ya shiga watanni bakwai sai wahalar ta ninku matuƙa. Har takai bata iyama kanta komai sai da taimakon Oum da Aba. A haka aka shiga watan haihuwa da ƙyar, har ALLAH ya kawo ranar haihuwar. Ansha gumurzu, gumurzu na haƙiƙa dan kwananta biyu akan gwiwa kafin a na uku ALLAH ya sauketa lafiya. Wannan karan ma dai namiji ne sargaɗeɗe mai kamanni da ƴan uwansa, sai dai shi ya ɗan ɗakko duhun fatar Mamy saɓanin Fadeel da Fawzan dake farare tarr dasu tamkar mahaifinsu da Oum. Jaririn nan ƙato ne na gaske, dan bayan fiddosa hatta ma'aikatan asibitin zuwa kallonsa suke da mamaki. Haka dai aka sallamesu suka koma gida, a wannan karon ma dangi tako ina sun cika gida anata huɗar arziƙi.      Ƙalubale na farko akan wannan haihuwar shine tunda Mamy ta ɗaura idonta akan jinjiri wata kalar ƙaunarsa mai zafi data bambanta data ƴan uwansa ta shigeta. Ƙalubale na biyu tun a asibiti yaƙi kama nn. Ƙalubale na uku Abah da kansa suna dawowa gida gaban ƴan uwanta da nasa ya sake tisama kowa alƙawarin Mamy na ranar haihuwar Fawzan akan mallakama Oum wannan ɗan ma a karo na uku, dan haka ya sake tabbatar musu wannan alƙawari na nan daram bai canja ba. Sai dai suyima Mamy addu'a kuma da fatan alkairin ALLAH ya kawo ƴaƴa na gaba da suma zasu kasance matsayin nata mallakin. Ƙalubale na huɗu shawarar da Umma ta bada akan tunda jinjiri yaƙi kama maman Kamila bazai yiwu a barshi a haka ba fa sai a koma asibiti, koda aka koma asibitin sai likitoci suka fahimci fa akwai matsala ne, matsalar canjawar kalar nn Mamy daga fari zuwa yellow, dole suka shiga binciken ainahin matsalar, suka kuma bada shawarar sai dai a shayar da yaron madara gudun kada a shiga hakkinsa, dama gashi yanata kukan yunwa. Ita kuma aka ɗorata akan magani da tabbatar musu in sha ALLAHU komai zai wuce ta samu lafiya kamar ba'ai ba. Jin haka sai Umma tace baza'a bashi wata madara ba Oum ce zata sha magani ta shayar da shi. Baba Sardauna ya yarda da wannan shawara ta matarsa, hakama Abah da sauran dangi. Dan haka mahaifin Oum wato Dr Kasheem Kura da kansa ya aikoma Mamy ingatattun magunguna tun daga Paris da zai bata ruwan nn. Dan su basu zo ba a lokacin babu jimawa da sake haihuwar matarsa (Maryam kenan mahaifiyar Oum ina fatan kuna fahimta). Itama ta samu ɗa namiji cikin na huɗu da yaci sunan Rafeeq. Oum bataje ba saboda yanayin da Mamy ke ciki a lokacin.       Cikin amincin UBANGIJI Oum nashan magani kuwa sai ga ruwan nn mai ƙyau. Aiko ta hau shayar da jinjirinta da yaci suna Ajwaad. Yayinda aka bar Mamy da jiyyar zuciya da kukan ɓoye. Gashi kuma babu yanda ta iya, dan ita dai tai alƙawarin nan babu wanda ya tirsasata, a zahiri kuma taƙi nuna ma kowa damuwarta saboda neman soyayyar Abah da take ganin saita wannan hanyar kawai zata iya samunta. Ita dai Oum ranta fes, ƴaƴanta uku cif sun kammala, tsakaninta da UBANGIJI sai godiya. Sai kuma aminiyarta Kamila da har abada take jin a ranta bata da kamarta a wannan duniyar idan ka cire iyayenta da iyayen riƙonta da mijinta. Ƙaunar yaran nan uku take da zuciya ɗaya, da iya gaskiyarta. Bata taɓa jin ƙaiƙayin cewar ba itace ta haifesu ba. Kai ita mantawama take da ba itan ce ta haifesun ba. Dan a zahirance dai Mamy kawaici take yi. Bata taɓa jingina kanta da yaran koda wasa. Sai ta faki ido ta dinga aibanta Oum a zuciya, gefe ga tsananin kishinta da take ji da hassadar finta komai na rayuwa da tayi. Wanda ada can iyakar kishin soyayyar mijinta Aliyu kawai take ji. Amma bayan auren data sake fahimtar wacece Oum a wajen Aliyu da nasarorin rayuwa dana iyayenta ke da shi sai hassadar hakan ta shigeta.         (Wannan hassadar al'adace kamar a zukatan matanmu akan kishiya. Ya rabba ALLAH ka yaye mana hassada dan mugun dafi ce mai kassara rayuwa da cigaban cikinta)........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖6️⃣9️⃣ ______________ .........To rayuwa fa ta fara shuɗawa. Abubuwa da yawa nata faruwa. Ciki harda yaye Ajwaad da Oum tayi bayan cikarsa shekara biyu cif yana sha daga jikinta. Tuni ta sanyama Ajwaad Auta, tunda dai Mamy da kanta ta tabbatar da iya gejin abinda zata bata kenan haihuwa ta gaba tata ce. Autancin ko yabi Ajwaad tun da ƙarancin shekaru. Dan ALLAH yayisa irin yaran nan masu tsananin ƙulafucin iyaye. Sam baya ƙaunar koda wasan wasa Oum tayi nesa da shi. Wani lokacin ko toilet ta shiga yana ƙofar bayi yana jiranta har saita kammala abinda take ta fito. Idan zataje wajen Abah kuwa a ranar girkinta sai fa da wayo da dabara idan ta tabbatar barcinsa yayi zurfi can cikin dare. Wani lokacin kuma dashi dole take tafiya ta kwantar da shi a falo ko in barcin nasa yay nisa ta maidosa cikin ƴan uwansa. Akowane motsinsa shi dai Oum ce. Gashi da shegen ƙiwa tun yana watanni biyar zuwa shida baya yarda da kowa sai Oum sai Fadeel idan yaso. Amma ko Abah da Mamy basu isa taɓashi ba ya hau ihu yana bin Oum da kallo yana kuka. Sanda ya cika shakara ɗaya da wasu watanni kuwa idan ka takura sai ka ɗaukesa cizo zakasha ta yanda dole ka saukesa ya koma wajen uwarsa. In ma anguwa suka fita bai yarda wani yako taɓasa daga jikin Oum. Baba Sardauna ne ma ke ɗan samun wannan alfarmar shima ana ɗan yarda da shi saboda yana bashi irin chocolates ɗin da yake so. A haka ya cika shekara huɗu aka saka shi a makaranta kamar sauran ƴan uwansa. Duk da su an sakasu tun suna da shekara uku-uku, shiko ƙulafucin uwa ya hanashi. A yanzun ma dai badaƙala ake sha dan baya ƙaunar zaman makarantar, yata kuka kenan da kiran Oum! Oum! Shi akaisa wajen Oum ɗin sa. Shi gida zaije wajen Oumyn sa. Karatu yaƙiyi ya hana sauran yara yi. Duk wanda ya nuna kulawarsa da son rarrashinsa ya danƙarama yaro cizo sai an rabasu da ƙyar. Ganin haka yasa makarantar suka bada shawarar a ƙara masa lokaci ya ƙara wayo, dan inma ba hakaba bafa karatun zai yi ba. Dole su Oum suka yarda da hakan, amma tana ƙoƙarin masa a gida ita da Fadeel musamman na ɓangaren addini. Gashi kuma da ƙwaƙwalwa Masha ALLAH.         Sai da Ajwaad ya cika shekara bakwai a duniya sannan Mamy ta sake samun ciki, a lokacin yana zaman makaranta da ƙyar dan yana a nursery 2 ma. A islamiyya kuwa Alhamdullah ya tashi da ƙwazon karatu kamar sauran ƴan uwansa biyu. A wannan karon abinda ya fara tadama Mamy hankali kamar Abah bai damu da cikinta ba kamar ukun can na farko, sai Oum ce ma ke dama-dama da ita da bata kulawa. Idan tai magana yace to mikuma ya rage shida keda uku rigis, ai sai fatan alkairi da addu'ar ALLAH ya sauketa lafiya. Wannan furuci nashi na cimata zuciya, amma haka take dannewa ta maida abin wasa. A haka ta shiga watan haihuwa, a kuma lokacin Abah ya fara musu gini dan yace wannan gidan ya musu kaɗan ga zuri'a suna tarawa. A wata juma'a Mamy ta sauka lafiya ƴan biyu duk maza. Musalta muku irin farin cikin da wannan ahali suka shiga a wannan karon ma ɓata lokaci ne. Anyi shagalin suna kamar yanda akai na baya, duk da Mamy taso ace na wannan karon yafi na bayan armashi kodan biyu data santalo. Haka dai suna ya tashi lafiya yara sukaci sunan Hassan da Hussain. Dan tace bata son a canja mata suna a barsu da nasu. Duk da a wannan karon Mamy batace ta mallakama Oum su ƴan biyu ba bata fasa yin hidima a gareta da jinjirayen ba kamar yanda ta saba. Dan har takai Ajwaad na nuna kishinsa a fili, sai dai suyita masa dariya kawai. Bayan yaye su ƴan biyu da wata uku Hussain ya fara laulayin haƙora, ya dinga gudawa irin na haƙora mai wahalarwa. Abin ALLAH kwana biyu kacal a wannan halin UBANGIJI ya ɗauke abinsa. Duk da rasuwar yaro ce ta girgiza wannan ahali, dan daga Oum har Mamy kuka rurus sai Abah ne ke lallashinsu, da ƙyar suka haƙura suka sabarma kansu da rashinsa. Sai kuma tunda Hussain ya rasu shima Hassan lafiya ta masa ƙaranci. UBANGIJI mai rahama da jin ƙai shima bai cika kwana arba'in ba yabi ɗan uwansa. Ai neman zautuwa Mamy tayi, da ƙyar ake tausarta. Sai dai kuma babu yanda ta iya da hukuncin ALLAH.        Tun bayan rasa ƴan biyu ko ɓatan wata Mamy bata sake yi ba. Har suka tare asabon gidansu da a yanzu suke ciki wanda ke maƙwaftaka da nasu Maanal. Zuwa yanzu tsanar Oum Mamy keji mai zafi a ranta, amma a zahiri bazaka taɓa fahimtar hakan ba, gefe ga uwarta da ƴan uwanta dake zugata. Ba Oum kawai ba, hatta duk wanda Oum ke huɗɗa da shi Mamy ta tsanesa. Dan haka bata taɓa son Ammie da su Maanal ba. Amma koda wasan wasa bata taɓa nunawa a koda fuskarta ba. Sai ma nunawa take kamar tanama Oum kawaici musamman akan tarayyar Maanal da Ajwaad dake a bayyane ga kowa. Ita ko Oum soyayya takema Mamy ta gaskiya da kuma zuciya ɗaya, jin girmanta take da kimarta ta yanda zuciyarta koda hasashe bata taɓa kallon munininta ba. Kai a yanzu koda Abah yazo yace da Oum ga munin Mamy to tabbas bazata amince ba. Ta bata matuƙar yarda da gaskiya ta yanda bata ko jin wani ɓurɓushin kishita a ranta. Kai sam bama ta mata kallon kishiya sai ƴar uwa. Hatta da sirrinta bata taɓa canjawa daga yanda take sanar mata ba a sanda suna amintaka da ƙawance. Komai buɗema Mamy take da zuciya ɗaya ta nema shawara. Kuma a cikin ƴan uwanta kaf babu wanda ya taɓa kallon illar hakan dan suma yarda ɗaya suka bama Mamy saboda ɗunbin hallaci da yakana da dattakon data nuna ga Oum ɗin. Lallai Mamy ta samu fada da soyayya tako ina daga zuri'ar Baffa Ishaq Darma. Yarda suke mata ta gaskiya, basa taɓa banbantata a matsayin bare a cikinsu, basa taɓa banbantata tsakaninta da Oum dake matsayin tasu. Kai sai suyi mata abu basu yima Oum ba musamman ma mahaifinta Dr Kasheem Kura. Dan shi yakance Mamy itace ƴarsa. Oum kuwa ta Baba Sardauna ce.         Itama a zahiri ta riƙe dukkanin abinda zasu kalleta da wannan mutuncin, duk da zuciyarta cike take da shirin maido da ƴaƴanta gareta komai tsahon lokaci da rayuwa zata bata. Hakama duk damar data samu daga Abah da yarda bata gamsar da ita ba, kullum cikin sake harin ninkin baninkin ɗinta take yi. Duk da kuwa ta wawashi kaso mafi girma daga soyayyar tasa. Dan tun fara girman su Fadeel Oum ta sake sallama mata Abah ɗin kaso saba'in cikin ɗari, ita kuma yake riƙe da talatin cike da kawaici da dattakonta. A yanzu ko tafiya Abah zai yi da ita ne. Idan wani abu ya taso kai tsaye Oum zatace yaje suyi da Mamy ita bazata iya yin nesa da yaranta ba. Tun abin na bama Abah haushi har ya haƙura ya sallama dan ya fahimci mai raba Fateema da ƴaƴan nan nata sai dai ALLAH. Musamman Autan ta uban ƴan ƙalata da ƙulafucin uwa.        Duk da Oum bata taɓa fitowa ta sanar ma yaran ainahin mahaifiyarsu ba tana nuna musu girma da darajan Mamy a garesu. Kullum cikin cusa masu soyayyarta take a zukatan yaran cike da hikima. Tana ƙawata musu girma da kimar Mamy a zukatansu. Tun abin baya tasiri a ransu harya fara. A hankali Fadeel da Fawzan suka ɗan fahimci wani abu kaɗan bamai yawa ba. Sai dai hakan bai taɓa canja musu Oum ɗinsu a matsayin da suke kallonta ba. Ita dai suka sani, ita kuma suke kallo da matsayi irin na uwa da mahaifiya. Amma suna girmama Mamy da bata hakkinta da mata soyayya kamar yanda Oum ta koyar da su take ma kan koyar da su ɗin. Shi dai oga Ajwaad Auta Oum ɗinsa kawai ya sani. Shi uban kowama ya mutu har liman in dai za'a bar masa Oum ɗinsa. Farin cikinsa ce ita, sannan duniyarsace. Bai haɗa soyayyarta data kowa ba a duniya...       Wannan halin na Ajwaad na cima Mamy rai matuƙa, dan ALLAH ya jarabceta da soyayyar Ajwaad fiye da duk sauran yaranta. Ƙaunar yaron take har ƙarƙashin zuciyarta. Ga shi kuma hankalinsa san baya a kanta yana akan maƙiyarta ne. Shiyyasa take sake jin ninkuwar zafin Oum ɗin matuƙa. Gashi ta fahimci itama Oum ɗin tanama Ajwaad wata irin soyayya mai girman gaske. Hakan na nufin bayan Aliyu sun sake yin tarayya akan abu guda kenan. Wato soyayyar AJWAAD ALIYU ABUBAKAR DARMA...      _MUN SAKE DAWOWA DAI CIKIN LABARIN RAYUWAR AJWAAD DA MAANAL DATA GABATA🙏😀_     *GIRO:-* A Giro dai an ɗaura auren Babu da amaryarsa Safarah. Safarah yarinya ƙyaƙyƙyawa mai busashen ido. Dan cikakkiyar ƴar tallace a tashoshin motoci na yankin ƙauyen Giro da cikin Suru. Musamman a ranakun kasuwanni. Kai har cikin Kebbi idan ta kama suna zuwa kawo kayan sayarwa ita da ƙawayenta. Gwaggo ta zaɓama Babu ita ne dan a cewarta itace dai-dai da Asiya. Anko sha biki, dan su Ammie sun sha kallo. Bajinta sosai Gwaggo tayi a bikin dan dabbobinta har goma ta saka a kasuwa. Bayan tarewar amarya a nan dai gidan ɗakin dake a tsakanin Gwaggo da Ammie ango yasha bidiri. Dan Babu dai kura ne ba'a bashi ajiyar nama. Duk da ma dai abin bai masa armashi ba saboda samun Safarah ba'a cikakkiyar budurwa ba ita dai. Amma tsabar iya bariki na yarinyar nan da dudu shekarunta goma sha tara ne a duniya sai ta dinga zumbuɗa masa ihu da kururuwa ita a dole tana shan wahala. Wannan ihu ya tadama Ammie hankali, bawai akan kishi ba, duk da bazatace bata kishin mijin nata ba. A'a saboda su Shahidah ne. Dan takai yaran nan sai da suka farka a barci suma. Yayinda itama kanta Gwaggo data fito tsakar gida a wannan tsohon dare take faman kiran sunan Babu da gargaɗinsa akan wai yabi Safarah a hankali, ya dai san yarinyar ƙarama ga mutuncinta ta kawo. Wannan abu shine ya taru ya saka Ammie kuka dan su Amaal nata jera mata tambaya akan ko mi ya samu amaryar haka. Sai dai bata kula yaran ba, daga ƙarshe ma ta musu tsawa suka kwanta. A ranta dai tana sake godema ALLAH da su Abah suka wuce da Maanal. Dan tabbas kaɗan daga aikinta tama fita itama koda safe ta tsare Babu ɗin da tambayoyi.       Wannan kuka da amarya tasha da ihun iskanci yasa kowa ya yarda ta kawo mutuncinta. Shi ko Babu tai masa ɗaurin goro dan bashi da damar  musawa. Ga wata irin kunya da nauyin Ammie da ALLAH ya jarabceshi da ita. Dan ƙiri-ƙiri ya kasa yarda ya haɗa ido da ita a wannan yinin baki ɗaya. Ko hanya suka haɗa duk sai ya daburce. Itako Ammie ta dake abunta ko'a fuska bata nuna masa ba. Amma a dare na biyu saita tura Amaal da Shahidah kwana ɗakin Zainabu ɗaya daga cikin matan gidan, kasancewar tasan mijinta baya gari. Dan gara ta nesanta yaranta da shiyyar gaba ɗaya kafin su fahimci abinda ke faruwa.          Aiko Ammie tayi dabara, dan daren yau ɗin ma bata canja zani ba. Sai da Safara tayi duk iya yinta ta hillaci Babu ya kasance da ita. Gashi dama ta ɗirki magunguna shima an ɗirka masa ta hanyar abinci. Ai sai ihun ya zama nasu su biyu yau ita da shi. Kai jama'a wannan iskanci dami yay kama haka. Cewar Gwaggo cikin mitar son yin barcin da suka hanata. Amma da safe ko'a fuska bata nuna ba saima kulawa take bama amarya ta musamman dan Ammie taji haushi. Sai kuma Ammien ta tabbatar mata ita ɗin ƴar halak ce dan bata nuna damuwarta ba koda a fuska.  Kasancewar daren jiya ta kwana salla da karatun Alqur'ani sai ta tashi sakayau zuciyarta cike mamaye da farin ciki. Musamman daya kasance da safe ta kira Oum a waya sun sha hirarsu harda Maanal dake ta faman bata labaran daɗin da Oum da Bestyn ke ciyar da ita. Shi kansa Babu ɗin sai yanayin na Ammie ya sake jefa shi a ƙaulani da ɗunbin kunyarta da shakkarta ma..........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖7️⃣0️⃣ ______________ ..........“Ni bazan je ba barci nake ji”.     Maanal ta faɗa tana ture hannun Ajwaad dake ƙoƙarin sauketa a saman gadonsa. Dan ɗakin ta shiga ta masa uwar ɓarna a wadrobe ɗinsa da duk abubuwansa. Ɗakin nasu ne su uku amma a tsare yake, kowa da sashen kayansa da abubuwansa da kuma ɗan gadonsa. Maanal kan shiga ɗakin amma bata taɓa komai na Fawzan da Babban Yaya sai na Ajwaad. Yau kamar abin arziƙi suna tare a ɗakin suna duk wani assignment ɗin da aka basu na islamiyya kasancewar zuwa gobe zasu koma. Sai Mamy tai kiran Ajwaad ta aikesa kai mata markaɗen alale da zatayi a gidan yau matsayin abincin rana. Wannan dama Maanal ta samu ta canja akalar assignment ɗin nasu ta koma zane-zanenta na fama. Dan tana son zane-zane sosai tun bata kai haka ba. Kai a makaranta makinta dabanne akan subject ɗin ma saboda yanda tai matuƙar ƙwarewa. Ko aiki aka basu awannan fanin hatta Ajwaad itace ke masa kai har su Fawzan bata suke da su Shahidah. Tana cikin zane-zanen ta ajiye ta sauka a gadon inda take ta koma masa bincike a kaya wai tana neman colours wanda take amfani da su sun fara bushewa basa mata da ƙyau. Daga haka ta ɓige da ɓarnarta tai kaca-kaca da komai. Tana jin zai shigo ta haye gadonsa da sauri tai likimo ita adole barci ma take yi. Shi ko tsaye yay kawai yana kallon fallasar datai masa da kayayyaki. Amma sai baice komai ba ya ƙarasa saman gadon ya ɗagota yana faɗin, “Tashi kije ɗakin Oum tana kiranki.”       Shine ta ƙwaɓe fuska da faɗin itafa bazataje ba barci ma take ji. Shiru yay yana kallonta, sai kuma ya saki hannun nata ya koma kan kayansa ya fara tattarewa yana maida komai inda yake. Dan shifa duk da ƙarancin shekarunsa komai nasa akan tsari yake da tsafta. Dan Ajwaad sam baya ƙaunar ƙazanta. Shiyyasa komai nashi a tsaftace a killace yake. Yana tsaka da maida kayan kuma sai ta sakko ta dawo wajensa tana masa surutu da nuna masa zanen agogon da tayi. Harara ya zuba mata ya ɗauke kansa. Ita kuma ta tsaya tana kallonsa kawai. Sai kuma ta kumbura baki da jefa masa book ɗin ta fice tana kuka wai ita babu ruwanta da shi kada ya sake mata magana kuma. Baiko kulata ba sai da ya kammala maida komai har books ɗin nasu dake baje a gadonsa ya gyara gadon sannan ya ɗauka book ɗin data jefa masan. Shiru yay yana kallon zanen agogon da tayi, yayi matuƙar ƙyau tamkar ka saka hannu ka cirosa. Sai yaga ya banbanta masa da duk abinda ta taɓa zanawa kodan bata taɓa zana agogon bane sai yau oho. Samun kansa yay da buɗe box ɗin da yake adana muhimman abubuwansa ya saka shi ciki ya maida ya rufe. Daga haka ya shiga bayinsu dake a ɗakin yay wanka ya canja kayansa sannan ya fito..     Wannan zanen agogon shine tushe kuma sila na ginuwar buri mai girma a zuciyar Ajwaad game da Maanal akan harkar zane-zane musamman agogo.... ____________★      Sosai Giro tama Ammie zafi, zafi mai tsanani ita da yaranta. Dan haka ta roƙi Baabu komawa Kano. Da farko ya turza, saboda gwaggo ta sakashi a ɗaki ta kitsa masa cewar yabar Ammie ta cigaba da zama anan Giro. Itako a karo na farko tattara kayanta tsaf dana yaranta washe gari ya fita shi da amaryar tasa da Gwaggo zuwa can gidansu wai babanta babu lafiya ta baro Giro bisa taimakon Baba Haruna. Taso ta kwana a kabbi. Sai dai rashin mukulli dan yana a hannunsa yasa haka suka fallo hanya. Cikin amincin UBANGIJI suka iso cikin Kano kusan tara na dare. Sai da suka shiga gida ta kira Oum ta sanar mata. Sosai Oum tayi mamaki, amma sai ta ture mamakin ta kwantar da Maanal datai barci a jikinta ta fita. Kitchen ta shiga ta haɗa musu abinci sannan ta kira Abah a waya Fawzan ya mata rakiya.      Sosai hankalin Oum ya tashi da ganin yanda duk Ammie ta rame ta lalace. Gashi suna haɗa ido kawai Ammie ta sakar mata kuka. Jiki na rawa ta ajiye abincin ta rungumeta tana lallashi. Sai da tayi kukan sosai sannan Oum tace ta tashi tai wanka. Wankan duk sukayi sukaci abinci, sannan Oum da Fawzan suka koma gida. Damuwa fal kan Oum. Washe gari rijib Ammie ta tashi da ciwo, dole suka wuce asibiti. Aiko aka basu gado dan likitocin sun tabbatar da jininta ya hau sama matuƙa. Sai da Ammie tayi kwanaki huɗu sannan aka sallemta suka dawo gida. Washe gari cikon na huɗu sai ga Baabu da amarya sun iso. Ammie batayi mamaki ba, kuma batace komai ba, duk da taga da wani wutar bala'i da rashin mutunci yazo garin. Dan babu kunya ya rufeta da zagi harda mari wai ta taho bada izninsa ba, ta raina masa mahaifiya miye-miye. Ko ci kanka batace da shi ba, hakan sai ya dake hasalashi ya fara nemo hanyar da zai musguna mata ta mangantu ya juye mata abinda ke a ransa. Ɗaki uku ne kacal a gidan, nata, nashi, sai na yara. Haka ya murje ido yace ta koma na yaran ita amarya ta zauna a nata. Ammie ta ce wannan ne kuma bai isa ba. Dan ita ba wulaƙantacciya bace, ba gori ba gidan nan mallakinta ne idan ya manta tunda da kuɗinta aka sayeshi. To dama fa ta samu, haka Baabu ya dinga zuba tijara har sai da Abah yazo ya fiddashi a gidan aka samu masalaha. Daga ƙarshe dai dole amarya ta zauna a ɗakin shi.      Tun wannan dawowa komai ya canja, canji mai ban mamaki daga ma'auratan dama gidan kansa. Musamman daga Baabu. Hatta ƴaƴansa yanzu ja baya suke da shi, dan abu kaɗan zakayi ya hauka da zagi. Ranar ma ƴar lelen tashi Maanal har duka taci, aiko ta haɗa inata-inata ta koma gidan Abah. Tafi sati bata shigowa gidan nasu kafin ta saki jiki kuma ta manta bisa tirsasawar Ajwaad ta koma shigowa. Ga amarya dai babu wata matsala. Ta kwantar da kanta yana fahimtar komai daki-daki kamar babu komai. Sai dare ta ishesu da ihu ita da miji. Wannan abu shine mafi girma tadama Ammie hankali, dole ta maida kwanan su Shahidah gidansu su Oum gaba ɗaya. Dama yanzu batun miji Ammie bata da shi a gidan, Baabu yana tare da amaryarsa tunda suka dawo. Sai da suka cika wata ɗaya cif sai gashi da takarda wai ya saki Ammie saki ɗaya.        Murmushi kawai Ammie tayi da faɗin, “ALLAH yasa haka shi yafi alkairi, amma kuma babu inda zanje. Zan zauna na cigaba da rainon ƴaƴana har lokacin aurensu sai dai kai ka bar min gidan tunda dama nawa ne”.      Wannan furuci nata shine ya kawo tashin hankali, tashin hankalin da dole sai da Abah da Oum suka shiga yanzu ma. Da ƙyar dai aka sasanta bayan Abah ya nusar dashi illar abinda yake shirin aikatawa. Shine fa ya maida Ammie. Haka aka cigaba da haƙuri Ammie bata da miji, bata taɓa tada kai ta kallesa ba har tsawon shekara biyu. (Kenan dai tun da amarya ta tare😭) Ko'a fuska Ammie bata nuna masa damuwarta, karatunta kawai take na Islamiyya da take zuwa da kula da tarbiyyar yaranta da sana'arta. Dan takai yanzu ma itace ke ciyar da kanta. Zuwa yanzu su Maanal fa an shiga secondary, Dan suna aji biyu ma duk da da ƙyar suka amsheta saboda sunce tayi ƙarama da yawa, yayinda Shahidah ke shirin kammalawa ita da Fawzan, babban yaya kuwa ya wuce ƙasar Saudiya karatu.           Amarya bata shiga sabgar Ammie, itama bata shiga tata, dan a zahiri bata da matsala da ita sai da Babu, sai dai tushen matsalar daga gare ta ne tazama macijin sari ka noƙe ne kawai. Har lokacin kuma dai babu ciki, sai da ta shiga shekara ta uku sai ga ciki, nan fa su Babu aka shiga murna da addu'ar haihuwar ɗa namiji. Ita dai Ammie ko tari bata musu ba, duk taɓarar iskancin da amarya keyi bata nuna tasan suna numfashi a gidan ba ma. Sai da ciki ya shiga wata biyar sannan ya ɗauketa suka wuce Giro, dawowar da basu sake yi ba sai da ta haihu akasha shagalin suna a Giro dan buri ya cika an haifi Namiji. Ashe duk wannan abun da ake Baabu na cikin Kano, tunda ya kai amarya gida Gwaggo ta sharɗanta masa hanashi komawa wajen Ammie wai har sai in matarsa ta haihu. Ammie bata taɓa sanin haka ba sai bayan dawowarsu da jinjiri da Gwaggo, wai itama ta dawo nan Kano da zama, ashe aure dai ya ƙare tsakaninta da Baba Haruna duk kuma akan Ammie ne, dan bayan tahowar su Ammie a wancan karon ansha fitina Baba Haruna ya saki Gwaggo shine fa ta ɗau alwashin yanda ya saketa itama sai an saki Ammie, idan kuwa ma ba'a saketan ba sai ta ɗanɗana fiye da abinda itama ta ɗanɗana. Wannan duk shine tushen matsalar da suke ciki a yanzu shiyyasa Amarya data san komai ta koma gefe ta nutsu tana shan kallo dan tace faɗan na manya ne ba nata bane.       Dawowar Gwaggo Kano ba ƙaramin tashin hankali su Ammie suka shiga ba ita da yaranta. Musamman Maanal mai bakin tsiwa datai matuƙar tsanar Gwaggo, kuma a zahiri take nunawa bata ɓoyewa. Yayinda Gwaggo itama ta tsani Maanal fiye da su Shahidah, ta kuma tsani Ajwaad, dan shima a dalilin ƙin Maanal da su Ammie daya ga Gwaggo nayi ƙuru-ƙuru ya sashi tsanar matar, dan sam Ajwaad baya son mugu da mugunta. Rayuwa tayi tsanani wa Ammie, uwar miji, da miji da kishiya sun saka rayuwarta gaba data ƴaƴanta. Shekaru kusan huɗu bata kwanciya da miji, baya shiga ɗakinta. Yanzu kuma haihuwar namiji tasa kullum cikin aibanta mata yara suke da shegantasu, dan akwai randa Baabu da bakinsa yace yana tantanamar ma su Shahidah ƴaƴansa ne. Wannan abu ya girgiza Ammie, ya sakata kuka mai tsanani da sake jin sabuwar kewar iyayenta data rasa. Amma ya zatai, haka ta haƙura ta share hawayenta ta barma ALLAH komai. A wajen Oum da Abah kawai take samun sauƙi da soyayya da ƙauna ita da yaranta.          Kammala secondary ɗin Shahidah yasa Abah tada zancen aurenta da Fadeel. Dan yace za'a fara nasu, ita kuma Amaal sai Fwazan ya kammala. A ɗan tsukun Fadeel yazo gida hutu, dama can shi da Shahidah tuni sun ƙulle, dan haka aka saka ranar aurensu ya koma saudia. Bayan komawar tasa Shima Fwazan ya shiga lallaɓa Oum akan kawai a haɗe nasa dana Amaal lokaci ɗaya dana Babban Yaya, sai su tafi jami'ar tare. Dan shi rashin ƙyawun result daya samu yasa dole ya ƙara shekara ɗaya a ƙasa sai da ya canja ssce ɗinsa duka.  Duk da a lokacin ita Amaal na ss2 sai yace kawai tayi exam ɗin itama su wuce tare. Oum ta tunkari Abah da zancen, yay shiru yana nazari, sai zuwa can yace ta bashi lokaci zai yi magana da Baabu, kuma zai kira Baba Haruna a waya....   ____________★          Kamar yanda suka saba tashi sallar asubahi kullum yauma hakanne. Saida Fwazan ya fara yo alwala sannan babban yaya ya shiga. Ajwaad shine ƙarshe, sai wani ciccin magani yake. Ya girma sosai a tsaye, dan a yanzu shi da mutuniyar tasa suna js3 ne. Suna shirin tafiya ss. Shekarun girma sun gama bayyana mai, dan har wani ɗan tsigin gemu ya ajiye (kamar jelar tsatso inji Ibro.😂 ALLAH ya gafarta masa da iyayenmu baki ɗaya 🙏).      Yanda yake tafiya kamar mara laka a jiki ya saka Fawzan sarkin tsokana faɗin, “Wai na Lilly kodai barcin nan bai isheka bane ba?”. Harrarsa kawai ya ɗanyi ya wuce abinsa, dama Fawzan tsokana, Ajwaad miskilanci. Haka suke kullum, sai ya ƙuresa ne yake tanka masa. Juyawa Fawzan yay ga babban yaya dake canja kayansa zuwa jallabiya, shi kam tako ina ya zama cikakken saurayi, ga cikar kamala da nutsuwa ta sake baibayesa,  duk da shima Fawzan ɗin tsokanar ce kawai, amma a nutsensa yake. Har sun kammala shiryawa yau ma Ajwaad na cikin bayi, babban yaya ya dubi fawzan da faɗin, “Wai mike damun auta ne yanzu?. Da babu wanda ya kaishi himma shirin fita sallar asuba, amma tunda nazo garin nan naga sai mun fita yake fitowa”.       Murmushi Fawzan yayi da ɗan sosa kai, sai kuma ya ɗage kafaɗa da faɗin, “Maybe yana wani uzirin ne”.     “Kamar ya?”.   Shiru Fawzan yayi saboda fitowar Ajwaad daga bayin a tunaninsa sun fita ɗin. Turus ya tsaya yana kallonsu, suma duk sai suka zuba masa ido........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖7️⃣1️⃣ ______________ .........Wani irin gumtse baki Fawzan yay yana danne dariyarsa da tsiya-tsiya. Idanunsa ƙyam akan sumar kan Ajwaad da yake gogewa da towel, a jikinsa kuma rigar wanka. Aiko Ajwaad yay wani irin masifar yin kicin-kicin da fuska tamakar zai sakar musu kuka. Yayinda Babban Yaya daya gama masa kallon tsaf shima ya ɗauke idanunsa yana murmushi. Hanyar fita ya nufa abinsa yana faɗin, “Ka same mu a falo idan ka shirya, dan kullum Abah yana maganar rashin fitowar ka tare damu, yana ganin kamar ma baka samun sallar”. Daga haka ya fice bai jira amsar sa ba. Shima sai Fawzan yabi bayansa, sai da yaje ƙofa zai fita sannan ya ɗan juyo ya sake kallon Ajwaad ɗin da har yanzu ya kasa motsawa daga inda yake. “Ka lallaɓa ni na faɗama Oum a haɗa auren ka da namu ka huta da wannan wankan asubar wlhy, dan Lilly dai ta isa aure shekara goma sha biyar ai ba laifi”.       Wata muguwar harara Ajwaad ya wurga masa, dan haka suke kamar abokai, to dama tsiran nasu ba wani yawane da shi ba. Ficewa Fawzan yay da sauri yana sake gumtse dariya. Koda ya fito inda babban yaya ke jiransu sai ya haɗiye dariyan. Kallonsa babban yaya ya ɗanyi sai kuma ya kauda kai. Cikin ɗan jin nauyin abinda zai faɗa ya ce, “Tun yaushe Ajwaad ya fara wannan wankan asubar?”.              Batare da Fawzan ya kallesa ba shima ɗin ya ce, “Ai tun bayan wucewarka saudia babu jimawa. Kaga kuwa fin shekara biyu kenan”.     Karan farko babban yaya ya dubi Fawzan ɗin, “Amma su Oum sun sani?”.         “Haba babban yaya yaza'ai su sani. Nima da muke ɗaki ɗaya baifi shekara ɗaya dana fahimta yana yi ba. Kuma ban taɓa nuna masa nasan yanayi ba. Sai dai cikin hikima na sake nusar da shi sake nesanta alaƙarsa da Lilly duk da zuwa yanzu duk abinda ya haramta garesu basa yinsa. Kamar taɓa jikin juna, shigowa ɗakin mu sai da dalili, yimata tsifar kai da wanke mata underwear, zama kusa da juna gab, itama kuma Oum tana matuƙar saka musu ido akan hakan. Duk da Alhamdullah suma tuni duk wannan abubuwan sun daina shi gaskiya”.        “Alhamdullahi naji daɗin hakan, amma duk da haka soyayyar dake tsakaninsu mai ƙarfi ce, barinsu a haka tunda har alamu sun nuna shi mai yawan buƙata ne yana da ƙyau su Oum su musu aure kawai, hakan shine babbar masalaha. Duk da nasan yanayin da yake ciki normal ne ga duk namiji irinsa dake a irin gaɓar waɗan nan shekarun na farkon balaga. Amma da alama shi yana cikin jinsin da al'amarinsu keda girma, dan ni da kai duk bamu tsinta kammu a irin wannan yanayin mai tsanani haka ba gaskiya”.       “Tabbas hakane babban yaya. Kuma kayi tunani mai ƙyau. Sai ka samu lokaci kafin ka koma kuyi maganar da Oum”.       “In sha ALLAHU ”. Ya faɗa yana miƙewa saboda fitowar Ajwaad. Babu wanda ya yarda ya kalla a cikinsu saima faman sake haɗe fuska yake yi. A tare suka fita gwanin sha'awa, hakan yasa Mamy da tun fara maganar tasu take tsaye tana jinsu ta sauke wani irin nannauyan numfashi. Dama ta fito ne daga sashen Abah zata koma nata ɗakin. Shi kuma ya fita ta ƙofar baya zasu haɗu da yaran su wuce massallaci...      A haka ranar Ajwaad ya yini yana faman fushi da kowa. Sai da Maanal ta shigo bayan azhar ta samesa a falo kwance. Sunje anguwa ne ita da Ammie tun safe, sai yanzu ne suke dawowa. Ko gida batabi Ammie sun shiga ba ta bama Amaal kayan da suka sayo a kasuwa na haɗin turare da Ammie keyi da kayan gyaran jiki ta shigo gidan su Ajwaad ɗin. Dan tasan zai shiga gidan nemanta. Itama kuma missing ɗinsa take ji sosai duk yau baya ganshi ba kasancewar fitar sassafe sukayi.       Itama dai tayi girma Masha ALLAH. Dan maƙerin bufurci ya fara bayyana kansa gareta ƙirji masha ALLAH. Tayi tsaho ƙyawunta ya sake fitowa. Sai dai tana nan kamar a hure babu wani ƙiba. Sai da ta zauna a kujerar kusa da shi tana faɗin, “Wash ALLAH na ni Manalu”. Sai kuma ta ɗan dubesa ganin baiko motsa ba har lokacin idanunsa a lumshe. Ƙaramar harara ta masa, sannan ta ɗauke goran ruwan daya aje kusa da shi yasha kusan rabi ta buɗe ta shanye sauran tana sauke numfashi da ajiyar zuciya. Sauran ɗan ruwan daya maƙale a goran ta zazzaga masa saman ƙyaƙyƙyawar miskilar fuskarsa. Dole idanunsa suka fara motsawa kafin ya buɗesu a hankali a kanta. Sai ta sake zuba masa ƴar harara, a shagwaɓe ta ce, “Besty ni kake wani shahararrenwa?”. Ta ƙare maganar da tura baki. Sake lumshe idanun yay tare da ɗan matsesu waje guda, sai kuma ya buɗe. Shima hararrar tata ya ɗanyi, kafin can ƙasa-ƙasa ya furta, “An shareki ɗin. Ni da kika tashi fitarki kin sanar dani zaki fita?”.        Sai da ta sake tura bakin sannan ta ce, “To ba Ammie bace tace sai na rakata kasuwa. Kuma ko lafiya ma banda shi cikina namin ciwo ga zazzaɓi ina ji amma tace langyare nake son yi mata dan tace na rakata. Shine kawai na bita gashi nan kaina ciwo yake min kuma ina jin ciwon cikin har yanzu”.          Yanzu kam yinƙurawa yay ya tashi zaune da ƙyau. Cikin bata dukkan hankalinsa da damuwa a fuskarsa ya kai yatsansa ɗaya saman goshinta. Zafi kuwa rauu dan idanunta ma har sun sirka. Miƙewa yay kamar da ɗan faɗa-faɗa yana faɗin, “Shine kuma kika zo nan kika zauna baki nema wajen kwanciya da magani ba?”.         Komai batace ba sai ɓata fuska data sake yi. Rankwashi yay kamar zai kai mata a saman kai sai tai sauri ta kauce tana matse ido. Bai rankwashe tan ba sai harara daya zuba mata ya wuce ƙaton fright ɗinsu dake a dining. Sai gashi ya dawo da first ald box ɗin su da goran ruwa marasa sanyi. Zama yay a inda ya tashi sannan ya buɗe box ɗin yana duba magungunan ciki. Maganin zazzaɓi ya ciro ya bata, harta kai zata zuba a baki ya dakatar da ita da faɗin, “Kinci abinci?”.      Kanta ta ɗan girgiza masa. A shagwaɓe tace, “Shayi kawai nasha, sai wani ɗan a wara a kasuwa kuma nayi aman shi”.       “Kina wasa da kanki ko?”. Ya faɗa a hasale. Ita dai batace komai ba. Cikin ɗan haushi-haushi yace, “Kisha maganin na samo miki tea kisha sannan kici abinci dan cikinki yanzu ya gama cinkushewa”.      Maganin ta zuba ya bata ruwa ta sha, kafin ya miƙe zuwa kitchen ɗinsu. Tea ya haɗa ya fito batare da yayma Mamy dake a kitchen ɗin tana girki ita da masu aiki magana ba. Itama ko kallonsa bata yi ba. Oum bata nan ita da Babban yaya sukaje gidan Babba Sardauna shine ya tuƙata. Fawzan kuwa yana ɗaki yana barci abinsa. Lokacin daya dawo ya sami Maanal ta kifa kanta a hannun kujera tai shiru, ta cusa hannunta ta riƙe cikinta. Cikin sauri ya ƙaraso yana kiran sunanta. Cikin dauriya ta ɗago idanunta har sun kaɗa, sai ta sakar masa murmushi dan bata son tayar masa da hankali.       “Cikin ne?”.   Da sauri ta girgiza masa kai tana amsar shayin da faɗin, “A'a barci ne kawai ke ɗibata”.     Badan ya yarda ba ya barta, sai dai ya zuba mata ido tana shan shayin. Ai kamar jira tana gama shan shayin ta miƙa masa cup ɗin cikin yay mata wani irin ƙullewa. Ba shiri ta dafe shi da duka hannayenta tana fasa ƙara. Wani irin zabura AA yay a rikice yay kanta, sai dai ya kasa sauke hannunsa a jikinta sai faman jera mata tambaya yake jikinsa na rawa. Dai-dai nan kamar an jeho Oum da Babban Yaya sai gasu sun shigo, itama Mamy da mai aiki da ƙarar Maanal ɗin ta isa kunnesu suka fito daga kitchen ɗin.  Duk kan Maanal ɗin sukayi, dan harta faɗo ƙasa tana haure-haure. Kafin ma kace mi ta sassanƙame musu alamar suma.     Hankalinsu ne yay masifar tashi musamman Ajwaad da Oum. Sai Babban yaya ne yay ƙarfin halin faɗin, “A kaita mota suje asibiti”.     Da sauri Oum ta ce, “Kira Doctor dai Fadeel”. Baiyi musu ba yay kiran Family doctor ɗinsu. Yayinda tace ma Ajwaad daya rikice shi kuma ya ɗaukar mata Maanal zuwa ɗaki. A saman gadon Oum aka shimfiɗar da ita sannan Mamy ta shafa mata ruwa. Wani irin wahallen numfashi ta kawo, sai kuma ta fashe da kuka tana matse cikinta da damƙe hannun Oum. Isowar Doctor ta sakasu fitowa aka bar Oum da Ajwaad da yaƙi fitowa. Bayan doctor ya dubata ya tabbatarma Oum zata fara first period nata ne fa. Allura yay mata har biyu, cikin ƙanƙanin lokaci sai barci. Daga ita har Ajwaad ajiyar zuciya suka shiga saukewa a jajjere. Kafin Oum taima doctor daya sake musu bayanin komai godiya. Sai da ya fita ta samu damar kiran wayar Ammie ta sanar mata. Addu'a kawai Ammien tayi ta cigaba da aikinta tana sauraren masifar da Gwaggo keyi tunda ta shigo gidan. Dama duk randa ta fita kasuwa ta sayo kayan sana'arta babu zaman lafiya. Gwaggo ta dinga zage-zage kenan da jifan Ammie da munanan kalamai harda faɗin bin maza take fita yi. Ammie dai bata kulata ba dan dama haka take yi yanzu. Hatta shi kansa Baabu ɗin ta tattarashi ta watsar a gefe kawai..... __________★          Har akai la'asar Maanal na barci a ɗakin Oum, a kuma lokacine rikici ya ɓarke can a gidan su Maanal tsakanin Ammie da Babu. Dan amaryarsa ce tai kiransa a waya ta tsara masa ƙarya da gaskiya akan wai ga Ammie ta saka Gwaggo a gaba tanata zagi. A fusace ya baro wajen aiki ya nufo gida. Babu wani ƙwaƙwƙwaran bincike kawai yana zuwa ya kama marin Ammie. Shine Amaal ta fallo ta sanar ma Oum. A rikice ta wuce gidan ko Mamy bata sani ba....           Ana idar da sallar Asr ɗin shima Ajwaad ya nufo gida. Dan hankalinsa duk yana kan Maanal. Kansa tsaye ɗakin Oum ya nufo, hakan yay dai-dai da farkawar Maanal a firgice. Silmiyowa tayi daga saman gadon Oum ta durƙushe ƙasa, hakan yasa Ajwaad ƙarasowa gareta da sauri yana tambayarta. Sai dai batako samu bashi amsa ba ta shiga kwara amai. Gaba ɗaya duk sai ya rikice yanata jera mata sannu. Itako aman take sosai. Sai da ta gama ta koma gefe ta kwanta yaraf tana maida numfashi. Sannun yaketa jera mata, yanda fuskarsa ta koma sai ka ɗauka ma shike ciwon. Sai kuma ya miƙa mata hannu yana faɗin, “Tashi muje ki wanke baki”.      Kanta ta girgiza masa. Da ƙyar ta iya furta, “Zan huta tukkuna”. Bai matsa mata ba, ya fita ya ɗakko abu ya fara gyara wajen. Ya gama ya maida komai zai dawo ɗakin yaci karo da fasa ƙararata. Ai a ɗari ya ƙarasa faɗowa ɗakin. Tana a inda ya barta, sai dai kallon hannunta take da duk ya ɓaci da jini. Hannun ta nuna masa tana sake fashewa da kuka, sai kuma ta miƙe a galabaice tana kallon gadon. Ashe har nan akwai jinin lurane basuyi ba tun ɗazun. Ganin tana niyyar nufar ƙofa yay saurin riƙota. Cikin son ganin ta kwantar da hankalinta ya ce, “Relax!”.       Kuka ta sake fashe masa da shi tana ƙoƙarin fisge hannunta, “Na shiga uku Besty jini fa? Jini Oum kizo jini”.         “Nace ki nutsu ko!!”.    Ya faɗa a tsawacen daya sakata nutsuwar dole. Sai dai jikinta rawa yake sosai tana cigaba da kallon hannun. Bakin gadon yace ta zauna amma taƙi, sai ya ƙyaleta kawai. Batare daya kalleta ba dan haka kawai yaji kamar yana jin nauyinta ya ce, “Ki jirani anan ina zuwa”. Daga haka ya nufi toilet ɗin Oum. Ruwa masu zafi ya haɗa mata, sannan ya sake dawowa inda take. Har yanzu tanata kallon hannun tana hawaye. Murya ya kwantar kamar bashi ke faɗa ba ɗazun.         “Kinga ki nutsu Besty ba wani ciwo bane ba fa. Dama doctor ya sanar mana zaki fara proud ne shiyyasa kike jin ciwon ciki. Shine sai yanzun yazo. Ki tashi kije bayi ga ruwa can na haɗa miki ki cire wannan kayan ki gyara jikinki kafin Oum ta dawo taje wajen Ammie ne. In kuma kina son sai kowa yazo ya ganki a haka ne to?”.      Da sauri ta girgiza masa kai tana miƙewa ta faɗa Bayin........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖7️⃣2️⃣ ______________ ........Ajwaad bai ji ƙyanƙyami ba ya cire bedsheet ɗin samman gadon Oum ɗin ya samo ruwa da omo da towel ya goge inda katifan ta ɗan ɓaci. Haka ya ɗaga katifan shi kaɗai ya juyata sannan ya ɗauka sabon bedsheet ya canja. Wadrobe ɗin Oum ya buɗe side ɗin da kayan Maanal suke a cike fal ya ɗauka mata kaya, tare da pant. Sannan yaje bakin toilet yana sanar mata idan ta fito ga kaya nan ta saka, ta kuma bar kayan data cire ɗin zai zo ya wanke”. Bata dai amsa shi ba ya nufi hanyar fita. Har yaje ƙofa sai kuma ya dawo da baya sakamakon saukar idonsa akan ledar da Oum ta aiki Amaal ta kawo mata ɗazun, Ledar ya ɗauka ya buɗe ya ciro abinda ke ciki. Bai fahimci miye ba, dan haka ya karanta bayanin jiki. Ganin audigar mata ya sashi maidawa ya ajiye, sai kuma ya sake ɗauka ya sake buɗewa. Ledan ya fasa ya ciri ɗaya ya ɗauka pant ɗinta sabo da ya aje ya saka kamar yanda ya fahimta. Daga haka ya fice.         Bayan tsahon lokaci Maanal ta fito jin motsin fitarsa. Kasa zama tayi gudun karta ɓata wajen, sai dai tanata bin gadon da kallo ganin ya canja kamar komai bai faru ba. Haka jiki a sanyaye ta ƙarasa ga kayan daya ajiye mata. Sai idonta ya sauka akan pant ɗin da ya sakama part ɗin. Sosai tawaro idanunta waje, sai kuma ta tunzura baki gaba da faɗin, “Besty ALLAH baka da kunya”. Ta ƙare maganar da murguɗa baki, sai kuma ta ƙarasa ta ɗauka pant ɗin ta saka dan tana ganin yanda Didin ta suke amfani da shi ai. Kayan ta saka tsaf tanata kumbure-kumbure. Sai kuma ta ɗauka wayarsa data riga tasan password ɗin ta buɗe. Hayewa gadon Oum tai ta sake kwanciya. Dan wani kalar jirin barci take ji sosai. Takai mintuna goma da kwanciya akai knocking ƙofar. Umarnin shigowa ta bada sai ga Bestyn ta. Ɗauke yake da tray a hannu, suna haɗa ido ta risinar da nata. Shima baiyi magana ba ya ajiye abincin kawai ya wuce toilet ɗin Oum ɗin kamar wasu masu jin kunyar juna. Kayan data cire ya tattare hadda p ɗinta dake a ɓace sosai. Tsabar rashin hankali da rashin wayo irin na Maanal maimakon ta wanke sai shima ta bar masa saboda yace tabar masa kayan data cire. Abin mamaki Ajwaad Sarkin ƙyanƙyami da tsantseni sai gashi tsaf ya wanke kayan har sau biyu kafin ya sakasu a injin wanki harda bedsheet ɗin Oum ya wanke fes. Sannan ya wanke bayin ya fita da kayan can backyard ya shanya amma banda p ɗin daya shanya anan toilet ɗin. Zuwa lokacin Maanal ta jima da komawa barci. Sai ma ɗauke tray ɗin abincin yay ya ajiye gefe sannan ya fice ɗakinsu domin yin wanka...        ★Rai a ɓace Oum ta dawo gidan tare da Ammie dake wani irin kuka mai ban tausayi saboda abinda ya faru a gidansu Maanal ɗin. Da farko bata lura da canja kayan Maanal ɗin ba dana bedsheet sai da ta zauna idonta akan trayn dake ajiye. Hannu takai ta taɓa wuyan Maanal, sanyi ƙalau zazzaɓin ya sauka. Barcinta take hankali a kwance. Ajiyar zuciya ta saki mai kauri, sai kuma ta maida dubanta ga Ammie.        “Kiyi haƙuri Asiya kukan nan ya isa. Kada kanki yazo yana miki ciwo. Tashi ma kiyi wanka ki shirya gidan baba zamuje. Dan na fahimci wannan karon sai na dangana al'amarin Habib da baba tukkuna, tunda baya gane yaren Aban su Fadeel da nawa.”      Kai kawai Ammie ta jinjina mata, ta tashi ta shiga toilet. Ita kuma ta buɗe wadrobe ta ɗakko mata wata sabuwar atamfa da bata taɓa sakawa ba da gyale da duka abinda zata buƙata sannan ta fita. Harta nufi ɗakin Mamy sai taci karo da Ajwaad. Sannu ya mata, ta amsa tana kallonsa ganin shima ya sauya kaya. “Fita zakayi ne Auta naga ka canja shiga?”.     Kansa ya girgiza mata, “A'a Oum, wancan sun ɓaci ne”.     Ɗan jimm tayi sai kuma ta ce, “Mamy fa?”.          “Tana ciki tunda kika fita. Oum ina kikaje wai?”.     “Naje nan wajen Ammien ku ne, yanzu ma zamu sake fita da ita gidan Baba. Idan Mamy ta tashi ka sanar mata, ga kuma Maanal nan na barci.....” Kansa kawai ya jinjina mata. Ita kuma ta juya ta koma ɗakinta ranta duk a dagule.        __________★   Shigar Baba Sardauna a cikin al'amarin Ammie yasa aka samu sauƙi tsakaninta da Babu a lokacin. Ga gwaggo ne dai babu abinda ta fasa wulaƙanci yima Ammie take iya iyawarta. Tunda kuma ta ƙyalla ido taga Maanal ta fara jini sai ta fara surutai, yara duk sun zama iyayen mata miye-miye. Saboda ƙwaɗayin Ammie kuma duk sun laƙema masu kuɗi, indai kwaɗayi abun yine suyi tayi watarana sai amma yaran cikkunan shege a titi. Babu wanda ya kula gwaggo da zatunkanta sai Maanal, rashin kunya ta mata sosai ranar har sai da ta saka Gwaggon kuka. Sai Ajwaad ne yazo yasa Maanal barin gidan da ƙyar. Aiko gwaggo ta haɗata da Babu yace sai ya daketa. Jin haka Maanal ta daina shigowa gidan har kwana huɗu.         A yammacin ranar Maanal ta nema jini ta rasa. Tana son gayama Oum tana jin kunya. Gashi bata shiga gidansu saboda Babu yace zai daketa. Kawai saita yanke shawarar samun Ajwaad, ɗakinsu ta leƙa, babu kowa sai babban yaya dake barci, dan haka ta fito. Can harabar gidan ta nufa, inda ta wuce Mamy da ƙanwarta da suke kira Maman Saheeba suna hira. Kallon banzar da Maman Saheeba ke mata yasa ko gaisheta bayi take ba idan tazo gidan. Dan haka yanzun ma bata kulasu ba har Mamy ɗin ta wuce garden neman Ajwaad. Tasan shi baya yawo, indai ba aikensa akai ba to zaka samesa ne a garden yana karance-karance daya ɗaukama kansa yanzu. Wani lokacin har faɗa suke yi dan ita karance-karance haushi yake bata, ya rage bata kulawa, bata san miyyasa ba bai son su cika kaɗaicewa daga ita sai shi a yanzu. A hankali ta zare novel ɗin dake a hannunsa, fuska ya yamutse tare da ɗago idanunsa ya saukesu a kanta. Zama tai kamar zatayi kuka tana kallon littafin, sai kuma ta sake kallonsa idanun nata cike da hawaye.        “Besty wai mike damunka kwana biyun nan. Sosai ka canja min, musamman tsakanin nan. Ka ɗauka dukkan hankalinka ka maida ga karatun novels. Baka son mu zauna muna hira mu kaɗai, ko assignment zamuyi sai kace sai a gaban Oum ko Mamy. Kana yin abu kamar ma baka son ganina.”       Maimakon amsa mata sai kawai ya lumshe idanunsa masu haske sosai ya sake buɗewa a kanta. Tsohon lokaci kafin ya motsa lips ɗinsa kaɗan ya furta, “Babu komai yanayi ne kawai”.      “Yanayi?”. Kansa ya jinjina mata kawai. Kamar zatai magana sai kuma ta fasa. Fuska taɗan shagwaɓe tare da faɗin, “Besty akwai matsala fa?”.      Cikin ɗan tsireta da idanu ya ce, “Tami?”.       Sake shawaɓe fuska tayi ƙasa-ƙasa kamar mai tsoron a jita ta ce, “Na daina ganin jinin, kuma ALLAH kunyar faɗama Oum nakeyi. Ina son zuwa wajensu Didi ina tsoron Baabu ya kama ni”.       “Oh nine baƙya jin kunya?”. Ya faɗa yana tsatstsareta da idanu.   Sai da ta waro idanunta waje sosai sannan ta ce, “Kai kuma zanji kunya Besty? Kai fa Besty nane. Ni dan ALLAH ka gaya min yaya zan gane ya ɗauke ɗin kenan naje nai wanka. Kuma ai irin wankan da aka koya mana a islamiyya zanyi ko?”.     Idanunsa kawai ya rumtse yana datse laɓɓansa da ƙarfi da haƙori. Miyyasa yarinyar nan bata ganewa ne wai? Taɓa shin da tai ya sashi dawowa hayyacinsa. Ta sake marairaice fuska. Sai kawai ya samu kansa da bata amsa. “Naji zan faɗa miki. Amma lokaci yayi da zaki fara fahimta”.       “Fahimta? Mizan fahimta?”.    “Ba komai”. Ya faɗa yana miƙewa. Tashi tai itama ta bishi, amma sai yay mata nunin ta koma ta zauna. Zaman tayi, shi kuma ya fice a garden ɗin. Babu jimawa ya dawo da takarda ya bata. Kafin yace mata, “Tashi kije na rubuta miki komai”.    Batai musu ba ta miƙe, hannu ya miƙa mata. Idonsa akan novel ɗinsa dake hannunta. Sai da ta tura baki gaba sannan ta miƙa masa ta wuce....        Kwana biyu dayin haka zazzaɓi mai zafi ya kwantar da Ajwaad. Zazzaɓin daya sanya har sai da ya kwanta a asibiti. Kwanansa biyar aka sallamesa. Ana sallamarsa kamar jira itama Maanal ta fara nata ciwon. Tasha jiki sosai kafin itama ALLAH ya bata lafiya.. _________★        Zancen da Fawzan yayma Oum itama ta samu Abah da shi, shi ba mutum bane mai son takurama yaransa. Sannan yakan nutsu akan abu idan sunzo masa da shi ya dubi halaccinsa da haramcinsa a wajen UBANGIJI. Sosai yay nazari akan batun ya kuma nema shawarar Baba Sardauna. Ɗari bisa ɗari Baba Sardauna ya bada goyon baya shima akan hakan, dan tunda har Fawzan ɗin ya furta ai masa auren ai masan kamar shine yafi komai dacewa. Dan haka su Abah suka shirya zuwa Giro. Sun kuwa je. Alhamdullah Baba Haruna ya basu auren Shahidah da Amaal, basu baro ba kuma sai da suka bada komai har sadaki. Aka kuma tsaida ranar aure. Kasancewar Baabu ya zama abinda ya zama yasa sai da suka dawo Abah ya sanar da su daga shi har gwaggo. Wannan al'amari yay matuƙar ƙona zuciyar gwaggo dan itafa duk wani jin daɗin duniya bata son ganin Ammie a cikinsa.       A ɓangaren Mamy kam komai batace ba, sai ma addu'a datai da sanya albarka kawai. Haka ƴan uwanta ma albarkar suka saka. Babban Yaya ya koma makaranta, haka Ajwaad da Maanal ma. Yayinda akema Fawzan nasa shirin yin sabuwar jarabawa shi da Amaal. A haka aka shanye watanni kusan biyar, su Amal sun kammala exam, akai bikin saukar Maanal da Ajwaad tare da walimar data ƙayatar. A wajen wannan walima ne Baba Sardauna ya ɗarsa nasa burin akan Ajwaad da Maanal. Sai kuma bayan kwana biyu dayin walimar yazo har gidan abinda bai cika yi ba. Zaunar da Oum da Abah da Mamy yayi, bai ɓoye musu komai ba akan batun da yazo da shi na son haɗa auren Ajwaad ɗin da Maanal tare da ƴan uwansu. Ya kuma kawo musu hujja mai ƙarfi akan abinda ya hango game da shaƙuwar yaran. Dan gara ya kasance akwai igiyar aure a tsakaninsu gudu sharrin shaiɗan saboda kusancinsu yayi yawa. Gashi kuma suna a wata gaɓa ce mai ban tsoro akan duk wani yaro dake a wannan shekarun musamman ma shi Ajwaad da Babban Yaya ya sameshi ya warware masa komai akan halin da Autan yake ciki tun kafin ya koma, shiyyasa ya saka ido shima ya fahimci komai ya ya kuma tabbatar. Su duka ukun babu wanda ya musa ko jayayya akan abinda Baba Sardauna yazo da shi. Sun kuma gamsu da cewarsa akan ai shiru da batun kada a sanarma Ajwaad ɗin da Maanal. Su kuma barsa da Baabu shi zai yi magana da shi.      Haka kuwa akayi, Baba Sardauna ya kira Babu har gidansa sukai magana ta fahimta. Ya kuma gamsu shima ya bada goyon baya. Bayan haka Baba Sardauna yay kiran Baba Haruna shima a waya suka tattauna. Shima kuma ɗari bisa ɗari ya gamsu. Daga haka aka fara shirin bikin ƴan gata su shidda. A ɓangaren Babu babu wani ƙwaƙwƙwaran shiri, dan gwaggo da Amaryarsa sun gama zugesa tsaf ta bayan fage. To dama dai Abah yayi niyyar shiryama yaransa biyu gida da kansa. Shi ko Ajwaad dama sai sun kammala secondary za'ayi biki. Oum kuwa duk wani abu da uwa ya kamata tayi ta ɗauki ɗammarar yin komai, duk da haka Ammie ta sameta da abinda ke a hannunta, ta kuma nema shawararta akan tunkarrar Babu da gadonta da iyayenta suka bari. Oum ta bata goyon baya badan zata amshi kuɗin a hidar yaran ba, sai ɗan abinda take shiryama zuciyarta. Tana shiri akan in har aka kammala bikin yaran to lallai koma miza'ayi dole Babu ya saki Ammie. Dan ta gaji da ganinta cikin wannan zaman zaluncin da ƙuncin. Ita ba kwanciya da miji ba, ita ba ƴancin aure ba, duk ta lalace ta rame ta fita hayyacinta. Kamar ba Ammie ƴar gayu ƴar ƙwalisa ba. Sarkin tsafta da gyara jiki. Tofa dole ne su taya mata ta amshi hakkinta a wajen Babu tun yanzun.      Babu wasa kuwa Ammie ta tunkari Babu da batun kadarorinta da komai ma da iyayenta suka bar mata akan son yin hidimar biki, abinda ya tadama Babu hankali kenan, dan kuwa ya salwantar da kaso biyu bisa ukun wannan dukiya, suma kuma dangi sun ci. Shi kansa kaso ɗayan daya rage ma yana a ƙila wakala ne kawai. Ƙin cema Ammie komai yay a lokacin, face kalmar “Yaji”. Yay gaba abinsa. Bata damu ba, ba kuma ta kawo komai a ranta ba tunda rayuwar daya ɗauka ma kansa kenan a yanzu..........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖7️⃣3️⃣ ______________ ........Matakin farko na shirin biki shine shirya zuwa Dubai da Oum tayi tare da Umma (Matar baba Sardauna) da Gwaggo Khadijah. Sai dai zasu fara zuwa suyi umrah ita da Ajwaad da Fawzan da Maanal. Amaal da Shahidah kuma za'a fara musu gyaran jiki dan ita Maanal bazata tare ba sai sun kammala secondary. Sunyi wannan tafiya Maanal na'a cikin ɗunbin farin ciki, dan wannan shine karonta na farko hawa jirgin sama. Fawzan ya tasata da tsokana da dariya. Itako ko'a jikinta. Sai mutum nata data dama da surutu wato Ajwaad, yana ɗan biye mata sama-sama batare da tasan dalilin komawarsa hakan a gare ta ba yanzu. Sunyi Umrah Alhmdllh, inda suka samu kwanaki goma sha biyu kafin su nufi Dubai, can suka haɗu da Umma da Gwaggo Khadijah da suka taho daga Nigeria su kuma. Duk kannin abinda ya kamata an shirya shi, suka tura kaya Nigeria, a kuma wannan lokaci ne Ajwaad ya bada aka yi agogon nan da Manaal ta zana ta hanyar babban aminin Baba Sardauna dake da company anan Dubai. Kusan komai a gaban Ajwaad aka yisa, wannan kuma shine ya zama dalilin farko na fara jin sha'awarsa akan hakan. Duk da yana da nashi burin.       Sun dawo Nigeria suka iske Saheeba a gidan, wai tazo hutu. Babu wanda yay magana balle kawo wani abu a cikin ransa game da haka. Tunda dama tana ɗan zuwa jefi-jefi (Saheeba ɗiya ce ga ƙanwar Mamy). Bayan dawowarsu da kwana biyu babban yaya ya iso shima. Shirin biki fa ya fara kankama, dan ta ko'ina babu wasa. Sai dai Ammie da Baabu suna tsaka da tafka rigima saboda wasa da hankali da yaketa mata akan batun hakkinta, wato dukiyarta da iyayenta suka bar mata. Oum ce ta tausheta akan ta bar batun har ALLAH yasa su Baba Haruna suzo wajen biki, koma mi za'ayi sai ayi kawai. Da wannan ta tausheta akan al'amarin....        A ranar akai kamu, normal kamu ne dai irin namu na mutan da, ɗan turare kawai aka fesama Amaal da Shahidah, sai ƙawayensu daketa ƙunshi. A ranar gayyar mutanen Giro suka iso. Hakama can gidan su Oum mutanen Yola sun iso. Sai wanda ke anan cikin Kano ta ɓangaren su Oum data ɓangaren Mamy. Dama ƴan paris kwanansu uku kenan. Koda yake Mammah ce kawai tazo saboda yara na karatu, hatta Auta Rafeeq ba'azo da shi ba.       Washe gari aka shirya walima anan cikin gidan su Oum ta iya mata, Umma ce ta ɗauki nauyin malaman da zasuzo mata suyi lectures da abincin da za'aci. Wannan Rana itace tushen komai na wargajewar alaƙar waɗan nan ahali guda biyu. Ranar da zukata suka rarrabe cike da ƙuna da girgizuwa. Ranar da komai ya lalace, zaren ƙaddarar daya ƙullesu a waje guda shekara aru-aru jarabawar ƙaddara ta datse shi da almakashi mai matuƙar kaifi. Datsa irin ta kwaf ɗaya da har yanzu an rasa mai sake kamawa ya ƙulla shi.       Masu shirya waje sun kammala wajen ƙarfe biyu na rana, a dai-dai lokacin Maanal na daga can ƙarshen garden ɗin zaune saman lilo ita kaɗai. Tunda ta tashi bata jin daɗi yau, haka kawai kuma sai take son kaɗaici. Kwana kusan huɗu kenan tana acan gidansu, yanzu ma hayaniyar ƙawayen su Amaal suka isheta dan tana ɗakinsu kwance yasa ta fito ta dawo nan gidan su Ajwaad. Koda ta shigo ciki nan ma hayaniyar tayi yawa, sai kawai ta nufi ɗakin su Ajwaad. Cike ta sameshi da abokan su Fawzan, sai dai babu Bestyn nata. Gaishesu kawai tayi ta ɗakko wayar Ajwaad dake caji a gefen gadonsa ta fito. A hanyar fita falon suka kusa cin karo da wata ƴar budurwar yarinya kanta ɗauke da boket cike da gorinan zoɓo da kunun aya. Sosai Maanal na son zoɓo a rayuwarta, dan haka ta tsaidata tana tambayarta. Yarinya ta bata amsa da cewar mamansu ce tace ta kawoma Oum a ƙara a baiwa baƙi. Sai kuma ta nuna mata na hannunta, ta ce, “Wannan kuma zan bama yayana”. Maanal tasan yayan nata abokin Fawzan ne sosai, dan baima da wani aboki sai shi, suma dai maƙwaftansu ne. Sai kawai ta amshi na ledan ta ɗauki ɗaya. Daga haka ta fice ita kuma yarinyar tai ciki tana tura bakin haushin ɗaukar ma yayanta da Maanal tayi, babu kuma damar magana tasan zata iya dukanta, dan yaran anguwar nan kusan duk tsoron Maanal suke saboda fitinarta. Manyan ma in dai kace zaka shiga sabgarta kasha rashin kunya kuwa. Can garden ta nufa, sai da ta gama kalle gyaran da akai sannan ta wuce can ƙarshe ta zauna a saman lilo ta buɗe zoɓon ta fara sha tana game a wayar Ajwaad ɗin. Tafi mintuna biyar da zama sai gashi, sai da ya kai zaune a kusa da ita sannan ta ɗago duk da taji ƙamshin turaren da suke amfani da shi tunda ya shigo wajen. Harrarsa tayi, shima ya rama dan faɗa sukai kwana biyu kenan shiyyasa ma ta koma gidansu. Koda ya rama hararar sai ta tura baki gaba. Baki ya taɓe da ƙarɓar zoɓon hannun nata shima ya hau sha. Haka suka dinga shan wannan zoɓo babu mai ma ɗan uwansa magana har suka kammala. A lokacin ne ya fiddo wani ƙyaƙyawan box ya miƙa mata. Kallon box ɗin tayi, sai kuma ta kallesa, ta kai hannu zata amsa ya janye da faɗin, “Oh nama manta haushina kike ji fa”.        “To bana huce ba”. Ta faɗa kamar zatai kuka.     “Kin tabbata kin huce?”. Da sauri ta ɗaga masa kai alamar eh. Sai ya sakar mata murmushi ya miƙa mata box ɗin. Wayarsa ta ɗaura masa a saman jikinsa, ta hau kiciniyar buɗewa. Da wani irin zaro idanu ta ce, “Wooow!!! Besty!. Amma agogon nan ya haɗu wlhy”.     Murmushi ya saki mai sanyi, ƙyawawan fararen idanunsa na kallonta da wani irin yanayi mai zafi. Cikin ƙanƙanuwar muryarsa data ƙara ƙanƙancewa a yanzu ya ce, “Besty, ai duk ƙyawunsa kin fisa ƙyau. Sannan kefa kika zana shi da hannunki shekaru shida kenan”.        Itama cikin sanyi ta ce, “Ni kuma Besty!”.     “Yes! Kefa”. Ya bata amsa yana zaro wani note book a aljihunsa ya miƙa mata. Amsa tai tana kallon zanen agogon da tabbas ta tuna itace ta zana shi. Sai kawai taji hawaye sun cika mata ido. Dan zanen agogon bashi da maraba da agogon daya batan. Cikin rawar murya ta ce, “Besty!”.       “Uhmyim Bestyn Besty!”.    Ya faɗa da wani irin shauƙin da shima kansa bai san mi yake yi ba. Ga idanunsa na wani irin mata kallo mai zafi, sun kuma ƙanƙance sun kaɗe kamar ba shi ba. Itama kanta kallon nasa take tsakkiyar ido da wani irin yanayi dake cizon zuciyarta. Fin mintuna biyu suna kallon junansu kafin kiran waya ya katse su. Wayar ta kalla cike da kasala, ganin Babban Yaya ya sakashi ɗagawa murya a sarƙe. Bata san mi babban yayan ya gaya masa ba. Ya dai miƙe a raunane yana kallonta da miƙa mata wayar. “Ina zuwa ki jirani anan”.     Kanta kawai ta iya jinjina masa. Sai da bayan ya wuce ta iya sauke numfashi. Sai kuma cikinta yay wani irin murɗawa. Fuska ta yamutse da sakin ƴar ƙara tana dafesa da hannu biyu. Sai kuma jikinta ya kama rawa. Tama rasa yanda zata fassara ciwon cikin nata. Ta jima tana matse-matse kafin ya saki mata. Sauka tai akan lilon ta wuce cikin gidan neman Oum danta faɗa mata cikinta na ciwo. Sai dai koda ta shiga ɗakinta cike yake da baƙi, ita kuma bata a ciki. Fitowa tai domin nemanta cikin nata ya sake murɗewa. Da ƙyar ta iya kai kanta ɗakin su Ajwaad dan gara ta nemosa shi sai ya nemo mata Oum ɗin. Cikin ɗakin yanzu kam babu kowa saɓanin ɗazun, ga cikinta yay matuƙar ƙullewar da tafi ta farko, dole ta durƙushe gaban gadon Ajwaad ta dafe cikin nata hawaye masu zafi na rige-rigen sakko mata daga idanunta zuwa kumatun ta. Tun tana fahimtar halin da take ciki har komai ya fara mata nisa. Sama-sama taji ƙarar buɗe ƙofa, tare da ƙamshin turaren Ajwaad. Kamar muryarsa taji yana kiran sunanta a rikice, sai kuma taji ya ɗagata gaba ɗayanta ya maida saman gadon, tana ƙoƙarin yimasa magana taji ya kwanto mata a jiki ya rungumeta, duk da a yanayin da take sai da taji hankalinta ya tashi, dan abune da kullum ake musu nasiha a kansa. Oum tayi, Ammie tayi, Abah da su babban yaya da su Didi suyi. Jikinta ne ya kama rawa jin yana ƙoƙarin cire mata kaya, ga lips ɗinsa na ƙoƙarin sauka akan nata. Ƙoƙarin turashi take amma bata da wani ƙarfi, sai ma kama hannunta da yay duk biyu ya murɗe da ƙarfin da har sai da taji zafin har a cikin ƙwalwar kanta da tsakkiyar zuciyarta. Ya kuma danne mata baki ta yanda ta kasa ihun datai niyyar yi. Daga haka bata sake fahimtar komai ba sai wata irin rikitacciyar hayaniya da ihun mutane mai hawa saman kai......          A hankali ta shiga buɗe idanunta da sukai mata nauyi, hakama jikinta kamar ba nata ba, ga wani irin zafi da take ji acan ƙasanta. Akan Oum dake a rungume da ita tana kuka ta saukesu, sai kuma ta fara bin mutane da kallo. A tsakar gidansu ne, saɓanin gidan su Oum data san ta shiga. Ba kowa ke hayaniyar nan ba mai ban tashin hankali sai dangin su na Giro, gwaggo har riƙeta ake saboda yanda ta birkice tana zage-zage daga ita sai bujen cikin zani da riga. Amma zani da ɗan kwali duk ta wancakalar. Gefe su Shahidah ne ke kuka suna rungume da Ammie dake kwance kashirɓan. Sam Maanal ta kasa fahimtar komai, face cigaba da kallon kowa da sauraren ihunsu da sam bata fahimtar komai a ciki. A haka Abah da baba Sardauna da likitan data san family doctor ɗin su Oum ɗin ne suka shigo. Abah da shima yake a matuƙar damuwa ne ya bama Oum umarnin ɗaga Maanal zuwa ciki. Amma sai Gwaggo tace Oum bazata shiga musu ba, kuka Oum ɗin ta sake fashewa da shi mai ban tausayi. Hakan bai sa Gwaggo taji tausayinta ba, ta saka ƴaƴanta biyu kama Maanaal zuwa ciki, a haka doctor ya bisu bisa umarnin baba Sardauna.       Fin mintuna ashirin sannan doctor ya fito, zuwa sannan gidan ya ɗan lafa bisa tsawatarwar baba Haruna da basu jima da isowa ba. Doctor ya buƙaci ganin iya su Abah, amma gwaggo tace sam ba'a isa ba, ya faɗi duk ma abinda zai faɗa anan gaban kowa. Dan ita bata son munafunci. Ganin yanda take nema tada sabuwar tarzoma Baba Sardauna yace ya faɗa ɗin. Cikin damuwa doctor ya tabbatar musu amma Maanal fyaɗe. Kuma dole ai gaggawar zuwa da ita asibiti saboda jinin dake zuba a jikinta yana ƙara yawa. Wata irin kururuwar tashin hankali gwaggo ta fasa ita da sauran ƴan Giro, yayinda Oum ta yanke jiki ta faɗi. Dole aka kwashi Oum zuwa gida, Maanal da Ammie kuma asibiti.      Anan gidan su Oum ɗin ma dai a harmutsen yake. Ga Ajwaad ya kulle kansa a ɗaki anyi-anyi ya buɗe yaƙi. Sai da aka ɓalle ƙofar. Samunsa sukai kwance wanwar a ƙasa babu numfashi, ga jikinsa duk ya ɓaci da jini, shima dole aka kwashe shi zuwa asibitin....      _____________★        Komai ya dagule, dagulewa mai ban tashin hankali ga waɗan nan ahali guda biyu. Ɗaurin aure dai bai yiwuba washe gari. Dan anyi zama a tsakanin manyan ana tuhumar Ajwaad da tun a daren jiya ya farfaɗo akan wannan ruɗaɗɗen al'amari. Ya jima bai tankama kowa ba, kafin ya buɗe baki da ƙyar yace musu eh ya aikata.        Wannan amsawa tashi ta matuƙar birkita kowa. Ajwaad ɗan shekara ashirin da ɗaya a duniya, da yarinyar da suka rayu tun ƙuruciya. Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un. Ran baba Sardauna a ɓace ya ce, “Shike nan tunda ya amsa ya aikata ɗin sai a ɗaura musu auren yau suma su tare kawai kamar sauran ƴan uwansa. Amma mi, a mamakin kowa sai Ajwaad ɗin ya shiga girgiza musu kai da faɗin, “Aure? Baba kuyi haƙuri ban taɓa kallon Maanal da sigar zama matar aure a gareni ba. Ita ɗin ƙanwata ce ai..”      Cikin ɓacin rai Baba Sardauna ya katsesa da faɗin, “Amma ka keta mata haddi?!!”.       “Kuskure aka samu”.   Ajwaad ya bada amsa babu ko ɗigon damuwa balle nadama a tattare da shi. Wani irin mari Abah ya fara sauke masa. Da ƙyar aka iya riƙesa dan hadda hauri ya fara kai ma Ajwaad ɗin. Da ƙyar aka samu ya zauna yanata zaginsa ga hawaye ba zuba masa. Tabbatarma Ajwaad yake dolene ya auri Maanal. Dan haka babu fashi za'a ɗaura auren yau ɗin na na su duka ukun. Zaram gwaggo tace sam bazasu haɗa zuri'a da su ba. Idan kuma har Babu ya amince babu ita babu shi har abada sai ta tsine masa wlhy..........✍️ _Tofa wannan fa shine rikici._ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖7️⃣4️⃣ ______________ ........Hankalin kowa ya tashi a falon. Aka shiga ƙoƙarin fahimtar da ita amma tace bafa zai yiwu ba, tana kan bakanta. Babu ya rasa yanda zai yi, jikinsa sai rawa kawai ma yake yi. Wannan ɓacin rai yasa Baba Haruna yanke jiki ya faɗi a falon, ga shi yanzu baida iko a kanta tunda babu aure tsakaninsu. Dama yana da hawan jini. Babu shiri aka kwashesa zuwa asibiti, sai dai kafin ma akai rai yayi halinsa ALLAH yay masa rasuwa.      Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un, wannan rasuwa ta sake harmutse kowa. Duk yanda su Abah suka kai da son a sake zaman sassantawa bai yiwu ba. Dan baba Haruna kafin ya rasu yabar wasiyyar a maidashi tushensa a biznesa dan ALLAH. Wannan yasa tun a ranar kaf mutanen Giro har su Ammie da su Maanal dake a cikin wani birkitacen yanayi kama hanyar Kebbi. Kwana sukai a hanya, sai washe gari kusan sha biyu suka isa Giro. Haka aka sallaci gawar baba Haruna bayan an masa sutura aka kaishi makwancinsa na gaskiya.        A wannan zaman makoki ne aka fasa batun fyaɗe da akama Maanal. Tare da tabbatar da a dalilinsa ne baba Haruna ma ya rasu. Mutanen ƙauye sai addu'a. Nan fa zaman gaisuwa ya zama zaman ƙananun magana da tsogumi. Takai ko fitowa Ammie da ƴaƴanta basu isa yi ba. Dole suka koma ƙumshe kansu a ɗaki. Ga Ammie babu isasheiyar lafiya, hakama Maanal ta koma yin abu kamar wadda brain ɗinta ke neman taɓuwa. Sai ta nuna kanta ta fashe da kuka tana faɗin, “Ni! Ni! Maanal Ajwaad yayma fyaɗe. Ni Manaal Ajwaad ya lalatama rayuwa? Ni Manaal Ajwaad yace bazai aura ba, bai taɓa sona ba. Nima bana sonsa, ban taɓa sonshi ba ai”. Sai ta saka dariya, kota fashe da kuka. Tun su Shahidah na ɗaukar al'amarin wasa har ya fara basu tsoro. Ga Babu tunda suka zo baiko shiga sabgarsu ba. Ko kallo basu ishe shi ba. Haka itama Gwaggo. Ga Ammie a kwance babu lafiya. Sun rasa wazasu tunkara da matsalar Maanal ɗin ma. A haka aka gama zaman gaisuwa kowa ya watse sai al'ummar gidan. Maanal dama su Shahidahn kansu suka fara fuskantar sabuwar ƙyara da tsangwama da habaici ga mutanen gidan. Takai yanzu abincima babu mai basu, sai in an gama girki an ajiye tukwane subi dare suna karto ƙanzon tuwo. Wadda ta kamasu kuma ta shiga musu terere a gidan da kiransu ɓarayi. Haka za'a fito ana zaginsu da musu gorin iskanci. Wai suma su Shahidahn waya sani ko tuni an lalata su, ALLAH ne ya tona asiri akan Maanal ɗin. Abinda zai baka mamaki da tausayi Babu duk yasan mike faruwa. Amma ko'a jikinsa ta ɗansa kawai yake da amaryarsa. A haka suka cika wata guda a gidan cikin wata irin wahalliyar rayuwa. Sai Maanal ta wayi gari da zazzaɓi da ciwon ciki, sai amai. Wannan salonta ne a duk sanda zatai period, amma sai Gwaggo ta fasa kururuwa ta tara kaf jama'ar gida da maƙota. Kai harma da sauran matan anguwa da suka dinga shigowa da gudu. Batare da tayima kowa bayani ba duk wanda ya iso yaga Maanal dake jikin Shahidah na huttan amai data gama sai a hau ƙus-ƙus. Su Shahidah basu fahimci abinda ake nufi ba sai washe gari da zance ya fara yawo wai Maanal nada ciki. Wannan abu ya birkita su Amaal da Ammie dake kwance cikin matsanancin ciwo. Sai dai basu san suma ta hanyar da zasu tabbatar Maanal nada cikin ko bata da shi ba. Zancen cikin ya sake ƙarfafa ciwon Ammie matuƙa. Yayinda komai ya sake musu tsanani. Sati guda suna cikin wannan uƙuba ta mutanen gida dake zaginsu da cin zarafin su da gori manyan gidan suka taru akansu. A gaban kowa Baabu yay ma Ammie saki biyu ya zama uku, ya kuma ce subar gidan dan shi baima da tabbacin su Shahidah ƴaƴansa ne. Dan abinda ya faru da Maanal na nufin itama ƙila Ammie ɗin tanayi tun da can. In ba hakaba miyyasa yaran basa kama da shi sai ita, sai Maanal ɗin data ɗan ɗebo duhun fatarsa. Dan haka suje su baza'a haifa musu ɗan dakan kuka ba a cikin zuri'a.       Duk da halin da Ammie ke ciki haka ta dinga kuka tana roƙonsa da manyan gidan amma kowa ya nuna babu ruwansa. Sai ma fara watso musu kayansu da akai waje. Dole suka tattara abinda zasu iya suka fito. Da ƙƴar suka samu wani mai akori kura dake ɗibar icce a garin ya ɗakkosu zuwa Suru. ALLAH ya taimakesu da ƴan kuɗi a jikinsu da Amaal ta kwaso a ɗakin gwaggo. Haka suka samu motar Kano, kuɗinsu ma bai kai ba direban dai ya taimaka musu a hakan ganin Ammie da Maanal a halin ciwo. Dan Maanal tunda zancen tana da ciki ya ɓullo sai ta sake birkice musu. Ga jinin proud ɗin ma da take saka ran zai zo yaƙi zuwa. Sai ta sake yarda a ranta cikinne da ita kenan.       Sun iso kano da daddare, haka suka buɗe gidan suka shiga. Ɗan kayan abincin da suka samu suka sarrafa, sannan suka shiga gyaran gidan dan an barsa ne kaca-caka lokacin da zasu tafi. Harda abinci dafaffe da duk ya ruɓe. Washe gari mutane suka dinga shigowa wai amsar kayansu da aka ara domin yin hidimar biki ba'a maida musu ba. Wasu ma harda yanka musu kuɗin kwanakin da sukayi. A bakin maƙwafciyarsu suke jin wai su Oum sun bar ƙasar ma gaba ɗaya. Wannan batu ya zafafa musu zukata, sunji tsanar su fiye da farkon rikicin. Kwanansu biyar mutane sunzo wai ai an sayar musu da wannan gida. Dan haka sun basu kwana biyu su fita. Hankalin Ammie ya sake tashi dan tasan dai wannan gida nasu ne, koma tace bata ne. Kawai washe gari sai ga kira daga Babu da Gwaggo, wai in basu tashi a gidan nan ba suka bari suka zo Kano sai sun saka an wulaƙanta rayuwarsu. Tsoro mai tsanani ya shiga zuciyar Ammie. Dan tasan gwaggo zata iya komai. Haka ta tattarasu tana jan jiki da ƙyar suka ɗauki abunuwansu masu amfani suka saida sauran suka haɗa ƴan kuɗin tace suje Minna. Gara ta koma tushen mahaifiyarta maybe ta samu ko wasu a dangin su ne na nesa.         Wannan shine mafarin barowarsu Kano, inda sukaje Minna can ma dai babu madafa. Dan sun gama zagaye-zagayen su sai da ƙyar suka samu wanda ya sanar musu ai ƙanwar mahaifiyarta Shamsiyya tana a Kaduna yanzu haka da iyalanta. Haka nan ma su tattaro suka sake juyowa garin Kaduna. Ga jikin Maanal na neman birkicewa. Dan da tayi tari sai jini. Gashi tana abu kamar wadda ƙwalwar kanta ta samu taɓuwa. Direban daya ɗakkosu a dikko jaction ya ajiyesu, suka nema motar Kaduna. Sai dai kuma kuɗinsu kona mutum ɗaya bai kai ba. Sunyi roƙon sunyi magiya amma babu wanda ko ya kallesu balle ya nuna musu tausayawa. Dan haka Ammie ta yanke shawarar yin bara maybe su samu su haɗa kuɗin motar ko zuwa safiya ne. Anan ƙarƙashin gadar dikko suka nema wajen zama ita da yaran, ga Maanal kwance bata gane komai da kowa. Hasalima numfashinta da ƙyar yake fita. Jefi-jefi masu mota na jefa musu sadakar, haka Shahidah da Amaal zasubi da gudu su tsunto idan iska ta ɗauka. Wani lokaci ma rikici ya ɓarke tsakaninsu da almajiran dake a wajen. Dare yaja sosai, dan kusan ƙarfe biyu ake magana. Jikin Maanal yayi tsanani, numfashinta yana wani irin fisga alamar rayuwarta na gab da salwanta. Su duka ukun rungume suke da ita suna kuka. Sosai kuma sautin kukan nasu ke fita saboda ƙarancin hayaniyar titin a yanzu. Babu yawan motoci, babu yawan mutane. Tsirarun mutane dake a wajen suka ɗan zagayesu suna kallo babu mai niyyar taimaka musu. A dai-dai nan wata baƙar mota wulik ta faka, dan har ya wuce su kaɗan ya dawo da baya-baya ya faka motar. Su biyu ne, a kallo ɗaya zaka fahimci ɗaya yaron ɗayan ne. Mai alamar mammalakin motar ƙyaƙyƙyawan matashin saurayi mai ginannen jiki da cikar kamala. Shine ya fara magana da tunanin ko haɗari akayi, dan haka mutanen dake zagaye da su suka dare aka bashi hanya. Mamaki ne ya kamashi ganin mace da yara ƴammata ƙyawawa duk da wahala ta ɓoye kaso tamanin na ƙyawun nasu, ga wadda ke rungume a jikinsu tana aman jini. Tashi hankalinsa yayi, bai saurari komai ba ya duƙa ya ɗauka ƴar budurwar yarinyar da bazata wuce shekaru goma sha biyar da wasu watanni ba. Sannan a cikin rikicewa yace suma su shiga mota a kaita asibiti. Ko musu su Ammie basu yi da shi ba. Dan komai basa ganewa a yanzu. Fatansu kawai shine Maanal ta rayu. Haka suka wawuro jakarsu ɗaya data rage mai ɗauke da muhimman takardunsu na karatu sai abinda ba'a rasa ba suka shiga motar. Wani irin gudu drivern saurayin yake zubawa na tashin hankali, abinka da dare sosai babu yawaitar mutane. Cikin abinda bai wuce awa ɗaya da mintuna arba'in ba suka iso Kaduna. Kai tsaye asibiti ya nufa da su. Babu ɓata lokaci kuma aka shiga baima Maanal taimakon gaggawa. Hakama Ammie da suna sauka a motar jiri ya kwasheta ta yanke jiki ta faɗi......      _________★       Kwanakin su uku a asibitin suna samun kulawa mai daraja. Alhamdullah jikin Ammie yay sauƙi sosai, hakama Maanal duk da ba'a barinsu ganinta saboda doctor ya tabbatar musu kaɗan ya rage zuciyar Maanal ɗin ta buga. Amma Alhamdullah sun samu nasarar dai-daita abubuwa. Sai dai duk da haka ta kamu da ciwon zuciya mai ƙarfin da sai dai a dinga tayata da addu'a.      Matashin saurayin nan daya faɗa musu sunansa Yazeed shine tsaye akan komai, hatta abinci sau uku a rana bai taɓa gajiyawa ba. Tuni ya sayo musu kayan sakawa da dukkan ƙananun abubuwan buƙata. Kuɗin asibitinsu da komai ya biya. Hatta na aikin da akace za'ama Maanal nan da wata ɗaya. Randa suka cika sati ɗaya yazo da mahaifinsa. Mutumin kirki shima nutsatstsen dattijo mai cikar kamala da ƙyawun haiba. Shima ya bama su Ammie kulawa, shine kuma ya bincikesu ko zasu bada number wani ɗan uwa a kira. Ammie batayi musu ba ta bada number Nenen ta da aka bata, kasancewar ta mata ɓoyo na musamman aka dace. Number dattijon ya amsa suka tafi, akan komi kenan zuwa gobe zasu ji.       Alhamdullah washe gari kuwa sai ga Nene da yaranta maza magidanta har biyu. Tana ganin Ammie ta gane jinintace. Itama Ammie na ganinta taga kamar mahaifiyarta ce tsaye a gabanta. Nan fa suka rungume juna aka hau koke-koke..     Wannan shine silar haɗuwar Nene da su Ammie. Bayan an sallamesu suka wuce gidanta. Yayinda Maanal data koma sanyi-sanyi bata magana, komai sai dai tabi mutane da ido ta cigaba da shan magani. Duk sati kuma anlkan kaita ganin likita. Ba kowa ke kaitan ba kuma sai Yazeed da baya nuna gajiyawa. Hakama mahaifinsa lokaci-lokaci yana zuwa duba jikin Maanal, dan Ammie dai Alhmdllh nata jikin da sauƙi. Dawowar su gidan Nene bai hana Yazeed da mahaifinsa cigaba da musu hidima ba, musamman ɗawainiyar asibitin Maanal dake fama da jiyya, duk da ba'a kwance take ba daka ganta kasan tana fama da jarabawar ciwo. A haka sukai kusan watanni tara, abubuwa suka fara dai-daita musu. Babban ɗan Nene yace yana son auren Ammie saboda halin matarsa ya ishesa. Amma mi sai rigima ta nema kaurewa. Ana cikin wannan halin ALLAH ya kawo dattijon arziƙi gidan. Wato Alhaji Usman Chalawa mahaifin Yazeed. Yazo domin duba su duk juma'a kamar yanda ya saba. Ganin rikicin dake faruwa babu wani ɓata lokaci ya ce shi yana son Ammie da aure. Dan ya fahimci lallai anzo wata gaɓa dasu Ammie zasu iya fara fuskantar ƙalubale a gidan. Shi kuma haka kawai tausayi bayin ALLAHn ke bashi, kodan shima ya ɗanɗani irin makamaciyar rayuwar a bayane oho. ALLAH sarki Ammie, dan kawai samuwar masalaha ta amincewa da Alhaji Usman Chalawa. Dan bata fatan raba ƙyaƙyƙyawar alaƙar dake tsakanin Nene da surukanta da ƴaƴanta. Sannan tana ma ƴaƴanta fatan ƙyaƙyƙyawar rayuwa. Ta kuma fahimci anan gidan Nene da wahala a dace da hakan dan a yanzu hakan ma Shahidah da Amaal suyar awara suke anan ƙofar gida dan rufawa kai a siri kasancewar suna kwaɗayin komawa karatunsu.       Alhaji Usman Chalawa dai da gasken yake. Dan sati guda kacal da yin wannan magana aka ɗaura aurensa da Ammie. Sati na sake zagayowa ta tare a gidansa. Tarewar data saka suka fahimci ashe ba ƙaramin mai kuɗi bane ba. Ga kuma matansa ƴan balaja'u musamman uwar gidan mahaifiyar Yazeed yaron kirki. Amma sai Ammie ta daure ta jure kodan yaranta su sami ƙyaƙyƙyawar rayuwa. Sun kuwa samu, dan su duka Alhaji Usman ya maida su makaranta. Har Maanal data ɗan fara samun lafiya kaɗan-kaɗan. Sai dai maimakon ss3 daya kamata ace zata shiga a yanzu sun maida ta ss1. Ruwan addu'a da wadda Ammie ke mata, da jan ta ajiki da ƴan uwanta keyi da wanda Daddy ke mata, da tattalinta da Yazeed yake duk da uwarsa bata so, itama kuma bata saki jikin da shi saboda wani abun kan tuno mata Ajwaad yasa Alhmdllh ta ɗan fara sakin jikinta. Duk da dai nan ɗin ma akwai ƙalubale daga matan gidan da yara, sai dai bai cika damun su ba musamman Maanal da a yanzu ta zama shiru-shiru. Miskila, mara son magana. Idan kaga murmushinta sai Ammie ko ƴan uwanta. Ta tattara hankalinta gaba ɗaya akan karatu da ibada. A haka ta kammala secondary, a Kuma lokacin Ammie ta sake haihuwa ta biyu a gidan Alhaji Usman Chalawa, kamar yanda na farko ya kasance namiji na biyun ma namiji ne, still a kuma lokacin akaima Shahidah da Amaal aure. Kuma dukansu Daddy ne ya zaɓa musu mazan. Bayan bikin Maanal ta fara jami'a itama anan Zariya. Kullum ake kaita a ɗakkota, dan driver na musamman Daddy ya ɗauka mata. Gefe ƴan uwanta na hidima da ita, Ammie da Nene na bata kulawa. Sai dai duk da canjawar komai akwai abubuwa da yawa har yanzu sun kasa canja kansu a gareta. Musamman wasu a cikin ɗabi'un da abaya ba nata ba. Kamar karatun English novels da abaya batayi sai Ajwaad, saka gilashi a ido da makamantansu da yawa da abaya duk ɗabi'un Ajwaad ne. Ammie na lura da ita, sai dai bata taɓa mata magana akan hakan ba, dan tasan sai a hankali Maanal ɗin zata manta komai. Sai kuma yanayin ciwonta ya taka rawar gani sosai na sauƙaƙa tanka matan akan irin hakan kodan gudun abinda zaije ya dawo.     Tana shekara ta biyu a jami'a Yazeed ya fito mata da ainahin abinda ke ransa game da ita. Bata wulaƙantashi ba, ba kuma ta amsheshi ba. Ta dai cigaba da girmamashi kamar yanda ta saba. Dan sosai take matuƙar ganin girmansa da kimarsa a cikin idanunta da zuciyarta. Da farko yaso ayi bikin ta cigaba da karatun a gidansa, sai uwarsa ta tada tujarar ƙin yarda. Haka akaita kai ruwa rana dai.        A haka cikin amincin UBANGIJI ta kammala karatunta, ta fito da sakamako mai ƙyau, bata wani jima ba ta wuce hidimar ƙasa a Jos, a can ne ta haɗu da Zulaiha da Aneesa da suma hidimar ƙasar ce ta kawosu Jos ɗin ƴan Kaduna ne. Nan fa suka ƙule ƙawance duk da bawani saki jiki take da su ba. Basu fi wata guda ba ta haɗu da RK, sunje sayya wani shago shima yazo, shine ya yarda atm card ɗinsa batare daya sani ba Maanal ta tsinta ta bashi. Wannan itace farkon haɗuwarsu kuma silar tushen alƙar dake a tsakaninsu yanzu. Duk da da farko bata kulashi amma yayta naci batare da nuna gajiyawa ba koda a fuskarsa.......       _________★     MUN DAWO LABARI🚪🏃🏃🏃🏃 Yanzun kam sai muga wane mai rabo ne da Maanal ɗin. AA Darma da a baya ya furta babu soyayya duk da ta'asar daya tafka?. Yazeed daya taka rawar gani a wata gaɓa ta rayuwarsu mai tsanani da wahala shi da mahaifinsa da dukiyarsu da ƙarfinsu da mutuncinsu?. RK daya tsinta dami a kala, ya kuma nuna juriya da haƙuri akan dukkan ja da Maanal ta dinga masa a ƙasa. Ya kuma taka tasa irin rawar shima a yanzu ko muce yake kan takawar. Ga tarihin Maanal da alaƙarta da AA ya sani, zai kasance akan bakansa ko shi zai janye yabar ma AA da Yazeed filin ne?. Da gaske AA ba son Manaal yake ba a wancan lokacin kamar yanda ya faɗa sai yanzun ne ya fara son nata kokuwa akwai wani AJIYA A DUHU ne daya kamata mu sani?.......✍️ _Abin fa da yawa, mudai je zuwa kawai🏃🏃🏃🏃🏃._ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖7️⃣5️⃣ ______________ Assalamu alaekum,Yan uwa barka da wannan lokaci, inde Kaya kikeso unigue Wanda bazakigannsu ajikin kowaba se yangayu toh kishiga group din mom safwan Muna turakaya ko Ina cikin amincin Allah Muna seda lace, atampa,shadda,voil,beil,sarka,kayan yara,takalmi ,jaka ,kayan yara, kayan kitchen,Kae mufa komae daruwankane Allah y bamu kasuwa me albarka nagode Ga inda zamu iya samun mu . 09064820534. Ga kuma link na group ɗin mu. https://chat.whatsapp.com/CuYcnxM1Z7VCYL5tqnyuL7 _____________ .........Daddy shine ya lallaɓa Maanal da su Shahidah fitowa wajen baƙin Giro. Gwaggo kakarsu, sai Babu mahaifinsu, sai Malam Aƙilu ƙani ga Baba Haruna. Wanda bayan barowar su Ammie Giro ya aure gwaggo.        Zama kawai su Maanal sukai batare da sun kalla kowa ba balle gaishesu. Sai da Daddy yay musu magana sannan suka gaishesu ciki-ciki, dan Maanal ma kam bakin kawai ta motsa. Baabu ne kawai ya amsa cike da zumuɗi idanunsa cike da ƙwalla yana kallon ƴaƴan nasa, farin cikin rayuwarsa. Ita kanta Ammie ɗin satar kallonta yake. Zuciyarsa na matuƙar rawa da ganin ɗunbin canjawar da tayi. Canjawar da a yanzu idan yace ya taɓa aurenta wani sai ya gallara masa maruka kafin ya ƙaryatashi. Dan shi duk ya rame ya lalace tsufa ya taso masa saboda ciwo. Ga zaman ƙauye da canjin rayuwa tamkar bai taɓa zama aji ba a rayuwarsa, ga fitinar yara guda biyu da ALLAH ya bashi tare da Sailu amaryarsa. Ɗansa namiji shalele ya zama fitinanne a garin Giro da kewaye, sai mace dake bimasa itama dai marabarta kaɗan da namijin..     Daddy ne ya katse shirun da gyaran murya. Kafin ya ɗaura da sallama. Duk suka amsa. Cigaba yay da faɗin, “Alhamdullahi da kasancewar mu anan, kafin komai zan fara da nasiha a garemu baki ɗaya musamman akan ku yarana. Ina roƙon ku kuyi haƙuri da koma minene zukatanku suke tunawa da suka faru a baya. Ba'a fushi da iyaye, ba kuma a ƙin su sai idan akan abinda zai zama saɓon ALLAH ne. Koma minene ya faru ya rigada ya farun ya wuce. To a barsa a ya wuce ɗin a tari gaba. Yau ga mahaifinku sunzo garemu da muhimmiyar magana kamar yanda suka faɗa, sai dai dama bamu kai ga tattaunata ba ALLAH ya kawo ku. Dama a nawa shirin shine na buƙaci ganinku a gobe idan ALLAH ya kaimu, sai kuma komai ya sauƙaƙa.” Sake maida hankalinsa yay ga su Babu, fuskarsa da murmushi ya cigaba da faɗin, “Inaga tunda ALLAH ya sauƙaƙa gasu sunzo kafin ma mu nemesu ya kamata mu tattauna ko”.        “Hakane”. Cewar Kawu Aƙilu yana gyara zama. Sai kuma cikin dakiyar murya ya cigaba da faɗin, “Kamar yanda ka faɗa abinda ya faru ya riga ya wuce hakane Alhaji, dan haka maganar tuna baya da anyi kaza ko anyi kaza babu zancen maimaita shi ko tada shi. Dama munzo nan ne akan batun ita Maanal, wanda yake neman aurenta yaje garemu a satin daya gabata kuma mun bashi. Saboda dalilan ganin shi ɗin mutumin  kirki ne da muke da tabbacin zai riƙeta da mutunci kamar yanda muka samu sauran ƴan uwanta a mutuncinsu.......”       Cikin mamaki da ruɗani Ammie da Nene da su Maanal duk suka kallesa. Yayinda Daddy ya kasa jurewa shima dan shi zatonsa haƙuri suka zo basu da neman yafiyar su Ammien akan abinda suka aikata musu a baya, ashe wata fitinar ce suka zo da ita kuma. “Me neman aurenta kuma? Wanene shi haka da mu anan bamu sanshi ba?”. Cewar Daddy da mamaki.            Wani irin ɗaure fuska gwaggo tayi, Babu zai yi magana ta hararesa. Cike da isa ta ce, “Sunansa Alhaji Bukar. Sanata ne babba a ƙasar nan, kuma mun bashi, munzo nan ne ma saboda mu tabbatar muku mun bashin sannan mu wuce da ita can Giro dan nan da sati biyu za'ayi biki kamar yanda ya buƙata”.       Tuni zufa ta gama wanke Daddy, ya dai daure da ƙyar ya maida dubansa ga Maanal da take ma su gwaggo wani irin shegen kallo, sai dai uffan batace ba. “Manaal” Daddy ya kirayi sunanta a hankali. Juyawa tai tana amsa masa.         “Waye kuma Alhaji Bukar?”.     “Daddy ban sanshi ba nikam, bana kuma buƙatar saninsa. Sai dai ina roƙonka cike da girmamawa ka faɗama waɗan nan mutanen su bar mana gida su koma inda suka fito. Idan ba hakaba wlhy wlhy wlhy sai na kawo musu human right.” sai kuma ta miƙe a hankali tana duban gwaggo da wani irin ƙasƙantaccen kallo. “Ke kuma idan kina buƙatar mutuncin furfurar kanki kiyi gaggawa tarkata komatsanki ku kama gabanku. Ashe kina da baki ko ido da kwallin kwaso waɗan nan ƙazaman ƙafafun naki zuwa garemu? Kin manta mu ba jininki bane? Kin manta a yawon tazubar uwarmu ta samo mu? Kin manta bazaku haɗa zuri'arku da lallatacciya mai ɗauke da cikin shege ba? Kin manta... Kin manta.... Da yawa. To karki yarda ki bari na tuna miki, dan tunawar na nufin shiga ukun ki, tun kina iya banbance su waye a gabanki ki koma inda kuka fito. Inba haka ba kuwa.....” ta saki wani murmushin da jinjina kanta tai wicewarta da karkaɗa ma gwaggo yatsa na tabbatarwa.       Harga ALLAH gwaggo ta matuƙar tsorata da yanayin Maanal. Eh tasan dama yarinyar tun tana ƙaramarta fitsararriya ce, amma bata san rashin kunyar tata har ya kai haka ba. Da ƙyar ta iya ƙarfafa zuciyarta ta maida dubanta akan Ammie. “Asiya ni ƴarki kema wannan ɗibar albarkar a gabanki kina jinta”.      Murmushi sosai Ammie tayi, kafin a karo na farko ta sanya idanunta a cikin na gwaggo. “Mi kuke son nace da ita Talle....”       “Talle?! Asiya ni kike kira da Talle?”. Gwaggo ta faɗa a zabure tana katse Ammie. Murmushin Ammien ta sake sakin mata, sai kuma ta ɗan laɓe baki, “Shi nasan sunanki, tunda shi na tashi nasan ana faɗa miki. Tabbas kamar yanda Maanal ta faɗa kuyi gaggawar barin gidan nan tunda mutuncinku, dan wlhy bazan hanata ɗaukar dukkan matakin datai niyya ba ita da ƴan uwanta. Tun farko ma da nasan abinda ya kawoku gidan nan kenan da bazaku ko zauna ba balle shigowa nan. Amma kunci arziƙin mahaifina ya fito ne daga ku, hakama mijin aurena daya ce na saurarenku, dan shi tuwo dai tuwo ne ba'a canja masa suna. Amma waɗan nan yaran baku da wani hurumi akansu, dan da bakinki kin tabbatar ma da duniya ba jinin ɗanki bane ba. Shima kuma ya tabbatar da hakan, idan duk kun manta maza kuje ku sake sabon tunani dan tuna hakan zai matuƙar taimaka muku. Idan kuma na sake ganin ƙafar ɗayanku a cikin gidan mijina na rantse da ALLAH sai kunyi dana sani da nadamar sani na. Yarinyata kuma nada mijin aure, kai koda bata da shi gara na jerata naita kallo matsayin kayan adon ɗaki da ace kune kuka zaɓa mata mijin aure........”        “Asia!”.     Daddy ya kirayi sunanta a hankali yana mai riƙo hannunta, ƙoƙarin fisgewa Ammie tayi idanunta na cikowa da hawaye, dan gaba ɗaya neman birkice musu take yi kamar ba Ammie Sarkin haƙuri ba, dole ya miƙe tare da jawota jikinsa kawai ya rungume. Murmushi Nene da ko a bata furta ba ta saki, hakama Shahidah da Amaal sai suka miƙe suna wata ƴar dariyar shaƙiyanci. Dan su kam ai ba sai sun ce komai ba, Auta ta gama komai ita da Ammie. Babu kam rawa jikinsa ya fara yi, da sauri ya duƙar da kansa ƙasa hawaye na cika masa ido. Yayinda gwaggo ta gama macewa a zaune ita da Kawu Aƙilu. Oho ko'a jikin Daddy, dama yayi hakan ne da gayya duk da sai da ya yaƙi kansa matuƙa saboda kunyar Nene. Kusan minti ɗaya tana a jikinsa kafin ya cirota a hankali ya zaunar da ita shima ya zauna a kusa da ita. Kallon su gwaggo yay babu ko kunyarsu ta sisi.          “Ina fatan basai mun cigaba da wata jayayya ba. Amma ni zan baku haƙuri, in sha ALLAHU kuma zamu zo gareku domin auren ita Maanal, dan kamar yanda mahaifiyarta ta sanar muku tana da mijin aurenta a hannu.”     Wani irin miƙewa Kawu Aƙilu yay a fusace yana kallon Daddy, “Alhaji munzo nan ne domin mutuntaka. Dan haka kada ka zubar da wannan darajar, kar kuma ka biyema sheɗaniyar can Asiya dan zamu iya yin komai a wannan karon kan yaran nan”.       Murmushi kawai Ammie tayi, hakama Daddy. Sai Nene ce a wannan karon ta furta, “To kudai yi a hankali”.     Harararta Kawu Aƙilu yayi, hakama gwaggo. Babu kam da har yanzu kansa ke'a ƙasa sai ya share hawaye. Cikin sanyin murya ya ce, “Gwaggo dama na ce muku abinda ake shirin yi kuskure ne, sannan mutumin nan wlhy bai dace da Maanal ba. Kada kuɗi su rufe muku idanu ku.....”       “Rufe min baki shashasha kawai sallamamme, anƙi a bari ɗin, mu da su kuma mu zuba ɗan halak ka fasa. Dalla tashi mu wuce”.       Komai Babu bai sake cewa ba ya miƙe. Haka suka fice yana waiwayen Ammie data ɗauke kanta gefe...... _______★     “Amma mutanen suna da ƙarfin hali gaskiya. Tab ɗi jan”.     Murmushi Daddy yayi da kallon Nene da tai maganar, sai kuma ya kauda cike da girmamawa ya ce, “Bayin kansu bane Nene kuɗi ne ke angiza su, amma in sha ALLAHU zan bincika wanene shi wannan Alhaji Bukar ɗin da suke faɗa. Karku wani damu da su in sha ALLAHU babu abinda zai faru. Ina ganin kuma kawai a haɗe auren nan na Maanal itama shine kawai masalaha. In ba hakaba zasu iya zagayewa su ɗaura mata aure da mutum nan fa”.         “Eh kaima kazo da magana mai muhimmanci, amma suma sun san basu isa yin hakan ba....”      “Idan har aka ɗaurama Maanal aure dan saboda su ma ai munji tsoron su kenan. Ka barsu suyi duk abinda suke tunanin zasu iya. Danni ma so nake suyi ɗin domin allura ta tono garma. Dan haka ina roƙonka Daddyn Hameed komai ayisa kamar yanda aka tsara tun farko. Yanda aka shirya bikin nan da farin ciki bana son a ɓata ma Yazeed shi dan ALLAH”.     Ɗan jimmm Daddy yay yana kallonta. Sai kuma can ya saki ajiyar zuciya da jinjina kansa. “Shike nan na fahimceki. ALLAH yasa haka shine mafi alkairi”.    A tare suka amsa da amine... Bayan fitar Daddy Nene ta kalla Ammie. “Asiya miyyasa kikace masa haka. Kamar bazai ji daɗi ba, zai kuma ga da gaske baƙya son wannan haɗin ne”.        “Nene sam ba so bane bana yi, bana son a ɓatama Yazeed farin cikinsa. Hakama Mahaifiyarsa ina son a bata damar masa auren gata kamar yanda ta shirya. Wlhy ban taɓa baƙin ciki ko fatan kasancewar Maanal matar Yazeed ba. Shi ɗin mutumin kirki ne. Amma ina fargabar ta tsinta kanta a irin rayuwar dana tsinta kaina a shekarun baya. Wadda gashi nan har yanzu tana bibiyata. Yanzu ashe Nene har mutanen nan nada ido da kwallin zuwa su nuna suna da alaƙa da yaran nan?....” hawaye suka shiga zarya a fuskarta..... ______________★         “Sir! An tabbatar min yau bata shigo aiki ba kwata-kwata”.      AS ne da furucin cike da girmamawa. Fin minti ɗaya kafin AA ya ɗago idanunsa daga rubutun da yake yi, akan AS ya zubasu. Hakan yasa AS saurin rissinar da nashi ƙasa. Shima janyewar yayi ya maida ga rubutun da yake yi. Kafin da ƙyar ya furta, “Tayi wani reporting ne akan rashin zuwan nata?”.       “Gaskiya bana jin hakan, amma zan sake bincikawa.”     Komai baice ba. Hakan ya saka AS fita sum-suma ransa fal mamakin boss ɗin nasa yau. Anya kuwa babu wata alaƙa tsakaninsa da yarinyar nan? Koda yake ɗan uwansa ne ya kawota companyn ai, maybe ƴar uwarsu ce. Da wannan tunanin ya kai a kujerarsa. Sannan ya jawo phone ya shiga neman shugaban department ɗin su Maanal.     A ɓangaren AA kam tunda AS ɗinsa ya fita sai ya samu kansa da kasa cigaba da fa aikin nasa, zuciyarsa ce ke ta faman kai-kawo. Karfa yarinyar nan da gaske take tabar aiki? Kai ina bata isa ba. (To wane ƙarfi gareka akan hakan?) Wani sashe na zuciyarsa ya ayyana. Fuska ya yamutse, sai kuma ya saki siririn tsaki yana kai hannunsa saman goshinsa ya murza. Fin mintuna biyu sannan ya miƙe. Jikin ƙaton window ɗin office ɗin nasa ya nufa, ya zubama waje ido na fin mintuna biyar. Sai kuma ya kalla agogon hannunsa mai shegen ƙyau. Wajen zamansa ya koma, ya ɗauka wayarsa dake fes-fes kamar ba'a amfani da ita yau da kullum ya shiga sarrafawa. Koda yay kiran number ɗin da yake buƙata sai ya ajiyeta ya ɗauka Bluetooth ɗinsa ya manna a kunnen...        “Assalamu alaikum Son”.   Daga can RK yay sallama. Cikin taɓe baki AA ya amsa masa, sai kuma ciki-ciki ya ce, “Ka nema ɗanka tun dare bai maka ba”.      Dariya RK ya sanya da faɗin, “Sai dai ƙari dan na riga na samu gaka nan. Lafiya kake mun kiran tsakar rana?”.        Ɗan jimm AA yay, sai kuma ya sake tsuke fuska kamar yana gaban RK ɗinne kafin ya furta, “Miya hana yarinyar nan zuwa aiki yau?”.      “Yarinya kuma? Wace kenan?”.   Kamar AA bazai amsa ba, sai kuma dai a daƙile ya ce, “Wadda ka kawo”.      “Oh Maanal wai? Am sorry laifina ne wlhy, naso shigowa na nema mata alfarma sai aikin gaggawa ya sameni, taje Kaduna ne Mamanta babu lafiya. Amma yanzu nan munyi waya ta tabbatar min jikin da sauƙi ma. Gobe ma zasu dawo”..      Ɓoyayyar ajiyar zuciya AA ya saki, a fili kam sai ya hau faɗa. Wai dan mi ita bazata zo da kanta ta sanar ba. Ai ita suka ɗauka aiki ba shi ba. Miye-miye ta inda yake shiga bata nan yake fita ba. Ko tanka masa RK bai sake yi ba ya yanke wayarsa........✍️      ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖7️⃣6️⃣ ______________ ........Wannan yanke waya ya sake ƙona ran AA matuƙa. Dama RK ɗin bai san yanda yake jin zafinsa bane. Aiko sai ya sake cika yay fam. Ƙarshe ya kira Oum da ƙorafi, sai masifa yake yi ita har ma ta kasa fahimtar faɗan. Sai da yay mai isarsa cike da kulawa ta ce, “Auta ɗauka ruwa kasha. Ka kuma ja numfashinka sau uku. Idan a zaune kake ka kwanta kai shiru na kamar mintuna biyar kaji ɗan albarka”.       Karan farko ya saki ajiyar zuciya. Sai kuma ya kashe wayar ya ɗauka ruwan yasha kamar yanda tace. Ya kuma ja numfashin da fesarwa sannan ya koma rukunin kujerun office ɗin ya kwanta a 3 sitter ya lumshe idanunsa. Fin mintina ashirin yana a wajen sai da akai kiran sallar zuhur sannan ya miƙe.....     ★A ɓangaren Oum kam, wayar RK ta kira. Bayan sun gaisa ta tambayesa mike faruwa shi da Autan ta. Kansa kawai ya girgiza bai ɓoye mata komai ba ya sanar mata. Sannan ya ɗora da faɗin, “Karki wani damu da shi, kin san masifa bata masa wahala yanzu. Saboda aikin kamfaninsa sai taƙi zuwa taga mahaifiyarta.”         Murmushi kawai Oum tai da faɗin, “ALLAH ya ƙyauta. Barni da shi idan ya dawo zamuyi magana. Kaima kuma ALLAH ka daina fusata min yaro”.      Ƴar dariya yay daga can shima. “Ya daina dai fusata kanshi Aunty Babba. Ko kuma ki masa aure koya rage wannan zafin ran mara amfani. Ni bara naje inada theater ne yanzu”.      Koda ya ajiye wayar sai ya saki murmushi. A fili ya furta, “Ajwaad kenan, ai kayi sakaci, in dai nine babu gudu babu ja da baya akan Maanal. Komai rintsi sai na mallaketa dan ina sonta. Sanin ainahin alaƙarku a yanzu bazai sa na janye ba tunda da bakinka ka furta ba sonta kake ba ba wani ya matseka ba. In sha ALLAHU a ƙarhen watan nan za'aje nema min aurenta sai dai koma mizai faru ya faru”. Ya ƙare zancen da murmushi....      Eh lallai Uncle RK namu ka shirya kenan😂👍. Ina bayanka walle🏃🏃🏃 _______________★          “Ammie mufa munce miki muna nan har biki”.     “Ban yarda ba, kowacce ta koma ɗakin mijinta ranar juma'a sai ku dawo. Ko kun manta duk kuna aiki? Kuma kun san zamanku a gidan nan bazai haifar da ɗa mai ido ba. Musamman Maanal. Idan kuma so kuke ku ɗaga min hankali itama a birkitata to”.      Da sauri Shahidah ta ce, “A'a kiyi haƙuri Ammie, zamu tafin anjima in sha ALLAHU”.            Badan su Shahidah sun so ba suka shiryo a ranar suka dawo Abuja. Dan sam Ammie taƙi yarda su sake tattauna batun su gwaggo. Da sun ɗakko maganar sai ta zame. Gashi ma daga ƙarshe ta korosu. Kuma har so sukai suyi mata maganar su Oum. Amma yaya zasuyi, farin cikinta shine nasu.          Washe gari dole su duka sukai shirin komawa kan ayyukansu. Duk da dai da farko Maanal ta turza akan rashin komawa wajen nata aikin. Sai da Shahidah ta buɗe mata wuta da tabbatar mata zata haɗata da Ammie sannan ta shirya rai a ɓace. Shahidahn ce ta sauketa sannan ta nufi nata wajen aikin. Shigowar Maanal ɗin dai-dai da fitowar AA daga mota hannunsa akan kunne ya manna waya alamar magana yake. A kanta ya fara sauke idanunsa dake cikin gilashi, cak ya samu kansa da tsayawa, yayinda ita kuma datai kamar bata ganshi ba tai wucewarta. Idanu ya lumshe a hankali tare da buɗewa a lokaci guda. Sai kawai ya miƙama AS wayarsa dan sam ba fahimtar mi'ake cewama daga can ɗin yake ba....      A reseption suka sameta tsaye ita da Yaqub suna signing. Nan ɗin ma tamkar bata gansa ba ta wani irin ɗauke ido tana sakarma Yaqub wani shegen murmushi daya sanya zuciyar AA ɗin neman kamawa da wuta. Dan Yaqub ɗin na gaishesa ma ko kulashi baiyi ba ya wuce fuu. Hakama sauran mutane da wasu a ma'aikatan dake wajen domin yin signing ɗin bai kula gaisuwar kowa ba. AS na biye da shi da drivern sa dake ɗauke da basket alamar abinci ne a ciki. Ƙus-ƙus ma'aikatan suka fara na shigowar boss a fusace yau. Maanal dai batace uffan ba, batama nuna tasan mike faruwa ba. Koda suka bar wajen Yaqub ya maimaita maganar shima bata kulashi ba. Sai dai me suna zama sai ga waya wai ana nemanta a office ɗin CEO. Jitai kamar tace bazataje ba, amma dai ta dake ta miƙe tana sanarma Yaqub da zasuyi wani aiki tare cewar tana zuwa. Da kallo su Zaharadeen suka bita bakunansu cike da gulma. Dama tun shigowarsu ita da Yaqub ɗin suke binsu da kallon gulma. Ita kuma bata basu fuska ba bayan gaisuwa tai zamanta bata ko kula tambayar da suke mata na rashin zuwa aiki jiya ba da sukai...        Bayan AS ya mata iso yace ta shiga. Batako kallesa ba ta tura kai cikin Office ɗin fuskarta a matuƙar ɗaure. A zaune gogan nata yake saman 1 setter dake a rukunin kujerun hutawar office ɗin. A saman Centre table ɗin abinci ne da alama shi yay zaman ci a wajen. Dan sanda ta shigo ma yana ƙoƙarin zuba kunun gyaɗa ne dake a wani kyakkyawan ƙaramin flaks. Yanda ta turo ƙofar babu neman izini da tsaiwar da tai daga jikin ƙofar baisa ya motsa ba ko kallon inda take. Hidimar zuba abincinsa ya cigaba da yi hankali kwance. Sai da ya kai dankali har kusan sau uku bakinsa tare da shan kununsa a nutse sannan ta tako cike da takaici inda yake.     A ɗan zafafe ta ce, “Gani”.   Nan ɗin ma bai kulata ba, sai da ya gama shan ƙamshinsa sannan ya ɗan dubeta a karo na farko. Babu alamar wasa ko rangwame a fuskarsa. Kusan kallon sakan goma sannan ya janye ya maida ga abincinsa ya cigaba da ci. Sai da ya sake jan wani minti ɗayan kafin a daƙile, a kuma kausashe ya furta, “Miye haɗinki da wannan yaron?”.       Ji Maanal tayi kamar ta danƙara masa ashariya. Amma sai ta danne cike da rainin wayo ta furta, “Soyayya”.       Sosai ya ɗago kam ya kalleta yanzu. Maƙoshinsa na wani kai-kawo a wuyansa, sai kuma ya janye idanun nasa da wani irin slowly daga kanta. “Hummm” ya faɗa kawai. Daga haka bai sake cewa komai ba ya cigaba da cin abincinsa. Takaici ya sata juyawa ta nufi ƙofa da nufin ficewarta. Sai dai me tana taɓawa ta jita gam alamar ta rufe kenan. Ta fahimci yana sarrafa kofar da remote ne, juyowa tai ranta a ɓace ta kallesa. Ganin abincinsa kawai yake ci kamar bai san da ita ba yasa ta datse lips ɗinta da ƙarfi. Da alama mutumin nan so yake sai sun raba hali a bainar nasi cikin ma'aikatansa kenan. A zahiri kam sai ta tako ta dawo inda yake. Batare data tanka masa ba ta fara dube-duben gefensa. Can ko ta hango abinda take nema a saman Centre table ɗin gab da plate ɗin abincinsa. Sai da tama remote ɗin kallon kusan minti ɗaya sannan kanta tsaye ta nufesa, duk da yanda zuciyarta ke bugawa da sauri-sauri sakamakon kasancewarsu gab da juna haka ta dake takai hannu zata ɗauka remote ɗin. Sai da ta ɗauka zata miƙe daga duƙowar da tai kawai ya saka mata ƙafa sai gata a ƙasa. Remote ɗin yay sama saboda firgitar da tai, shiko ya sa hannu ya cafesa. Yayinda ita kuma ta dafe ƙugunta tana mai datse lips ɗinta da ƙarfi saboda azabar data ratsata. Harda sakin ƴar ƙara.       Duk da har cikin ransa yaji zafin da tajin shima amma sai ya maze baiko nuna a fuska ba. Kofin kununsa ya ɗauka ya ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya kawai ya zuba mata manyan fararen idanunsa dake cikin gilashi. Mus-mus take da baki alamar ƙunƙuni ga hawaye na zuba, shi sai abin ma ya so bashi dariya amma ya dake. Indai rashin kunya ce ai yasan ta iya fiye da kowa, kura ce kawai tayi lafiya. Harara ta zuba masa da suka haɗa ido. Sai ya ɗan waro idanunsa waje da faɗin, “Ni kike ma harara?”.         “Anyi ɗin, kuma ALLAH zai saka min karya nin da kai”.      “Tunda bakinki bai iya daina tsiwa yanzu ma na fara karyaki ai. Ni tsoro ma nake kada ki haifa min fitunannin yara irinki”.     “ALLAH ya kiyaye, ka nema mai haifa maka ƴaƴanka can. Kuma duk zaluncin da kaimin sai na haɗaka da Oum”.           “Maza kar ɗan ƙuda ya rigaki”. Ya faɗa yana miƙewa a wajen. Can ya koma saman office chair ɗinsa. Hankalinsa kwance ya fara aikinsa. Sai kawai Maanal ta samu kanta da dakin hawayen da take faman riƙewa suka zubo. Hannu tasa ta share su, sannan ta miƙe tana ɗingishi ta nufo inda yake. Daga ɗan nesa da shi kaɗan ta tsaya, muryarta na ɗan rawa ta ce, “Dan ALLAH ka buɗe min ƙofa na tafi, kada mutane su fara min kallon wani abu a companyn nan. Bana son abinda zai zubar min da mutuncina.”        Tsohon sakanni bai kulata ba, bai kuma tanka mata ba. Sai da ya mula dan kansa batare da ya kalletan ba dai ya tura mata wasu takardu. Hankalinsa ya sake maidawa a computer ɗin saman desk ɗin cike da dakewa ya ce, “Ki zauna kiyi signing a cikinsu”.       “Na minene?”.   “Cinikin kanki”. Baki ta tura, cikin ƙunƙuni ta ce, “Kaina yafi ƙarfin ciniki ai”. Bai kulata ba, sai kan waya daya ɗauka ya kai kunnesa. Ana ɗagawa ya furta, “Turo min Kayende”. Daga haka ya ajiye kan wayar. Sai a lokacin Maanal takai zaune a ɗaya daga cikin visitor chairs ɗin gaban desk ɗin nashi. Dai-dai nan akai knocking, ya bada iznin shigowa. A kaikaice Maanal ta hararesa, sai kuma ta ɗauka ɗaya daga cikin tarin ƙyawawan pens ɗinsa dake cikin wani kyakkyawan abu. Tana jin wanda ya shigo ɗin yana gaishesa, a taƙaice ya amsa masa, sai kuma cikin bada umarni yace masa ya kwashe wannan kayan. Cike da girmamawa ya amsa masa, ya koma wajen kayan ya fara tattarewa. Ita dai takardun take dubawa, dan tafi son sanin na minene kafin ta sanya hannun. Amma sai bata fahimci wani abun kirki ba yanda take so. Ficewar kayende ya bata damar faɗin, “Ni ban fahimci komai anan ba”.          Ƙin tanka mata yay duk da sarai ya jita, harta fidda rai ma sai kuma a daƙile ya ce, “Zaki tsaya neman sanin na minene ɗin ne ko zakiyi abinda nace”.     Baki ta tura gaba, sai kuma ta shiga ƙunƙuni tana saka hannun. Haka ta dinga binsu ɗaya bayan ɗaya tana signing. Fin mintina goma sannan ta kammala. Gabansa ta turasu batare da tayi magana ba. Shima baice komai ba ya ɗauka ya dudduba. Ganin tayi duk yanda yake buƙata sannan shima yay nasa saka hannun a inda duk ya dace ya sake tura mata.         “Ki kaisu office ɗin CMO. Wannan yaron kuma idan na sake ganinki da shi sai ya bar companyn nan”.     Cike da takaici take kallonsa, har tana jin ma ta kasa cewa komai. Sai da ƙyar ta iya furta, “Kana nufin korarsa zakai? Ka rabashi da hanyar cin abincinsa? To ai saika koremu tare ni da shi”.     Ƙin tanka mata yay, hakan yasa wani irin haushi da takaici suka sake baibayeta. Ta jima tsaye tana ƙoƙarin haɗa abinda zatace masa akai knocking ɗin ƙofar. Tamkar ya manta da ita a office ɗin ya bada izinin shigowa. Director Mustapha ne. Sai da ya ƙare mata kallo sannan ya ƙarasa shigowa ciki. Batako gaida shi ba ta fice fuuuu. Sai ya samu kansa da binta da kallo. Dukan desk AA yay da ƙarfi, a ɗan rikice Director Mustapha ya ce, “I'm sorry Sir”. Yana nutsuwa. Sai kuma ya ƙaraso ya gaishesa. Bai amsa masa ba, sai ma wani banzan kallo da yake binsa da shi. Sosai Director Mustapha ya sake nutsuwa. A ƙasan ransa yana sake jin tabbacin lallai akwai wani abu tsakanin oga da yarinyar nan kam. A zahiri kuwa sai ya sake neman afuwa kansa a ƙasa. Siririn tsaki AA yay da bashi izinin zama. Haƙurin dai ya sake basa sannan ya kai zaunen.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖7️⃣7️⃣ ______________ ........Maanal bata wani daɗe a office ɗin CMO ba ya sallameta. Dan nan ɗin ma cike-ciken wasu takardun tayi yay mata ƴan tambayoyi ya sallameta. Koda ta koma nasu Office ɗin bata kula kowa ba ta zauna. Tana lura da da kallon ƙurillar da su Deeni ke mata. A haka lokacin salla yayi. Saita samu kanta da saurin fita kafin ma Yaqub yace zasu fita tare. Ana idar da sallar ma wuff ta koma office, badan tsoron AA ba, sai don bata son zama silar yankewar hanyar cin abincin kowa. Sai dai bata daɗe da shigowa ba Yaqub ɗin ya shigo. Ajiyar zuciya ya ɗan sauke da faɗin, “Oh ashe kin dawo, ina can ina nemanki. Kina lafiya kuwa yau?”.      “Lafiya Lau nake Yaqub, wannan aikin da Director Steven ya sakani tun last week nake son kammalawa.”      Cikin gamsuwa ya ce, “Okay haka nada ƙyau. Bari naje kitchen tunda ke nasan ba zuwa kike ba”.    Kanta kawai ta jinjina masa. Ya fice ita kuma ta cigaba da aikinta. Sai dai a ƙasan ranta tausayi Yaqub ke bata. Sam bai da damuwa. Ga nutsuwa da rashin son hayaniya. Gashi ya matuƙar sanin aikinsa dan ita kanta tana ƙaruwa sosai da mu'amularsu ta fanin aikin. Amma ga wannan ɗan balaja'un na neman sanya ma alaƙar tasu ido da ƙahon zuƙa..... ___________★               “Amma Baba sai kace ƴar nan bakune kuka haifeta ba. Kuna da damar amsheta fa a hannun Alhaji Usman Chalawa. Amma kun zauna yana muku gadara. Nasan mutumin nan tamkar yunwar cikina, ɗan zafin kai ne, dan na tabbatar shine ya sakasu yi muku wannan rashin mutuncin ma har mahaifiyar tasu”.        Cikin rawar baki Kawu Aƙilu ya shiga bama Sen... Bukar haƙuri. Tsabar zubar da mutunci harda duƙawa yana sake maimaita masa ya kwantar da hankalinsa, in dai Maanal ce fa kamar ya samu. Dan bata da miji sai shi. Hakama gwaggo hakuri take bashi. Babu ne dai baice komai ba, dan shi hankalinsa ma baya a kansu sam. Baima san mi suke tattaunawar ba. Cikin ƙara tsimewa Sen.. Bukar ya ce, “Shike nan zan ƙara muku lokaci, idan kuma kuɗin auren dana baku ne yay kaɗan zan ƙara ninkasu. Dan gaskiya ina buƙatar auren yarinyar nan kusa kaɗan. Saboda da ita nake son shiga gidan gwamnati dazan fito takarar gwamnan jihar mu ne”.      Wani irin washe baki Kawu Aƙilu yayi shida gwaggo. Cikin sake gurfana ya ce, “Kayyasa Masha ALLAH, muna murna, muna kuma fatan alkairi. Batun wagga ɗiya kuwa Manalu karma komai ya dameka. Ka bamu kwana kaɗan zamu gama da komai da komai”.         Gwaggo ma cike da zumuɗi ta shiga jera masa addu'a tana zungurin Babu dake gefenta. Amma ko gezau yayi matuƙar nisa a tunani. Miƙewa Sen.. Bukar yay yanama yaronsa Rabilu umarnin basu jakar gabansa. Sheƙeƙe ya kallesu yana faɗin, “Ga ƙarin kuɗi nan za'a kaiku airport yanzu domin komawa gida. Nan da sati uku zuwa huɗu naji daddaɗan labari. Dan zan yi tafiya ne ma zuwa kasar waje shiyyasa nace sati huɗun. Kafin dai na dawo kun kammala da komai da komai yazama matata kawai nake jira”.        Nan ma sake gurfana sukai suna jera godiya da tabbatar masa an gama. Abin nasu ma har ya so bama Rabilu mamaki da takaici, irin wannan zubar da mutunci haka, amma dai ya gimtse. Bayan fitar ogan nasa yace su tashi dan shine zai kaisu airport ɗin, tunda dama dai shine ya ɗakkosu daga gida, yanzu ma shine zai maida su...       Wannan kaɗan ne daga Sen... Bukar in har yana neman aure. Sam baya ƙyashin kashe kuɗi ga dangin yarinya da ita kanta yarinyar. Maƙalau gwaggo ta kama jaka ta matse a hijjabinta. Kawu Aƙilu naso ta bashi amma ta hana ta haɗe gabas da yamma. Shi ko Babu sai da ma suka taɓashi ya dawo hankalinsa. Haka kuma ya miƙe ya bisu kawai kamar wanda baya gane komai...... ____________★          A makare yanzu kam ta fito sallar la'asar saboda meeting da sukayi da Director Mustapha gaba ɗayansu Junior Watch Designers na department ɗinsu akan wani ƙaramin project. Kasancewarta ita kaɗai mace sai da ta bari duk suka gama fitowa sannan ta fito daga conference room ɗin. Gudu-gudu sauri-sauri ta isa massallacin, da sauri ta nufi wajen alwala. Kafin ta kammala har an kai raka'a ta farko. Cikin hanzari ta shiga naɗa veil ɗin abayarta da iska ke neman kwashewa. Kamar zatai kuka ta samu da ƙyar dai ya zauna. Juyowar da zatai dan barin wajen ta hango AA dake ƙoƙarin fitowa a mota alamar daga wani waje yake. Yanda ya zuboma wajen ido ya bata tabbacin ya jima yana kallonta. Ɗauke idanunta tai kamar bata ganshi ba tai saurin faɗawa cikin massallacin.       Koda aka idar kasancewar bata samu sallar duka ba tana a cikin ƴan karshen fitowa. Kusan duk an wuce kitchen, dan haka ta nufi komawa ciki ita dai kam. Dan har yanzu zuciyarta bata ji zata taɓa cin abincin Companyn ba da ake dafawa.          “Sister Maanal”.    Muryar AS ta ratsa kunnenta daga bayanta kaɗan. Juyowa tayi, sai dai bata amsa masa ba har ya ƙaraso. Fuskarsa da murmushi ya furta, “Barka da rana, dama boss ne yace a kiraki”.         Idanu ta zuba masa sosai. Sai dai fuskarta harta canja. Kamar zatai magana sai kuma ta fasa ganin mutane a wajen, ta jinjina masa kai kawai. Shima bai sake cewa komai ba yay gaba a ransa yana sake jinjina miskilancin ta. Ganin sun nufi hanyar gate kamar zata tsaya sai kuma ta hango motar AA ɗin a can waje gefen titi. Mita take a zuciyarta kiran mi yake mata kuma a waje, itafa idan yace zai cigaba da takurama rayuwarta ALLAH zata fiddo masa kalarta, ya bar ganin tana wannan sauke kan bata son kowa a ma'aikatansa ya fahimci tana da wata alaƙa ta ɓoye ko zahiri ne da shi shiyyasa. Da wannan ƙunƙunin ta ƙaraso. Sai dai ta dogare a waje, yayinda shi kuma yaƙi sauke gilashin motar. Sai da AS ya ɗan masa knocking sannan, a hakan ma bai buɗe kai tsaye ba sai da yaja wasu sakanni. Saukar gilashin ya bata damar ganinsa zaune a mazaunin driver dan gilashin tinted ne. Hannu kawai ya ɗagama AS alamar yaje. Cike da girmamawa ya ce, “Okay sir a dawo lafiya.” daga haka yabar wajen ya koma cikin Company. Shiru ita da shi babu wanda ya tanka, amma shi kallonta yake ta cikin mirror ɗin gefensa. Yanda take ta faman ɓata fuska da motsa lips alamar ƙunƙuni take masa ya sashi lumshe oily ayes ɗinsa yana ɗan sakin miskilin murmushin da iya lips ɗin kawai ya motsa. Karaf kuwa sai a idon Maanal data matso inda yake a kufule. Gimtse fuskar yayi, itama ta sake gimtse tatan tana harararsa. Cike da takaicin murmushi data gani yanayi tabbacin da ita yake tunda kallonta ta kamashi yana yi, “Gani”.       “Na ganki ai”.    Ya faɗa cikin halin ko'in kula idonsa a kanta. Janye nata idanun tai daga kansa tana jin kamar ta balbalesa da masifa. Amma dai ta daure kodan securitys da zasu iya hangosu. Ita kuma bata buƙatar hakan. Kamar ya karanci abinda take tattaunawa da zuciyar tata ya miƙa hannu ya buɗe murfin side ɗin mai zaman banza tare da faɗin, “Get in”. Sosai yanzu kam ta zuba masa idanu babu ko ɗar, shima ya ko zuba mata nasa cikin tsakkiyar natan. Jitai tsigar jikinta na tashi amma tai jarumtar riƙe kanta da ƙyar. A dake ta ce, “Ni aiki nazo ba yawon banza ba”.         “Niko kinga yawon banzan na fito”. Ya bata amsa a daƙile. Kafin ta samu damar bashi amsa ya cigaba da faɗin, “Kina ɓatan lokaci, idan kuma kika bari na fito ALLAH da kaina zan ɗaukeki na sakaki”.       Tasan zai iya fiye ma da abinda ya faɗa. Wanda ya iya keta mata haddi a cikin gidansu me kuma ya rage. Garama ta shiga tunkan ya kunyata ta a bainar nasi. Sai dai bata shiga kai tsayen ba, sai da ta gama masa ƙunƙuni da hararar motar sannan ta zagaya ta shiga. Ƙin rufe murfin tayi, dan haka ya ranƙwafo tare da kai hannu zai rufo. Hakan ya basu matsanancin kusancin da har take jin kamar zai rungumota ne. Ga ƙamshin turarensa ya wani buɗeta tamkar yanzunne yake fesawa. Samun kanta tai da rawar jiki, sai kuma a zabure takai hannu ta jawo ƙofar ta rufe bam kafin shi yayi. Shiru yay yana kallon ƙofar batare daya janye jikinsa ba. Jin numfashinta kamar yana fisga da ƙarfi, ga sassanyan ƙamshin khumran data saka da wanda tai turaren kayanta na wani saukar masa da kasala. A hankali ya maida idanunsa kanta, ya zubama ƙyaƙyƙyawar cute fuskarta manyan idanunsa. Idanunta a rumtse suke, hakama lips ɗinta sai ɗan motsi yake, ga fuska ta takure kamar zata saki kuka. Idanunsa dake kallon lips ɗin ya janye cikin slow motion yana mai haɗiyar wani busashen yawu daya tokare masa maƙoshi. Kamar wanda aka kwaɗama guduma a ka ya janyo belt ɗin gefenta kawai yaja jikinsa baya ya maƙala ta gefen tsakkiyarsu. Da mugun ƙarfi tako saki numfashinta har sai da ya sake kallonta, sai kuma ya girgiza kansa a hankali yana mai janye idanun tare da lumshesu, sake buɗesu yay a saman titi yana kunna motar. A hankali taji sun fara tafiya, dan haka ta sake sakin sauran numfashin data riƙe tare da buɗe idanunta. Ƙin kallon sashen da yake tai, sai ma ƙoƙarin haɗiye hawayen da suka cika mata idanu take yi. Dan haka kawai yanayin nasu ya tuna mata wani abu. Shiru motar ta ɗauka sai sanyin ac dake ratsasu, dan ko rediyo bai kunna ba. Sai wayarsa da aketa faman kira tana haske da ɗan motsi kawai, bai kuma kula ba kamar ma bai ji ana jera masa kiraye-kirayen ba. Tafiya ba wata mai nisa ba duk da a hankali yake tafiyar suka iso wani katafaren wajen Saloon mai shegen ƙyau. Kallon wajen kawai Maanal take yi, yayinda shi kuma ya samu waje yay parking. Sai da ya kashe motar gaba ɗaya sannan ya juyo yana kallonta. Muryar san nan ƙasa-ƙasa kamar abin dole ya furta, “Muje”.        Itama kallonsa tai a karo na farko ta ce, “Ina ɗin?”.       “Ina kikaga mun zo?”.     Ya faɗa cikin tsatstsareta da kaifafan idanunsa. Fuska ta ɓata sosai, bakinta a sama ta ce, “Ni mizanyi anan wajen? Haka kawai ka ɗakkoni daga wajen aiki ka kawoni nan......” sai kuma ta cigaba da magana cikin ƙunƙunin da baya ji.        “Kar dai ki zagen mara kunya kawai”.      “Toni ka maida ni inda ka ɗakkoni mana. Na gaya maka ina buƙatar zuwa nan wajen ne. Haka kawai dan neman mutum dai da faɗa.....”            “Ai ba sai kina buƙata ba, tunda ni ina buƙata ya wadatar. Ragguwan banza kita yawo da gashi a tsefe kina buɗema mutane suna gani. Oya fita kona ɗaukeki da kaina har ciki wlhy”.       Sosai idanunta suka kawo hawaye, dan har yanzu Maanal ba ƙaunar kitso take ba, ta gwammace a wanke a gyara mata kawai. Sai gashi ta marairaice fuska kamar ba ita ke shirin masa tsiwa ba. Idanunsa ya kauda daga kallonta yama buɗe motar ya fita alamar bazai ma saurareta ba. Sake tashi hankalinta yay, tana tunanin fita ta gudu taji an buɗe side ɗin da take. Da sauri ta dubesa, sai ga hawayen da take riƙewar na silmiyowa da gudu. Baki ya taɓe, tare da fara jan hannun jacket suit ɗinsa sama. Hakan na nufin shirin ɗaukar tata yake kenan da gaske. Ai da sauri ta fito tana harararsa da share hawayen dake cigaba da sakko mata. Murmushi yay abinsa cike da mugunta yay ma bayanta ƙaramin gwalo, sai kuma ya maida fuskarsa ya gimtse ya rufe murfin data bar masa a buɗe kamar baiyi komai ba. Haka ya tasata gaba cikin wajen tana shartar hawaye. Dai-dai nan Nurry da ƙawarta ke fitowa a kusa da wajen saloon ɗin daya kasance bakery. Cak tai wani irin tsayawa zuciyarta na bugawa da sauri, tuni ta saki ledojin hannunta tana mai bin AA da Maanal dake shigewa cikin saloon ɗin da kallo. Itama dai ƙawar tata AA Darma ɗin take bi da kallo tana haɗiyar yawu, sai da suka gama shigewa ta maido dubanta kan Nurry ɗin da faɗin, “Kanbu Nurry AA ɗinki ne fa da mace? Miya kawosa nan wajen saloon ɗin mata to ma?”.        Nurry bata tanka mata ba, sai nufar wajen saloon ɗin da tai a sukwane jikinta har rawa yake tana neman faɗuwa. Ai babu shiri itama ƙawarta ta kwashi ledojin data zubar ɗin tabi bayanta da sassarfa dan gara dai ayi komai akan idonta........✍️     _😂Tofa AA Darma kana cikin alheri yau da alama gaskiya 🥱😆🏃._ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖7️⃣8️⃣ ______________ .......Shigowar Nurry dai-dai AA na jama Maanal kujerar zama ita kuma fuskarta rufe da veil ɗinta tana share hawaye. Yayinda matan dake a wajen sun zo ai musu gyara suka musu caaa da idanu. Ma'aikatan kuwa har rige-rigen tambayarsa suke yi abinda za'ayi mata. Fuskarsa babu ɗigon fara'a, bai kuma kalla kowa ba tunda ya shigo ya buɗe baki da ƙyar ya ce, “A duba mata kan idan yayi datti a wanke, sai ai kitso”.      Da sauri Maanal ta janye veil ɗin daga fuskarta tana sake ɓarke masa da kukan da kowa kema kallon na shagwaɓa da taɓara. “Ni wlhy bana son kitso, kuma kaina babu wani datti da yayi, koba ranar na wanke ba”.        Maganar take da iya gaskiyarta tana kuka tana kallonsa. Dan haka ya wani kalar ɗage mata gira da wara mata shanyayyun idanunsa irin na ki kiyaye ni. Ƙasa-ƙasa yanda ita kaɗai zataji kuma ya furta, “ALLAH idan baki daina min wannan rigimar ba tsaf zan riƙeki na matseki a wanke kan a kumayi kitson ƴan ƙanana ko zamu kwana anan. Dube ki abin kunya kina kukan kitso kamar ba ƴammata ba”.      Ai kamar ya tunzurata sai ta sake ɓarke masa da kukan da yafi na farko. Hakan ya saka wasu dariya, wasu ko na mamaki da tunanin ƙaramar ƙanwarsa ce dai halan. Yo irin wannan taɓara haka. Ya shigo yana faman shan ƙamshi da ɗaɗɗaure fuska, amma kalla yanda yake wani kashe murya ƙasa-ƙasa da ko jin abinda yake faɗa ma babu mai yi. Wanda kuwa suka sanshi mamaki suke yi, AA Darma dai shugaban matasa mai Mawaad Company ne haka available. Tab ɗin, ita kuma wacece wannan? Su dai a sannin da sukai masa baida wata ƙanwa mace da suke jini ɗaya wato iyaye ɗaya ai, hasali ma shine Auta a gidansu kamar yanda duniya ta sani. Oho basu dai da mai amsa musu duk wannan.          Cike da kwarkwasa wadda zataima Maanal gyaran ta ce, “Ranka ya daɗe za'a ɗan wanke yayi datti”. Mugun harara Maanal ta zuba mata, zatai magana yaja kujerar da aka kawo masa shima ya zauna kusa da ita sosai. Kasa cewa komai tayi sai kallonsa take tana hawayenta. Shima dai kallon nata yake cikin ido sosai yana danne dariya da ƙyar. Kafin ya janye a kasalance yana wani ɗan gyaran murya kamar wanda ke neman rasa kansa. Handku ɗinsa ya ciro fari tas yana tashin ƙamshi ya miƙa mata, cike da kwantar da murya kamar ba shine ke mazurai ba ya ce, “Yi haƙuri to daina kukan, badai nine ba zan rama miki da kaina. Ai ina nan bazan bari su miki da zafi ba, idan ma kina so zan goya ki a bayana mu tafi gida a ƙafa har gida”.         “Ni bana so duka, kaina ciwo yake min”. Ta faɗa idonta dake cika da hawaye a cikin nasa. Dole sai shine ya sake janye nasa yanzu ma. Dan data san tasirin da yanayin nata yake masa a cikin jiki data tausaya masa. Cikin ɗan ƙara samun kansa da shaƙewar murya ya saka mata handky ɗin cikin hannunta yana faɗin, “Ciwon kai ba, zan saya miki magani. Faɗa min mi kike son kici naje na sayo miki yanzu”.        Kafaɗa ta maƙe alamar bata son komai. Amma sai ya shiga lallashinta kamar ba AA Darma ba. Gaba ɗaya sun manta kansu a yanzu da matsayinsu komai ya rikiɗe musu zuwa baya, bayan data shuɗe musu da ɗunbin tarihin tunawa suyi kuka da dariya idan ya kama duk a lokaci ɗaya. Ƙoƙarin miƙewa yay siyo mata cake da tace tana so. Caraf cikin ma'aitan wata tace, “Sir basai kaje da kanka ba bara a amso mata nan kusa da mu”. Tsabar neman ɗuwawun zama ko kuɗin bata amsa ba balle jiran amsarsa tai ƙoƙarin ficewa. Amma sai Maanal da takaici ya cika ta dakatar da ita da faɗin, “Ni naka nake so”.       Dariya taso bashi amma ya danne da ƙyar baiyi ba. Batare da yace komai ba ya miƙe ya fita. Ita kuma ta harari ma'aikaciyar. A yayin fitar tasa ne ya ɗan kusa buge Nurry da tun ɗazun tai sumar tsaye saboda mamakisa daya gama cika mata zuciya da ruhi ganin yanda yake abu kamar bashi ba. Kai itafa sai taga ma kamar a mafarki take. Kai in ko mafarki ne wannan mafarki ya mata muni da yawa, ALLAH dai ya farkar da ita ta daina gannin wannan tashin hankali. Gulmar AA ɗin da wasu mata keyi a kusa da inda take tsaye dan har ya fice shi batare daya ma lura da ita ba ya sata fahimtar fa ba mafarkin bane gaske ne. Sai taji zuciyarta na neman tarwatsewa. Karan farko ta motsa jikinta kamar mara laka ta fice itama tabi bayansa. Tasan halinsa sarai baya ɗaukar raini ko rawar kai, dan haka ta tsaya har ya fito daga cikin bakery ɗin hannunsa ɗauke da ledoji guda biyu. Yanzun ma sam hankalinsa bai kai gare ta ba, dan haka cikin kwantar da murya ta ce, “Assalamu alaikum Yaya AA”.       Cak ya tsaya daga tafiyar da yake yi, sai kuma kamar mai ciwon wuya gently ya dubeta, irin duban nan na sau ɗaya ya ɗauke kansa yana shanye dukkan sassaucin fuskarsa. Da sauri ta matso inda yake sosai. Muryarta har rawa take wajen gaisheshi. Sau ɗaya ya amsa mata, har yayi kamar zai wuce sai kuma a daƙile yaɗan sake dubanta. “Mikike yi anan?”.             Wani irin sanyi taji a ranta da ƴar kulawar tasa. Saita samu kanta da sake kwantar da murya cike da yanga ta ce, “Munzo sayen snacks ne a bakery ɗin nan”.       “Okay”. Ya faɗa yana wucewarsa. Binsa tai da kallo kamar mayya, hawaye na ciko mata idanu. Ƙawarta da itama jikin nata ke a sanyaye ta ƙaraso gareta. Batace mata komai ba ta share hawayenta sai kuma ta miƙa mata hannu ta amshi bag ɗinta. Wayarta ta ciro ta shiga laluben number yayarta. Bugu ɗaya kuwa Saheeba ta ɗauka. Sai kawai ta sakar mata kuka. A ruɗe Saheeba ta shiga jera mata tambayoyi. Da ƙyar cikin garsheƙar kuka Nuratu ta sanar mata komai. Sai dai maimakon taji Saheeba ta amsa mata sai taji muryar Mamy, ashe lokacin suna tare ne Saheeban na'a sashenta.      Cikin ɓacin rai Mamy ta ce, “Ki bisa wajen Saloon ɗin ki ɗauka min hotonsa shi da yarinyar”.         “Amma Mamy zai gane nice na ɗauka na tura muku, kuma ALLAH sai ya hukuntani”.       “Okay kinfi tsoronsa kenan akan umarni na ko Nuratu?”.     “Ba haka bane Mamy. Dan ALLAH kiyi haƙuri”.     Ƙwafa Mamyn tayi, tare da yanke kiran kawai. Hakan yasa Nurry sauke ajiyar zuciya. Ko giya tasha ai bazatayi gangancin aikata abinda Mamyn tace tayi ba. Yaya AA fa, tab ɗin wlhy dandaƙar ɗan akuya zai mata har gaban uwarta ba damuwarsa bace. Dama dai ace bai ganta bane da zata iya ta ɗauka ɗin. Amma ya ganta ta gansa har sunyi magana ai ko zata cika duniya da rantsuwa yasan itace ta aikata. Haka ta samu kanta da zama a cikin mota ita da ƙawar tata suna dakon jiran fitowarsu..... ____________★           “Daddy wannan shine bayanin dana samu a kansa. Sunansa Bukar Bala Ɓatagarawa. Senator ne kuma.”      Murmushi mai faɗi Daddy yayi tare da gyara zaman wayar tasa yana kallon Yazeed dake masa bayanin dan video call suke yi. Kafin ya iya cewa komai Yazeed ya ce, “Daddy wai miya haɗaka da shi ne kake masa irin wannan binciken?”.      Kai tsaye Daddy ya ce, “Maanal yake so”.         Cikin matuƙar mamaki da razani Yazeed ya ce, “Maanal kuma Daddy”.     “Ƙwarai da gaske, dan har yaje ya samu iyayenta acan Giro sun gama magana......”     Tsaf Daddy ya zayyane masa komai. A take yanayin Yazeed ɗin ta canja, idanunsa suka kaɗa jazur. Cikin tsananin damuwa ya ce, “Daddy wannan nake gudu dama tun farko. Yanzu shike nan na rasata? Wannan fasiƙin mutumin zasu bata saboda zalunci?”.           “Baka rasata ba Yazeed, sam baka rasata ba. In har ina raye in sha ALLAHU bazaka rasa Maanal ba. Ka kwantar da hankalinka kai dai kabar komai a hannuna. Yanzu yaushe zaka dawo? Kwana biyar fa ya rage ɗaurin auren nan amma babu ango babu alamarsa”.        Sai da Yazeed ya haɗiye yawu mai ɗaci sannan a sanyaye ya ce, “Daddy zan taho zuwa alhamis insha ALLAHU. Kayan dana maka bayani nake son naga saukarsu akan idona. Kuma sunce sai Wednesday zasu iso. Shiyyasa na bari alhamis sai na dawo”.       “Bazai yiwu ba Yazeed. Ka taho Wednesday ɗin kawai. Kada mutanen nan suga rashin damuwarka akan ƴarsu tayi yawa. Ita ɗin ƴar uwarka ce kada ka wulaƙantata kodan Baba da Inna dan ALLAH. Ka kwantar da hankalinka ka ƙyautata mata sai ALLAH ya mallaka maka abinda kake so cikin sauƙi. Maganar Alhaji Bukar kuwa kada ma ta dameka, dan bazatai wani tasiri ba da izinin UBANGIJI.”         “In sha ALLAH zanyi duk yanda kace Daddy. Bara naje akwai meeting da zamu shiga dama”.     “Okay babu damuwa sai na jika, ALLAH yay maka albarka. Ya azurtaka da zuri'a masu albarka da zasu maka biyayya kamar yanda kake mana”.      “Amin Daddy na gode”.    Kai kawai Daddy ya jinjina tare da yanke wayar. Sai kuma ya maida dubansa ga Ammie da tun fara wayar tasa ta shigo, har zata juya ta koma ya hanata ta hanyar dakatar da ita da hannu. Dole ta dawo ta zauna. Akan kunnenta sukai duk zantukansu, sai taji zuciyarta ta raunana da tausayin Yazeed ɗin. Yaron kirki mai natsuwa da sanin mutuncin iyayensa.. har ga ALLAH tana son Maanal ta auresa, sai dai tana tsoratar mata wahala da ƙiyayyar uwar miji dan itama ta ɗanɗana a baya tasan ciwon da hakan ke da shi...... ____________★        Kafin a kammala kitson nan babu kalar fitinar da Maanal batai ma AA ba. Damma manya akayi mata shikku. Sosai kitson yay mata ƙyau, amma sai faman haɗe fuska take yi. Shi dai wanda take yi domin shi ɗin bai kulata ba. Sai hotuna da yay mata a kaikaice batare data fahimta ba. Fuuu ta fice a wajen, wanda sukai mata kitson na mata bye ko kulasu batai ba. Suma dai sunayi ne don neman fada kawai, dan zukatansu sun gama yarda ƙanwarsa ce ita. Dole ta bari ya ƙaraso ya buɗe motar dan key ɗin na hannunsa, sai dai yanda taga kamar yana tafiya slowly ga hannunsa saman cikinsa ya sata zuba masa ido dan tun ɗazun dama ta lura kamar yana shiga wani ɗan yayi na kai ciwo amma jarumar fuskarsa na dannewa. Fuskarsa ama a yanzun a ɗan yamutse take alamar dai something is happing.       “Baka da lafiya ne?”.    Kallonta yay da idanunsa da suka canja launi, sai kuma ya janye kamar baya so ya ce, “Mi kika gani?”.        Kallon nasa ta cigaba da yi batare da tace komai ba. Shima sai ya basar kawai ya buɗe motar ya shiga. Kafin ta zagayo ta shiga dole ya kife kansa a steering saboda yanda cikinsa ya sake murɗa masa. Dama tun jiya haka yake sama-sama. Dauriya kawai yay ya fito aiki dan baya son ɗagama Oum hankali. Wannan yanayin nasa kuma a garesa normal yanayi ne daya daɗe ciki tsahon shekaru. Dan ma ƙaddarar rayuwa ya ɗan lafar da al'amarin nasa a baya kaɗan.        “Ajwaad”.   Maanal ta kira sunansa. Sai da ya ɗan cije baki sannan ya ɗago ya zuba mata firgitattun idanunsa da suka saka zuciyarta harbawa. Babu shiri ta janye nata da sauri. Lumshe idanun yay cikin ƙarfin hali ya motsa lips ɗinsa kaɗan.       “Bazaki daina kirana da Ajwaad ɗin nan ba ko?”.      Batare data kallesa ba ta ɗan tura baki da faɗin, “To ba sunanka bane?”.          “Sunana ne, amma ke baƙya cikin masu faɗarsa. Idan kuma kika ƙara i will teach you a lesson”.     Baki ta taɓe kawai. Shima sai bai sake cewa komai ba ya sake maida idanunsa ya rufe. Kusan mintuna biyu batare daya buɗe ba ya ce, “Har yanzu kina driving?”.         Kamar zata gaya masa baƙar magana sai kuma ta danne a taƙaice ta ce, “Uhmm”.    Numfashi ya ɗan sauke kaɗan, sai kuma ya buɗe murfin ya fita a motar. Ta side ɗin da take ya zagaya, ita dai tsoro ne keson shigarta da tunanin mike damunsa ne. Buɗe inda taken da yay ya sata juyowa tana kallonsa.           “Fito ki koma can”.      “Amma ni fa gaskiya.....”   “Please Besty bana son surutu cikina ke ciwo”.      Haɗiye sauran maganar tai kawai, ta zuro ƙafafunta ta sakko. Ɗan matsawa yay ya bata hanya. Sanda ta shigo shi har ya zauna ya rufe ma, bayansa ya kwantar a jikin kujerar idanunsa a lumshe. Sai da ta rufe sannan ta ɗan zuba masa idanu, sai kuma a hankali ta ce, “Na kaika wajen Rafeeq ne?”.     Fuskarsa ce ta ɗan sake tsukewa, sai kuma ya buɗe idanun slowly a kanta.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖7️⃣9️⃣ _____________ .........Zuba mata su yay kamar a fusace, dan haka ta janye nata.      “Nace miki ina buƙatar ganinsa ne?”. Ya faɗa cikin nuna jin haushi.     Baki ta taɓe batare data tanka masa ba, sai da ta tada motar tai reverse sannan ta fita a wajen. Idanunsa a kanta yana kallon yanda take tuƙin. Shine ya koya mata mota kusan gab da ƙaddara zata rabasu. Dan in bai manta ba bayan sun kammala jsce ɗinsu ne ta damesa tana son iya mota. Da farko Oum taƙi tace sai ta kammala secondary. Amma tai ta damunta dole tace ya koya matan. Da yake tasa kanta a lokacin cikin abinda baifi sati ba ta iya. Wani lokaci idan an aikesa ya fita da mota suka tafi tare takan matsa masa sai ya bata, idan yaƙi ta tasashi gaba da rigima dole yake batan duk da yana jin tsoro dan tayi ƙarama sosai.... Ganin tana shirin ɗaukar hanyar asibiti ya dakatar da ita. “Malama nace bazanje asibiti fa. Normal ne idan naje gida nasha lemon tsami zai daina”.      Gefen titi ta ɗan gangara, cike da damuwa a fuskarta ta ce, “Kana wasa da lafiyarka ko, lemon tsami magani ne, kuma ni ban taɓa gani ko jin dan mutum na ciwon ciki ya sha wani lemon tsami ba”.        Murmushi ya ɗanyi da lumshe idanunsa ya sake buɗesu a kanta. “Kece dai baki sani ba saboda yarinta”.      “Niba yarinya bace ba wlhy”.    Ta faɗa tana murguɗa baki. “Oh really?”. “Kaima ka sani ai”. “Yanzu dai na sani ɗin kam, tunda ni dai yarinya na sanki a gabana. Amma tunda ke da kanki kin yarda kin girma zanfi kowa farin cikin hakan kodan halin da nake ciki”. Ya faɗa cike da shaƙiyanci. Harararsa tai da sake tada motar ta ce, “Kai dai ka sani.”       Murmushi yayi mai faɗi ya maida idanunsa ya lumshe da harɗe hannayensa duka a ƙirji. (Humm In ba Maanal ɗin ba wake ganin yawan murmushin AA haka arhar banza).       “Saka belt ɗin ki, ki kaini gida kafin tunani na ya canja na nema hanyar tabbatar da girman naki a titin mutane to Madam Maanal Giro”.         Sam ba fahimtar inda zancen nasa ya nufa tai ba. Amma taji a ranta akwai shaƙiyanci a ciki. Bata kulashi ba ta sanya belt ɗin ta sake tada motar. Hanyar anguwarsu ta ɗauka, dan gara ta masa yanda yake so su rabu lafiya kawai.....      Ganin hanyar da Maanal ta ɗauka ya saka Nurry dake binsu a baya tun daga shagon Saloon saurin dannama Mamy kira. Bugu biyu ta ɗaga, ko sallama batai ba ta ce, “Yauwa Mamy ga su nan sun nufo nan gidan, kuma itace ma ke tuƙasu, amma kamar baida lafiya ma”.         Kai ta jinjina tana sauraren abinda Mamyn ke faɗa daga can, kafin ta yanke kiran sannan taja motar zuwa hanyar nasu gidan. Ƙawarta ta ce, “Amma Nurry baƙya tsoron ya gane kece kika faɗa ma mamansa”.      “Bazai gane ba, shiyyasa nake so ta gansu da idonta ai.”      Kai kawai ƙawar tata ta jinjina alamar gamsuwa.....         A ƙofar katafaren gate ɗin gidan nasu ta tsaida motar, hakan ya sashi buɗe idanunsa ya kalleta. Ganin tana ƙoƙarin kunce belt ya ce, “Yanaga kin tsaya anan? Ki shiga mana”.         “No ka ƙarasa da kanka, ni zan koma daga nan”.     “Bazaki gaida su Oum ba?”. “Next time”. Kansa ya jinjina kawai ya cire nasa belt ɗin. “Kije da motar zan aiko driver ya amsa”.         “A'a zan hau taxi”.     Dakatawa yay daga ƙoƙarin fitar da yake, ya ɗan juyo yana kallonta. “Kin san fa bana son musu, taxi kuma na haramta hawanta daga yau”.         Komai batace da shi ba saboda yanda ya tsatstsareta da idanu. Shima sai bai sake cewar ba ya buɗe ya fita. Sai kuma ya ɗan duƙo ta glass ɗin windown. “Kije gida magrib ta kusa. Kuma kiyi tuƙi a hankali”.       “Ni Company zan koma ɗaukar kayana”.     “No ban yarda ba kije gida. Driver zai taho miki da su. Ki kula da kanki”.          “ALLAH ya ƙara lafiya”.     Ta faɗa itama tana maida glass ɗin ta rufe duka tare da yin baya. Yana tsaye yana kallonta har sai da ta ɓace masa. Ajiyar zuciya ya sauke mai nauyi tare da furzar da iska. Sai kuma ya shafa cikinsa yana yamutsa fuska kaɗan. A hankali ya juya yay knocking gate ɗin gidan nasu. Maigadi ya leƙo yana tambayar waye. Ganin AA ya sashi haɗiye sauran maganar, mamaki fal ransa na ganinsa a ƙafa. Bai dai ce komai ba ya gaisheshi. Shi kuma ya amsa masa yana wucewa ciki. Da Mamy ya fara cin karo zaune a gaban sashen Oum, sai Naufal da Anum dake wasa da keke. Yanda ta wani zuba masa idanu tun daga nesa ta sashi janye nasa da ga kallonta. Cikin dauriya ya ƙarasa inda taken, su Naufal da sai yanzu suka gansa suka sheƙo da gudu suna masa oyoyo. Daurewa yay ya tarbesu, sannan ya shiga gaishe da Mamyn. Bata amsa ba, sai mugun kallo da take jifansa da shi.       “Ina motar taka?”. Ta jefa masa tambaya a bazata. Bai iya ƙarya ba, ya kuma tsani mai yi, amma ya fahimci yau dolensa ma ya yi tan. Batare daya yarda sun haɗa ido ba ya ce, “Tana gareji Salihu ya kaita. Nima taxi na biyo”.      Rasama abin cewa Mamy tayi, dan yayi wani kicin-kicin da fuska, sai kawai ta zuba masa idanu. Shiko ya sake ciɗin-ciɗin da fuska. Batare daya yarda ya sake kallonta ba ya saki hannun su Naufal ya nufi sashensa dan ruwa kawai yake buƙatar sakarma kansa. Ko Oum baya son ta gansa a wannan yanayin. Ita kanta Mamy ɗin bai so ta ganshi a hakan ba....        A ɗan tsawace ta dakatar da shi, dole ya tsaya yana mai lumshe idanunsa, sai kuma ya dawo da baya inda take. Miƙewa tai batare data sake kallonsa ba cike da bada umarni ta ce, “Anjima ka sameni zan yi magana da kai”. Daga haka tai wucewarta. Da kallo kawai ya bita, wani abu mai nauyi na masa kai-kawo a cikin wuya da maƙoshi, yayinda idanunsa suka kaɗa sosai. A hankali ya furzar da iskar numfashi, sai kuma ya nufi sashen nasa.... __________★      Baki a wangale maigadi ke kallon Maanal daya buɗema gate. Taja motar a hankali zuwa cikin gidan. Bawai tuƙin nata ne ya bashi mamaki ba, dan yasan tana jan mota idan tazo. Ganin ɗirkekiyar motar da take ja ɗin ce da kuma sanin da yay mata bai taɓa ganin ta tuƙa wata mota ba sai ta gidan ya sashi a mamakin....        Turus itama ta tsaya tana kallon motar RK lokacin da take fitowa. Sai kuma ta ɗan leƙa gaba kaɗan. RK ɗin ne shima da kansa zaune a cikin motar tasa ya zubama motar data ajiye ido ko ƙyaftawa bayayi. Ta tabbatar kallon ƙurillar da yakema motar ya gane ta wacece ne. Sai kawai ta dake abinta ta ƙarasa garesa. A hankali ya janye idanun nasa daga kallon motar ya maida kanta. Batare da ya amsa sallamar da take masa ba ya furta, “Dama kina jan mota haka?”.        Guntun Murmushi kawai tai masa ta ce, “Uhmm!”.      “Masha ALLAH, kinyi ƙyau kuwa da motar”. Ya faɗa yana fitowa da ƙyau daga motarsa.     “Oh harda zolaya ma abin kenan?”. “Babu wata zolaya gaskiya na faɗa miki. Naje ɗaukarki a office AS ɗin Boss ɗinki yace kun fita tare tun la'asar. Shiyyasa na wuto nan dan na matsu na ganki”.        Murmushi tayi batare data tanka maganarsa ta farko ba ta ce, “Kamar wanda ya shekara bai ganni ba?”.     “Miye maraba my queen. Kwana huɗu fa. Ya kuka baro su Ammie?”.     “Lafiya Lau suke, suna gaisheka. Ya aikin?”.     “Alhamdullahi munata fama. Shi AA ɗin yana office kenan?”.     Murmushi ta saki a taƙaice, dan ta fahimci dole dai so yake sai anyi maganar AA ɗin nan. Sai kawai kanta tsaye ta ce, “Yana gida baida lafiya. Dan da wajenka ma zan kaishi yace na dai ajiyesa a gida”.          “Mike damunsa?”.      “Kamar ciwon ciki yace”.   “ALLAH ya bashi lafiya, yasa kaffara ne. Bari nai salla zanje na duba shi.”      “Okay ai ni dama da motar tashi ka wuce, sai driver ya bika da ita”.    “A'a, bashi ya baki ba da hannunsa”. “Dama yace zai turo driver ya ɗauka ne. Ni kuma bana ma so Didi taga motar a gidan ne”.        “Dan mi to?”.   “Kawai”. Shiru kawai yay yana kallonta. Yasan ƙarshem zancen kenan. Yau ma ai babu laifi an amsa masa magana da tsaho sosai. Ajiye zancen yay shima gefe ya fara wanda ya kawo shi ganin magrib na sake gabatowa. “Magriba na gabatowa. Ga shi inada uziri da daddare. Kuma ina son muyi magana yanzu ALLAH yasa ban takura ki ba”.     Kanta ta jinjiina masa alamar eh. Shima sai ya cigaba da faɗin, “Maanal na karanta diary ɗinki duka. Ba kuma zanja wani zance ko neman ƙarin bayani ba daga gareki ko daga wani, ina son ki bani dama magabata su shigo cikin al'amarinmu. Idan kuma babu damuwa ina son bikin anan kusa”.       Duk da wani irin motsawa da zuciyarta tayi haka ta dake. Tai ƙasa da kanta tana sakin miskilin murmushi. Sai kuma ta jinjina kan batare data kallesa ba tace, “Duk da ƙaddarar data shiga cikin rayuwata da mutunci na ka amince zaka aureni a haka Rafeeq?”.           “Maanal! Ke nake so ba jikinki ba. Kuma kema kince ƙaddara ai. Ƙaddara kuma babu wanda ya isa faruwarta ga kansa balle wanninsa. Haka ALLAH ya tsara miki rayuwa ai. Dan haka ki manta da baya kamar ma bata faru ba. Ni ke nake so Maanal, ke nake so ki zama uwar ƴaƴana. Halayenki, tarbiyyarki sune gaba a komai. Yanda na fara sonki ban san ke ɗin wacece ba, sanin ke wacece bazai sa na taɓa canjawa ba. Ni dai kawai fatan da nake da roƙo ki soni koda kwatar soyayyar da nake miki ne, wanda nake mikin ta ishemu rayuwa in sha ALLAHU”.       Karan farko Maanal ta ɗago tana kallonsa, idanunta na zubar da hawaye. “Nagode Rafeeq. Nagode sosai da ɗunbin soyayyar da kake min. Kuma ni ban taɓa ƙinka ba, ba kuma zan taɓa ƙinka ba. Sai dai kasan akwai ƙalubale a gaban mu”.       Sai da ya miƙa mata handky ɗinsa sannan ya ce, “Nami?”.       “Yaya Yazeed, ya taka rawar gani sosai a rayuwata, shima bai gujeni ba duk da yasan wacece ni. Wasu dalilai ne yasa kawai nake gujema aurensa domin samun zaman kafiyarsa shima. Amma a yanzu ban san yanda zan tunkare shi shi da mahaifinsa ba, kai har ma Ammie”.    Ta faɗa tana share hawaye. Murmushi ya saki mai faɗi har haƙoransa na bayyana. Sai kuma ya gyara tsaiwa sosai. “Sweetheart na fahimce ki, kuma abinda kika faɗa gaskiya ne. Amma muyi addu'a, da. ban taɓa kallon Yazeed a ƙalubalena ba game dake dama. Duk da ina fargabar kada ki zaɓesa ki barni, ta wani gefen kuma jin rawar daya taka a rayuwarki ta ƙara sani ganin girmansa da jin kimarsa a raina fiye da da. Amma tunda kece kika bani dama a yanzu da kanki na samu dukkan ƙwarin gwiwa. Zan iya karawa da kowa domin mallakarki. Karki wani damu zanyi maganin wannan matsala ɗin in sha ALLAHU. Ke dai kawai ki kasance cikin shirin zama amaryar Rafeeq Kasheem Kura anan kusa kaɗan”.      Murmushi tayi da juya masa baya. Shima sai yay dariya. Leda ya ciro a mota ya miƙa mata. “Ga wannan ki shiga da shi ciki bara naje, idan na gama da wuri zan dawo. Idan kuma dare yayi a shirya mini lokaci na musamman zan kira waya mu ƙarasa anan. Amma dan ALLAH bana son ganin hawayen nan masu daraja suna fita. Baki ji yanda nake jin zafin a zuciyata ba”.        Kai ta jinjina masa kawai. Ta amsa ledar tai godiya. Sai da taga ya shiga mota sannan ta nufi ciki, ya ɗan bita da kallo ta cikin mirror yana murmushi. Sosai yake jin zuciyarsa na ƙara samun nutsuwa. Tabbas yana son yarinyar nan. Ba kuma yajin akwai wani abu da zai bari ya rabasu. Alaƙarta da AA ta baya ko a ƙasan slippers ɗinsa bai ji ta damesa ba. Tunda a kaf labarin bai ji a inda ko sau ɗaya AA ya furta yana sonta ba ko ita tana son shi. Daga ƙarshe ma da bakinsa yace shi baice yana son aurenta ba. Hakan na nufin babu soyayya kenan shaƙuwace kawai da kowa kema kallon soyayyar. Da wannan tunanin ya fice a gidan..... __________★         “Hajiya! magana ta gaskiya yaron nan al'amarinsa nada matuƙar nauyi da tsauri. Ni kaina na shiga mamaki da ruɗani da Hajiya ta sanar min aikin da duk mukai masa bai shigesa ba. Shiyyasa na tsananta bincikena a kwana biyun nan, dalilin ma ce miki ki dakata da zuwa sai yau kenan”.      Cikin matuƙar damuwa Hajiya Basariyya ta ce, “To malam yanzu yaya ake ciki kenan? Dan gaskiya yarinyata na sonshi sosai. Kuma nima ina mata sha'awar aurensa”.        Ƴar dariya malam yayi, sai kuma ya kalla Huznah da keta faman kuka a jikin Maman Yaseerah. Janyewa yay ya maida ga Hajiya Basariyya. “Hajiya ku kwantar da hankalinku komai zai yi dai-dai. In har za'abi dukkan matakan da zan bayar zata aureshi. Sai dai akwai ƙalubale babba a gabanta....”       Cikin sauri Huznah da tun da malam ya ce zata iya auren AA ta ɗago da sauri ta ce, “Kowane irin ƙalubale ne zan iya ɗauka Malam, wlhy ina son shi, zan iya ɗaukar komai in har zan zama mallakinsa”.        Dariya malam ya sake yi da faɗin, “Kin tabbatar zaki iya?”.      “Ko miye kuwa Malam”. Kansa ya jinjina mata, sai kuma ya miƙa mata zabgegen carbin hannunsa. Da sauri ta amsa, zaɓar ɗaya yace tayi, tako zaɓa ɗin. Amsar wanda ta zaɓa yayi ya rufe idanunsa yana muy-muy da bakinsa. Su dai duk idanu suka zuba masa kawai.........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖8️⃣0️⃣ ______________ .......Fin mintuna uku ya buɗe idanun nasa tare da ajiye carbin sannan ya dubi Maman Yaseerah. “Wato Hajiya babban ƙalubalen shine akwai wadda ke'a zuciyar yaron gaskiya da jimawa. Dan haka yaƙi biyu kawai da zamuyi zai sa ta samu damar aurensa. Na farko shine cire yarinyar daga zuciyarsa gaba ɗaya, ba kuma zamu iya yin hakan ba sai mun san wacece ita. Na biyu zamuyi aiki akan iyayensa, ta yanda ko baya so zasu sakashi dole amsarta. Mu kuma idan ta shiga daga ciki sai muyi aikin karɓa mata zuciyarsa ta yanda bazai sake kallon wata mace ba a duniya sai ita. Kai hatta uwar data haifesa wlhy sai dai tabi bayanta”.       Gaba ɗayanzu babu wanda fuskarsa bata washe da murmushi ba. Sai Hajiya Basariyya ce ta ce, “Amma malam taya zamu san wadda ke cikin zuciyar tasa ne to? Sai naga kamar hakan zaiyi wahala”.           “Bazaiyi wahala ba Hajiya. Wannan aikin na yarinyarki ne. Ita zata bincika mana ai”.      “Karka damu Malam zanyi ƙoƙarin hakan. Sai dai akwai wata yarinya Nuratu da muka haɗu, itama tana sonshi, ban sani ba ko ita ce a zuciyar tashi, dan har ciwon nan itace ta jimin shi”.           “Nuratu!”.      “Eh malam”.   Ɗan jimm yay, sai kuma ya sake ɗaukar carbi ya bata. Amsa ta sake yi ta zaɓa. Kamar dai ɗazun yanzu ma ido ya rufe na wasu mintuna sannan ya buɗe. “Gaskiya ba ita bace. Abinda na gani a kanta mahaifiyarta ke son ta aureshi da wata ta kusa da ita dake a cikin gidan su yaron. Suma kuma suna aiki a kanshi sosai, a yanzu haka ma suna shirin yin mai zafin gaske duk dan itama ya aureta.”         “Eh lallai, ashe suma waɗan nan shegun kansu ne. To aiko Malam ai mana maganinsu, dama nace bazan yafe mata ciwon da ta jima Huznah ba. Jiba yanda ta maida min da fuskar yarinya kamar ƴar yarbawa ko goburawa. Ashe itama ba sonta yake ba shegiyar yarinya kawai”.      “Karki damu da wannan Hajiya nasu mai sauƙi ne. Yanzu zan haɗa mata abubuwa taje ta cigaba da amfani da su. Nan da kwanaki uku zan kammala aikina nima. Itama sai tai ƙoƙarin samo mana wadda ke'a zuciyar tashi”.     Godiya suka shiga jera masa kamar shine mai basu biyan buƙata. Maybe ma basu samun lokacin yima UBANGIJIN dake basun magiya irin haka ba. Gidan su Maman Yaseerah suka koma, dan anan zasu yini zuwa anjima su koma Kaduna...... ___________★       Bayan sallar magrib AA ya baro massallaci. Kai tsaye sashen Mamy ya nufa. Bai sameta a falon ƙasa ba, dan haka ya haye sama. Sai da yay sallama a ƙofar bedroom ɗinta ta amsa da bashi izinin shiga sannan ya shiga. Tana zaune kan abin salla, tunda ya shigo kuma ta zuba masa idanu. Hakan ya sashi tsayawa yay shiru. Wani irin ɓacin rai taji ya tokare mata maƙoshi, a kausashe ta ce, “Ni zan taso kenan”.           Komai bai ce ba ya ƙarasa takowa har gabanta ya zauna a saman lallausan carpet ɗin wajen ya tanƙwashe ƙafafu. Kansa a ƙasa ya gaisheta. Kai da ka gansa kasan babu wata shaƙuwa a tsakaninsu. Sai ma shakka da girmamawa irin ta na sama akan na ƙasa. Sai da ta gama shan ƙamshinta cikin kaushin harshe ta furta, “Ajwaad miye matsayina a wajenka?”.      Idanunsa ya lumshe a hankali, maƙoshinsa na kaikawon ɓacin rai a cikin wuyansa. Da ƙyar ya iya amsa mata da, “Mahaifiya”.      “Ai baka ɗauke ni a mahaifiyar ba. Saboda Fateema ta fini. Inda ka ɗauke ni da ban sharɗanta maka sharaɗi ba harda ALLAH ya isa kaƙi bi. Ya mukai dakai a shekarun bayan akan wannan shegiyar yarinyar ƴar matsiyata?”.          Kasa bata amsa yay, sai dai fuskarsa tai masifar rinewa. Mamy ta daka masa tsawa jikinta har yana rawa. “Wlhy zan mareka. Wane alƙawari ka ɗauka min akan Maanal! Da zaɓin matar aurenka?”.        Karan farko ya kalleta da rikiɗaɗɗun idanunsa da sukai masifar kaɗewa, sai kuma ya maida kansa ƙasa. Cikin kwantar da murya da girmamawa ya ce, “Mamy ban karya alƙawarinki ba. Kuma ni yarinyar nan babu abinda ke tsakanina da ita yanzu sai ma'aikaciya a company na. Shima kuma aure nace zanyi”.        “Karma kayi, nace kadama kayi. Idan aka ɗaura maka auren dasu ka sake su a washe gari. Dan kama karkaɗe kunnenka kaji nan da wata guda za'ayi bikinka da Nuratu da Huznah. Sannan Maanal na baka sati huɗun kacal ka sallameta daga kamfaninka. Idan ba hakaba wlhy wlhy duk abinda na maka kaine kajawosa ciki harda muguwar addu'a. Dan ko mutuwa nayi ban yarda ka cigaba da mu'amala da ita ba. Inko ba haka ba ALLAH ya isa ban yafe maka ba wahalar ɗaukar cikinka da nayi dana naƙudar haihuwarka. Kuma wlhy zan taka har gidan iyayenta a wannan karon naja musu kunne itama kuma Fateeman zanyi fito na fito da ita dan na fahimci itace ta dawo da yarinyar rayuwarka ita munafuka anmimiya. To zan bata mamaki a wannan karon dan ban haifa mata ƴaƴan banza ba balle tace....”        “Dan girman ALLAH Mamy kada kiyi haka. Kada kije musu gida. Ni kike da iko a kaina, zan kuma yi miki biyayya. Amma dan ALLAH kada ki ɓata yardar da Oum tai miki, kada ki raunana mata zuciya akan abinda ke da hannunki kika ɗauka kika bata harda shaidu. Hakama Abah bana son yayi nadamar yardar da yay miki. In dai Maanal ce zan barta, bari na har abada na cigaba da mata addu'ar samun wanda ya fini”.          “Wannan kuma ya rage naka. Ni dai na gama magana. Kuma ka samesu da maganar Huznah da Nuratu da kanka a cikin satin nan.”     Kansa kawai ya iya jinjina mata. Daga haka ta tashi zata kabbara sallarta. Shima sai ya miƙe dan ƙoƙarin tada salla ake a masallaci...... __________★             “Auta wai ina kika samo mana wannan azababbiyar mota haka ne? Ya subahannallah motar nan ta haɗu ni da Honey sai santi mukeyi fa a waje. Maigadi yace kece kika zo da ita”.        Baki Maanal dake kokarin kaiwa zaune a kujerar dining ɗin ta ɗan taɓe, batare data kalla Didin tata ba ta ce, “Daga office ne fa.....”      “Aka baki?”.   Shahidah ta faɗa cikin katseta. Karan farko Maanal tayi murmushi tare da buɗe kular gabanta. “Kai Didi wazai bani mota kuma. Aikin nawa nai musu. Kawai fa Ajwaad ne baida lafiya yasa na kaishi gida, shine yace nazo da ita zai aiko a ɗauka. Kuma gashi har yanzu shiru”.        Idanu sosai Shahidah ta zuba mata kamar mai tuhumarta da su, hakan yasa Maanal faɗin, “Kai Didi wai wannan kallon fa?”.     “A ai dole na kalleki Auta, Ajwaad fa. Yaushe har kuka fara shiri haka da shi....?”      “Nifa babu wani shiri. Kawai yau kaina ya isheni ne naje kitso, shi kuma ya ganni a wajen zan hau taxi yace sai na shiga ya saukeni a gida. Kawai muna hanya sai cikinsa ya kama ciwo shine ya roƙeni na tuƙa na ƙarasa da shi gidan......”       Ita kanta data gama shirya ƙaryar sai taji ta kasa kallon Didin tata. Shahidah da mamakin yau Maanal da kanta ta kai kanta wai kitso ya cikama zuciya sai ta ma kasa magana. Dai-dai nan Uncle Sadeeq ya iso dining ɗin shima. Kujera yaja kusa da matarsa ya zauna. Maanal ta gaisheshi. Ya amsa mata da kulawa yana ɗorawa da faɗin, “Auta wai ƙyautar mota kika ciwo mana ne yau haka a gidan? Irin wannan zazzafar mota haka. Har yanzu fa a kaf Nigeria mutanen dake da motar nan basu da yawa. A Abujan nan ma tafi yawa. Sai Lagos suma. A Abuja kuma AA Darma na cikin wanda suka mallaketa a farko-farko        “Ai ta AA ɗin ce”. Cewar Shahidah tana ƙoƙarin zuba masa abinci.     “Yauwa koda naji, kai lallai wannan ogan naku kam na ji dake. Anya Yaya Yazeed da Doctor basu samu sabon rival ba?”.           “Kai Yaya ”.     Maanal ta faɗa kamar zatai kuka. Dariya yayi shima yana ɗaga hannayensa alamar surrender. Sai kuma yay zipping bakinsa. “Okay nayi shiru.”       “To kace ba haka kake nufi ba?”.    “Nace ba haka nake nufi ba Auta ”. Dariya Shahidah ta sanya musu da faɗin, “Kai kudai shiriritarku bata ƙarewa, kaita biye mata ga abincinka ma zai huce”.        “To Honey idan ban biye mata ba wa zan biye mawa. Ƙurama da ƴaƴanta take wasa a dawa ai. Yanzu dai serious AA na ji dake Auta. Zan so gaskiya gobe na ganki a motar nan”.      “Assalamu alaikum”. Sallamar mai gadi ta hana Maanal amsama Uncle Sadeeq zancensa. Shine ya amsa tare da bashi iznin shigowa. Sai da ya gaishesu sannan ya miƙama Maanal ledar hannunsa. “Auntyn yara gashi wani ya kawo a baki. Wai daga office ɗinku”.      Amsa Manaal tayi, koda ta buɗe sai taga handbag ɗinta ce a ciki, miƙewa tai tana ajiye bag ɗin da faɗin, “Yauwa bara na baka key ɗinsu ka bashi ya ɗauki motar nan”.     “Ai ya tafi, yana bani ya juya abinsa ”.    Da mamaki Maanal data dakata ta juya tana kallonsa. Sai kuma ta ce, “Ya tafi fa? Ita kuma motar wazai ɗauka?”.       “Ai a cikin mota yazo shima fa”.    Rasama abin cewa Maanal tayi, sai kawai ta koma ta zauna. Maigadi ya musu sallama ya fita. Abincinsu suka cigaba da ci, sai dai kowa da abinda yake tattaunawa da zuciyarsa musamman Maanal da Shahidah..... __________★          “Anya Autana yau wani bai biya maka kujerar Makka a hanyar dawowa office ba?”.     Cikin ɗan waro manyan oily ayes ɗinsa ya ɗago yana kallon Oum. Sai kuma ya saka yankakken Apple ɗin daya ɗauka a bowl ɗin gabanta a bakinsa. “Oum ke dai kawai kin fara tsufa ne idanunki basa ganina tar, dole Abah ya zo ya fiddo kuɗin miki wankin ido ko ya ƙaro amarya mai jini a jika”.         Dariya tayi da ɗaukar fillo ta ɗan dakesa a kafaɗa, “ALLAH ka maida ni kakarka Auta, kai ba'a ce za'a maka wankin ido ba sai ni. To ina nan har jikokinka sai na gani da waɗan nan idanun. Amarya kuma ƙaryarta sai dai na aljanna”.      Yanzun kam dariya ya ɗanyi har jerarrun fararen haƙwaransa na bayyana sosai. Ya kwanto kansa saman kaɗar Oum ɗin yana ƙara saka hannu a bowl ɗin ya ɗauka strowbarry ɗaya. “Tab yagwgwal kenan, Oum zuwa sannan ai inaga sai an haɗaki a tsumma kenan. Inama laifin ƴaƴan dai, ko idan su Naufal sunyi, kai sai dai ma Anum itace mace”.       Kunnesa Oum taja tana dariya, shima dariyar yake sai kuma ya dafe hannunta yana ƴar ƙara. “Wayyo first love zaki ciren kunne. Abah kazo dan ALLAH matarka zata cire kunnen jin”.     Dariya sosai Oum keyi, ta kuma ƙi sakin masa kunne. A haka RK da babban yaya suka shigo suka samesu. Babban yaya ya zauna kusa da ita shima yana kai hannu cikin bowl ɗin ya ɗauka yanka ɗaya na kankana da faɗin, “Oum dan ALLAH cire kunnen duka”.        Sakin ma AA kunne Oum tayi da faɗin, “Oh zuga zugi to anƙi ɗin”.     Dariya Babban Yaya da RK sukayi, RK ya ce, “Kaima fa ka sani kunya zaka sha in dai wannan yaron ne da babarsa. Dama shiru ka musu idan ta cire kunnen sai musha dariyar da ƙyau”.         “Kuma fa haka ne Uncle R, nima da shishshigin tsiya.”      Murmushi AA yay mai faɗi da yima babban yayan gwalo. Aiko ya jawo fillo shima ya kai masa duka. Tarewa Oum tai kafin ya sauka akan AA ɗin. “Wayyo babban yaya so kake yay ciwon jiki. Ga wahalar aiki da ya shawo dama”.          Baki buɗe Babban Yaya ya ce, “Yo Oum shi ba namiji bane?”.       “Ingarma ma kuwa in dai Autana ne, dan gidan nan yafi kowa ƙarfi”.     “Ato faɗa musu shi da ruɓaɓɓen kawun nasa Oum”. AA ya faɗa yana musu gwalo. Filo biyu yanzu kam RK ya ta kwakuso yayo kanshi. Da sauri AA ya wani wantsala bayan kujerar cike da action mai birgewa. RK ya bisa yana faɗin, “Yau sai ka gayan waye ruɓaɓɓen...”     Dariya sosai Babban Yaya da Oum ke musu. Dan sai faman zagaye falon suke kamar wasu yara. Kai kamar ba AA ba sarkin miskilanci da kamewa, kamar bashine Mamy ta gama yima tujara ba. Bawan ALLAH ya shanye ya danne dan kar Oum ta fahimci komai. Farin ciki sosai su Oum keji a ransu, dan sun jima basu ga irin wannan yanayin a tattare da Ajwaad ba. Yau kuma sai basu san musabbabin farin cikin nashi ba. Shigowar Abah ta raba wannan faɗa, dan kuwa tara-tara sukai shi da RK Abah ya kama masa shi, aiko RK ya bubbuga masa filon.         Sai da Oum tazo ta ƙwace tana faɗin, “Eh lallai yau naga taron dangi, kun tarar min kan yaro”.       Tafawa Abah da RK sukayi, ita kuma ta janye hannun AA dake faman tura baki gaba. “Kaga ƙyalesu zasu gani a kwanon abincinsu yanzun nan”.       Da sauri Abah ya ce, “A haba ya zaki mana haka.”       Gwalo AA yayma Abah da RK, RK ya ta hararesa yana ƙara kawo masa filo Oum tai saurin tarewa. Yayinda Babban Yaya ke kwasar dariya abunsa da faɗin, “Kaga Abah kai da Uncle R kun jama kanku, yau babu ku babu cin girkin Oum a gidan nan”.           “Aa baza'ai haka ba, sai mu bata gaƙuri ai Fadeel. Kai har ma ɗan gwal ɗin nata ko Brother?”. Abah ya faɗa yana kallon RK. Shigowar Fawzan ya hana RK bana Abah amsa, duk sai sukai shiru suna kallon Fawzan ɗin da sam babu walwala a tare da shi. Hasali ma bai kula kowa ba ya wuce gaban Oum ya zauna a ƙasan carpet ya ɗora kansa akan ƙafarta. Dan gefe da gefenta AA ne da babban Yaya. A rikice Oum ta shafa kan Fawzan ɗin. Ta ce, “My baby miya faru? Baka da lafiya ne?”..........✍️ ✨ZAFAFAN DAI ✨ 1 ƘALBIM (Mamu gee) 2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo) 3 DUNIYAR MU (Huguma) 4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull) Book 1:-500 Book 2:-1000 Book 3:-1500 Book 4:-2000 0022419171 Access bank Maryam Sani Gumi Shaida:- 09033181070 Kati MTN:- 09032345899 Ƴan NIGER 🇮🇷 1000CF 89825722 Nousaiba Lawali Maradi Shaida:-09033181070 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖8️⃣1️⃣ ______________ .......Hannunsa ya ɗaura akan nata dake shafa kansa, muryarsa cike da rauni ya ce, “Oum Nibras ce, wai ni takema gorin haihuwa yau, ni ɗin nan ni, ni dake da ƴaƴa har biyu a gidan nan, ga Naufal ga Anum”. Sai hawaye suka fara gangaro masa. Shi dama haka yake yana da rauni sosai. Babban Yaya da AA sun fisa ƙarfin zuciya. RK ne ya kai duƙe gabansa, sai kuma a hankali ya jawosa jikinsa ya rungumesa. Haka shima AA a hankali ya zamo daga kujerar ya zauna a kusa da su yakai hannunsa saman bayan Fawzan ɗin. Tuni idanunsa sun juye, fara'ar fuskarsa ta ɓace ɓat. Haka shima Babban Yaya sakkowa yay ƙasan ya zauna, su ukun duk sai suka sakashi a tsakkiya. Oum da tuni hawaye sun cika mata ido har sun fara sauka ta janye dubanta daga kallonsu ta maida kan Abah dake tsaye kawai shiru yana kallonsu shima. Tabbas babbar damuwarta a duniya yanzu shine ganin zuri'ar Fawzan data Ajwaad. Rashin samuwar ƴaƴa daga Fawzan har yanzu na tayar mata da hankali, tana cikin damuwa. Dan haka take tsaye kansa da addu'a sosai da sadaka. Haka shima AA akan aure......       Wani kalar miƙewa da AA yayi a fusace ya sakasu zabura su duka. Tamkar wani sojan da allurar ɗaukar fansar yaƙi ta tsikara ya nufi ƙofa, dama ransa fal yake da damuwar Mamy, yanata dannewa ne kawai dan kar Oum ta gane. Ai babu shiri Abah yay saurin shan gabansa. “Ajwaad! Ina zakaje?”.          Idanunsa ya rumtse da ƙarfi maƙoshinsa na wani irin masifar kai-kawo a wuyansa da sauri-sauri. Sai kuma ya buɗesu akan Abah, cikin zafin rai ya ce, “Ita wacece da zata dinga wulaƙantashi? Kodan taga tayi na farko ba'a ɗauka mataki ba shine ta sake maimaitawa yau, idan haihuwar iyawace miyyasa tata uwar ta haifeta ita kaɗai! Sai na koya mata hankali yau a gidan nan”.     Murmushi sosai Abah yayi, sai kuma a hankali ya riƙo hannun AA ɗin daya sake yunƙurawa zai wuce. Maidosa yay jikinsa ya rungumesa kawai, tare da ɗora hannunsa a saman bayansa ya shiga shafawa. Sai kuma ya riƙo hannun Oum dake tsaye a gefensu tana hawaye, jikinsa ya matsota sosai itama ya rungumeta ta gefe. Dai-dai nan Mamy ta shigo falon da sallama, bayanta Nibras ce ke kuka sosai kamar wadda akace uwarta ta mutu. Zabura AA yayi daga jikin Abah, sai da ƙyar ya sake dannesa. Cikin wani irin raɗaɗin da yake jin zuciyarsa ya ce, “Abah ka barni, ka barni na koyama wannan wawuyar iya magana wa miji tunda inda ta fito ba'a koyar da ita ba......”       “Ya isa! Ya isa! Haba Autan Oum ɗinsa. Please cool down kaji my sweetheart.”     Abah ya faɗa cike da lallashi yana cigaba da shafa bayan AA da matsesa a jikinsa da har rawa yake saboda masifa. Shifa dama idan yay fushi sai addu'a. Sosai Nibras taji hankalinta ya sake tashi, kukanta ya ƙara ƙarfi, AA ɗinta yana fishi da ita, ina bazata iya ba, da tasan abinda zai je ya dawo kenan da bata faɗama Fawzan ɗin abinda ta faɗa ba. Dan ita fushin AA yafi ɗaga mata hankali akan na Fawzan ɗin. A hankali ta fito daga bayan Mamy da itama take kallon AA ɗin zuciyarta na sake girmama al'amarin sa. Ga wani ƙududun ganin duk yaran anan tare da Oum. Wannan zaman hirar daren da suke zuwa wajenta yana ƙona mata rai, ita wani lokacin ma daga gaisuwar safe ba sake ganinsu take ba sai wata safiyar, amma ita Oum in har suka dawo aiki wani lokacin ma sai sun fara zuwa sashenta kafin su wuce wajen matansu. Da sunyi isha'i kuma nan suke sake tahowa wani lokacin ma anan ake haɗuwa dinnar dole. Eh dole mana, dan ita dai ba'a san ranta bane ba, a hakama dan matansu nata ne duk yanda Oum ɗin taso jan ra'ayin Saheeban da Nibras basa sakin jiki da ita. Garama Nibras saboda AA yafi zama sashen Oum ɗin tana nacin zuwa ta zauna...      Durƙusawar Nibras gaban AA da Abah yaja suka zauna ya maido Mamy a hanyyacinta. Babu wanda bai zubama Nibras ido ba na mamaki, itako shaiɗanci na soyayyar da takema AA ya rufe idonta bama ta fahimci shirmen da take shirin sake tafkawa ba. Muryarta na rawar kuka ta ce, “Yaya AA dan ALLAH kayi haƙuri kada kayi fushi da ni. Wlhy sharrin shaiɗan ne ya sani faɗa masa hakan kuma nayi nadama.....”        “Baki da hankali ma, nima zaki bama haƙuri ba wanda kikama laifinba ashe!!”. AA ya faɗa a matuƙar hargitse yana yunƙurowa kamar zai falle fuskarta da mari. Da sauri Oum ta riƙo hannunsa cikin nata. Sai kuma ta kalla Nibras data rumtse ido a tunaninta marinta AA zaiyi. Cikin taushin murya da yakana ta kirayi sunanta.       “Nibras!”.    Idanunta ta buɗe a hankali, sai kuma ta kalla Oum ɗin. Hannu takai ta share hawayen dake cigaba da gangaro mata sannan ta ce, “Na'am”.     “Zonan”. Babu musu ta matsa jikin Oum dan mafita take nema kawai da AA zai huce. Fushin nasa sukar rihinta yake yi. “Nibras gaskiya Auta ya gaya miki bashi kikama laifi ba ɗan uwansa kikamawa. Dan haka Fawzan zaki bama haƙuri. Sannan ina jan hankalinki da tausasa harshenki ga miji a yayin magana koda cikin fushi ne, ita kuma haihuwar nan mu yarda ALLAH shike badata, komai kuma nada lokacinsa. Kefa shaida ce kunje kunga likitoci ba sau ɗaya ba ba sau biyu ba amma ana tabbatar da ku dukanku lafiya lau kuke, lokacine kawai baiyi ba. Nibras Baba shekara goma sha huɗu Umma bata gaɓa ko ɓatan wata a gidansa ba, amma ko mu dake a gabansu bamu taɓa jin eheem ga kowanne su akan hakan ba. Har ALLAH ya iyakance yau gasu twins a raye harda nasu yaran. Kuma lokaci ne ALLAH zai kawo kinji. Muna muku addu'a a dukkan motsinmu kinji ko”.       Da sauri Nibras ta ɗaga kanta tana satar kallon AA dake a gefen Oum ɗin.  Kafin ta matsa kusa da Fawzan da RK da Babban yaya suka saka tsakkiya. Hannayenta duk biyu ta haɗe waje guda muryarta na rawa ta ce, “Dan ALLAH kayi haƙuri Jaan, sharrin shaiɗan ne dana zuciya. Amma in sha ALLAHU bazan sake ba na tuba.”         ALLAH sarki Fawzan sarkin haƙuri, sai ya sakar mata murmushi, muryarsa a sanyaye ya ce, “ALLAH ya yafe mana baki ɗaya ya wuce.....”     Bai ƙarasa ba AA ya miƙe fuuu ya fice a falon. Da kallo duk suka bi shi, musamman Nibras dake jin zuciyarta na kumfa a cikin ƙirjinta. Ji take kamar ta bishi da gudu ta rungumesa. RK ne ya katse yanayin da faɗin, “Aunty dafa autanki ne babban Yaya a gidan nan da kowa yaga takansa. Dan discipline Master za'ayi na gaske”.      Dariya Abah da Fawzan da Oum suka sanya, Babban Yaya yayi murmushi. Mamy kam wani shegen kallo ta watsama RK a kaikaice. Yayinda Nibras kanta ke a ƙasa kwai. Cikin nutsuwa da dattko Abah ya shiga musu nasiha Oum na taya shi, yayinda Mamy ta miƙe batare data tofa komai ba tunda ta shigo. Kallonta Oum tai fuska cike da murmushi. “Madam ya baki mana addu'a ba zaki tafi”.     Murmushi Mamyn ta saki kaɗan, “Oh baku gode bama dana taro muku ƴar taku dake shirin fita a gidan. ALLAH ya kiyaye gaba ni nayi nan mu kwana lafiya”.       Murmushi Abah da Oum suke yi, wata ƙaunarta na sake ratsasu. Hakama RK da su Fawzan, duk murmushin suke yi. Nan dai suka ƙara musu nasiha har RK da Babban Yaya musamman Nibras. Ta nuna nadamarta sosai, duk da ita hankalinta sam ba'a kansu yake ba yana ga AA daya fita a fusace. Ta san yau ko barci da wahala ta iya yi mai daɗi, sam bata son ganinsa a damuwa, balle kuma ace itace ta ɓata masa ran ai al'amarin yayi girma da yawa gaskiya......      Humm wannan Nibras ALLAH ya taroki dai to🏃😥. Wai da irinsu a gaske🤔 ko sai a novels 🥱🥺😌. __________★        “Kai malam wai fushin ne har yanzu dai?”.     RK ya faɗa idonsa akan AA dake zaune a bakin gadonsa da waya a hannu yana sarrafawa. Daga wanka RK ɗin ya fito daga cikin bayinsa, dan yau anan ɗin zai kwana. Tunda suka baro sashen Oum shi da babban yaya yayo nan. A inda AA ɗin yake har yanzu anan ya samesa, yayi wanka ya canja kaya zuwa kayan barci. Tun daga amsa sallama bai sake kula RK ɗin ba shima kuma bai bi takansa ba ya ajiye dai basket ɗin da Oum ta haɗo musu abinci ya wuce toilet. Shine yayo wanka ya fito. A inda yabar AA ɗin ya sake samunsa, shine ya jefa masa wannan tambaya ta “Kai malam wai fushin ne har yanzu dai?”. Dai-dai yana zama a bakin gadon yana goge fuskarsa da ƙaramin towel. Karan farko AA ya ɗago ya kallesa, sai kuma yay guntun tsaki yana ajiye wayar. Shiru na wasu mintuna kafin ya ce, “Bazaka gane ba wlhy na tsani yarinyar nan. Ni banga mi Ya Fawzan ya gani a jikinta ba har yake zaune da ita. Gaba ɗayanta a zubinta ma shashasha ce”         “To miji da matar sa ai ba'ace miya gani a jikinta ba. Kawai dai ita na kula tanada matsala ne. Ince ko cikakken 5 months ba'ai da yin irin wannan case ɗin tsakaninsu ba. Boko da ƙarancin ilimin addini ya mata yawa ne kawai, ga gata data samu a gidansu mara amfani. Yo mara amfani mana tinda babu cikakken tarbiyyar ɗiyan malam bahaushe a tare da ita dam, gefe kuma nake gani akwai sharrin ƙawaye kamar dake zugota”.        “Oh, shine kuma duk zata tattaro haukarta tana saukewa a kansa. Ni ban san mike damun ya Fawzan ba sam, bana son wannan sanyin halin nasa. In dai zai ware rana ɗaya yaci mata uwa ai da ta dawo hankalinta. Kawai ka zauna yarinya ƙarama ƴar cikinka na raina maka wayo, da auren wuri yay daya haifeta ai”.      Dariya RK yay da ɗan dukan kafaɗar AA ɗin, “Common Oum's boy hakan fa normal ne ga ma'aurata. Bari dai kayi auren malam zama ka ɗauki fiye da hakan. Mace kuma ko jika kayi da ita a ɗakin aure ai dai-dai kuke tunda ta gama ƙure maka girma”.          Harrarsa AA ɗin yay. “Oh irinsa zaka zama kaima kenan?”.     Cikin dariya RK ya ce, “Idan ta kama mizai hana. Balle ma nasan ni tawa mai hankali ce zata dinga lallaɓani bazata bari ta ganni cikin fushi ba. Kai ni yanzu ma fa zuwa nai muyi magana da Aunty da Yaya akan batun nawa wannan kuma rikicin ya shiga tsakkiya. Magana ta ALLAH aure nake so, idan har anyi azumin nan dani a tuzuru bana son nayi babbar salla a gwauro”.      Sosai AA ya taɓe baki, sai kuma ya koma ya kwanta yana ɗaukar wayarsa, cikin halin ko in kula ya ce, “Ka samu matar kenan?”........✍️ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖8️⃣2️⃣ ______________ .......Harara shima RK ya maka masa yana miƙewa, sai da ya ɗauki hanyar closet ɗin AA ɗin sannan ya amsa masa da, “Bazaka bani auren ƙanwar taka Maanal ba kenan da kake min wannan tambayar rainin wayon?”.       Sai da AA ya wani cije lips saboda yanda furucin na RK ya dakar masa zuciya. Amma sai ya zaɓi masa shiru bai tanka ba. Shima RK ɗin bai sake magana ba sai da ya kimtsa ya fito daga closet ɗin cikin pyjamas. Zama yay ya jawo basket ɗin kayan abincin ya shiga zubawa. Batare daya kalla AA ba ya cigaba da faɗin, “Da gaske nake Ajwaad ina son ka muje Kano wajen Abbu da a weekend ɗin nan, amma sai mun fara zuwa wajen Baba Sardauna first, dan Maanal ta bani dama bai kamata kuma nayi wasa da ita ba.”        Shiru AA bai tanka masa ba. Dan haka RK ya ɗago yana kallonsa. Wayarsa kawai yake faman latsawa babu alamar ma yana da niyyar tanka masan. “Ikon rabbu, kaifa wani lokacin ɗan wulaƙanci ne baka jini bane wai?”.       A ɗan tunzure AA ya ce, “Malam mind your own business kaji, ka tafi kaje ka nema aurenka ina da abunyi. Dan zan mayi tafiya ne zuwa Chaina wannan weekend ɗin”.          “Chaina kuma? Yin uwar mi to?”.    Nan ma banza AA ɗin ya masa. Sai kawai RK ya taɓe baki da jan abincinsa ya fara ci. “Kai dai ka sani, idan ka tashi ka ƙarasa har katangar bangon duniya ba Chaina ba ma. Kai wlhy ina matuƙar tausayin matar da zata aureka a duniyar nan Ajwaad. Shiyyasa ma kayi kwantai har yanzu babu mashinshiniya. Ya kamata Oum ɗin taka ta saka a fara maka ruƙiyya ko aljanun kanka zasu ragu mu huta muma.”        “SHURI ne a kaina”.    AA ya faɗa yana miƙewa, bathroom ya shiga ya bar RK da dariya. “Ai da alama har shurin ma da kukoki za'a iya samu ALLAH. Murɗaɗɗen banza”.     AA na jiyowa amma bai sake tanka masa ba. Ya jima a bayin sannan ya fito, bai kula RK ba ya haye gadon yay kwanciyarsa. Shima RK ɗin sai bai sake kulashi ba. Sai ma ƙoƙarin neman number ɗinsa dake a hannun Maanal yake. Sai da tana gab da tsinkewa ta ɗauka, cikin yanayin mai barci tai masa sallama.         “Oh oh har kinyi barci yau haka da wuri?”.     Daga can Maanal ta ce, “ALLAH na gaji ne Ya Rafeeq.”      “A niba yayanki bane. Ga dai ƴaƴan ki nan ɗan balaja'u. Dan nima yanzu Yaya zan koma kiransa ma”.         Cikin rashin fahimta ta ce, “Ni kuma dai, a ina na samu Yaya?”.     “AA mana, gashi nan ya tasani gaba sai masifa yake min”.     Wani irin zuuuuu zuciyar Maanal tayi, amma sai ta dake tai ɗan murmushi mai sauti da faɗin, “Ai gara dai ka lallaɓashi dan kasan shine mai baka auren nawa.”         “Shiyyasa ai nake haƙuri da mugun halinsa. Naji ni na ajiye kawun a gefe zan girmamashi, idan ya bani ke sai mu dawo dai-dai my queen.”      Nan ma murmushi kawai tayi batace komai ba. Shima sai ya saki batun AA ɗin ya miƙe ya fita daga ɗakin ya koma falo suka cigaba da hirarsu. Duk da ma dai shine ke maganar ita kam sama-sama ne. Bai cika damuwa da hakan ba saboda zuwa yanzu ya gama fahimtar ta akan miskilancin ta da rashin yawan magana. Jin tanata hamma yay mata sallama. Koda ya dawo ɗakin samun AA yay har yayi barci, sai shima kawai yay shirin kwanciyar. Sai dai abinda bai sani ba duk AA na jinsa, dan idanunsa biyu kawai yayi shiru ne. Sai da ya tabbatar RK yay barci sannan ya tashi zaune. Wayar RK ɗin ya ɗauka ya fita falo, yasan password ɗonsa, dan haka ya buɗe ya shiga masa bincike dalla-dalla. Sannan yay tsiyatakun da zaiyi a ciki ya dawo ya ajiye masa wayar sannan ya kwanta. Yana hararar RK dake barcinsa hankali kwance.....       😆😆An dai ji k... (Na daiyi shiru😂🤪) __________★         “Wai shi wannan tagumin na miye Baby? Ba komai ya wuce ba”. Fawzan ya faɗa yana kallon Nibras. A hankali ta janye tagumin da tayi, tare da sauke ajiyar zuciya. Sai kuma ta matsa ta kwanta a jikinsa kanta a saman ƙirjinsa. Ji take inama a jikin AA take haka.     “Jaan”. Ta kira Fawzan ɗin da sunan da take kiransa. Amsa mata yay idanunsa a lumshe yana shafa bayanta.         “Dan ALLAH ka kira Yaya AA a waya mana na ƙara bashi haƙuri. Kar yay barci da fushina”.      Ɗan jimm Fawzan yayi kafin ya buɗe idanunsa a kanta. Duk da maganar tata tayi masa wani banbarakwai sai ya daure ya ce, “Nibras na faɗa miki zai huce. Kema kin san halin Auta ai. Yana da zafi amma baida riƙo. Zuwa safe normal zaki ganshi kamar komai bai faru ba. Amma duk kinbi kin damu kanki. Please ajiye batun wani Auta a gefe zo kiga na nuna miki wani abu”. Bai bata damar magana ba ya haɗe lips ɗinsu waje guda. Kicin-kicin turesa ta shiga yi, sai dai bai mata da wasa ba. Dan in dai wannan wahalar ce ya saba sha a wajen Nibras a duk lokacin da yake buƙatar hakkinsa. Kuma a farkon aurensu ba haka take masa ba. Daga baya ne dai matsalar tasu ta fara. Sai sun sha uban daru wani lokacin ma ya nuna mata ƙarfi sannan. Amma bai taɓa faɗama kowa hakan ba saboda Fawzan akwai haƙuri. Ta ɓangaren zurfin ciki kuwa shi da AA suna kamancece niya..       Koda suka gama dai-daita tashi tai ta bar masa ɗakin. Da kallo kawai ya bita, zuciyarsa dai sai son kawo masa wani tunani take yana turewa. Daga ƙarshe ya miƙe ya shiga bathroom domin tsarkake kansa..... ________★       Washe gari suna breakfast a sashin Oum kowanne cikin shirin tafiya office RK ya sanar ma Oum batun zuwa Kano da yake son yi da kuma abinda zai kaisan. Har ga ALLAH sai da gaban Oum ya faɗi ta ɗan dubi sashen da AA yake har tana neman ƙwarewa da shayi. AA ɗin ne cike da dakewa ya miƙa mata ruwa yana mai tsatstsareta da idanunsa da suka ɗan juye..       (Magana ta ALLAH Uncle RK kana saka Oum da ɗanta a cakwakiya fa🥱 ka kiyaye mu😂🤣🏃🏃.) Murmushi Oum ta ɗan sakarma AA na yaƙe, tare da sanya masa albarka bayan tasha ruwan. Sai kuma ta maida dubanta ga RK da shima ke mata sannu. Amsa masa tayi tana jinjina kanta. Sai kuma ta maida hankalinta ga abincin tana juya abinda ta ke son faɗa a cikin ranta. Fin mintuna biyu sannan ta ce, “Ita Maanal ɗin ce ta baka dama Rafeeq?”.        “Eh Aunty, tun kwana biyar ma daya wuce. Jiya kuma muka sake maganar da ita dan nace miki yaje kd. Sai kawai naga nima ya kamata naje su Abbu su san da zancen shi da Baba Sardauna ayi a wuce wajen ko ya kika gani”.       “Hakan yayi, ALLAH ya zaɓa abinda tafi alkairi.”      “Amin ya rabbi”. RK ya faɗa fuska washe da murmushi. Miƙewa AA yay tsam, tare da ɗaukar wayoyinsa. Ɗagowa Oum da RK sukai suna kallonsa. Batare da shi ya yarda ya kallesu ba ya ce, “Oum na wuce office bye”. Sai kuma ya ɗan duƙo ya kama hannunta ya sumbata. Kafin ta samu damar yin magana har ya fice. Murmushi RK yayi da faɗin, “Uhmm Aunty wannan ɗan naki dai sai ke. Ko har yanzu fushin jiyan ne oho masa. Nace ya shirya muje Kanon wai shi Chaina zaije, haka ya balbaleni da bala'i daren jiya laifin matar Fawzan ya koma kaina”.       Murmushi kawai Oum tayi, “Ya dai faɗa ne kawai. Duka yaushe ya dawo ƙasar ma, balle a yanzu da suke kan project babba a Company.”         “Nima abinda na gani kenan, amma nasan sa kamar ɗan sama jannati yake ba wahala gantalin ke masa ba. Bara nima naje anata kirana daga asibiti. Komi kenan zan dawo mu sake tattaunawa dai”.     Kai ta jinjina masa tare da addu'ar fatan alkairi. Ya amsa da jin daɗi yana mai ficewa. Dan bayan uwa da uba a duniya ƴar uwar tasa da mijinta sune na biyu da yake matuƙar so da girmamawa. Yana musu kallon iyaye na biyu a rayuwarsa ne duk da suna amsa sunan yayu ne......       Wani irin gajiyayyen numfashi Oum ta sauke bayan fitar RK, sai kuma ta ajiye cokalin hannunta ta dafe kanta da taji yana mata nauyi. A hankali Abah dake kallonta ya kai hannu ya taɓata, firgigit ta dawo hanyyacinta, sai kuma ta zuba masa ido kamar yau ne ta fara ganinsa. Zaune ya kai a kusa da ita, tare da jimƙe hannunta cikin nashi sosai, cike da kulawa ya ce, “Fatima na mike damunki haka da irin wannan zurfin tunani? Ko akan Fawzan ɗin ne dai? Dan ALLAH ki kwantar da hankalinki,  jiya fa ina lura dake bakiyi wani barcin kirki ba sam, shin haihuwa bata ALLAH bace ba. Kuma lokaci ne”.       A hankali hawayen da suka cika mata ido suka shiga silalowa. Sai ta kauda kanta da sauri tana ƙoƙarin sharewa. Fuskar tata ya kamo cikin duka hannayensa, idanunsa cikin nata ya ce, “Zarah na kin san fa damuwar ki na tayar min da hankali, hakama yaranki da zarar sun ganki a damuwa hankalinsu tashi yake yi. Ki duba har na fita na sake dawowa saboda ban gamsu da yanayin dana fita na barki ba”.            “Kayi haƙuri Zaki na, in sha ALLAHU zan kiyaye. Zan kuma cigaba da musu addu'a su dukansu”.      “Yauwa haka shine dai-dai, ALLAH yay miki albarka kinji.”.     “Amin tare da kai kaima da yarana duka”.     Murmushi ya saki tare da jan hancinta kaɗan ya kashe mata ido ɗaya, ta saki dariya tana mai saka kanta a ƙirjinsa. Shima dariyar yayi yana rungumota. Sun jima a haka kafin ya ɗagota ya fara bata abincin a baki cike da kulawa.           “Gadanga!”.       “Uhmyim Fateeman Gadanga minene?”.      “Ajwaad da Rafeeq”. “Miya samu Ajwaad da Rafeeq ɗin?”. Sai da taja numfashi mai nauyi sannan ta ce, “Rafeeq ne yake cigaba da damuna akan aurensa da Maanal.”          Ɗan tsai Abah yay yana kallonta, sai kuma ya sauke numfashi shima yana mai furzar da iska. “To ni Fateema mi kike so nayi? Yaron kin nan ya cika murɗi. Tunda shi taurin kai ne aikinsa basai a bar Rafeeq ɗin ya aureta ba. Ni zanyi farin ciki da hakan, dan har cikin raina ina ƙaunar Yarinyar nan, har gobe tana a raina wlhy, zan so ta kasance a cikin zuri'ar nan tamu”.........✍️ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖8️⃣3️⃣ ______________ ........“Humm amma Gadanga kasan Auta na matuƙar son Maanal. Ka duba al'amarin nan, kada mu biye ta nashi zurfin ciki ne kawai ke damunsa. Ka duba yanda bayan samun lafiyarsa ya shiryo yazo ƙasar nan yayta wahalar nemanta, duk da bai fito ya faɗa mana ba ai munji a majiya mai ƙarfi akan ƙoƙarin sa.”        “Amma yanzu daya gantan wane mataki ya ɗauka?. Tunda kika bani labarin komai ai na sanya ido a kansa, amma ban taɓa ganin wani yunƙurinsa ba, ko gidan Shahidah bai taɓa zuwa ba sai dai su haɗu a wajen aiki. Ni kuma ba zanje nema a bashi auren yarinyata dole ba. Itama sai ta zaɓa ta darje. Idan kuma har Rafeeq ya mata zan tsaya tsayin daga na mata auren gata, shiyyasa ma ranar juma'a ɗin nan zamuje Kaduna ɗin. Mijin Asiyan na aurar da ɗa kuma ya gayyaceni, sai muyi amfani da wannan damar muje gareta duk da ina jin matuƙar kunya wlhy”.       Fuska sosai Oum ta ɓata tana kallon Abah. Idonta cike da ƙwalla ta ce, “Amma ya kamata ku mana uziri, ku fahimci Ajwaad, sannan ita kanta Maanal tana son shi ai, ka zauna da shi kuma zakaji ta bakinsa. Zuwa Kaduna kuma ALLAH nima kunyar sake haɗuwa da Asiya nake yi, shiyyasa naketa tufka da warwarar tunkararta. Dama Majdiya ta faɗa min zancen bikin. Amma dan ALLAH ka duba al'amarin nan na Ajwaad a sassauta masa”.          “Ai in dai bashi ne ya kawo min zancen ba bai isa na masa ba. Kema kuma ban yarda ki saka shi ya min ba. Ki barsa ya mangantu a karan kansa ni naga ƙarshem miskilanci.”     “Amma Gadanga.......”   Kai ya girgiza mata tare da ɗaura yatsarsa akan lips ɗinta. Idanunsa a cikin nata ya ce, “Please Fateema ki fahimceni, in dai maganar Ajwaad ce na gama ta a gidan nan. Zuwa Kaduna kuma ku shirya ku duka zamu je”.        “Na fahimceka, amma hukuncin ya mana nauyi a sassauta mana”.     “Sassaucin a hannunku yake ai. Sai dai ina sake gargaɗi bana buƙatar fargarwa daga gareki a kansa.”     Rasama abin cewa Oum tayi, sai kawai ta zubama Abah daya miƙe ido. Sallama ya mata ya fice yana sanar mata ya koma wajen aiki...     Da sauri Saheeba tabar kitchen ɗin Oum ɗin ta baya, da alama duk tattaunawar Abah da Oum a kunnenta ne. Kai tun zaman RK da AA ma tana a sashen. Ta shigo ne wai zata amsarwa su Naufal abinci dan ita yau ta makara da girki, masu aikin sashen Mamy kuwa ba wani iya abinci sukai ba, ita ko Oum da kanta take girki bata saka masu aiki. Shine taci karo da hirar RK da Oum. Mai aikin Oum ta bama abincin su Anum tace ta kai musu, idan kuma takai kada ta dawo kitchen ɗin sai ta kirata. Shine ta laɓe tana saurare. Bayan fitar RK harta fito sai ta hangi Abah daya dawo, shine itama ta dawo da sauri ta sake laɓewa taji komai nan ma.       Da sassarfa ta isa sashen Mamy, masu aiki ne keta faman gyara, ganin bata a ƙasa ta haye sama nemanta. Acan kuwa ta sameta zaune a dining zata karya. Zama tayi itama a saman dining ɗin ta gaisheta. Mamyn ta amsa tana kallonta, dan yanayinta ya nuna da zance tazo. Saheeba kuwa ta cigaba da faɗin, “Humm Mamy da ga sashen matar can nake. Yau dai mun sami tabbacin itace ta dawo da yarinyar nan rayuwar Ajwaad. Tana can tana tsara Abah akan Ajwaad ya auri yarinyar shi kuma yana botsare mata. Wai ashe kin san bayan samun lafiyar Ajwaad tafiyar da yace zai yi ɗin nan ya barmu a can Nigeria yazo neman yarinyar nan”. “Nigeria?”. “Wlhy kuwa Mamy nan yazo ya dinga nemanta lungu da saƙo. Ni wlhy yanzu ma wani tunani yazo min, wai minene ma'anar sunan kamfaninsa na agogo?”. Tsai Mamy tai tana kallon Saheeba zuciyarta na wani kalar tsaitsinkewa. Sai kuma a hankali ta girgiza kanta. “Ban sani ba Saheeba. Ban kuma taɓa maida hankali akan na sani ba. Wani abu su Fateeman sukace akan sunan kamfanin?”. “A'a, basu ce komai ba. Nice dai nayi tunanin yanzu.” Ture plate ɗin abincin Mamy tai gefe, batare data sake cema Saheeba komai ba ta miƙe. Bedroom ta nufa, hakan yasa Saheeba rakata da idanu tana wani ƙyaƙyƙyafta su. Sai kuma ta miƙe tana murmushi. Sashenta ta nufa. Tana zuwa tai kiran uwarta a waya ta zayyane mata komai. Daga can mamanta tai ƴar dariya da faɗin, “Kai Saheeba ALLAH ya shirya min ke. Yanzu to mi tace?”. “Tashi tai ta shige ɗaki Umma. Wlhy na fahimci idan ba wuta-wuta mukai mataba yanzu zata canja ra'ayinta ne akan auren Nuratu da Ajwaad maƙiya sumana dariya. Kin dai ji abinda malam ya faɗa ai yarinyar can Huznah take komi shegiya ita da uwarta ba zaune suke ba. Ga kuma wannan maƙallaiyar mayyar Maanal ɗin da danginta, munafukar can kuma ta ɗaure musu ƙugu, idan ba munafunci ba ta bari ƙanin nata ya auri yarinyar mana ba sai suje suyi zumuncin ba da ƙyau” “Ke ko tayi haka tunda tasan burin yarinyar da iyayenta cin dukiya ne, ai gara aci wadda ba tasu ba. Ta ƙaninta kuwa aita ubansu ce akwai gadonta a ciki. Ai Yaya Kamila ta tafka babban kuskure a rayuwarta wlhy da gyarashi sai dai ALLAH kawai. Yoni ina zan iya mallakama kishiya ƴaƴana dan neman wata soyayyar mijin banza can. Gashi nan har yanzu bata sami yanda take so a mijin ba ƴaƴa kuma sun nuna basu santa ba”. “Ai Umma sai ma kina gidan nan zakiga ikon ALLAH. Jiya dai mai aikina ke faɗa min rigima Fawzan yasha da wacan sakaran. Ban dai gane kan zancen ba sai na bincika dan wai har ga haɗa kaya zata bar gidan ita Mamyn ta hanata, a sashen uwar tasu akai shari'ar, taga kuma Ajwaad ɗin ya fito a fusace”. “Hummm ita wannan gaɓuwar ai ban san irinta ita da uwarta ba. Kamila ce bata jin shawara, amma sai da aka faɗa mana yarinyar sakarai ce gata da boko sun maidata shashasha amma tace zata bari ai. ALLAH ya ƙara suyita yi mu ƴan kallo ne”. “Wlhy kuwa Umma. Bara naje anjima zan kiraki”. “To shike nan sai na jiki”......      ___________★         Tun daga gate kowa ke faman bin motar da kallo. Bawai dan basu san motar ba ne. A'a kowa ai yasan ta boss ce. Dan mota ce fitacciya kasancewar irinta a Abujar kaɗan ce ma, ba kuma ko yaushe yake hawanta ba shi kansa. To amma boss kusan mintunansa goma da isowa tuni ma har ya shige office. Mamakin waye kuma ya zo da motar a yanzu ya sakasu binta da kallon ƙurulla. Guri Manaal ta samu tai parking a parking space ɗin da boss ne kawai ke ajiye motarsa. Batai mamakin ganin motarsa a fake ba, dan tasan ya isa shigowa, saboda ita ta ɗan makara yau ɗin. Fitowar ta a motar yasa kallo ya koma sama ga kowa. Tayi ƙyau sosai cikin riga bubu ta lass ruwan toka da ratsin orange, sai ƙaramin veil shima orange data yana a kanta. Fuskarta tayi wani irin fayau saboda ƙitson da tasha jiya. Yanda ɗaurin nata ya ɗan zama baya kamar ta saka hula ya bayyana kitson kaɗan. Ga ƙamshinta mai sanyi na tashi da har sai ka kasance a kusa da ita gab zaka ma iya jinsa. Kamar yanda ta saba duk wanda ta haɗu da shi takan gaisheshi ta wuce abinta, yayinda su kuma suka fara ƙusƙus na gulma akan ganin ta a motar boss. A Maimakon Office ɗinsu kai tsaye sama ta nufa, bayan ta shiga cikin elevator ta gaisa da wanda ta samu ciki kasancewarsu manyan ta.          Yanda AS ya wani gaisheta kafin ita ta gaisheshi yaso bata mamaki, amma sai ya dake ta amsa masa tare da ajiye key ɗin hannunta a gabansa. A taƙaice ta ce, “Kaba boss”. Kafin ya ce komai ta juya abinta ta fice. Da kallo AS ya bita, tabbas yasha ganin ƴammata ƙyawawa masu ji da kansu suna zarya a companyn nan saboda boss, kuma yasha ji a ransa sun dace da shi, amma magana ta ALLAH shi da kansa ya yarda yarinyar nan ta musamman ce, irin musamman ɗin da komai nata yay dai-dai da boss. Inama ace zai so ta. Hummm ALLAH sai yafi kowa murna. Da wannan tunanin ya miƙe tare da ɗaukar key ɗin ya nufi CEO office ɗin. Sai da yay knocking aka bashi damar shiga sannan. Kamar kullum sarakin na zaune cikin kujerar office. Baƙaƙen suit ɗin jikinsa sun wani sake ƙawata cikar kamalarsa, yanda yay busy sosai zaka san aikin gabansa mai muhimmanci ne matuƙa. Dan ko ɗagowa ya kalla AS bai ba. Kansa a duƙen ya furta, “Lafiya dai Ahmad?”.       “Eh lafiya Lau sir, dama Sister Maanal ce ta kawo key wai a baka”.     Cak ya tsaya daga aikin da yake yi, kafin ya ɗago manyan fararen oily idanunsa gently ya saukesu a kan AS. Dole AS ya rissinar da nasa, dan kallon ya masa nauyi da yawa. Shima AA ɗin sai ya janye nasan ya maida ga aikinsa.                 “Ita bata san hanya bane zata aiko ka? Ka maida mata ta kawo da kanta”.     Murmushi ne ya so kufcema AS, amma ya dannesa da ƙyar. Cike da girmamawa ya ce, “Okay sir, na barka lafiya”. Daga haka ya juya ya fita. Ɗagowa AA yay ya ɗan zubama ƙofar ido, sai kuma ya shafi ƙasumbarsa ka ɗan ya sake maida hankalinsa kan aikinsa....        _________★     Zaune take tana aiki ita da Yaqub daya jawo kujerarsa kusa da ita, nuna mata wasu abubuwa yake da take neman ilimi a kansu a cikin computer ɗinta. Yayinda munafukan nasu su Deeni ke faman zinɗensu da baki. Sai da AS yay knocking duk suka ɗago, batare da ya jira umarninsu ba ya turo glass door ɗin ya shigo. Kai tsaye ya wuce inda Maanal ɗin take bayan ya musu gaisuwar gaba ɗaya. Murmushi ya ɗanyi tare da ajiye mata key ɗin a gabanta da ƙaramar takarda daya rubuta abinda boss ɗin ya faɗa, dan haka kawai yaji shi kam bazai iya maimaita mata da bakinsa ba. Kallon key ɗin Maanal dake binsa da kallo tayi, sai kuma ta sake maida idanunta a kansa. Takardar AS ya nuna mata kawai, batare da yace komai ba ya juya ya fita. Suko duk suka rakashi da idanu, sai kuma suka dawo da dubansu ga Maanal ɗin data basar kamar komai ma bai faru ba ta cigaba da aikinta. Ba kuma ta taɓa key ɗin da takardar ba. Ji suke kamar su taso su ɗauka su buɗe suga mike a ciki, dan suma dai gulmar zuwan Manaal ɗin a motar Boss harta iskesu. Kai yau hatta da Yaqub ji yake kamar ya ɗau takardar ya duba. Amma dai sai ya dake.       Haka suka cigaba da ayyukansu har lokacin break yayi. Maanal da tasan ba salla zatai ba bama ta motsa ba. Dan da safen nan taci karo da baƙonta na wata. Sai dai koda Yaqub yace ta taso suje catai masa yaje tana nan zuwa zata ƙarasa wani abu ne. Badan yaso ba ya fita, suma sauran duk sun fice sai ita kaɗai. Aikinta ta cigaba da yi, dan Maanal akwai himma da nacin aiki, kamar yanda take da nacin karatu. Can idonta ya sauka akan takardar nan da key, ɗan zuba mata ido tai, sai kuma ta kai hannu ta ɗauka ta warware. _Kiyi hakuri boss ne yace na dawo da shi ki kai masa da hannunki_. Iya abinda aka rubuta kenan. Kanta kawai ta girgiza ta naɗe takardar ta jefa a kwandon sharar su dake office. Shi kuma key ɗin ta jefa shi a wani ɗan basket mai ƙyau da take zuwa kayan sweet da take sha, sai dai yanzu babu komai a ciki dan ta shanye ta kuma mance tazo da wasu. Ta sake maida kanta a aiki bayan ta ɗauka meat pie ɗaya ta fara ci. Kamar abin almara taji ƙamshin mayataccen turarensa na sake ƙarfi a hancinta. Da farko ta share da tunanin iska ce ko hancinta ne. Sai kuma dai taji abin na neman wuce wuri dan haka ta ɗago.        Samun zuciyarta tai da girgizawa sakamakon saukar idanun nata a kanshi, sai kuma ta janyesu da gudun tsiya ta hau waige-waige a office ɗin nasu alamar dai tabbatar da babu kowa dai ko........✍️       🤣Ko waye oho. 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖8️⃣4️⃣ ______________ ........A hankali ya wani kalar taɓe baki. Cikin halin ko'in kula da ganin yanda ta ke waige-waigen ya ƙarasa shigowa cike da izzar nan tasa da ƙasaita hankalinsa a kwance. Sai da yaje jikin desk ɗinta ta kashe-kashen daya kasance daga ita babu kowa sannan ya tsaya. Kaɗan ya ɗosana jikinsa a desk ɗin yay irin tsaiwar maza tare da harɗe ƙafarsa akan ɗayar daya dogara, gaba ɗaya ƙarfinsa naga desk ɗin. Idanunsa har yanzu akan Manaal da kamar tayi suman zaune ne ma oho mata😂.          Babu wani ko ɗar balle tunanin wani ya shigo ya gansa ya kai hannu ya zare meat pie ɗin dake hannunta da take ci. Bakinsa ya kai ya gutsira, ya lumshe idanu yana mai taunawa a hankali...      “Amma kasan hakan na nufin sakani a masifa ko? Dan ALLAH dan mi zaka zo nan a wannan lokacin da kowa ke can yana salla kai kana nan ɗaukar magana?”.        Shiru kamar bai jita ba. Sai da ya mula dan kansa sannan ya buɗe lumsassun idanun nasa a kanta. Cikin halin ko'in kula ya cigaba da cin meat pie ɗinsa hankali kwance. Marairaice masa tai sosai idanunta na cika da ƙwalla, dan ta fahimci masifar bazata kaita ba. “Please dan ALLAH ka fita kada wani ya shigo ya ganka anan ka jamin surutu. Salla fa akeyi”. Da kaga yanda take maganar kasan bata da nitsuwa, dan sai leƙe-leƙe take kamar mai shirin yin satar naman miya a gidan soja.       Baki ya sake taɓewa da janyo bowl ɗin da meat pie ɗin yake ya sake ɗaukar wani. “K miya hanaki zuwa sallar?”.            “To ina ruwanka dan ALLAH da abinda ya hanani, ni dai dan ALLAH ka tafi kada ma'aikatanka su sakani a bakin duniya”.        “Tunda babu ruwana da abinda ya hanaki zuwa salla. Kema ina ruwanki da ganina anan to. Naga dai company na ne, ina da damar shiga duk inda nake so a lokacin da nake so ko”.          Yanzu kam sosai hawayen suka ciko mata idanu, ta tsatstsaresa da kallon da bama tasan tana yi masa ba. Cike da rauni ta ce, “Kadai fi son ka ganni a masifar ko Ajwaa....” ta kasa ƙarasawa saboda kallon daya watso mata. Baki ta sake tunzurawa sosai. Baki ya ɗan laɓe ya janye idanun ya sake kai hannu zai ɗauka meet pie ɗin da ya rage saura biyu kawai. Ai babu shiri ta kai hannu ta buge nasan cike da tsiwa ta ce, “Malam wai miye haka zaka cinye min abinci”.        Bai kulata ba ya ɗauke bowl ɗin ma gaba ɗaya, sai da ya gutsira sannan ya kalleta cike da iskanci yana wani ƙanƙance su ƙasa-ƙasa ya furta, “Ko mai meat pie ɗin ta kama ba sai na.....”            “Na shiga uku. Sai kayi mi?..” Maanal ta faɗa tana mai waro dukkan idanunta a kansa. Kaɗan ya rage ya kwashe da dariya. Amma dai ya dake ya basar. Sai ma dan neman magana ca yay, “Ni kibar min wannan kallon karna ƙware. Sannan miye wani kin shiga uku bana son fassara zance. Sai nayi ƙyautarki nake nufi”.     Harara ta watsa masa ta koma kan kujerarta ta zauna. Dan ta fahimci idan ta biye masa ALLAH zama ta iya zubewa a wajen. Pretending ɗin danna keyboard ta koma yi, shi kuma ya cigaba da cin meat pie ɗin yana duba drawing papers na zanen da tayi dake yashe a desk ɗin. A haka ya kammala cinye mata tas babu ko tausayi balle ya rage mata, ya ɗauka ruwan da tasha ta rage ya shanye. Sannan ya maida gaba ɗaya hankalinsa ga papers ɗin. A bazata taji saukar furucin sa cikin kunneta.         “Kiyi gaggawar dakatar da Rafeeq yin abinda kika saka shi, in ba hakaba zaki haɗa rigimar da ke kanki baki san ƙarshenta ba”.       Kallonsa kawai ta ɗago tana yi dan kamar ba shine yay maganar ba. Dai-dai nan Ema... Da Zaharadeen suka shigo suna dariya. Cak suka tsaya tare da jan birki saboda cin karo da abinda basu yi tunanin gani ba. Boss da kansa a office ɗinsu. Tashin hankali. Cikin firgicewar bazatar ganinsa da sukai suka shiga gaisheshi. Sai lokacin ya ɗago ya zuba musu kaifafan idanunsa. Yayinda Maanal ke jin kamar ta fasa ihun da sai Abuja tayi girgiza gaba ɗayanta. Dai-dai nan suma wasu biyun suka sake kawo jiki,  ai a sukwane suka taka birkin da yafi nasu Deeni. Shiko tuni ma ya ɗauke idonsa a kansu ya cigaba da dube-dubensa kamar bai san da kowa ba a wajen sai kansa. A haka har suka gama shigowa, babu kuma wanda zai shigo bai taka birkin firgici ba da ganin CEO ɗin. Shi kuma yaƙi kulasu sai jeruwa suke kamar ƴan layin tuwon dare a boarding school (lolx🤣😂). Maanal kam ai ta kasa kallon kowa, tai ƙasa da kai kamar maƙaryaci a gaban sarki. Sai ta gefen ido ake ƴar kallan kallo tsakaninta da su Yaqub.       Fin mintuna biyar sai da ya mula dan kansa ya ajiye Drawing papers ɗin ya gyara tsaiwa sannan ya ɗago idanu ya sauke a kansu bayan ya zuba duka hannayensa a aljihun wandon suit ɗinsa. Babu alamar wasa a tare da shi ko sassauci ya ce, “Waye Abideen a cikinku?”.         Cikin tashin hankali Abideen ya ce, “Nine sir”.      Kallon sama zuwa ƙar AA ya masa. Sai kuma ya ja idanunsa ya maida a kan fuskar Abideen ɗin yana sauke masa wani zafafaffen kallo. Tsohon mintuna biyu kafin ya janye a matuƙar daƙile. Pen ya ɗauka a gaban Maanal da ƙaramar takarda ya fara rubutu, sai kuma can ƙasa ya furta, “Nawa suka biya ka?”.         A tare su Zaharadeen har ma da Maanal suka maida kallonsu ga Abideen da duk ya rikice. Rantse-rantse ya fara. AA da ko nuna yana ma jinsa baiyi ba ya ajiye pen ɗin da short note ɗin da yay a gaban Maanal ya miƙe sosai, batare da ya sake kallon kowa ba yay hanyar fita yana faɗin, “Ka tattara komanka ka saman a office”. Daga haka ya ratsa ta tsakkiyar hanyar da suka dare suka bashi ya fice abinsa.      Shi ko Abideen hankali tashe yake kirama kansa ya shiga uku ya lalace. Sai da AA yay nisa sannan su Yaqub suka sami damar baibayesa da tambaya. Maanal dai suman zaune tayi da mamakin mugun sabon halin da AA ya ɗauka yanzu. Koda yake tuni fa yana da mugun halinsa, kawai dai ƙuruciya yasa bata fahimta a wancan lokacin. To dan ALLAH in ba mugun hali ba taya zaka zo ka turke staff ɗinka a bainar nasi kana masa wannan kausasan tambayoyin na nuna isa da izza. Wai mi masu kuɗi suka ɗau kansu da rayuwarsu ne?......       “Sis.. Maanal dan ALLAH kizo muje ki bashi haƙuri, wlhy zan faɗa masa gaskiya....” furucin Abideen da ke binsu da wannan furucin su duka a birkice ya dawo da ita a hanyyacinta. Yayin da su Zaharadeen ke ƙoƙarin kamashi dan ya nutsu asan mafita. Amma ina duk ya ruɗe. Sai da ƙyar suka danna shi ya zauna a kujera. Ema ya bashi ruwa yasha.       “Ni dai shawarar dazan baka Abideen ka tashi kaje kasan dai boss baya son jira. Kuma tabbas tunda ya shigo office ɗin nan da kansa case ɗin nan naka babba ne. Amma ka rufama kanka a siri ka gaya masa gaskiya a tambaya ɗaya nasan zaka iya samun sassauci tunda ya tsani ƙarya ko kwalo-kwalo akan laifi kaima ka sani”.      Musa ne da wannan magana cikin damuwa. Dukansu sun gamsu da shawarar Musa ɗin. Dan haka duk suma suka shiga cema Abideen ɗin ya tashi yaje. Da ƙyar ya iya miƙewa ya fita. Duk suka bisa da kallo. Sai da ya fice gaba ɗaya Zaharadeen ya kalla Maanal cikin sauke ajiyar zuciya da ƙwarewa a gulma. “Sis... Manaal wai tun ɗazun boss yana nan ne dama? Sannan yayi wata magana ne?”.       Karan farko Maanal ta watsa masa harara. Cike da tsiwa ta ce, “Miyyasa baka tambayesa ba sanda yake nan? Ko sai ni marainiyar wayonka”.       Mutsut Zaharadeen ya haɗiye gulmarsa. Dan wani irin kwarjini ma yaga Maanal ɗin ta ƙara masa. Ga shi ta wani tsare sa da mayun idanunta masu haske. Harara ta rakashi da shi, sai kuma taja siririn tsaki ta maida kanta ga aikinta. Akan rubutun da yay ta sauke su. _“Ki saman ki bani amsata nan da awa ɗaya a office, in ba hakaba wlhy zan dawo da kaina na ɗaukeki na kaiki. Kar kiga ba canja topic yanzu tausayi kika bani”_. Muƙut ta haɗiye yawun daya maƙale mata a maƙoshi. Ita kam ga shiga uku da mutumin nan. Kafin ta samar ma kanta mafita Yaqub ya zauna dan su cigaba da aikinsu. Dole ta haɗiye komai da bashi hankalinta dan aikin mai muhimmanci ne. Sai dai kaso sittin na hankalinta ya tafi ga al'amarin AA ne da ƙarfin halinsa..... _________★          Tunda taga awa ɗayan daya bata ya kusa cika hankalinta ya ƙara tashi, dan ta tabbatar AA baya faɗar magana bai cikata ba, tun ma kan yakai haka. Ta kasa samun nutsuwa, ta kasa tsaida zuciyarta waje guda. Ga Abideen har yanzu bai dawo ba tunda ya fita. Office ɗin nasu yanzu kam yay tsitt kowa damuwa shimfiɗe a fuskarsa. Sai dai fa kowa ya maida hankali akan aiki tuƙuru. Ganin fa saura mintuna biyar rashin nutsuwarta ya ƙaru. Kamar ance ta ɗago ta kalla ƙofa sai idonta akan AA ya wani kafe office ɗin nasu da kaifafan idanunsa. Ai bama tasan ta miƙe ba har Yaqub na ɗagowa shima ya kalleta. Key ɗin motar nan da wasu documents ta ɗauka tana faɗin, “Sorry Yaqub ina zuwa. Na manta CTO yace na kai masa documents ɗin nan tun ɗazun.” bata jira amsarsa ba ya fito. Dai-dai AA na gittawa da baƙonsa da alama ya nuna rakkiya ya masa, tsabar wulaƙanci yi yay kamar bai ganta ba, sai da ta ɗan kallesa taga ya mata wani salo da yatsu biyu ta baya yana saki wani ɗan iskan murmushi. Jitai wani ƙululu ya tokare mata maƙoshi. Amma babu yanda ta iya dole ta nufi elevator. Tana isowa AS ya bata umarnin ta shiga kawai. Harararsa tayi sannan ta wuce fuuuu ciki, tako bugo ƙofar har sai da AS ya ɗan zabura, dan harga ALLAH tsoro yaji saboda abin yazo masa a bazata..........✍️ 🤣🤣 An dai ji kunya AS da tsoro.😂 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖8️⃣5️⃣ ______________ .........A nutsensa ya turo ƙofar ya shigo. Ya kuma maidata ya rufe sannan ya shiga takowa cikin office ɗin. Duk da ƙamshinsa da motsinsa bai sa ta motsa daga tsayen da take ba. Sai ma sake kumbura take yi taf har ya ƙaraso bayanta daf ya tsaya. Tsabar yanda ya fita tsaho har tsakkiyar kanta yana gani tsaf, gently ya ranƙwafo a bayan nata batare da jikinsa ya taɓata ba ko kaɗan, fuskarsa a saitin kunnenta yana busa mata numfashinsa saman dokin wuya cikin raɗa ya furta, “Ko sai na ƙarasar dake ɗin ne dai saman kujerar?”.       A wani irin zabure Maanal tai gaba camak kamar wadda aka sarrafa da remote. Sai kawai hangota yay a saman kujerar. Murmushi ya saki da wani lumshe idanu sai kuma ya buɗe su yana miƙewa tsaye sosai ya shafo kwantaccen gashin sajensa zuwa wanda ya zagaye madaidaicin bakinsa. Maimakon yaje ya zauna a kujerarsa sai ya zauna visitor chair ɗin shima dake kallon wadda ta zauna. Basket ɗin saman desk ɗin nashi ya jawo, ya ciro ƙyawawan kulolin da aka shirya abinci. Tuni wani irin ƙamshi ya cika mata hanci, duk da shekaru sun shuɗa, ƙamshin girkin Oum bazai taɓa shuɗewa daga zuciyarta ba sam kamar yanda tasan shima kansa Ajwaad bazai taɓa manta na Ammienta ba. Dan haka ta fara satar kallon abincin. Sai da ya gama zubawa dai-dai cin mutum ɗaya sannan ya sake matsowa sosai da kujerar, sai dai duk da hakan sam jikinsu bai taɓa na juna ba akwai ɗan space. Abincin ya ɗebo a spoon ya kai bakinta. Ƙin buɗe bakin tayi, shiko ya wani zuba mata idanu. Hawaye ne suka fara taruwa a nata idanun, dan haka ta kauda kanta gefe a hankali tana mai haɗiye abinda ya tokare maƙoshinta. Shima idanun nasa ne suka kaɗa sosai, amma da yake namijin duniya ne sai ya saki ɗan murmushi irin na danne damuwar nan. Muryarsa da wani kalar sanyi da kulawa ya furta, “Karfa na cinye ki dawo kina min rigima”. Shuuuuu hawayen da take faman riƙewa suka ziraro daga idannunta tai murmushi, wasu abubuwa ne masu nauyi da suka shuɗe ke tsikarin zuciyarta, ƙirjinta ya mata nauyi matuƙa. Slowly ya kauda nasa kan shima daga kallonta, idanunsa sun sake masifar kaɗewa. Kusan minti ɗaya suna a haka kafin ya juyo, tissue dake saman desk ɗinsa ya zara biyu ya miƙa mata batare daya kalleta ba. Itama bata kallesan ba ta amsa tissue ɗin, hawayen ta share, tare da dunƙule tissue ɗin cikin hannunta taƙi zubarwa. “Ka kori Abideen ne?”. Ta faɗa batare data kallesa ba har yanzu. Shi kam juyowa yay ya sauke nauyayyun idanun nasa a kanta, sai kuma batare da ya bata amsa ba ya furta, “Ci abincin first”. “Ni bana jin yunwa.” “Na sani”. Ya bata amsa a taƙaice yana sake kai spoon ɗin bakinta. A hankali ta furta, “Bani zanci da kaina” tana kai hannu zata amsa spoon ɗin. Matsar da hannunsa yay kaɗan yana zuba idanunsa sosai cikin nata. Dole tai ƙasa da nata ta buɗe bakin kaɗan. Ƙaramar ajiyar zuciya sukayi a tare bayan ya zare spoon ɗin ita kuma ta fara tauna abincin a hankali... Lips ɗinta kawai dake motsi yake kallo, sai kuma ya ɗan murmusa kaɗan da faɗin, “Kin tuna ranar da kika fara girki, da irin abincin nan kika fara har na samu wannan ciwon?”. Yay maganar yana kallon gefen babban yatsar hannunsa na dama gab da wajen tafi. Itama hannun ta kalla, dai-dai wajen akwai madaidaicin tabo da akallo ɗaya zaka fahimci sanda aka jisa ba ƙaramin ciwo bane. “Oum!! Mamy!! Babban yaya ku kawo taimako hannun Besty ya gundile, ya gundile Abah kalla jini, wayyo Yaya F mun bani Besty ya zama mara hannu”. Ya faɗa yana kwaikwayon ƙaramar muryarta a wancan lokacin. Ai bama tasan ta sanya dariya ba. Taja mayafinta ta rufe fuskarta tana mai kifeta a desk ɗinsa komai na dawo mata kamar a yanzu yake faruwa. Shima dariyar yake sosai kamar ba shi ba. Ya ɗan girgiza kansa... “Kai yarinyar nan kinyi rashin ji wlhy. Kefa kika jimin ciwon, amma kika fini ihu da raki da cika kunnen mutane, ban isa kuma nace kece ba ki isheni da rigima da tsiwa. Ai naci girkinki na farko da wuya dai”. Batare data ɗago ba ta ce, “Amma ai kaine kasa na ji maka ciwon ko, ba kaine kace na yanka albasan a hannunka ba”. “Amma sai nace ki yanka ni? Anya bazan ramaba ma yanzu?”. Da sauri ta ɗago tana waro dukkan idanunta a kansa, fuskarta tuni ta ƙwaɓe da shagwaɓa ta ce, “Kuma sai ka rama ɗin?”. Shima kallon nata yake sosai cikin ido, sai kuma a hankali ya rissinar da nashi yana mai girgiza kai. “Zanyi tunani, idan da yiwuwar na yafe to”. Baki ta tura tare da masa harara, shi kuma ya taɓe nasa yana sake kawo mata abincin daya ɗibo a spoon saitin baki. Kafaɗa ta maƙe masa zatai magana ya ce, “Shiiii”. “To ka bani zanci da kaina”. “Kin tabbatar?”. Da sauri ta jinjina masa kai. Plate ɗin ya miƙa mata babu musu. Dan shima dai ya fahimci idan bai batan ba za'a iya samun matsala. A hankali ta cigaba da cin abincin, sai kuma ta sake ɗakko masa batun Abideen kodan kauda wannan kallon da yake mata. Idanun nasa kuwa ya janye, sai kuma ya a harɗe hannayensa a ƙirji da kwantar da jikinsa a kujerar sosai. Tsohon minti ɗaya kafin ya amsa mata da. “Miye damuwarki wai da zancensa? Ko shima saurayin naki ne? Dan naga ke samarin naki basu da adadin ƙirga”. “Eh mana, farin jini ai kenan, ko kuma kana kishi ne?”. “Mizai sa nayi kishi kuwa ina matsayin Yaya. Kidai sani sai na tantance wanda ya dace kozan bashi ke”. Har ƙarƙashin rai zancen nashi ya soki zuciyar Maanal. Amma sai ta dake itama cike da basarwa ta ce, “Ba damuwa Yayana, ai duk yanda kayi dai-dai ne. Amma dai inada zaɓina gaskiya, nasan kuma bazaka min auren dole ba, kaima shine zai kasance zaɓinka ai ko?”. Ta ƙare maganar cikin salon waro idanunta a kansa. Wani hayaƙin takaici ne ya turniƙe sa, dan har launin idanunsa sun sauya. Janyesu yay daga cikin nata batare daya amsa mata ba. Itako saita wani ɗage kafaɗu da ɗan taɓe baki. Ta ce, “Koda yake ai kasan zaɓin nawa ma. Kai dai kawai ka fara shiri nan da wata biyu zaka aurar da ƙanwarka in sha ALLAHU. Dan Rafeeq ya tabbatar min baya son ya wuce hakan, nima kuma hakan nafi so. Dama ya kawo min ƙararka daren jiya”. Da ace Maanal na kallon kalar mugun kallon da AA ke mata data tsuke bakinta, koda yake tana jinsa a jikinta. Amma ta daure ta danne abinta. Karo na farko yaja tsaki. Kallonsa tayi, amma shi kuma sai ba kallonta yake ba yanzu. Hasalima ya jawo laptop dake a saman desk ɗinne kamar a fusace. Gabanta ya tura, babu wasa a muryarsa ya furta, “Ki duba za'a tura miki saƙo a email ɗinki. Next week akwai tafiyar da kamfani zai yi har da ke ciki zuwa ƙasar Chaina. Tafiya ce ta kwana goma zuwa sati biyu. Wannan zanen nake son ki duba min shi kafin lokacin tafiyar, kije da laptop ɗin”. Da mamaki ta ce, “Kamar ya? Amma dai kasan baza'a barni a gida ba, dan mi zaku saka sunana?”. “Saboda dolene kiyi tafiyar”. Dangwarar da plate ɗin abincin hannunta tayi, tare da faɗin, “Idan na ajiye aikin gaba ɗaya fa?”. “Wannan ne baki isa ba ai”. “A matsayinka na wa?”. “Mi kike ci na baka na zuba”. “Ajwaad kana shigar min hanci da yawa fa”. “Ki fyatoni kawai ki huta mana”. Rasama abin cewa tayi dan takaici. Shi ko da yasan ya kaita maƙura idanu kawai ya zuba mata cike da kallon ƙurullar daya saka illahirin jinin jikinta yamutsawa. Zuciyarta ta shiga kumburowa kamar ƙwaɓaɓɓiyar fulawar burodi bugun ƙato. Da ƙyar ta danne rawar da muryarta ke neman yi cike da masifa ta ce, “Wai wannan wane irin haramtaccen kallo ne dan ALLAH. Nifa wlhy ana takura rayuwata, ana shiga haƙƙinna, idan ba'a son aikin nawa a koran a kamfanin mana.....” daga ƙarshe ma harshen nata ya harɗe ta yanda ita kanta bata ma fahimtar abinda take faɗa. Shi dai ya zuba mata ido kawai yana hukuntata da su. Sai da tayi mai isarta ta gama sannan ya tura mata goran ruwa gabanta.      “Ai bance ina so ba”. Ta faɗa cike da tsiwa. “Hakane”. Ya bata amsa shima baki a taɓe. Sai kuma ya tsuke fuska kamar bashi ba ya gyara zamansa ƙafafu a harɗe hakama hannuwansa harɗe a ƙirjinsa. Babu alamar wasa a tattare da shi ya furta, “Kinyi abinda na saki?”.        Harrarsa tayi, duk da yanayin nashi ya sa zuciyarta shiga tsoro, amma a dake ta ce, “Kai ka isa ne ka sakani abu nayi?”.     “Oh haka kika ce?”. Baki ta murguɗa masa kawai. “Hummm ki cigaba da min wannan gatsinan zanyi maganinki soon. Na kuma baki nan da gobe ki dakatar da Rafeeq daga yaudarar da kike son masa. Idan ba hakaba zan baki mamaki”.. Murmushi tayi mai ciwo da zuba masa idannunta da suka kaɗa. “Oh mamaki? Ai ka daɗe da bani mamaki tun shaiɗan na baƙauyensa. Ajwaad ka daina wahalar da kanka da tunanin wannan abubuwan da kakeyi zaisa na ji tsoronka. Kasa a ranka ni Maanal matar Rafeeq ce in sha ALLAHU. Ina raga maka ne saboda Oum da Abah da Mamy, amma wlhy idan ka cigaba da shiga sabgata zaka sha mamaki na”.     Daga haka ta miƙe tana ajiye masa key ɗinsa tai ƙoƙarin wucewarta. Amma sai ya saka mata ƙafa babu shiri ta koma cikin kujerar daɓar ta sake zama. Cike da isa ya ƙara jawo tashi kujerar gabanta ya wani tattare ko'ina ta yanda ko space ɗin fitar numfashi mai ƙarfi bai rage mata ba. Idanunsa da suka juye gaba ɗaya ya sauke a cikin nata, ya kuma hanata janyewa duk da ƙoƙarin hakan da take yi. Sai kawai taji kamar ta saki kuka ta huta.        Wani ɗan iskan murmushi ya sakar mata, batare da ya sake cemata komai ba ya kamo hannunta ya ɗaura mata ƙaramar shopping bag mai tambarin apple a jiki, ya sake ɗakko key ɗin motar nan ya saka mata shima, ya ɗauka laptop ɗin itama ya ajiye a saman ƙafarta. Har lokacin idanun nasa a cikin nata yaja kujerar baya ya miƙe abinsa cike da takunsa na isa ya zagaya ya koma kujerar zamansa, desk ɗin ya dafe da duka hannayensa biyu ya ranƙwafo, duk da ba kusa suke da juna ba sai da taji wajen ya sake mata nauyi da matsatsi.        “Fatan nasara”.    Ya faɗa a hankali sannan ya kai zaune a kujerar ya hau ayyukansa. Tsuru kawai tai tana kallonsa na tsawon lokaci. Shiko ya cigaba da aikinsa kamar ma ya manta da ita, dan kalamanta wani mugun saka zuciyarsa tafasa suke ainun. Itama kasa cewa komai tayi, sai kawai ta miƙe tana mai ajiye masa key ɗin motar ta wuce abinta da shopping bag ɗin da laptop ɗin kawai. Dan wadda ya bata ranar ce ta kuma fahimci wayace. Tana buƙatar wayar ne a yanzu dan har sim cards ɗin suna a hannunsa dama, bata sani ba kuma ko ya haɗa mata da su. Sai da ta fice ta maida ƙofar ta rufe sannan ya ɗago a hankali ya sauke idanunsa akan key ɗin. Janyewa yay ya maida kan ƙofar kamar yana hangota har yanzu a wajen. Sai kuma ya furzar da iska yana mai ajiye document ɗin hannunsa da ɗan ƙarfi ya tura duk hannunsa biyu cikin sumar kansa ya shiga yamutsata, tare da kwantar da bayansa jikin kujerar yay sama da kan nasa yana furzar da zazzafan huci. Tsohon lokaci ya ɗauka a haka da shima bai san adadi ba, kafin ya sake sauke numfashi mai nauyi ya cigaba da aikinsa...........✍️ _😂Jaraba, idan aka haɗu kamar abin arziƙi, amma daga ƙarshe da wahala a rabu lafiya sai da bala'i🤣, wai mike damun gayun nan ne😆😆? Maga dai yanda za'a ƙare da batun zuwa chaina😌🥱. 🏃🏃_ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖8️⃣6️⃣ ______________ .........A Kaduna kam shirin biki ake sosai, dan a yau laraba akai gagarumin kamun amarya daya zaga ko'ina na media. Waje suka kama yasha ado da kwalliya kamar yanda itama amarya tasha ado. Dj ya warware sauti ƙawayen amarya da amarya da ƙawayen uwar amarya da ƙannen ango har ma da gayyar soɗi suka cashe gwargwadon iko. Amarya tasha turare har yana hawar mata kai. Ango dai baima ƙaraso ba sai bayan sallar isha'i. Shima a media ya tsinta shagalin kamun. Tsaki kawai yay ya dinga wuce videos ɗin dan shi a nasa tsarin baya buƙatar duk waɗan nan bidi'oin. Amma yasan bai isa cewa baza ai ba Mammah ta hargitsa masa hazo. Yau ɗin ma itace ta kafa masa dogon gargaɗi akan ya dawo Kaduna domin halartar events ɗin da za'ayi. Duk da dama dai yayi niyyar hakan shima bisa umarnin Daddy. Yaso fara tsayawa Abuja wajen Maanal amma sai aka samu akasi, dole ya haƙura ya wuce akan zuwa gobe zai koma Abujan, dan baya tunanin Maanal zata zo wajen bikin nan. Shima a karan kansa baya son ma tazo ɗin...       Ammie da Nene da surukan Nene da Sakina sunje wajen kamun, duk da da dai Ammie batayi niyyar zuwan ba Hajiya Majdiya tace suje. Dan zuwa yanzu kam sun ƙulle da Ammie sosai bisa umarnin Oum da tuni ta zayyanema ƙanwar tata komai dake tsakaninsu da su Maanal. Su Ammie sun sha habaici, dan har Hajiya Yaya ma taje wajen kamun. Amma kamar yanda Ammien ta saba sai ta nuna bama tasan suna yi ba. Su Hajiya Basariyya dai anata safa da marwa su amarori. Ta shige taro tayi damal-damal dan ta san sirrin komai da takun komai, gefe kuma ta gogama Ammie kashin kaji da bata haushi. Sai dai kuma hakan bai samu ba, dan ta firgita da ganin su Ammie a taron kamun batare da tayi tunanin zatazo ɗin ba. Duk sai jikinta yay sanyi.      Itako Ammie bama ta nuna ta san da zamanta a wajen ba. Sai da tsabar munafuncin Hajiya Basariyyan ya sata zuwa ta wani ranƙwafo tanama Ammie magana a cikin kunne. Ba wata magana bace mai ma'ana, amma mutane sai su ɗauka wani sirrin ne akeyi irin na iyayen biki. Nan ko tambayarta tai kawai wai mi za'a kawo ma baƙinta. Murmushi Ammie tayi tana sake jinjina makirci irin na Hajiya Basariyya, itama sai kawai ta amsa mata da komai ma a basu zasu ci. Daga haka ta maida hankalinta ga wata ƴar uwar Daddy da yaranta da suka ƙaraso wajen, dan suna ɗasawa sosai da Ammien....      ______★       A media su Manaal sukai kallon kamun, sai kuma ga Amal ta kira Shahidah. Nan suka ɓige da zancen suna dariya. Dan sun fahimci duk anayi ne wai a basu haushi. Ita Maanal ma tunda suka fara wannan zancen sai kawai tai shiru ta maida hankalinta ga saita wayarta. Dan tunda ta dawo ta cireta a kwali ta sanyata a caji. Ganin ta cika ta ciro ta dan ta saka sim card ɗinta, ɗayan kuma ta ajiye akan gobe in sha ALLAHU zata sayo wata wayar dan riƙe waya biyu ya kamata kenan. Shiyyasa bata taɓa damuwa da wannan iPhones ɗin banzar ba ita kam. Bayan sun gama wayar ma tashi tai ta nufi ɗaki domin kwanciya.... _____________★         Kamar yanda RK ya faɗa a safiyar yau yay shirin zuwa Kano, dan haka misalin goma na safe daga asibiti daya leƙa Mawaad Company ya wuce. Maanal na tsaka da aiki Yaqub na mata bayani aka sanar da ita tana da visitor a waje. Ta ɗan yi mamaki, amma sai zuciyarta ta hasaso mata RK ne. Dan shi kaɗai ne ke zuwa companyn wajenta. Amma to miya hanashi shigowa har office ɗin nasu?. Rashin mai bata amsa ya sata miƙewa tana cema Yaqub tana zuwa. Kai kawai ya jinjina mata, dan haka kawai yaji kishi a ransa da koma waye wannan visitor ɗin. Canjawar yanayin nasa ya saka su Zaharadeen.. kwashewa da dariya. Bai kulasu ba, dan ya fahimci sa'idonsu ya fi na mata....             RK dake tsaye jikin motarsa ya zubama Maanal dake nufosa idanu. Sosai tai masa ƙyau cikin atamfar jikinta data kasance skert da riga. Daka ganta kaga cikakkiyar bahaushiya ƴar asali. Zazzaƙar muryarta data rangaɗa sallama ta ratsa kunnuwansa. Amsa mata yay fuskarsa da murmushi, sai kuma cike da tsokana ya furta “Anya bazan saceki ba daga nan a biyomu da kayanmu kawai”.       Batare da niyya ba ta saki guntun murmushi, tare da ɗan jan gyalenta ta rufe fuskarta. Sai hakan ya sashi sakin dariya cike da shauƙi. A haka ta gaishe shi, tare da ɗorawa da faɗin, “Amma miyya hanaka shiga ciki?”.            “Boss ɗinki mana, yace in dai da soyayya nazo na dinga tsayawa a waje nayi, in ba hakaba kuma zai hukunta mu ni da ke”..        Sosai mamaki ya kashe Manaal a tsaye, a ranta tana sake jinjina halayyar Ajwaad. Yanzu ashe sai da ya iya yima RK maganar nan? ALLAH ta ɗauka wasa yake yi iya kanta gargaɗin nasa kawai zai tsaya. A fili kam sai cewa tai, “Yanzu kai kuma kaji maganarsa ka daina shiga kenan?”.     “Kai haba shi ɗin mi, kawai dai dan ina a hanya ne shiyyasa. Jirgina nanda minti arba'in zai ne”.        “Kanon dai?”.    “Eh mana, ai da zafi-zafi ake dukan ƙarfe my queen. So nake next week in sha ALLAHU a gama komai na mallaki ƴar baiwar nan kafin na zube ƙasa”.           “Humm daɗin baki”.      “Oh haka kike tunani kenan? Ai tsakani na da ke har abada babu daɗin baki. Duk abinda kika ji baki ya furta shine har a ƙarƙashin zuciyata”.     “To ALLAH ya tabbatar da hakan”.   “In sha ALLAHU ya tabbatar. Na ganki a online jiya da dare, ya dawo miki da wayar ne?”.    “Oh kaga ma na manta shaf, ya dawo da ita, gashi na manta da taka a gida”.            Murmushi yay mai sanyi da faɗin, “No taki ce, ki cigaba da amfani da ita kawai. Dan ma nasan bazaki yarda muje a sai wata ba shiyyasa nayi shiru”.       “Amma Yaya Rafeeq.....”   “Shiiii!!! Don't say anything madam. Yimin addu'a kawai na wuce kar naje airport a makare”.        Murmushi ta masa, tare da jera masa addu'ar daya buƙata. Cikin nuna jin daɗi yake amsa mata da amin. Kafin suyi sallama ya shiga mota. Tana daga tsaye a wajen har sai da ya fice yana ɗaga mata hannu sannan ta juya ta koma ciki fuskarta cike da murmushi. Koba komai zuciyarta na girmama RK, yana da wani kaso mai girma kuma a wajenta, dan yana sakata a farin ciki da sauƙin kan nan nasa. Jinin Oum ai ba abin da zata taɓa wulaƙantawa bane a rayuwarta har abada....       Cikin wani irin takaici da raɗaɗin zuciya AA dake kallonsu ta jikin gilashin office ɗinsa ya kai hannu ya shafa ƙasumbarsa. Babu abinda ya tsaya masa a ƙahon zuciya ya ƙi ya wuce sai sassanyan murmushin da yaga sunama juna da wanda ta shige tana yi. Wato ya fahimci Rafeeq bazai gane karatun kurma ba, sai ya fito masa a ainhinsa sunyi uwar watsi tukunna.        Ji yay gaba ɗaya ma aikin ya fita masa a rai. Sai kawai ya fito a office ɗin. Ko kallon AS baiyi ba ya wuce. Gaba ɗaya yabar companyn, sai ma ya nufi villa dan dama yana da meeting da ministar yau..... Yanda basu haɗi ba yau kwata-kwata baya buƙatar su haɗun, dan yana son ya bata lokaci shima ya nema mafita....    A ɓangaren Maanal ma dai tayi mamakin yau bai tsakura mata ba. To sam bama su haɗu ba har lokacin tashi, sai tayi tunanin ko dai baizo office ba yau, kokuma yaji gargaɗin data masa. Koda yake tasan mutumin nan tasan halinsa. Gargaɗinta bazai sa ya fasa abinda yay niyya ba, akwai dai abinda yake shiryawa. Hakan na nufin dole ta saka ido, dan tayi alwashi a ranta saifa ta tabbatarmasa a yanzu WUTSIYAR RAƘUMI TAYI NESA DA ƘASA. Rafeeq da kowa yake ganin bazata iya aura ba shine zaɓinta....       _🏃Yauwa ƙawalliya, ina bayanki sai Uncle Rafeeq ko Abuja ba kowa🤪. Dangin AA ku kama Nuratu da Huznahn ku yafi muku🥱🏃_. ____________★       “Yanzu ke wane mataki kika shirya ɗauka ne Kamila?”.    Numfashi Mamy ta sauke mai nauyi, sai kima ta dubi Maman Saheeba datai maganar. “Inaga zanje Kano a weekend ɗin nan”.         “Kano kuma? Yin me? Wajen wa kuma?”.     Sai da Mamy taja fasali, ta sake furzar da numfashin takaici sannan ta ce, “Abbu”.       “Mahaifin Fateema fa kenan?”. “Yes shi, harma da Baban Yola da Baba Sardauna. Ita kanta Gwaggo Khadi ɗin da Mah-mah ɗin duk zanyi magana da su”.      Sosai yanzu kan Maman Saheeba ke murmushi. Ta ce, “Wato dai tarihi ne zai maimaita kansa?”.          “Wannan itace kawai mafita ai. Idan ba haka ba narasa ta inda zan ɓulloma al'amarin. Ke dai kawai mu fara shiri ma Nuratu. Amma fa kamar yanda na sanar miki ina son a haɗa masa da yarinyar nan da su Abdull suka kawo, dan so nake na birkita Fateema matuƙa fiye da akan su Fawzan”.        Gimtse fuska Maman Saheeba tayi. Mamy ta kamo hannunta cike da lallashi. “Dan ALLAH ki fahimceni ƙanwata, badan na tozarta Nuratu bane ko ƙuntata mata. Dan babu wata ɗiya da za'a auro da zata kasance a sama da su jinina. Shiyyasa ko'a yanzu a komai kin san kema Saheeba tafi Nibras a gareni. Dan yanzu haka ma al'amarin Nibras ɗin ya fara kaini wuya wlhy. So nake shima Fawzan ya ƙara aure. Ya duba tsakanin Barirah da Mabrooka ya zaɓi ɗaya. Shekara kusan shida babu wani bayani, sai rikici ya haɗosu ta dinga zuba masa gori kamar ance mata shine baya haihuwar. Shekaran jiya kamar Ajwaad zai daketa, kin sanshi akan ƴan uwanshi ba ragi babu ragowa. Ƴar tsirkun gidan tamu dai da Abahn su suka kwakkwaɓe shi da ƙyar. To gara yay auren mu tantance ina matsalar take.”        “Tab ɗin amma Aunty kin fa san halin Hajiya Rahane, zata iya komai akan wannan taɓararriyar ƴar tata mace tilo guda ɗaya”.      “Nima kuma zan iya komai akan nawa ɗan Gambo. Fawzan nada haƙuri a cikin ƴan uwansa. Sannan matsalar rashin haihuwar nan tashi na damuna wlhy”.      “Dole akwai damuwa kam, ALLAH ma yasa ba munafukar gidan naku ce tai masa wani abun ba kamar ita dan kada ya haihu, kai ni hatta rashin auren Ajwaad ina ji a raina a kwai lauje cikin naɗi. Dan komai matar nan zata aikata tunda ba ƙaunar yaran take ba, kawai munafunci ne su kuma sun kasa ganewa sam. Tunda ba gashi ta dake dawo da mayyar yarinyar nan rayuwarsa ba”.........✍️ _Nifa bara na faɗa gaskiya, bana son babar Saheeba ɗin nan wlhy. Idan nazo wajenta kamar na jawota na fallasa mata maruka haka nake jin raina🥺☹️🙄😲🏃._              09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖8️⃣7️⃣ ______________ ........“Humm taya zasu gane tunda ba haka nan ta barsu ba. Kedai kawai a rufe rufau. Shiyyasa yanzu a shirye nake kan batun dawowarsu wajena. Auren Ajwaad ɗin kawai nake jira na fara ƙaddamar da komai na shiri na.”       “Ina bayanki wlhy ALLAH kuma ya taya miki. Sai kuma ya ran nan su Naufal uwar tace min kwana biyun nan hankalin yaran ya fara karkata a kanta.”            “Hummm nima na fahimci hakan. Kin santa kamar mayya take, amma zan sake sabon shiri akan su suma. Yanzu dai ki shirya muje Kano ɗin tare Please”.     “A'a Yaya Kamila kada muyi haka dake. Ai idan suka gammu tare zasu iya zargin wani abun. Kidai je ko ke da Yaya Raliya mana”.      “Kema kin kawo shawara. Bari zan yi magana da Yaya Raliya ɗin..” _________★        Da mamaki Maanal dake sauka a taxi take kallon Abideen dake tsaye a ƙofar gate ɗinsu. Yana ganinta shima ya tashi tsaye sosai daga jinginar da yay da mashin ɗinsa roba-roba. Da girmamawar data bata mamaki ya ce, “Barka da dawowa sister Maanal”.        Ɗan zuba masa idanu tayi, sai kuma cikin kasa daurewa ta ce, “Abideen lafiya kuwa? Mi kazo yi gidan mu?”.     Murmushi yayi tare da shafa kansa. “Magana nazo muyi dan ALLAH ki daure ko mintina biyar ki bani”.           Shiru kamar bazata ce masa komai ba, sai kuma ta jinjina kanta. “Okay shigo ciki”. Ta faɗa tana shigewa....     A cikin rumfar bunun da akai adon gidan da ita har uku suka zauna. Ya sake gaishe da Maanal da girmamawar da take sake ɗaure kanta.        “Humm Abideen ni wlhy sake ɗaure min kai kake. Wai wannan sissinkuy da kan na miye haka?”.     “Girmanki ne Sister Maanal. Nazo nan ne domin neman afuwarki dan ALLAH. Sannan na roƙeƙi ki bama boss haƙuri kota hanyar Dr RK ne na koma kan aiki na, na san na aikata kuskure. Kuma wlhy sharrin shaiɗan ne dana zuciya. Amma in sha ALLAHU bazan sake ba. Dama ban taɓa aikatawa ba sai yanzu, kuma Alhamdullahi bamma kai ga ƙarasa badu abinda suke buƙatar ba sai wasu kaso a ciki”.         “Su wanene? Mi kuma suka buƙata ka basu kai kuwa. Ni sai sake rikitani ma kake, miye alaƙata kuma da boss da zan saka shi ko roƙonsa ya maida ka wajen aiki...”      “Humm Sis... Maanal kenan. Bara dai na buɗe miki zancen. Kusan sati biyu kenan idan baki manta ba ranar wata laraba mun fito daga company ni da ke da Yaqub bayan an tashi, sai ke kika shiga taxi keda Yaqub ni kuma nace zan ƙarasa wajen ɗan uwana a ƙafa dake aiki a companyn AREWABOOKS”.      Kai Maanal ta jinjina masa alamar eh anyi haka.     “Yauwa to bayan wucewarku wani dattijon Alhaji mai suna senator Bukar ya tareni da buƙatar son yin magana da ni. Da farko ban damu ba, saboda mutane da yawa irinsa sun sha biyo ma'aikatanmu mata domin suna son su ko sanin inda suke. Ya buƙaci na shiga motarsa, shine yake tambayata miye sunanki? Babu wani damuwa na sanar masa. Ya tambayen aikinki a Mawaad nan ma na faɗa masa har kaɗan daga halayyar ki dana sani. Shine yamun godiya tare da ɗaukar maƙudan kuɗi ya bani, ya kuma ce na bashi number ta dan zan masa wani aiki a kanki. Kin san zuciya bata da kashi, ganin kuɗin daya bani daga tambaya kawai na bashi amsa da batafi ƙwara huɗu ba sai ban masa masu ba na bashi. To tun daga ranar fa duk wani motsinki a Company sai na tura masa. Ina miki video batare da kin sani ba da ɓoyayyar camara ina tura masa kullum. Wlhy ban san taya boss ya gane ba shine jiya yake tuhuma ta akai. Kuma jiya kamar yanda kuka bani shawara na gaya masa gaskiyar komai dana aikata amma duk da haka yace naje gida sai ya nemeni. Wlhy hankalina a tashe yake sis... Manaal. Ina cikin damuwa matuƙa, da aikin nan nake taimakon mahaifana, dan shekarar babana uku kenan yana fama da jiyya, nine babba a gidanmu nine koman su. Na samu aikin nan ne a dalilin Dr Rafeeq, lokacin da aka kwantar da babana a asibitinsa saboda zaman shiru sai naita zane-zane shine ya gani yace zai sama min aiki kodan na kula da iyayena dan a lokacin hatta kuɗin asibitin mun kasa biya duka. Ban san alaƙarki dasu boss ba, amma nasan kina da kusanci da Dr Rafeeq sosai, dan ALLAH ki jagoranceni wajensa kozai taimakeni ya bama Boss haƙuri tunda ɗan uwansa ne jininsa, kuma yana jin maganarsa......”       Wani irin kallon takaici Maanal ke masa, wato wannan dattijon da yake magana shine yaje Giro wajen mutanen can neman aurenta, ashe akanta ne ma AA yayma Abideen haka. Ranta a ɓace ta miƙe tana faɗin, “Ai Inaga zuwa gareni bashi da wani amfani Abideen. Tunda ai kaima kana da alaƙa da Rafeeq ɗin, kamar yanda ya samar maka aiki nima aikin kawai ya sama min, kaga alaƙar tamu duk iri ɗaya ce”.     Cikin sauri yasha gabanta. Kamar zai duƙa ya ce, “Dan girman ALLAH ki gafarceni, sannan ki yafe min kuskurena. Wlhy ba rasa aikin bane kawai damuwata, cutar dake da na dingayi ta hanyar miki video ina tura masa batare da kin sani ba. Ban fahimci hakan zai iya zama illa ba sai da boss ya fargar dani. Tabbas yanda rayuwa ta lalace senator zai iya amfani da waɗan nan videos ɗin wajen ɓata miki suna ta hanyar maidasu a mummunar siga, alhalin kuma ke baki ma san an yi ba.”      Wani irin mugun bugawa ƙirjin Maanal yayi, dan ita kanta hankalinta bai kai can ba sam. Ai bama tasan ta shiga ambaton “Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un”. Shi ko Abideen na faman jera mata kalaman ban haƙuri kamar zai yi kuka. Tsallake shi tai ta wuce ciki, ta barsa yana faman roƙo da magiya.... Koda ta shiga bata iya ta kula su Barrah ba dake mata oyoyo, sama-sama ta tattaɓasu ta wuce ciki. Tana shiga ɗaki ta sakama ƙofa key, sai hawaye shaaa. Haka kawai zuciyarta ke bata kamar abinda AA ɗin ya hango zai faru zai iya faruwa koma yana gab da faruwar. Tunda ita bama tasan wanene Senator Bukar ɗin nan ba ai. Ya ALLAH, tabbas ya kamata ta bincika, kuma a wajen AA ɗin kawai zata samu dukkan information ɗin da take buƙata.  Wayarta ta ciro a bag, sai da ta fara sarrafata sai kuma ta tsaya cak dan tunawa da ai bata da no ɗin AA ɗin. Jagwab takai zaune a cikin sofa. Zuciyarta ce ta bata shawarar kiran RK ta tambaya number ɗin AA ɗin, sai kuma wani sashe na zuciyar ya ƙwaɓeta. Ta hasko AS, shima dai ta ce a'a. Oum. Nanma taji bata gamsu ba. Dama dai tana da layin Yaya Fawzan ne ma, shi kam ƙila ta iya tambaya. To ko RK ɗin zatace ya bata layin Fawzan ɗin?. Gamsuwa da wannan shawarar ya sata kai hannu zata ɗauka sabuwar wayarta sai idannunta suka sauka akan wayar RK daya bata.        (Mizai hana ki duba a wayar nan ko zaki samu no ɗin ma) Wani gefe na zuciyarta ya ambata mata. Ai da sauri ta ɗauka wayar kuwa ta hau binciken numbers ɗin Kai daki-daki abinda bata taɓa maida hankali tayi ba. Bawani yawane da su ba, dan kusan ma da alama duk contacts na family ɗinsa ne a ciki. Amma sam babu sunan AA babu alamarsa. Har zata ajiye cike da damuwa sai kuma ta sake scrolling ta koma tsakkiya inda taga My S1 da 2 har ma da 3. Sai kawai ranta ya bata My Son yake nufi, babban yaya 1, Fawzan 2, AA 3. Cike da tabbatarwa ta jinjina kanta. Amma gudun samun matsala sai tace bari ta ɗan gwada amma bazatayi magana ba tunda tasan dai RK zai gani ya kira shi ba ita ba..... ______★       “Kamila Kano kuma? Wace irin tafiya ce haka ta ujila kin san fa gobe juma'a, kuma na sanar muku Saturday zaku rakani Kaduna ko?”.         “Hakane Abahn su, nima tafiyar ta dole ce. Kuma ai a goben zanje na dawo in sha ALLAHU. Sai nabi jirgin safe na dawo da yamma. Dan ALLAH kayi haƙuri ka barni, ALLAH idan banje a goben ba da wahala na samu lokaci”.     “Humm to wai mizaki je yi ne?”.   “Nafa gaya maka Yaya Raliya ce bata jin daɗi, tunda aka gama hayaniyar bikin nan sai a hankali. Jiya su gambo sukaje, shiyyasa nace nima bari naje gobe ai kaga dai baza'ace ba'aga mutum ba. Da harda Oum ɗin yara ma zamu je, to bana son takura mata tunda jikin bawani yayi tsanani bane ba”.         Ɗan iska kaɗan Abah ya furzar daga bakinsa tare da lumshe idanunsa ya buɗe kamar yanda AA keyi idan zai yi magana. “Shike nan ALLAH ya kaimu. Aiko sai ki daure ki ƙarasa gidan Baba dan kwana biyu yayi mura shima. Ya hana na faɗa muku ne dan kar Fateema ta tada hankalinta”.          “ALLAH ya bashi lafiya. In sha ALLAHU can ma zan fara zuwa, har Baban Yola ma saina leƙa su dan kwana biyu bamu je ba. Da bikin nan naso zuwa sai kuma tafiyar nan tamu ta ratsa”.     Kai kawai Abah ya jinjina mata ya cigaba da aikinsa. Ita kuma ta miƙe cike da farin cikin samun nasara tace masa tana zuwa. Nan ma hannu ya ɗaga mata kawai..... _________★        Bugun shigar kiran na bugawa ne da bugun zuciyar Maanal. Sai da wayar tana gab da tsinkewa sannan aka ɗaga. Sosai ta rumtse idannunta ta kasa cewa komai, daga can shima kuma baice komai ba har na tsawon sakanni. Sai zuwa can ƙasa-ƙasa ya furta.         “Ina massallaci, idan na fito zan kira”.    Daga haka ya yanke. Da masifar ƙarfi ta saki numfashinta data riƙe, tare da buɗe idanunta. Kai anya zata iya kuwa? Kodai ta barshi kawai. Kai ina bazata iya ba, maganar videos ɗin nan sune tashin hankalinta. Kada mutumin nan yaje ya aikata abinda zai zama sanadin bugawar zuciyarta. Ganin lokacin sallah zai ƙure ya sata haƙura da tunanin ta tashi ta hau cire kaya duk da ba sallar zatayi ba, tana dai son yin azkar ɗinta a irin lokacin kamar yanda ta saba. Jiki a sanyaye ta wuce bathroom yin wanka.        Har akai sallar isha'i bai kira ba. Ita kuma ta kasa fita dan gudun kada ta fita ya kira. Bata son zuwa da wayar falo kuma ya kirata a gaban Didi da Uncle Sadeeq. Koda Linda ta shigo ta sanar mata abinci ya zama ready catai ta kawo mata ɗaki yau ta gaji ne. Ta kuma ce tana gaida Didi. Da girmamawa Linda ta amsa mata ta fita, ita kuma ta hau shirin barci. A haka Linda ta sake dawowa ɗauke da abincinta. Kasa taɓa abincin tayi, ta zauna a bakin gado ta ɗauka novel ta hau karatun dole wai duk dan cinye lokaci. Sai dai sam ba wani fahimta take ba sam.       Sai ƙarfe tara da wani abu kiransa ya shigo. Zabura tayi daga kwancen da take tana duba wayar, ganin shine ke kiranta video call ma sai da zuciyarta ta girgiza. Ji take kamar taƙi ɗagawa, amma zuciyarta na ingizata. Haka ta tashi zaune ta warware ƙaramin veil ɗin data naɗa a kanta ta rufe jikinta sannan ta ɗaga dai-dai gab zata tsinke. Ai wani irin faɗuwa gabanta yayi lokacin daya bayyana mata a screen ɗin wayar tar. Jikinta har rawa yake ta kife wayar da sauri tana ambaton sunan ALLAH numfashinta na wani sam da ƙasa da sauri-sauri.....      Daga can shima AA ɗin kife wayar yayi da sauri yana ambaton sunan ALLAH, harga ALLAH shi duk zatonsa Rafeeq ne fa, ko video call ɗin yayisa ne dan tabbatar da Rafeeq ɗin yana a Kanon ne kamar yanda yace zai je. Dan gaba ɗaya ya manta ne da maganar kiranshi da yace zai yi ɗazun sai yanzu yana cikin wanka abin yazo masa a rai, shine yana fitowa batare da tunanin komai ba ya shiga masa video call daga shi sai guntun towel daya saka iya ƙugu zuwa gwiwa. Gashi ya ajiye wayar a saman mirror ne ta yanda ta hasko jikin nashi sosai. Ya jima tsaye hannayensa duk biyu dafe da mirror ɗin yana ambaton sunayen ALLAH kafin ya samu ya ɗan dai-daita. Wayar ya ɗauka, har yanzu tana online sai dai baya ganin komai sai duhu. Zama yay da ƙyau ya katse kiran, maƙoshinsa sai yawo yake cikin wuyansa da sauri-sauri. Gaba ɗaya yama rasa wane kalar tunani zai yi akan wayar Rafeeq a hannunta. Sai duk yaji zuciyarsa ma na masa zafi. Ɗayar number RK ya shiga kira, sai dai harta katse ba'a ɗaga ba. Cike da takaici ya sake ajiye wayar, sai da ya bada wasu sakanni zuciyarsa ta ɗan sauka sannan ya sake ɗaukar wayar yay mata normal call.........✍️ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖8️⃣8️⃣ ______________ .........Harta yanke ba'a ɗaga ba. Haka ya sake kira. Kira fin biyar bata ɗaga masa ba. Ya cije lips, dan duk duniya Oum kawai yakema kira fiye da ɗaya sai ko Abah. Amma daga basu ba in har ya maka kira ɗaya baka ɗaga ba shike nan, sai in ka kirashi back, bai kuma zama lallai ya ɗaga maka ba sai yaso koda shike da buƙatar wani abu kuwa.      Samun kansa yay da sake kiran, yanzu ma har ya fidda rai sai kuma yaji an ɗaga. Ɓoyayyar ajiyar zuciya ya sauke acan ƙasan maƙoshi, tare da kai hannu ya shafa kwantaccen gashin kumatunsa dake jiƙe da damshin ruwan wanka. Kamar ɗazun yanzu ma shiru tai masa, amma sai ya danne yay sallama. Amsa masa tai murya ƙasa-ƙasa, kai daga ji kasan a cikin kunya take.          “Am sorry nazata Rafeeq ne, shiyyasa na kira a wannan yanayin”.      “Uhm”. Kawai ta faɗa a can ƙasan maƙoshi, alamar matsanancin nauyinsa take ji har ma bata son maganar. Shina ya fahimci hakan, dan haka ya saki batun kawai.          Cikin son kauda wancan yanayin ya katse shirun da sukayi da faɗin. “Kina son ganina ne?”.      Da sauri ta ce, “A'a, dama.......”   Sai kuma tai shiru. Numfashi ya ɗan sake fesarwa, kafin a ƙagare ya furta, “Daman mi?....”         Sosai tsigar jikinta ke tashi saboda yanda yake magana can ƙasan maƙoshi. Ga wani amo dake ratsa mata zuciya na fita daga cikin silent voice ɗin nashi. Daƙyar ta iya danne kanta, da ɗaɗɗaya ta ce, “D..a man akan Abideen ne”.           Lips ɗinsa ya ciza da ƙarfi, kamar wanda yake a gabanta idanunsa suka ɗan kaɗa. Muryarsa na ɗan canjawa da ƙara kauri ya furta, “Miye damuwarki da shi ɗin wai?”.        “Yazo gidanmu ne”.     “Gidan ku?”. “Eh har ya sanar min komai daya faru. Wlhy hankalina a tashe yake da maganar videos ɗin nan. Kada mutumin nan ya cutar dani kamar yanda ka faɗa, kuma wlhy ko saninsa banyi ba, bamma taɓa ganinsa ba.”          “Amma yake iƙirarin an bashi aurenki?”. Yay maganar cike da zafi.     “Ni wlhy ban sanshi ba ƙarya yake min. Ni dan ALLAH ka bani number ɗinshi zanyi magana da shi”.        A taƙaice ya ce, “Banda”. Shiru ta ɗanyi na wasu sakanni dan jin yanda yay maganar a Zafafa. A tunzure, kuma cike da shagwaɓa itama ta ce, “Toni ya kake so nayi?”.     Shiru ya mata, har sai da ta cire wayar a kunne ta kalla. Ganin yana online ya sata sake jin haushi. Cike da tsiwa ta ce, “Ni zaka wulaƙanta dan na nema taimakonka?”.     Nan ma shiru. Ai a fusace ta yanke kiran, tare da dangwarar da wayar. Shima a nasa ɓangaren wayar ya ajiye kawai ya miƙe. Zuciyarsa sai kumbura take a cikin ƙarji. A haka yay shirin barci ya haye gadonsa. Yana ƙoƙarin ɗaukar Alkur'ani dan yin karatu wayarsa ta motsa. Ɗauka yay da tunanin itace ta sake kira. Amma sai yaga number yarinyar nan ce dake damunsa, yayi blocking numbers ɗinta fin huɗu, amma yanzu saita koma kiransa da sabbin lauyuka. Kasancewar kusan irin wannan lokaci take kiransa a kullum yasa ya gane. Maida wayar yay ya ajiye batare daya ɗaga ba ya cigaba da buɗe Alkur'anin. Dan yanda yake jin zuciyarsa karatun kawai zai yi yaji sanyi......    _________ WASHE GARI.          Yau juma'a, koda Maanal taje office signing kawai tayi ta fito. Dama tama tsayar da mai taxi ɗin daya kawo ta. Tana ƙoƙarin shiga taxi ɗin motar AA ya shigo. Kallo ɗaya taima motar ta ɗauke kanta ta shige abinta. Sai dai tana ƙoƙarin rufe murfin taxi ɗin idannunta suka sauka akansa. Shima kallona yake cike da wani yanayi na tuhuma-tuhuma, mamaki, da kuma kewa. Fuska ta yamutsa tare da ɗauke idanunta a kansa tace ma mai taxi ɗin, “Muje”. Mai taxi da bai san mike faruwa ba yaja motarsa yay gaba...      Daga Mawaad Company wajen gyaran jiki aka sauketa. Dan Didi nacan tare da Barrah. Itama gyaran jikin aka shiga yi mata, dan Manaal ƴar gaye ce. Aka mata ƙunshi dai-dai misali baƙi da ja kaɗan da yay mata ƙyau kamar itace ma amaryar. Dan Didi sai tsokanarta take yi. Ita dai murmushi kawai take yi batare da tace komai ba. Basu baro wajen ba sai la'asar. A gajiye suka shigo gida. Nan ma kuma basu zauna ba suka ƙarasa shirinsu. Biyar da rabi a train station tai musu. Sun iso Kaduna ana magriba. Amal ce da su Munaya suka zo ɗaukarsu. Ai fa Munaya ta maƙalƙale Maanal dan ALLAH ya haɗa wannan ƙauna. Gashi kuma Munaya na kama da Maanal ɗin sosai.       Sun iso gidan cike da mutane, dan yau za'ai mothers event. Ɗazun akayi Sister & brothers event da ƙannen Yazeed suka shirya ma amarya. Kusan ma duk danginsu ne a wajen sai ƙawayen amarya. An kuwa rankwashe an ƙwalle dan ango kansa dole ya halarci wajen bisa tirsasawar Hajiya Yaya. Kasancewar su Maanal na wajen gyaran jiki basu maida hankali a gani ba. Koda yake ita bama tana bibiyar komai bane, Didi ce idan ta gano da Amaal ke bata labari.          Koda suka fito a mota da yawan mutane sukai musu caa da idanu. Wasu ma har suna ɗan ƙus-ƙus. Cikin ikon ALLAH kuma Maanal na fitowa akan Yazeed ta fara sauke idanunta. Ya fito daga sashen Daddy abokansa kusan shida da duk ta sansu zagaye da shi. Yayi masifar ƙyau cikin shadda ɗinkin tazarce, ga hula ya murza fuskarsa na fidda wani annurin gyaran fuskar da yasha. Sosai ya zama wani sakwakwa saboda ganin Maanal. Har takai suma abokan nasa duk suna zuboma inda sukaga yana kallo idanu. Suma dai kamar sun ɗan shiga shock da gannin Maanal ɗin, sai sukai duru-duru.          Ɗauke kai Maanal tai tare da jan hannun Munaya da Barrah tai wucewarta sashen Ammie. Haka kawai ta ɗan ji ɗaci a ranta. Sai faɗi take, (yace bai son aure amma gashi yana faman zuba kwalliya da washe baki kamar tsohon gwauro) a fili kam miskilar fuskarta ta shanye komai. Suna shiga ta saki su Barrah ta ɗane Ammie.       “La'ila yarinyar nan wai karyani zakiyi ne dan ALLAH”.      Ammie ta faɗa tana kai mata mintsini. Dariya Maanal ta sanya da sake mamaye Ammien sosai. Sai kuma ta mata kiss a gefen fuska tana faɗin, “I miss you sweetie na”.      Dariya ƴan falon suka sanya. Dan dangin Daddy ne da suka sauka anan sashen Ammie ɗin. Sai yanzu Maanal ta farga da mutane. Sai kuma taji kunya ta shiga ɓoye fuskarta a jikin Ammie. Nan ma dariya kowa ke mata har dasu Amaal da suka shigo. Sai kawai ta janye jikinta ta nufi bedroom ɗinta da gudu. Dan tasan duk rintsi Ammie tasan zasu zo bazata bari kowa ya shiga ɗakin ba tunda ma akwai na baƙi ai. Aiko babu kowa ɗin, an dai gyarshi tsaf yanata ƙamshi.....       Bayan sun huta Ammie ta sakasu shiryawa domin zuwa wajen event ɗin. Maanal taso ta turje. Amma Ammie taita lallashinta. Dan bata son Manaal ɗin ta zauna a gida a fassara zaman nata da wani abu daban. Haka badan taso ba ta shirya tsaf cikin wani swiss lass fitted gown datai masifar zauna mata a jiki. Ta zauna tai kwalliya dan a ɓangaren kwalliya ma Maanal artist ce sosai. Ta koya kuma ta iya saboda sonta da ado, dan ma yanzu kura tayi lafiya. Su Amaal ma har Ammie duk itace ta musu kwalliyar, tai ɗauri daya saka kitsonta fitowa ɗas kamar ka lashe. Koda suka fito babu wanda bai yaba ba a falon. Wasu a dangin Daddy ɗin har suna faɗin, “Kai jama'a yarinyar nan ma ai tafi amaryar ƙyau da komai ga nutsuwa wlhy. Amma uwarsa na neman cuta masa. Ga yarinya mace har mace Masha ALLAH”.      Ita dai Maanal da su Ammie babu wanda yace komai. Haka suka fito compound. Kusan duk an wuce. Sai ɗai-ɗaikun mutane a gidan da suka rage. Dan ana kai wasu ne ana dawowa. Dole Maanal taja mota ɗaya, Amaal taja ɗaya Shahidah ma haka. Dan mota uku sukai, a hakan ma a ɗan matse suke dan Ammie tace bazatai driving ɗin dare bane dan Daddy ya hana.....   ___________★                Gida ne katafaren gaske daya amsa suna gida. Komai a cikinsa tsari ne irin na gogaggun ƴan boko da sukaci suka yada kai aka kuma tashi a cikin rayuwa irin ta turawa. A nutse farar bafulatanar dattijuwar ke sakkowa daga staircase ɗin dake tsaye ƙam a tsakiyar katafaren falon tamkar an zana. Sosai ta manyanta, sai dai tsufane irin na masu jin daɗi da babu wahala. Ga ƙaramin jikin Fulani ALLAH ya bata. Cike da girmamawa masu aikin dake ta ƙoƙarin shirya abinci a ƙaton dining table suke mata sannu da fitowa. Amsa musu tai da kulawa. Kafin ta furta, “Babu wanda ya fito ne har yanzu?”.         “Eh Mah-mah, amma Alhaji ƙarami da Yaya Rafeeq yanzu suka dawo suna a sashen Yaya Rafeeq”.     Kanta ta jinjina kawai. Sai kuma ta sake juyawa upstairs ɗin tana faɗin, “Ku ƙarasa wani yay kiransu. Bara nama Doctor magana”. Daga haka ta sake hayewa saman.      Fin mintuna goma sai gasu sun fara firfitowa. Kamilallen tsoho da akaga jiya akaga yau Dr Kasheem Kura ne ya fara fitowa matarsa Hajiya Maryam Ishaq Darma biye da shi. Sai ga kuma wata matashiyar mata da bazata wuce shekaru talatin ba da ɗoriya itama. Sosai take kamanni da Mah-mah da su Oum. Hakan na nufin itama ta fito daga tsatson Baffa Ishaq Darma ne. Yara biyu biye da ita ƙyawawa da shekarunsu zasu iya kaiwa biyar da bakwai. Da gudu suka barta suka nufi tsoffin kakanninsu. (Rufaidah kenan, itace Autar su Abah, dan Baba Umar Ishaq Darma mahaifin Abah ne ya haifeta. Itace kuma ke auren Sulaiman ƙanin Oum dake bima Hajiya Majdiya, RK kuma ke bi masa. Yaransu uku duk maza, babban mai shekara tara bai kai ga fitowa ba. Suna zama a dining ɗin RK da Sulaiman da suke kira Alhaji Ƙarami suma suka sakko. Hira suke suna dariya kamar wasu abokai, duk da Alhaji Ƙarami ya girmi RK nesa ba kusa ba akwai shaƙuwa mai yawa a tsakaninsu. Rayuwar Turai sun tashi sune abokan juna, sune ƴan uwan juna. Suma duk kujera suka ja suka zauna, bayan RK ya gama ɗaga yaran sama suna dariya.        “Barka da dare Abbu, Mah-mah barkan ki”.     Murmushi Hajiya Maryam da Dr Kasheem sukayi a lokaci guda idanunsu akan RK da yay gaisuwar. Cike da kulawa Mah-mah ta ce, “Auta anya tuzurancin nan bai isa ba haka nan? Na fara gajiya da baka abinci fa a gidan nan”.       Kai RK ya shafa yana murmushi, sai kuma ya kalla Abbu. “Abbu ai kai baka gaji da kawowa naci ba ko?”.          “Nima kamar na kusa fara ƙorafi irin Mah-mahn ku”.      Dariya suka sanya gaba ɗaya. Alhaji ƙarami ya ce, “Abbu kaima bazaka bashi kariyaba yau?”.      “A'a ina zan bari aima Autana tawaye Alhaji ƙarami. Kawai dai nima ina son yayi auren ne na gaji da ganinsa haka nan.”           “Ai ni nama daina cewa komai Doctor. Amma gab nake da dubawa cikin ƴaƴan dangi na aurama Rafeeq da Ajwaad da Najeeb. Su ukun nan tuzurancin su ya ishi kowa a family ɗin nan. Garama su yanzu suna a ƙasar tasu, shiko Najeeb yaje ya tare a ƙasar turawa da anyi magana yace bussines”.       Fuska da murmushi Abbu ya ce, “Insha ALLAH zasuyi kwanan nan. Dan autanki dai gobe zamu tattauna akan nashi batun. To Inaga Ajwaad ɗin da Najeeb ɗin ma duk za'ayita ta ƙare, dan ta bakin Kamila sai an biyo musu ta bayan gida.”         “To ALLAH ya tabbatar da alkairi”.    A tare duk suka amsa da Amin, kafin kowa ya fara ƙoƙarin zuba abinda yake buƙata a plate ɗin da ya ɗauka. Dining ɗin RK ya ɗan kalla sai kuma ya duba Rufaidah.        “Ƙanwa! Wai ina spider man ne?”.     Baki ta ɗan taɓe da faɗin, “Yana ɗaki Yaya Rafeeq, fushi yake har yanzun. Daga ni har Mah-mah ya daina kulamu a gidan yau. Tunda kuka fita ma bana tunanin mun gansa, shi a dole sai yabi Mamy Abuja bayan kuma ga makaranta ba hutu akayi ba”.       Dariya Abbu yayi, cike da manyantaka ya ce, “Ai laifinku ne. Daga ke har Maman taki kun cika faɗa ne. Shi kuma ku lura yaro ne da bai son yawan hayaniya, komansa irin na iyayensa ne Ajwaad da Fadeel, shiyyasa ma yake ƙulafucinsu, dama kun barshi yabi Kamila ɗin sai a maidoshi ranar lahadi”. “Tab Abbu murɗa-murɗa kenan. Garama Fadeel ɗin da ɗan sauƙi. Amma wannan Autan na Aunty Babba sai ita wlhy. Ai sai mu tattara idan yayi aure mu maida masa can su ƙarata. Dama ai duk duniya ba wanda Abdull ke ƙauna sama da Ajwaad”.       “To ai hali yazo ɗaya ne”.   Cewar Alhaji ƙarami. Dariya duk sukayi, sai kuma RK ya miƙe yana faɗin, “Ina zuwa bari na fito da shi.” abincin su sudai suka cigaba da ci. Kusan mintuna biyar kuwa sai gashi ya fito goye da matashin yaron a bayansa. Sosai yake kamanni da Alhaji ƙarami. Kai da ka gani kasan shi ya haifi abinsa. A kujerar kusa da shi ya saukesa, shiko yaron sai wani ciccin magani yake. Yaki ƙallon kowa. Dariya sosai Abbu yake gumtsewa, dan ganin Mah-mah da Rufaidah da yaran ke kira Ummy na hararrar yaron. Shi kuma sai wani ƙara tsare gida yake yi.      “Ni mutum ma idan ya sake shiga sabgata a gidan nan ba sai nayi kuli-kulin rakiya da shi ba”. Cewar Mah-mah. Aiko Abdull sai ya sake tura baki gaba yaƙi kallonta. Kasa haƙuri Abbu da RK da Baba Ƙarami sukai suka sanya dariya... Haka sukaci abincin nasu cike da raha. Dan akwai shaƙuwa mai ƙarfi a tsakanin wannan zuri'a. Musamman daya kasance mahaifinsu mutum ne mai sauƙi da sanyin hali. Dan kaf halayen Rafeeq irin nashi ne. Mah-mah ce ma mai ɗan zafin yanayi............✍️        09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖8️⃣9️⃣ ______________ ........Shigowar su Maanal cikin hall ɗin ya matuƙar ɗaukar hankali. Dan a dai-dai lokacin da ake addu'a ne. Wajen ya kasance tsit. Suko yanda aka zubo musu idanun bai damesu ba. Sai ma wajen zama da suka samu aka ƙarasa addu'ar da su. Kafin a fara abinda ya shafi mutane. Duk motsin Maanal a idon Yazeed ne, ita ko taƙi yarda ma ta kalla inda suke shi da amaryar tasa da tasha ƙyau. Itama amaryar hankalinta duk yana akan Maanal ɗin, sosai take jin tsanarta, amma tsoron nunawa take a gaban Yazeed. Dan ranar data nuna ɗin ya tabbatar mata zai iya fasa aurenta akan Maanal. Dan haka ta kiyaye idan tana son kasancewa da shi. Dole ta kama kan nata take kuma yin taka tsantsan. Amma a ranta wata irin wutar ƙiyayyar Maanal ce mai ci da zafi da ƙarfi ke sukarta. Hakama mahaifiyarta Aunty Sabuwa. Dan ko yanzu taso yin abinda zai wulaƙanta su Ammie a wajen mai bima Hajiya Yaya ita kuma Sabuwar yayarta ce ta ƙwaɓeta. Dan ita tana da hankali da sanin yakamata matuƙa..      Taro ya tashi lafiya. Ammie ce kawai taje taima amarya da ango liƙi. Amma su Amal duk ƙi sukayi, balle Manaal da dama ko motsawa batai ba. Hasalima charting suke ita da RK hankali kwance. Ana tashi sune ƴan gaba-gaba a masu wucewa gida. Yanayin gajiyar tafiya da rashin samun isashen hutu suna shigowa gidan kowa makwanci ya nema. Washe gari safiyar asabar aka tashi da shirin ɗaurin aure. Sai yinin biki da Hajiya Yaya zatayi. Zuwa dare ayi dinner sannan a kawo amarya. Sai washe gari walima da buɗan kai baki ya tashi. Duk da nan gidan anguna ne bana su amarya ba cike yake...      Sosai abin duniya ya dami Yazeed. So yake yaga Maanal amma hakan ta gagara. Dan jiya daga wajen mothers event ɗin nan dole hotel ɗin da abokansa suka sauka yaje ya kwana. Ya kira wayarta kuma a kashe. Yanda ya kwana da ita a rai ya sashi zuwa gidan yau da wuri. Dama anan sashen Ammie aka haɗama abokansa breakfast, sai ya samu damar fakewa da hakan kuwa. Bayan ya gaishe da dangin Daddy dake nan sai ya zauna suka cigaba da hira. Dan yaga kowa tsakanin Shahidah da Amaal dake shirya abincin abokan nasa da Aunty Sakina amma babu Maanal. Cikin raɗa-raɗa yake tambayar Munaya da tazo gaisheshi.       “Uncle sun fita ita da Aunty Amrah.”    Sai da ya kalla agogon hannunsa da mamaki ya furta, “Fita kuma da safen nan? Ina suka je to?”.       “Nima ban sani ba”.    Shiru kawai yayi ransa na ƙara jagulewa da tunani. Sai kuma ya miƙe ya fita. Can waje ya koma ya tsaya a ƙofar gida. Duk ma inda suke ai dole in sun dawo tannan zasu shiga gidan. Yana a wajen kusan minti talatin yana dakon jiransu sai ko ga napep ta tsaya a ƙofar gate ɗin. Amrah ta fara fitowa tana dariya, sai Maanal fuskarta da murmushi, da alama dai wata maganar suke data basu dariyan. Su duka hannayensu da kaya. Amrah ce ta fara lura da yayan nasu, ganin yanda ya tsume fuska ya sata haɗiye dariyarta. Ita dama Maanal tuni ta daina murmushin duk da bata gansa ba, sai da ta juyo zasu nufi hanyar shiga idonta ya sauka a kansa. Ɗan turus tayi tana kallonsa, sai kuma tai ƙoƙarin janye dubanta a kansa a taƙaice ya ce, “Good morning ” ta raɓa zata wuce.        “Zonan”.    Ya kirata a dake. Cak ta tsaya, jitake kamar tace bazata zo ba. Amma dai ta dake ta dawo da baya, yayinda Amrah ta amshi kayan hannun nata. Dan daga gidan Amaal suke, ɗinkunan su ne da tela bai samu gamawa ba sai jiya, shi kuma mijinta ya amso jiya da dare shine yau Maanal ɗin suka je ɗakkowa a gidan...          “Fushi ake dani ko?”.       Ya faɗa cikin kwantar da murya, kamar ba shike tsume fuska ba. Batare data kallesa ba ta ce, “Mi kamun da zanyi fushi da kai Yaya. Kawai dai yanayi ne”.      Murmushi ya saki mai armashi. Sai kuma ya sake matsowa kusa da ita sosai. Cike da lallashi ya ce, “To nidai ina roƙon afuwa dan ALLAH. Har yanzu kuma baki maida wayarki ba ne?”.     Kallon wayar tata dake hannunta tayi, batare data kallesa ba. “Kwana biyu da suka gabata na maida.”         “Shine kuma koma a taɓani. Naso sauka Abujan sai aka samu matsala. Dan bammayi zaton ganinki a kd ɗin ba”.     Yanzu kam murmushi ta saki, murmushin daba cika gani yay a fuskarta ba. Sai dai batace komai ba. Kafin shima yace wani abu wasu ƴan uwan Hajiya Yaya suka iso. Wani shegen kallon banza suke zuba mata, dan labarinta duk ya gama karaɗen danginsu daga jiya. Yayinda shi kuma Yazeed hankalinsa ke a kansu yana musu sannu da zuwa. Da wannan damar Maanal ta zame jikinta ta gudu. Sai waigawa yay yaga wayam bata a wajen. Yaso bin bayanta, sai baƙin suka sake janye hankalinsa dole ya haƙura...... _________★        Da mamaki Oum ke kallon AA dake shaƙar barci a gadonta. Da alama ma ya manta da yau zasuyi tafiya. Tunda suka kammala breakfast yau a ɓangarenta su duka gidan aka cigaba da hira shi kuma ya tashi ya shige bedroom ɗinta basu sake jin ɗuriyarsa ba. Umarnin zuwa kowa ya shirya da Abah ya basu ya saka kowa tashi ya nufi shiryawa. Ita dama cikin shirinta take dan haka ta shigo domin ganin mi AA ɗin keyi a ɗaki, kawai saita ci karo dashi a bargo ma ga ac ya ƙure.       Ac'n ta kashe, kafin ta ƙarasa gaban gadon tana kiran sunansa, dan tasan bashi da nauyin barci. Idanu kuwa ya buɗe a hankali ya sauke a kanta.     “Kowa nacan ya shirya kai kana nan kana barci Auta?”.          “Oum ALLAH ni barci nake ji, weekend ɗin nan nefa mutum ke ɗan samu ya huta. Wai inama za'aje ne?”.      “Koma inane idan munje zaku gani. Kuma ka tashi kafin Abah ya shigo ya samu baka shirya ba”.     Fuska sosai ya ɓata. Sai kuma ya yaye duvet ɗin ya tashi tare da sakkowa. Oum dai na tsaye tana kallonsa. Gadon ya fara ƙoƙarin gyarawa. Oum ɗin ta dakatar da shi.      “Kaga barshi jeka shirya zan gyara”.     Kafaɗa ya maƙe mata ya cigaba da gyarawa, sai da ya gama tsaf sannan. Wannan ba komai bane a garesu su duka. Dan Oum ta riga ta horesu da aiki har girki babu wanda bazai iya yi ba su duka ukun. Yana fita tayi murmushi, dan tasan a cike yake fam.  Itama ɗan shishshirya abinda take buƙata ta shiga yi...      Kusan sha ɗaya duk sun fito cikin shiri, AA ne ƙarshen fitowa cikin ƙananun kaya. Aiko Abah ya korashi canjawa. Oum ya kalla a shagwaɓe, ta masa alamar ba ruwanta. Sai ya tura baki ya koma. Aiko Fawzan ya shiga dariya da tsokanarsa. Babban yaya yayi murmushi su Nibras na taya shi dan sun san su dai babu damar yi a zahiri. Abah ma murmushin yayi, yayinda Mamy tai kamar bata san anyi ba. Bai wani jima ba sai gashi ya fito cikin wani arnen yadi omo blue daya ji ajiyayyen ɗinki. Ya kawo hula ya murza. Kusan su duka sai da suka ambaci masha ALLAH a zukatansu. Dan manyan kaya nama AA masifar ƙyau shi kuma baya son sakawa. Nibras kam ji take kamar ta haɗiyesa ta huta. Fawzan da bakinsa baya iya shiru ya shiga yimasa hoto da faɗin, “Kai wankan nan gaskiya bai kamata ya tafi a banza ba tuzurun gidan mu. Dolene na poster ka a media ko zamu samu wata tace tana so mu haɗa mata da cin hanci.”        Dariya su Abah suka sanya. Oum ta ce, “Yarona yafi ƙarfin sai an haɗashi da cin hanci sannan ya auru. Fawzan ka kiyaye mu”.    “Oum kada fa ku cika baki, yanzu yayin yara ake masu jini a jika shi kuma ya zama tuzuru”.          AA dai bai kulashi ba. Sai ma kama hannun Anum yay suka shige mota. Aiko zaram Nibras ma taje jikin motar ta tsaya. Babu wanda ya damu da hakan, sai ma Abah da Oum da Mamy suka shiga tasu motar tare, Babban yaya ma ya shiga Saheeba ta shiga kusa da shi. Sai Naufal ya shiga baya. Can kuma AA a mazaunin driver Fawzan ya shiga kusa da shi Nibras da Anum suka shiga baya. Fawzan yasan AA ba ƙaunar tuƙi yake ba a rayuwarsa, dan haka ya kallesa da faɗin, “Zaka iya kaimu har Kaduna babu wata damuwa”.       Kallonsa shima AA ɗin yay da faɗin, “Wai dama Kaduna zamuje? To yin me?”.       “Nima ban sani ba, amma biki Abah yace ai kamar”.     “Yanzu saboda zuwa biki aka hanani barci na. Kuma dan ALLAH ba sai a tafi a train ba”.           “To ya muka iya, kasan Abah da Oum akan son dangi. Ni kaina yau inada wani ɗaurin aure a cikin Abujan nan, yanzu dai bani driving ɗin kawai”.       “No barshi muje, idan na gaji sai ka amsa”. Cewar AA yana yin horn. Shi ya fara fita, Babban Yaya biye da shi sai drivern Abah a ƙarshe. Haka suka ɗauki hanya a jere gwanin sha'awa. Babu damar yin gudu dan in ana tafiya tare da Abah dama babu zancen gudu yaci ƙaniyar mutum. Sai dai abinka da lafiyayyun motoci cikin amincin UBANGIJI sha biyu da kusan arba'in a Kaduna tayi musu. Babban Yaya da Abah suka koma motar AA. Nibras suka haɗe da Saheeba data amshi tuƙin Babban yaya, oum da Mamy suna tare da driver. Su gidan Ammie aka nufa da su. Su kuma su Abah suka wuce masallaci domin yin sallar juma'a da ɗaurin aure.     Invitation card ɗin Abah ta miƙama AA. Bayan ya gama dubawa ya juyo yana kallon Abah ɗin, dan suna baya shi da Babban Yaya. “Abah kasan nifa ba wani sanin Kaduna ɗin nan nayi ba.”          “Eh mu samu mai napep ai zai kaimu in sha ALLAH”.    Haka kuwa akayi, dan da mai napep duka samu ya jagorancesu har zuwa masallacin da aka rubuta a jikin katin. Sun kuwa samesa cike da jama'a, da alama akwai wasu ɗaurin auren bayan wanda suka zo..... ____★         Su Oum ma sun isa gidan Alhaji Usman Chalawa. Tun fa a kallon anguwar jikin Mamy ya fara ɗan sanyaya, dan tayi zaton har yanzu su Ammie a irin waccan rayuwar ta baya suke. Ko dataga gaban ƙaton gate ɗin da sukai parking sai tai ɗif. Godiya driver yay ma mai napep ɗin daya jagorancesu suma, Oum ta masa alheri sannan suka samu waje sukai parking a nan gefen gidan. Akwai ƴan biki dake ta shigi da fita dan haka suma suka shige. Tabass gida ne babba kuma sashe-sashe. Duk da nasu yafi ƙawa da girma sun san anan ɗin ma babu raini gidan masu akwai ne. Basu san inda zasu nufa ba dan haka Oum tai ƙoƙarin kiran layin Shahidah. Bugu biyu kuwa ta ɗaga, cikin girmamawa tai sallama da fara gaishe da Oum ɗin. Murmushi Oum tai tana amsa mata, kafin ta ɗora da faɗin, “Gamu a harabar gidan ku bamu san ina kuke ba”.       Cikin mamaki da kuma rashin fahimta Shahidah ta ce, “Oum gidan mu? Wai nan Abuja?”.       “A'a Kaduna, inda ake biki”.   Ai ji Shahidah tai tana neman rikicewa. Hakama Amal ta saki soson shafa hodan hannunta tana kallon Shahidah. Suna a ɗakin Maanal ne suna shiryawa dama. Dan sai yanzu suka samu dama saboda aiki. Cikin sauri Shahidah ta yanke kiran, ta ja mayafi Amal biye da ita suka fito. Su Ammie na falo da su Hajiya Majdiya da suka kwana anan suma. Tambayarsu Ammie take lafiya? Ina zasu haka?. Batare da sun tsaya ba sukace suna zuwa.      Cike da farin ciki Oum ta kama Amaal da Shahidah ta rungume a jikinta. Musamman ma Amaal da sai yau ne ita suka gaɗu. Itama dai Mamy murmushin yaƙe ta shiga yi, yayinda Saheeba keta wani faman taɓe baki. Nibras dai ƴar kallo ce, dan ita dama nata baƙin halin akan AA ne kawai. Sashen Ammie su Amaal suka musu jagora, inda shigowar tasu tayi dai-dai da miƙewar Ammie da Hajiya Majdiya dan zataje ɗakin Ammien tai salla. Cak Ammie ta tsaya kamar wadda ta suma. Itako Hajiya Majdiya ta shiga ƴar dariya tana kallon yanda Oum da Ammie ɗin suka tsaya suna kallon juna kamar kaji. Kai daka kalla Ammie kasan a ruɗe take, dan jin take kamar irin mafarkin data saba yi ne akan Oum ɗin. Ɗan jujjuyawa tayi ta kalla kowa a falon, ƙarshe ta sauke idonta akan Amaal da Shahidah da duk suka koma yanayin tsoro. Dan su fargabarsu basu san yanda su Oum suke a zuciyar Ammien tasu ba a yanzu. Saboda tunda aka rabu bata sake yin maganar waninsu ba..........✍️       09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖9️⃣0️⃣ ______________ ........Sai kuma a mamakinsu sukaga a hankali Oum ta nufi Ammie. Ai tuni itama Ammie ta zaburo kansu suka rungume juna. Hakan ba komai bane, dan duk wanda yasan tarayyar Ammie da Oum yasan alaƙace mai ƙarfin gaske irin ta yaya da ƙanwa ciki ɗaya. Ciki ɗayan ma irin wadda akafi shaƙuwa ɗin nan. Su duka hawaye suke yi, hawayen kewa da begen juna da farin cikin sake haɗuwa a gaɓar da babu zato babu tsammani musamman ga ita Ammie. Ɗayan ƙaramin falon Ammie dake a rufe dan kar mutane su ɓata Amaal tazo ta buɗe. Sai da su Oum suka gaggaisa da mutane anan falon sannan suka shiga. Gaba ɗaya Ammie ita tama rikice, ta rasa ina zata kama ina zata saka su Oum. Yayinda su Oum keta sake mamakin ganin yanda ta canja, duk wanda yasan Ammie a shekarun baya ya ganta a yanzu za'a iya kwana ana gaddama da shi akan ba ita bace ba. Gaba ɗaya ta zama matar manya. Tayi ƙiba ta ƙara haske da cikar kamala. Dan ita kanta Mamy a wannan gaɓar jitai ta raina kanta. Saboda ko suturar dake a jikin Ammien ka kalla kasan lallai nagaba yayi gaba yanzu kam, na baya sai labari. Gefe kuma ga ganin Hajiya Majdiya a tare da Ammie ɗin ya sake tabbatar ma Mamy lallai dama Oum na tare da su Ammie kenan take munafuntar ta (kun san idan mutum nada halin banza kullum gani yake haka kowa yake ma😏)....      Salla suka fara gabatarwa saboda gudun fitar lokacinta. Kafin a cika musu gaba da abinci kala-kala. Kan Ammie dai a matuƙar ɗaure yake da ganin sanayya tsakanin Hajiya Majdiya da su Oum. Daga ƙarshe dai ta kasa haƙuri ta magantu. Dariya Hajiya Majdiya tayi, kafin ta warwarema Ammie komai. Matuƙar mamaki da al'ajab ne ya nema kashe Ammie, ta dinga raba ido tsakanin Hajiya Majdiya da Oum. A lallai tabbas bata san ƙannen Oum ba a fuska a tarayyarsu har suka rabu, saboda lokacin su suna ƙasar waje, amma tasan labarinsu, tana jin kuma tana ambatar ƙanwarta datai aure amma tana acan kasar wajen mijin kuma na nan Nigeria saboda yanada mata biyu a Zaria amma yana zuwa can wajenta dan yana kasuwanci a ƙasashen ƙetare. Cikin kasa daurewa Ammie ta ce, “Aunty! Dama Maman Najma ce kike yawan bani labari da mijinta ke Zaria amma ita tana can Paris”.        “Tabbas itace Asiya. Shekara shida kenan da dawowarta Nigeria har ma da su Abbu. Dan yanzu haka su suna Kano ne”.      “Ikon ALLAH kenan, shekaru biyar kenan muna tare amma bamu san akwai muhimmiyar alaƙar data taɓa haɗa ƙaddararmu ba. A lokuta da dama wasu al'amura na Maman Najma kan so sakani a ruɗani wlhy. Dan sai kita dawo min cikin idanu duk da bakwa kama ko kaɗan a fuska.”          “Gaskiya ne bama kama da Majdiya da Rafeeq sam. Garama Sulaiman shi kam da kin gansa zaki san akwai alaƙa. Mu kamar mun kwaso Mah-mah ne. Itako Majdiya da Rafeeq Abbu. Wai ni naga kowa banda Baby na fa, ko bata zo bikin bane?”.      Murmushi Ammie tayi. “Tazo, suna tare da su Najma Nene ta aikesu.....”    Dai-dai nan kira ya shigo wayar Ammie. Ganin Daddy ya sata ɗauka batare data ƙarasa maganar ba. Fuskarta da murmushi ta ajiye wayar tana kallon Oum. “Aunty dama harda su Yaya kuke tare?”.        “Ai mu duka gidan ne ba'a bar kowa ba. Halan har an ɗaura auren?”.     “Eh an ɗaura harma sun shigo. Amma inaga su basu ƙarasa wajen walima bane ba. Dan yace gasu nan a hanya a shirya musu abinci a sashensa.”            “Oh oh ji son bama mutane wahala. Maimakon su ci acan kamar kowa”. Mamy ce mai maganar. Dariya Ammie tayi, da faɗin, “Babu wata wahala Mamy, hakan ai shine dai-dai suzo na gansu shekara nawa”. Daga haka Ammie ta fice. Da wani shegen hararar ƙasan ido Mamy ta bita, sai ko karaf a idon Hajiya Majdiya. Mamaki sosai ya kama Hajiya Majdiya dan abu ne da basu taɓa gani ga Mamy ba. To kodai sunada matsala ne da Hajiya Asiyan? Kai to amma a dukkan labarin da Oum ta bata na alaƙa da tarayyarsu babu wani saɓani ai, hasalima Mamy bata da yawan shiga sabgar mutane. To kodai idonta ne ya gane mata ba daidai ba? Kai to gaskiya hakanne. Da wannan tunanin ta saki zancen a ranta suka cigaba da hirarsu.....      ★ Har cikin gida motar su AA ta shigo dan suna biye da Daddy ne. Yanzu kam Fawzan ne ke driving ɗin. AA na gefensa Abah da Babban yaya na baya. A kusan tare duk sukai ƙoƙarin fitowa. Hakan yayi daidai da fitowar su Huznah daga sashensu. Cak taja wani kalar wawan birki. Itama dai cikin kwalliya take, sai dai ɗan kwalinta a hannu ta yana siririn veil a kanta. Tare take da wasu ƴammata guda biyu. Sai wata dake biye da su da makeup box a hannunta, da alama dai kwalliya zatayima Huznah ɗin. Dan su sauran biyun da kwaliyarsu raɗam a fuska. Bakinta har harɗewa yake wajen ambaton “AA Darma! A gidanmu?”.           Duk kallonta ƙawayen nata sukai, wadda ke'a gefen haggunta ta ce, “AA Darma naki da kuka haɗu a Abuja lokacin bikin Yaseerah?”.       Bata iya ta bama ƙawar tata amsa ba. Jiki na rawa ta juya sashensu da sassarfa. Wani iri zallo zuciyarta keyi kamar zata fasa mata ƙirji ta fito. Hajiya Basariyya na falo tsakkiyar ƙawayenta su Maman Yaseerah Huznah ta faɗo musu. Tama manta a cikin taron mutane suke. Yanda take ƙwala kiran “Ummy! Ummy!” yasa Hajiya Basariyya miƙewa zaram. Tareta tayi tare da girgizata tana faɗin, “K Huznah lafiyarki kuwa? Wane irin kirane wannan? Jibafa yanda kike shigowa kamar wadda aka biyo.”          “Ummy AA Darma fa na gani a gidan nan”.      Rasama inda Hajiya Basariyya zata kamo AA Darma tayi. Ta ce, “Waye kuma AA Darma?.”         “Ummy AA Darma ɗin ne baki sani ba? Mijin da zan aura na Abuja”.   Ai sosai Hajiya Basariyya ta waro idanu waje, hakama Maman Yaseerah zaram ta taso inda suke. Hannun Huznah ɗin ta kama sukai cikin bedroom, Hajiya Basariyya ta take musu baya.       “K Huznah nutsu, da gaske kike kuwa”.     “Wlhy da gaske nake Mamah.” “Tab ɗin jan, eh lallai malam yayi gaskiya. Hakan na nufin aiki yayi kenan”. Maman Yaseerah ta faɗa tana kallon Hajiya Basariyya....... _In dai da gaske aikin nan yaci nima ai arakani wajen malamin nan zai min aiki akan makaranta AJIYA A DUHU musamman ƴan Discussion House da ƴan AREWABOOKS ina son a musu ASIRI su fara son Uncle RK🥱🥱🥱🤪🏃🏃🤣👍_ __________★       A yayinda haɗuwa ta kasance tsakanin AA Darma da Huznah, Ammie da Oum acan Kaduna. Anan Kano RK ne tare da Alhaji ƙarami yayansa da Abbu mahaifinsu suka kai ziyara gidan Baba Sardauna. Ƙyaƙyƙyawan bafilatanin dattijo mai tarin cikar kamala data addini. Anga jiya anga yau ana fatan ganin gobe. A yanzu shine uba kuma jigo da gaba ɗaya ahalin Baffa Ishaq Darma ke kallo a matsayi na kamar mahaifi. Shine garkuwa kuma shine alƙali mai tsawatarwa da zartarwa akan a tsakanin wannan zuri'a. Hakama matarsa ta karɓi wannan girma bisa ga bashi dukkan goyan baya ta hanyar amincewa ita ɗaya daga cikin wannan zuri'ar ce ba matar ɗa dake kallonsu a matsayin dangin miji ba. Dan bata da abin cewa ga wannan zuri'a sai godiya da fatan alkairi. Ita kanta mantawama take ba daga tsatsonsu ta fito ba.      Baba Sardauna ya girmi Abbu sosai, dan sai dai suyi sa'anni da Baba Umar mahaifin Abah kenan. Ga kuma girma irin na matsayin yayan mata a tsakaninsu. Harara Baba Sardauna ya makama RK bayan ya gama amsa gaisuwar Alhaji Ƙarami.          “Ni bazan amsa gaisuwarka ba ai Rafeeq. Dan lokaci kaɗan ma ya rage kai da wannan ɗan naka Ajwaad da Najeeb na sakaku a ɗaki na zane ciki da bai sannan nakai hotunanku massallaci ko za'a samu mai taimakonmu ya baku matan aure koda guragu ne. Kun wani ajiye gemunan ƙarya kamar na ALLAH. Ku yanzu dan ALLAH Moddibo da Saleem basa birgeku, da ƙananun shekarunsu amma yaran bibbiyu....”         “Ayi haƙuri Baba a mana afuwa. In sha ALLAHU zamuyi”.     “Haka kullum kuke faɗa. Har gara kai ma kana bada haƙuri da nuna zakayi, amma waɗan can biyun inaga sai mun haɗa da roƙon ALLAH dan da alama akwai iska marasa san aure a tare da su”.          Abbu dake murmushi ya ce, “Ai kaima dai ka faɗa Yaya. Ni wlhy canai idan suka wuce wannan shekarar kawai a samu wanda suka dace a aura musu sai dai akai musu ɗakunansu, ba sai suyi yacce zasuyi da su ba”.       “Shawara mai ƙyau wlhy Kasheem. Dama jiya-jiyan nan muke maganar nan da Kamila da tazo. Sai kuma ga Khadijah ta kira waya Itama tana mun complaine akan Raihana da Nuwaira.”          “To ai sai asan mafita kawai Yaya, duk da shi yazo da nasa batun ne yanzu haka wai acewarsa. Ni kasan ba kama zancensu nake ba su ukun nan dan munafukan bakinsu ɗaya da kake gani. Najeeb da Ajwaad da Rafeeq ba, ALLAH kaɗai zasu gaya min akan aure na yarda dasu”.        Dariya Alhaji Ƙarami yay da faɗin, “Kai Abbu, ALLAH kun kasa fahimtarsu ne kawai.....”        “Ohhh yanzu na gane, Sulaiman kuke ɗaure musu ƙugu kenan ku yayun nasu”.      “A'a wlhy Baba. A dai yi haƙuri, in sha ALLAHU wannan karon komai ma yazo ƙarshe. Ina kuma goyon bayanku dan muma ba son zaman nasu muke haka ba”.        “To Alhamdullah ai haka muke son ji”. Cewar Baba Sardauna yana gyara zama. Sai kuma ya kafe RK da tunda ya duƙar da kai bai ɗago ba. Cike da kulawa ya ce, “Ɗan nema, zonan naji ɗuminka, dama kwana biyu nayi kewarka kaje ka maƙale a Abuja wajen ɗan uwanka”.     Murmushi RK yayi, tare da miƙewa ya isa gaban Baba Sardauna, zai zauna ƙasa ya kamashi ya zaunar a kusa da shi, tare da ɗan rungumesa. “Fitinanne wai ni kake jin kunya kuma?”.       Dariya RK ya fashe da ita, hakama Alhaji ƙarami da Abbu. Aifa nan baki ya buɗe aka shiga gaisuwa. Sai kuma hira ta ɓalle. Suna cikin hirar sai ga Baba Umar. Shima dai nutsatstsen mutum mai cike da kamala. Dan zasuyi shekaru ɗaya da Abbu. Shi mutum ne da baida yawan magana. Dan duk cikinsu ya fisu haƙuri. Bazaka taɓa cewa ya haifi kamar Abah ba, abinka da ana jin daɗi.          Sosai suka tattauna akan al'amarin dake damunsu na rashin auren RK, AA, da Najeeb daya kasance ƙani ga Abah. Shima dai yaƙi auren, har ga ƙannensa biyu sunyi har da yara. Shine ƙani na uku a wajen Abah, sai Saleem da Moddibo sannan matar Alhaji ƙarami data kasance Auta. Shi yama girmi su AA ɗin. Sosai Baba Sardauna da Baba Umar suka ji daɗin kawo matar aure da RK yayi. Sun kuma tabbatar da babu wasa a satin nan zasuje Kaduna nema masa aurenta. AA da Najeeb kuwa su zasu zaɓa musu matan aure dan ayi bikin rana ɗaya dana RK ɗin.       A wani irin farin ciki mara misali RK ya tsinta kansa. Har ji yay ya ƙagara su baro gidan Baba Sardauna dan ya samu ya kira Maanal ya sanar mata wannan albishir, duk da yasan suna a cikin biki yau. Kasa haƙuri yayi tun suna a gidan ya tura mata daddaɗan text massage, Dan basu baro gidan Baba Sardauna ɗin ba sai da sukai sallar isha'i a massallacin ƙofar gidansa. Suna ƙoƙarin fitowa kuma sai ga Hussain yazo gidan tare da matarsa da yaransa biyu shima. Nanfa kuma aka sake zaman sabuwar gaisuwa, dan RK da Hussain ɗin sun jima ba'a haɗu ba. Ƙarshe dai sai goma suka baro gidan.      Sanda suka iso har Mah-mah da Rufaidah da yara sun gaji da jiransu sunci abincinsu. Suna a falo suna hira, yara kuwa sun tafi sun kwanta. A rayuwar Mah-mah da Rufaidah sam babu surukuta, zama ake irin na uwa da ƴa. Dole rayuwar gidan su Rafeeq tai matuƙar birgeka, dan rayuwace mai cike da so da ƙaunar juna. Babu munafunci, babu makirci. Kowa na ƙoƙarin bama ɗan uwansa hakkinsa dai-dai gwargwado. Zama Abbu da Alhaji ƙarami sukai anan falo wajen Mah-mah, yayinda RK yay sashensa dan burinsa kawai yay kiran Maanal ya mata albishir........✍️ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖9️⃣1️⃣ ______________ ........A falon Daddy akama su AA masauki, kafin Daddyn ya ɗaga waya yay kiran Ammie akan a kawo musu abinci. Da to Ammie ta amsa masa, tare da ajiye wayar suka cigaba da haɗa abincin ita da su Shahidah da Hajiya Majdiya. Hakan kuma yayi dai-dai da shigowar su Maanal, Amrah, Najma, Aneesah, Zezaah (ƙawayen Maanal kenan na sarvese). Dole ne matasan ƴammatan kai musu kallo ɗaya ka ƙara. Dan babu wacce batai ƙyau cikin tata shigar ba. Taku suke cike da nutsuwa sun kamo kuloli na waina masa da Ammie tasa akayi a gidan Nene, yayinda Almajirai uku ke biye da su da wasu kulolin manya da sukafi biyun da suka kamo. Gaishe da mutanen dake a falon sukayi sannan suka ƙarasa kitchen inda akace musu su Ammie na nan.       “Kai yaran nan ALLAH yay muku albarka, kamar kun san yanzu nake tunanin kiranku”. Ammie ta faɗa tana kallonsu. Amsa mata duk sukayi da Amin. Maanal ta matsa jikinta ta rungumeta. Kallonta tai da mamaki. “Lafiyarki kuwa Maanal?”.       Fuska ta ɗan ɓata, sai kuma ta kamo hannun Ammie ta ɗora a saman ƙirjinta dai-dai saitin zuciyarta. Kamar zatai kuka ta ce, “Ammie zuciyata ce ke bugawa da sauri, gabana kuma nata faɗuwa. Sai nake jin kamar wani abu babba na kusanto ni”.        Shiru Ammie kawai tai tana kallonta. Itama zuciyar tata na raunana. Dan bata raba ɗayan biyu kasancewar Ajwaad a gidan nan ya sakata jin hakan. Ya rabba wannan wace irin tarayya ce haka?. Amma dai bari tai mata tambaya. Fuskar Maanal ɗin ta shafa, cike da kulawa ta ce, “Dama yana miki haka?”.         Kai ta girgiza ma Ammien tana sake narke mata a jiki. Ammie ta sauke ajiyar zuciya, tare da shafa mata kai ta ce, “Kairan in sha ALLAH kinji my babie”.     Kai ta ɗagama Ammien sannan ta saketa saboda umarnin da Hajiya Majdiya ta basu na ɗaukar abincin da aka shirya su kai sashen Daddy. Manaal da Najma ne a gaba, sai dai Najma ɗin ma ta gota Maanal, dan itace ta fara shiga falon da sallama Maanal biye da bayanta. Da wani irin sauri Najma ce ta tsaya cak tana mai waro idanunta da faɗin, “Lah wa nake gani kamar su Yaya Fawzan da Yaya AA? Abah! Babban Yaya”.       Da wani kalar sauri itama Maanal ɗin ta tsaya, hakama su Amrah duk suka tsaya suna kallon inda Najma ɗin ke kallo, sai ma ta ajiye kular hannunta ta nufi inda suke cike da mamaki da farin ciki. Ba ƙaramin girgiza zuciyar Maanal tayi ba, dan nata idanun akan AA ɗin suka fara sauka. Kamar shima kuma ance ya kalletan sai nasa idanun a kanta. Da sauri ta janye nata zuciyarta na zallo. Cikin ƙarfin hali ta maida su akan Abah da ya furta, “Finaly yau dai gani ga Autan Oum”.          Ƙasa Maanal tayi da kanta tana murmushi, sai kuma ta cigaba da takowa cikin falon ta ajiye kayan hannunta inda su Amrah suka ajiye, gaban Abah taje ta durƙusa, har cikin ranta itama tana jin daɗin ganinsa. Abah ubane da bazata taɓa mantawa ba a rayuwarta. Ya nuna mata dukkan gata da soyayyar da ko ita ɗin a cikin ahalinsa ta fito iyaka kenan. Shiyyasa har gobe shine uba mafi kima da daraja da take kallo a cikin idannunta. Hatta da babu sunan mahaifi kawai yake amsawa a zuciyarta. Amma uba na gaske da bugun ƙirji a nunama duniya Abah ne farko. Cikin rawar murya alamar tahowar kuka ta shiga gaishe shi. Shima a mamakin duk wanda ke'a falon idanun Abahn cike suke da ƙwalla. Amma sai yay jarumtar sakin murmushi tare da kai hannunsa ya kamo nata. Kamar abinda take jira kenan hawayen suka shiga rige-rigen sakkowa.        “My daughter nima so kike nayi kukan?”. Ya faɗa cikin taushin murya da kulawa. Kanta ta girgiza masa. Kafin ta share hawayenta ta ɗago ta ɗan kallesa. Murmushi ya sakar mata, itama sai tayi murmushin. “Abah nayi kewarka matuƙa”. Ta faɗa a hankali. Gefe ya kauda kansa, yasa babban yatsarsa ya ɗauke guntun hawayen daya ciko masa idanu shima. Har cikin ransa yana ƙaunar yarinyar, ɗaukarta yake tamkar yaransa guda uku daya mallaka a duniya. Sake juyowa yayi gareta da murmushin dai. “Nima nayi kewarki Maanal. Bantaɓa kwana na tashi babu ke a zuciyata ba. A kullum ina ji a raina akwai wani giɓi da babu a cikin ƴaƴana. ALLAH yay miki albarka, ya kare rayuwarki, ya azurtaki da farin ciki mara yankewa. Ya rabbi kasa iyakar jarabawar kasancewa a nesa da juna da mukai kenan.”      Jiki a sanyaye kowa dake a falon ya amsa. Yayinda kan AA ke a ƙasa babu mai ganin fuskarsa balle yanayinsa. Gaishe da su su Aneesah sukayi suka fita, sai Najma da Manaal dake gaban Abah suna magana ƙasa-ƙasa da kowa baya ji. Dan hatta Daddy dake a kusa da su baya jin mi suke faɗa. Dai-dai nan Huznah ta shigo hannunta ɗauke da babban basket an shiryo abinci, sai yara biyu biye da ita da kayan ruwa da lemuka. Gaba ɗaya hankalinta akan AA da kansa ke ƙasa har yanzu yana latse-latsen waya. Babu ko kunyar mahaifinta dake a falon kanta tsaye gaban AA ɗin ta nufa ta dire basket ɗin, murya can ƙasa cike da iyayi ta ce, “Barka da zuwa gidanmu Sweetheart”.      Ɗan jimm AA yay zuciyarsa na kai da kawon wai da shi ake ko wa? Ga shi kamar yasan muryar. Sake yin magana da tayi ya sashi ɗagowa a karo na farko, manyan idanunsa da suka ɗan kaɗe ba kamar sanda ya shigo gidan ba da suke fari tas ya zuba mata. Harga ALLAH yayi mamakin ganinta anan ɗin, amma sai ya dake ya wani kalar janye idanunsa ya maida akan wayarsa. Duk da zuciyar tata ta raunana da salon nasa haka ta dake tare da basarwa ta juyo tana kallon sauran mutanen falon. Karon farko gabanta ya faɗi sakamakon saukar idonta akan Abah, ya ALLAH, wlhy batasan harda mahaifinsa ba, ai da ta kama kanta. Ita tsabar ganinsa ya firgitata duk zatonta abokansa ne ma. Zaram ta miƙe daga gaban AA ɗin ta nufi inda Abah yake. Sai da ta watsama Maanal dake mata kallon mamaki harara sannan ta durƙusa cike da girmamawa tana gaishe da Abah. Amsa mata yay cike da kulawa dan kamannin Daddy a bayyane suke gareta. Ya tambayeta sunanta ta gaya masa tana faman sinne kai wai ita taji kunya. Kafin ta juya tana gaishe da su Babban Yaya. Ta gane Fawzan dan haka bayan gaisuwar ta tambayesa ina Oum da Mamy.          Fawzan da al'amarin yarinyar ya ɗaurema kai ya bata amsa cikin dauriya. “Su Oum na tare da Ammie”. Zaram kuwa ta miƙe da faɗin, “Lah ai ban sani ba”. Kafin wani ya samu damar magana har ta fice. Tsabar mamaki daya lulluɓe Daddy ya saka shi suman zaune ya kasa magana. Sai kuma Huznah ɗin na fita Hajiya Basariyya da Maman Yaseerah suka shigo da sallama. Shi Abah ba wani sanin Maman Yaseerah yayi ba, duk da kuwa ƙanwarsa na matsayin kishiyarta. Koda suka gaishesu ya amsa ne da tunanin duka matan Daddy ne, dan kamanin Huznah yafi fitowa a fuskar Hajiya Basariyya. Fuskar Maman Yaseerah da murmushi ta ce, “To wai ni ina surukin namu anan?”.       Karan farko Daddy daya kasa daurewa ya ce, “Suruki kuma?”.      “Eh mana Alhaji. Ai baƙin Huznah ne, nazatama har sun sanar maka, shine muke maka batunsa kwanaki, har mukace ka shirya za'a kawo kuɗi kace a jinkirta a gama na Yazeed ko. Kamar AA naji tana ambatonsa da shi ita Huznahr”.       Wani irin ɗagowa AA yayi ya kalla Hajiya Basariyya mai maganar, yayinda Abah da su Babban Yaya duk suke kallonsa su kuma. Shi ko Daddy Hajiya Basariyya ya zubama idanun kawai. Sai falon yay shiru akama rasa mai iya yin magana. Wani irin takaici ne ya gama turniƙe AA, jiyay bazai iya daurewa ba, dan haka ya buɗe baki a fusace zai yi magana, amma sai Babban Yaya dake kusa da shi ya kama hannunsa ya riƙe. Dole yay shiru, tare da haɗiye maganar. Tsaf Daddy ya lura da abinda ke faruwa. Dan haka a dake ya cema su Hajiya Basariyya, “Okay naji, kuje zasuci abinci tukunna”.        Baki Hajiya Basariyya ta sake buɗewa zatai magana Daddy ya harareta, dole ta haɗiye. Suna fitowa Maman Yaseerah ta ce, “Kada ki wani damu shirin nan namu fa ya hau, kin san Malam akwai iya tsara abu”.       “Anya kuwa Aminiya, kina ganin yanda yaron ke kallon mutane babu ɗigon sassauci, wlhy sai yanzu na fahimci abinda Huznah ke sanar min a kansa. Lallai da ganinsa zai yi baƙin taurin kai.”          “Karki wani damu da taurin kansa, zamu bi dashi ne tsaf ya mata biyayya kamar babu gobe. Yanzu dai kawai muyi yaƙin shigarta gidan. Ammafa ni ina mamakin munene alaƙarsu da Asiya ne haka wai?”.      “Nima wlhy ina son sanin wannan dangantar, amma ki bari, akwai ta hanyar da zan bincika”.     ★A ɓangaren Huznah ma tana can sashen Ammie, hatta Mamy tayi mamakin ganinta, amma sai ta basar. Cike da ladabin daya bama Ammie da su Amaal mamaki take gaishesu, sai wani sissinkuy da kai take. Ita Oum ma bata wani maida hankali a kanta ba, hirarsu suke da Maanal dake jikinta kwance. Dan itama tun shigar su Hajiya Basariyya falon Daddy ta baro can.      Saheeba dai da Nibras harara suketa antayama Huznah a kaikaice, dama kuma basu tanka ba koda tai gaisuwa. Bayan ficewarta cike da takaici Huznah tai tsaki da faɗin, “Ya akai tasan nan? Ko biyomu tayi ne? Nifa ban san ballagazanci wlhy. Yo ko mata sun ƙare mi Yaya Ajwaad zai yi da ita, balle ma yanada matarsa a hannu. Ai wlhy inaga sai Nuratu ta sake mata wani sabon zanen a fuska zata kiyayi mata saurayi”.      Da mamaki Oum ta ce, “Ban gane ba, ke ina kika san wannan ɗin Saheeba?”.          Batare da Saheeba ta kula kallon gargaɗin da Mamy ke mata ba ta ce, “Oum itace fa wadda sukai faɗa akan Yaya Ajwaad da Nuratu a Abuja”.      “Ikon ALLAH, ai ni ban ganeta ba sam wlhy. To ya akai tasan nan ɗin?”.    Amaal da Shaheeda da Ammie mamaki ya gama kashesu, Maanal kam yi tai kamar bata ji mi suke tattaunawa ba. Sai ma karanta saƙon da ya shigo mata a waya take wanda AA ne kuma ya turoshi akan tazo, amma ta masa reply da a (anƙi ɗin). Amaal ce ta bama Oum amsa da, “Oum ai anan gidan take, ɗiyar matar tsakkiyar gidan nan ce”.          “Oh shiyyasa na ganta a gidan Shahidah kenan. To ALLAH ya rufa mana asiri ”.    Da Amin kowa ya amsa aka saki zancen. Bayan sun kammala cin abinci ne Ammie da Oum da Hajiya Majdiya da Mamy sai Amaal, Shahidah da Maanal suka nufi sashen Daddy da yay kiran Ammie a waya. Sun samu suma sun kammala cin abinci, dan haka akai zaman gaisawa cike da mutunta juna. Abah nata tsokanar su Amaal. Dan yanda sukai jiki suka zama manyan mata ya bashi mamaki. Hakama yaransu da su Waleed duk suna zagaye da shi yanata sanya musu albarka da musu wasan jika da kaka. Sai da ya gama tsokanarsu yaran suka fito suka bar su Ammie can. Da wannan damar Abah yay amfani wajen bama Ammie haƙuri da neman gafararta akan abinda ya faru a baya. Ya ɗora da faɗin,..........✍️ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖9️⃣2️⃣ ______________ ........“Nasan zakuyita mamaki akan rashin bin bayanku da bamuyi ba a wancan lokacin, a randa kuka wuce a ranar Fateema jikinta ya rikice matuƙa, dan yanke jiki tai ta faɗi, dole muka wuce da ita asibiti, amma sai suka turomu Abuja dan al'amarin nata banbane, paralysis na neman kamata. Tashin hankali yasa bamu tsaya Abujan ba kawai muka fara shirin fita da ita waje da tunanin bazamu daɗe ba zamu dawo sannan gwaggo ta huce, ashe wasa farin girki, dan shima Ajwaad sai ciwo mai ban tashin hankali ya samesa, ga depression. A haka suna cikin jiyyar su duka biyun Fateema ta matsa ni da Fadeel muka taho Nigeria domin ku, kai tsaye kuma Giro muka nufa, amma sai muka samu cewar wai ai suma sun wayi gari kun gudu, kuma an sanar dasu a majiya mai ƙarfi kuna dangin mamanki ba kuma a ƙasar suke ba. Bamu da wani dalilin ƙin yarda da su, dan haka muka juya muka koma. Amma Fateema naji tace ƙaryane, baki da wani dangi a ƙetaran Nigeria, ta sake tada hankalinta har takai jikinta dana Ajwaad yayi rikicewa mai ban tsoro, dan Ajwaad akwai daren da ma har mun gama yarda ya rasu, sai kuma ya farfaɗo gabannin asuba. Sai da akaita tausarta tare da mata alƙawarin a hankali zanta bincikenku sannan,  muka maida hankali akan Ajwaad kuma. A lokacin ne kuma aka bani ambassador, shiyyasa bamu dawo Nigeria ba, amma inata ƙoƙarina batare data sani ba akan neman ku. Sai dai kuma ALLAH bai ƙaddara ba sai a dalilin samuwar aikin Maanal a kamfanin Ajwaad ta dalilin Rafeeq. Dan ALLAH mu yafi juna Asiya, mu ɗauka dukkan abinda ya faru ƙaddararmu ce babu mai canjata. Mu dawo da zumincinmu tamkar a baya can.”        Hawayen dake gudu a fuskarta Ammie ta share. Ta ce, “Babu komai Yaya komai ya wuce. Ni dama ban taɓa ƙullatarku ba wlhy. Sannan ban san ma Maanal a ina take aiki ba dan basu sanar min ba. Da tun kafin kuzo nan ma nice zanzo gareku, ban dan Rafeeq nada alaƙa da ku ba shi da Maman Najma. ALLAH ne kuma bai ƙaddara haɗuwar tamu ba shiyyasa, tunda gamu tare da Majdiya fin shekara huɗu”.       “Ikon ALLAH ai yafi gaban wasa. Wannan wata hikima ce ga UBANGIJI mai ɓoye al'amura ta yanda yaso, a kuma inda yaso. Shi kuma yasan dalilin yin hakan garemu”.. Haka ne. Kowa ya faɗa cikin jinjina kai.... _________★        Da yamma sosai su Abah sukai shirin wucewa, sai dai fa Oum tace suje ita sai gobe in sha ALLAHU. Jin haka AA yace shima ya fasa, ƙafar babarsa ƙafarsa. Wani irin takaici ne ya turniƙe zuciyar Mamy, dan haka kawai take ji a ranta wani abun Oum ke son ƙullawa. Sai kawai catai ai itama kuwa tana nan ɗin. Sam babu wanda ya kawo komai a ransa a tsakanin Oum da Ammie, sai AA ne yay wani iri. Daga baya kuma yace to kawai shi bari ya bisu. Yana ganin hararar da Mamy ke masa amma ya basar. Nibras kam wani sanyi taji a ranta, dan har hankalinta ya tashi da zaman AA a tsakiyar kuraye biyu da take kallo. Wato Maanal da Huzna😂, yayinda Huznah da keta dama-dama da AA ɗin taji kamar tayi kuka. Haka dai babu yanda ta iya suka wuce. Dama Maanal ko'a kwalar rigarta, sai ma hirarsu suke da Fawzan....         Da daddare akai gagarumar dinner ɗin datai tsawa da amsa kuwa a garin na Kaduna kamar yanda su Hajiya Sabuwa sukai fata. Yau ma su Ammie sunje, kuma harda Maanal. Inda rigima taso tashi a hall ɗin, saboda matsawar Hajiya Majdiya Maanal da su Shahidah sukaje yima amarya da ango liƙi. Aiko Yaya Yazeed ba kunya Maanal na liƙa musu kuɗi yana liƙa mata, sai kawai abokansa ƴan neman magana suka taso suka rufe Maanal da liƙi aka daina liƙama amarya. Nanfa masifa ta tashi, Aunty Sabuwa da Hajiya Yaya suka miƙe zuwa wajen. Wani kalar fisga da Hajiya Yaya taima Maanal kaɗan ya rage tai muguwar faɗuwa ALLAH ya taƙaita Yaya Yazeed ya tareta. Wayyo ina wuta su saka Maanal, nan fa ƙannen Yazeed sukai ma Maanal zobe wai zasu daketa, sai da Oum ta shigo tsakkiyarsu cikin ɓacin rai ta janye Maanal ɗin dan daga ita har Mamy sun halarci dinner ɗin suma. Gaba ɗaya suka bar hall ɗin banda Mamy data maƙale, dan dama damar hakan take buƙata na keɓewa da Hajiya Basariyya....        Abu kamar wasa tun a daren ƙawayen amarya da ƙannen Yazeed suka dinga posting hotunan Maanal a media suna faɗin maganar banza a kanta. Cikin ƙanƙanin lokaci kuwa abu yayta yawo. Kafin wayewar gari al'amari ya zama babba, dan tunda ahalin su Hajiya Yaya suka dawo daga wajen dinner sabon rikici ya dake ɓalle. Ga amarya an kawo amma bata batunta ake ba. Wannan tashin hankali ya saka Maanal ta tashi da matsanancin ciwon kai da zazzaɓi. Dole da safe Nene tai shirin wucewa da ita gidanta. Saboda wannan rikici ya zama wani babban al'amari daya bama kowa mamaki, wato zancen fyaɗe da akaima Maanal sai gashi a bakunan mutane harma da Media dangin Hajiya Yaya na gorantama Ammie da Maanal. Matuƙar tashin hankali Ammie da su Amaal da su Oum sun shiga, dan sun rasa daga ina wannan magana ta fita. Sirrine da babu wanda ya sanshi a gidan daga Daddy sai Yazeed. Ai sai fa jikin Maanal yay bala'in birkicewa, abinda ake gudun dai ya nema kaiwa ga faruwa, sai da akai gaggawar kiran likitanta abokin Yaya Yazeed dake anan cikin Kaduna..      Wannan fitina ba'a samu kwantawarta ba sai da Baban su Hajiya Yaya yazo gidan da kansa. Shine fa yay musu kaca-kaca yace kuma biki ya tashi kowa ya shirya ya koma inda ya fito tunda amarya ta shiga ɗakinta. Sauran shagali kuma ya soke su, wanda kuma yake ganin bai isa ba zai yi ga fili ga mai doki. Hakan ya ƙara baƙanta ran Hajiya Yaya da Aunty Sabuwa, sai dai babu yanda kuma suka iya..     Wannan masifa ta bama Oum mamaki, kishi kamar bala'i, ai sai taji ta sake ƙaunar Mamy a ranta. Ta kuma sake jin girmanta da kimarta, dan su dai irin wannan masifa basu taɓa shigar koda kwatankwacinta ba. (Nace Humm Oum ai gara irin su Hajiya Yaya da taki kishiyar😭). Zuwa yamma Alhamdullah aka samu jikin Maanal ya dai-daita musamman ta bangaren zuciyarta, ganin kuma Oum da Ammie ga Nene ga ƴan uwanta duk a tare da ita kowa na lallashinta ta sake ƙarfafa kanta. Daddy ma da Baba da kansu suka dinga lallashinta da bata haƙuri. Sai ma taji duk kunya ta kamata. To wai miye ma na damuwar, ai abinda kowa ke faɗan gaskiya ne, ai an mata fyaɗen. Tunda dai abune da bazai gogu a rayuwarta ba mizai sa ta dinga shiga damuwa dan an maimaita faɗar an mata da baki. Wanda ma ya aikata ɗin alfahari fa yake da hakan. Sai kawai taji wata irin tsanar AA ta sake tasirantuwa a zuciyata. Aiko bayan sallar isha'i ta zauna ta rubuta text massage ta turama RK akan in dai masu zuwa nema masa aurenta suka wuce gobe zata bama wani dama. Dan a yanzu auren kawai take iya kallar ma kanta a matsayin mafita..        Aiko hankalin RK ya tashi da ganin wannan saƙo nata, dan shi bai san mike faruwa ba duk yau bai duba ko ina na media ba sunje wani ƙauye da Abbu ya sai gona zai fara noma ne. can suka yini shi da Alhaji ƙarami da Abbu ɗin. Ƙoƙarin kiran Maanal ɗin yayi amma sam taƙi ɗaga masa, dole yay kiran Hajiya Majdiya tunda ta sanar masa tana kd ɗin gidansu Maanal biki. A bakinta yaji komai dake faruwa, ya kuma shiga media ya ga sauran. Hankali tashe a daren ya samu Abbu da zancen zuwansu nema masa aure Kaduna a gobe maimakon next week Friday da sukace. Babu yanda Abbu bai so ya fahimtar da shi dai ya bari Friday ɗin ba amma ya birkice, har abin ma ya bashi mamaki shi da Mah-mah. Dole suka amsa masa da cewar za'aje goben in sha ALLAHU.       A daren Abbu yay kiran Baba Sardauna suka tattauna sosai. Baba Sardauna mutum ne mai fahimta dan haka ya amince suje goben kamar yanda yarinyar ta bada dama kawai.... ____________★     WASHE GARI ganin jikin Maanal da sauƙi Mamy da Oum sukai shirin komawa Abuja da safe. Hakama su Hajiya Majdiya. Dama gidan ya koma tsit duk an watse, sai amarya da ango dake can sashensu suna yin baƙi. Koda yake ango fa yana a sashen Ammie ya tare da shi ake jiyya. Sai Ammie ta korashi yake tafiya wajen amarya akan dole. Bayan wucewar su Oum Ammie tace suma su Shahidah su fara shiri su wuce. Dan ta fahimci cigaba da zaman Maanal a gidan zai haddasa wani sabon rikici ne. Tunda Yazeed yaƙi tsaida zuciyarsa waje ɗaya. To gara su wuce ɗin Maanal ɗin ta ƙarasa jiyyar a can. Haka dole badan sun so ba suka hau shirya kayansu akan zasu wuce da sassafe gobe tunda sun sami jirgi. Amaal kuwa a daren Ammien tace a ranar zata wuce gidanta....       Bayan sallar azhar babu zato baƙin Kano suka iso garin Kaduna. Sai dai shi Daddy yasan da zuwan nasu dan tunda safe RK yay kiranshi ya haɗashi da Abbu sukai magana. Sai Daddy yaji ya gagara yima Abbun musu, ya basu damar zuwan. Dama yasa a shirya abinci a sashen Ammie, duk da batasan na miye ba bata tambaya ba suka shiga kitchen ita da su Amaal. Manaal kuwa na ɗaki kwance dan jikinta babu ƙarfi, dan ma tana ƙoƙarin danne komai ne ta ƙarfin tsiya.           Tun kafin baƙin su iso su Amaal sunje sun shirya abinci kamar yanda Daddy ya bada umarni. Hakan yasa suka kara tunanin baƙin ta ɓangaren kasuwanci ne, dan in dai bakine da babu alaƙa haka Daddyn ke musu. Ashe a gidan Ammie ce ma kawai tasan da zuwan baƙin dan itace tai girki, sauran ko basu san da zuwan wasu baƙi ba musamman ma sashen Hajiya Yaya. Garama ita uwar ƴan tsirkun gidan Hajiya Basariyya taga alamomi. Amma itama ganin Daddyn nata dama-dama saita zata baƙinsa ne can na kasuwa maybe sukazo masa ALLAH ya sanya alkairi...      Tarba ta mutunci da mutunta juna aka samu a tsakanin Daddy da su Baba Sardauna. Da su Yaya Nuhu (Wato ƴaƴan Nene uku Da daddyn ya buƙaci suzo. Dan ita Nene tun a ɗazun da hantsi Daddyn yaje yay mata bayanin komai har gida. Ta kuma bada goyon baya ɗari bisa ɗari tare da tausar zuciyar Daddy akan ya bari Rafeeq ya auri Maanal dan haɗin Yazeed da Maanal bazai haifar da ɗa mai ido ba sam balle farin cikin da ake fata. Alhamdullah ya fahimceta shima dan jiya ya kwana ne yana auna abubuwa a ransa. Gefe kuma ga Ammie taje har ɗaki tana masa kuka da roƙo da magiya akan yabar batun Maanal da Yazeed ɗin dan ALLAH ya aura mata koma waye).        Bayan tattaunawa irin ta manya masu ilimin addini da sukaga duniya duniya ta gansu suka yanke rana har ma da sadaki a take. Dan yanda suka buƙaci ayi nan da sati uku zuwa wata guda sam Daddy baiyi musu ba. Duk da zuciyarsa cike take da rauni da tausayin Yazeed. Shi baima san ta yanda zai tunkari Yazeed ɗin da wannan batu ba. Gefe kuma shi kansa yana takaicin rashin wannan alkairi da yaso haɗawa tsakanin jininsa dana Ammie. Wata irin tsanar Hajiya Yaya da Sabuwa yaji ta ƙara faɗi a zuciyarsa. Dan wannan karon sun kaishi maƙurar da dole sai ya ɗauki mataki a kansu kam...... _________★        A Abuja kam su Oum sun tadda AA cikin matsanancin ɓacin rai da damuwa. Dan shima yaga wani kaso na abinda ke yawo a media ɗin tun jiya. Hankalinsa ya tashi matuƙa, tare da tausayin kansa da Maanal. Yata ƙoƙarin gwada kiranta amma sai ya kasa. Hakama ya gwada kiran Mamy domin ya roƙeta ta cire takunkumin datai masa amma ya kasa. Dan yayi alƙawarin koda soyayyar da yake ma Maanal zata kasance ajalinsa bazai taɓa bijire ma Mamyn ba balle akai ga tona mata asiri a wajen mutane masu daraja da suke mata kallon girmamawa da mutuntawa. Koba komai ita ɗin mahaifiya ce, tanada babbar daraja a garesa, darajar da zai iya sadaukar da koma miye akan ta. Saɓon UBANGIJI ne kawai Oum da Mamy da Abah zasu sakashi ya bijire musu, dan wannan kam har abada babu biyayya a tsakaninsa da su. Amma buƙata takai da kai ta rayuwa koda zai cutu zai sadaukar, dan haka ya amincewa kansa ne zai auri Maanal kawai da amincewar Mamy dan itace kawai matsalarsa a yanzu. Hankalin Oum ya tashi, dan ya kafe shi kada a kira masa kowanne likita lafiyarsa ƙalau. Lallashin duniya yaƙi sauraren kowa, daga ƙarshe ma yace shi zai yi tafiya ne zuwa gobe.       Ita kanta Mamy yanayin AA ɗin ya bata tsoro, amma ta zaɓi dakewa akan janyewa. Dan a ganinta ai dama sai anji wuya ake jin daɗi, dolene tabi kowacce hanya domin dawo da yaranta hannunta. Abah kuwa ransa a ɓace yake da AA, taurin kan yaron da kafiyarsa na zafafar ruhinsa. Dan haka ya tattara al'amarin AA ɗin ya watsar gefe, dan har gobe yana akan bakansa na har fa sai AA ya buɗi baki da kansa ya roƙa a nema nasa auren Maanal bayan ita kanta yaje ya bata haƙuri da neman gafarata, ya kuma sanar masu dalilinsa na bijirewa a baya..........✍️ Oh-oh tarnaƙi kenan🏃🏃🏃 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖9️⃣3️⃣ ______________ .........Washe gari kamar yanda AA ya faɗa ya bar gidan batare da sanin kowa ba. Yayinda Abah ya samu kira daga baba Sardauna akan batun nemawa Rafeeq aure da sukai jiya a Kaduna. Tare da batun hukuncin da suka yanke akan AA da Najeeb suma. Dan haka a weekend ɗin da za'a shiga za'ai taron family na gaggawa. Duk da zuciyar Abah ta girgiza matuƙa haka ya danne ya amsa da to, yayi kuma ALLAH ya sanya albarka. Baba na yanke kiran ya wani zube a kujera yana ambaton sunan ALLAH. A kuma dai-dai nan Oum ta shigo ta samesa tana hawaye da waya a hannu da alama itama dai ta samu batun kai kuɗin Rafeeq ɗin gidan su Maanal kenan.       “Gadanga ka gani ko, kaga abinda naketa son ka fahimta game da al'amarin nan kaƙi ko. Ni Rafeeq zaima haka ya zagaye yaje yasa a nema masa auren Maanal? Auren Maanal fa, yarinyar da Ajwaad ke matuƙar so.....”     “So?!!”.. Abah ya katseta a fusace yana mata wani irin kallo. Cikin zafin rai ta cigaba da faɗin, “So kike magana Fateema? To wane irin so Ajwaad kema Maanal? Lokaci yayi da zaki daina son kanki da yawa saboda soyayyar ɗanki ta rufe miki idanu. Shin idan Rafeeq baisa an nema masa auren Maanal ba yaya kuke son yay muku? Ki gaya min shi Ajwaad ɗin bai san akwai alaƙa tsakanin Maanal da Rafeeq bane? Tun a farko miyyasa bai ɗauki matakin nuna masa yana sonta ba? Girman kai! Ko tsabar ya rainama mutane wayau ne? Ko kuwa ita Maanal ɗin bata san ciwon kanta bane? To wlhy bari kiji, kodai ku kama kanku ke da ɗanki, kokuma ku haɗu da fushina. Kuma wannan ya zama gargaɗi na ƙarshe da zaki sake zuwa min da wannan zancen. Kuma shima na bashi kwana uku kacal ya sanar da wadda yake so dan cikin weekend za'ai family meeting, idan ba hakaba duk Wadda aka zaɓa masa wlhy, wlhy dole ya aura. Na gaji da case ɗin Ajwaad a gidan nan tunda bai san ciwon kansa ba, shi kaɗai bazai cigaba da bani ciwon kan da ƴan uwansa dake manya basa bani ba. Ke kuma kina biye masa saboda sonsa ya rufe miki ido.”      Ya tashi fuuu ya fice daga falon ma gaba ɗaya. Wasu irin hawaye masu raɗaɗi da zafi ne suka shiga sakkoma Oum da gudu, ga jiri na neman zubar da ita a ƙasa. Babu shiri takai zaune. Hayaniya take jiyowa kamar a gidan, jiki na rawa ta miƙe ko ganin gabanta batayi ma da ƙyau ta fito tana faman haɗa hanya....          “Naga dai ya fito da jakka har ya saka a mota tun bayan dawowarku sallar asuba. Sai kuma ya sake cirewa ya ɗauka yazo ya fita da ƙafa. Amma wlhy ban yi tunanin akwai matsala ba duk da na fahimci ransa a ɓace yake dan ko gaisuwata ma bai amsa ba.”     Wannan furucin kawai Oum ta iya ji daga bakin maigadi sanda ta fito daga haka ta silale a wajen. Sai farkawa tayi ta ganta a gadon asibiti su Fawzan zagaye da ita. Ganin ta buɗe idanu duk sukai kanta, Babban Yaya da Fawzan na gefe da gefenta, a kallo ɗaya zakai musu ka fahimci sunyi kuka, dan idanun ƴan maza duk ya kaɗe. Hannayenta dake cikin nasu ta ƙara damƙewa, sai hawaye sharrr, muryarta na rawa ta ce, “Fadeel Ajwaad, da gaske Ajwaad yabar gida?”.         Kai kawai babban yaya ya duƙar, hawaye na ciko masa idanu dan bai san amsar da zai bata ba. Sai ta juya ga Fawzan, shiko bashi da ƙarfin zuciya irin tasu, sai hawaye sharrr, ƙoƙarin cire hannunsa yay daga cikin nata amma ta sake damƙesa. “Fawzan kuka kake kaima. Kodai na rasa Ajwaad ne, dan ALLAH ku gaya min.” sai kuma ta shiga yunƙurin tashi zaune. Da sauri suka maidata suka kwantar. Abah dake ta ƙoƙarin danne nashi tashin hankalin ya matso kusa da ita sosai ya zauna, cikin muryar lallashi ya ce, “Fateema ki kwantar da hankalinki dan ALLAH. Ajwaad fa ba ƙaramin yaron da kike goyawa bane har yanzu. Karki manta shekara ɗai-ɗai har talatin ne da shi da ɗoriya. Duk ma inda yaje zai dawo....”      Kuka Oum ta sake fashewa da shi tana faman girgiza kai. “Dan ALLAH kada kaimin haka Gadanga, ka dawo min da yarona. Kuma kun san Ajwaad nada lalura kada yaje wani waje ya shiga matsala. Wlhy bazan yafe muku ba bazan kuma yafema kaina ba....”         Kallo ɗaya yay mata ya kauda kansa gefe. Fin minti ɗaya sannan ya sake kallonta, “Nace ki kwantar da hankalinki, in sha ALLAHU a yau zai dawo gida, dan na saka a binciko min duk ma inda yake ko ƙasar nan bai isa bari ba a yanzu dan na saka an dakatar da komai nasa daga aiki, hatta account ɗinsa”.     Wani irin nannauyar ajiyar zuciya Oum ta sauke. Yayinda Mamy da takaici ya cika ta taɓe baki a kaikaice. Ita har mamakin ƙarfin halin Oum nan take a ranta, mtsoww wai su za'aima pretending. A zahiri kuwa itama matsawa tai kusa da gadon Oum ɗin ta fara lallashinta....      __________★         A Kaduna kuwa bayan wucewar baƙi Daddy ya kira Ammie a waya, dai-dai nan itama Nene ta iso. A tare suka nufi sashen Daddy, inda yake tare da ƴaƴan Nene uku. Sosai Ammie tayi mamakin taron, amma sai ta danne suka gaisa. Babu wani ɓoye-ɓoye ko jan zance babban ɗan Nene Yaya Nuhu ya mata bayanin komai. Duk da jin al'amarin kamar daga sama taji sanyi a ranta, har bata san sanda ta saki ajiyar zuciya ba. Sai dai ƙasan ranta wani kalar abu mai nauyi take ji. Godiya ta dingama Daddy saboda fahimtarta da yayi ya janye batun Yazeed cikin sauƙi haka. Gefe kuma tanama Maanal addu'a da fatan ALLAH yasa Rafeeq ya zama sanadin kwaranyewar damuwarta. Yasa kuma iyakar wahalarta kenan. Sun tattauna sosai game da tsaida bikin sati uku kawai da akayi, dan hatta da sadaki sun ajiye abinsu. Dan haka dai babu zama shiri kawai ya kamata a fara...         A waya Daddy ya kira Maanal da Shahidah da Amaal suma. Shi da yaran Nene sukai musu bayani. Da ƙarfi Maanal ta rumtse idanunta, cikin jarumta ta shiga kokawa da zuciyarta, yayinda take ambaton sunayen ALLAH har ta samu nutsuwar da take buƙata. Ta kuma tunatar da kanta hakan shine dai-dai, shine kuma zai bata masalaha da kwanciyar hankali a wannan gaɓar. Batace komai ba dai a gabansu, hakan kuma na nufin nuna alkunya da kowa yay zato. Sai dai hankalin Shahidah da Amaal harma da Ammie na kanta. Koda suka dawo sashen duk motsinta na a idonsu, amma a mamakinsu bata nuna wani reaction ba sam. Saima a mamakinsu yanda ta ɗan warware daga kwanciya ciwon kwana biyun nan da take ciki tayi. Sai duk suka cigaba da mata addu'a a zukatansu, duk da ƙasan ransu na jin tausayinta saboda sanin har yanzu tana son Ajwaad. To amma tunda shi bai nuna yanayi ba har yanzu basu da wani dalilin damuwa da son ganin sai ta aureshi ai...       Washe gari suka shirya suka koma Abuja, suka bar Nene da Ammie da fara tsara shirin biki. Koda suka iso Abuja ma duk motsin Maanal a idon Shahidah ne, sai dai har suka kwanta bataga wani damuwa a tattare da ita ba. Washe gari kuma safiyar litinin, sukai shirin office yara makaranta suka wuce. Shahidahn da kanta ta ajiye Maanal a kamfani, ita kuma ta wuce nata aikin. Yau kam a kallo ɗaya su Zaharadeen suka fahimci Maanal ɗin a Manaal ɗinta take. Dan tun daga gaisuwa ko Yaqub bata sake kulawa ba ta shiga ayyukanta. Lokacin tashi kuma nayi tana a ƴan farko na barin kamfanin. Washe gari ma haka tai musu, bata shiga sabgar kowa da komai, aikinta kawai ke kawota. Ko'a zaman meeting da sukai sau biyu dan kamfani na shirin fitar da agogon data zana ga ƴan kasuwa a dakenta take. Sai kuma a meeting ɗin taji cewar CEO yayi tafiya, dan AS ne yay dukkan zaman a madadinsa. Batabi takan zancen ba balle ta nuna ya dame ta...     ________★       AA dai bai koma gida ba. Suna kuma da tabbacin yana a ƙasar dan an hanashi fita. Amma an kasa gane inda yake. ALLAH sarki Oum duk ta fita a hayyacinta. Ita kanta Mamyn abin fa ya fara damunta. Sai dai tana ƙoƙarin ganin ta danne dan a ganinta AA nayin duk wannan abunne dan ta amince ya auri Maanal. Itako tana akan bakanta ko Oum zata mutu Ajwaad bazai auri yarinyar nan ba sai zaɓinta. Ga batun meeting na family kwanakin na sake matsowa. Nibras ma ta matuƙar tada hankalinta, duk ta rame bata da aiki sai kuka. Yayinda Babban Yaya da Fawzan suka kasa zaune suka kasa tsaye sunata kai kawon binciko inda AA ɗin ya ɓoye kansa batare da sanin Abah ba. Matsalar da aka samu ya rufe duk wayoyinsa ma ta yanda baza'a sameshi ba. Sai a safiyar alhamis babu zato kawai sai gashi ya dawo da kansa. Baki hanci idanu duk maigadi ya saki yana kallonsa, shiko cike da basarwa ya ja box ɗinsa yay ciki, dan taxi ce dama ta ajiyesa. Kai tsaye kuma sashen Oum ya nufa, su kansu masu aikin sashen Oum ɗin daya shigo duk sai da suka shiga shock. Suma bai kulasu ba balle amsa gaisuwarsu, sai tambaya daya jeho musu akan ina Oum. Baki na rawa suka bashi amsa da tana sama dama duk mutanen gidan bata da lafiya.       Saman ya haura zuciyarsa na wani kalar bugawa, ko kallon Saheeba da Nibras dake a falo suna shirya abinci a dining baiyi ba nan ma, kai tsaye bedroom ɗin Oum ya nufa, shigar sautin muryarsa da yay sallama ya sakasu juyowa gaba ɗayansu lokaci guda suna kallonsa. Yayinda shi kuma nashi idon ke akan Oum datai wata zabura har tana ture hannun Babban Yaya dake bata abinci, abincin daya ɗibo a spoon ya zube musu a jiki ita da shi. Hawaye ne suka ciko idannunta dake kallonsa, ta nunashi a hankali lips ɗinta na rawa. “Ajwaad! Da gaske kai ne ka dawo? Ko mafarkin dana saba yi ne Fadeel?”.      Kafin wani ya samu bata amsa AA da nasa idanun suka kaɗe ya shiga takowa a hankali, gefenta ya zauna tare da kwantar da kansa a kafaɗarta, cikin wata irin murya mai rauni sosai ya furta, “Oum ki gafarceni. I miss you, really really miss you”. Sai kawai ya kife kan nasa a kafaɗar tata, tana mai jin damshin hawayensa na sauka mata. Itama sai hawayenta suka shiga sakkowa a guje, tasan a duk duniya abinda zai saka Ajwaad ɗinta hawaye ba ƙaramin abu bane ba. Gefe Mamy ta kauda kanta, zuciyarta na mata wani irin ƙuna, jitai sam bazata iya daurema zaman ɗakin ba, sai kawai ta nufi hanyar fita. Da sauri Nibras da Saheeba da suka biyo bayan AA suka bata hanya ta fice.         Abah kam ajiyar zuciya kawai yake faman saukewa da godema ALLAH. Dan shi kansa kwana biyun dannewa kawai yake yi, amma yana cikin matsananciyar damuwa akan batun AA ɗin da halin da Oum ke ciki. Yana dannewa ne kawai baya nunawa a zahiri. Su kansu su babban Yaya tausayin Autan nasu ne ya sake shigarsu, duk da suna jin haushin abinda ya aikata ɗin. Bayan AA ya ɗago ya share hawayen Oum ya juya yana bama Abah da su Babban Yaya haƙuri suma. Babu wanda ya nuna masa komai dan a ganinsu babu amfanin hakan, tunda har ALLAH ya dawo musu da hankalinshi gidan batare da ankai wani mataki ba ai Alhamdullah. Dan danan sai ga Oum ta ware kamar ba ita ba, taci abincin sosai tasha magani. Shima kuma ta tsareshi yaci abinci dan duk ya faɗa nata a ido.       Sai da komai ya nitsa yaje sashensa har yay wanka sannan Abah ya zauna da su, AA ya sake bada haƙuri tare da neman gafarar su, musamman Mamy data nuna fushin ta a fili, harda tabbatar da cewar wai tana fushin ne saboda halin daya jefa Oum a ciki. Al'amarin Mamy na bama AA mamaki da tayar masa da hankali, shin wace irin zuciya ce da ita? Miyasa ta zaɓi irin wannan rayuwa ga waɗan da suka aminta da ita. Miyyasa shi ta yarda ta nuna masa ainahinta sauran ƴan uwansa kuma taƙe musu lulluɓin biri da mahaifinsu da Oum? Amma ba komai, yayi alƙawarin cigaba da rufa mata asiri, da mata addu'a da nasiha ko hakan zai sa ta gane, dan har abada baya fatan ace Oum da Abah sun gane wacece Mamy, ya tabbatar zuciyar Oum zata iya bugawa.       Nasiha sosai Abah yay musu daga ƙarshe ya ɗakko batun zuwansu Kano da batun kai kuɗin auren Rafeeq gidan su Maanal. A mamakin kowa sai sukaga AA yayi murmushi mai sanyi, babu alamar damuwa a tare da shi ya ce, “ALLAH ya sanya alkairi”.       A firgice Oum data kasa daurewa ta ce, “Ajwaad! Maanal fa akace an kaima kuɗin aure, kuma Rafeeq?”.    Kansa ya jinjina batare da ya yarda ya kalla kowa ba ya ce, “Eh Oum naji, Rafeeq mutumin kirki ne ai, na tabbatar zai riƙe min ƙanwata da mutuntawa, dan haka ina musu fatan alkairi”.       Babu wanda baiyi mutuwar zaune ba a falon. Baki sake Abah da Oum suka kalla juna, hakama Fawzan da Babban yaya kallon AA ɗin kawai suke. Mamy tai ƙasa da kanta tana sakin wani ɓoyayyan murmushin cin nasara, koda suka haɗa ido da AA sai ta lumshe masa ido. Kansa kawai ya maida ya ɗuƙar...........✍️ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖9️⃣4️⃣ ______________ ..........“Nifa wannan yanayin na Ajwaad ya fara bani tsoro babban Yaya. Anya babu abinda ke damun yaron nan? Ko wanda bai san alaƙar baya data shuɗe tsakaninsa da Maanal ba ya kalli idanunsa yasan akwai soyayyar ta a ciki, amma batun aure yaƙi ya amsa. Wannan abu na birkita min tunani”.        Nannauyan huci Babban yaya ya furzar, idanunsa akan Fawzan ya ce, “Bakai kaɗai ba, ni kaina a wannan gaɓar zuciyata ta fara shiga nazari. Fawzan mu dukanmu mun san soyayyar Maanal ce ta hana Ajwaad aure, ka duba kaga jiyyar da yayi, yasha wahala matuƙa, amma ace yanzu haka na faruwa? Wlhy nayi zaton duk randa Ajwaad ya haɗu da Maanal sai yasa an ɗaura musu aure a washe gari koda tsiya-tsiya”.         “Kowama irin wannan hasashen yake yi Babban Yaya. Amma kaga yanda abubuwa ke tafiya.”      “Yanzu yana ina?”.    “Ai sashensa ya nufa”. “Inaga muje mu sameshi”.                 Ajiyar zuciya mai ƙarfi Abah dake bayansu batare da sun sani ba ya sauke. Yayinda zuciyarsa ke faman kai-kawo. Tabbas shima a yau irin tunaninsu yake yi, dan al'amarin Ajwaad ɗin ya fara bashi tsoro, yaro kamar mai aljanu. Yayi zaton a wannan zaman da sukayi yanzu zai amsa abinda suke buƙata ne koda jin abinda ke shirin faruwa. Shin mike faruwa ne? Mike damun yaronsa?. Da wannan tunanin ya juya ya koma sashen Oum.           A hankali Saheeba ta fito daga maɓoyarta itama. Ta riƙe ƙugunta da duka hannayenta biyu tana hararar sashen Oum, sai kuma kamar wadda aka tsikara zaram ta zabura hanyar sashen AA. Dan ya kamata tasan mi su baban Yaya zasu tattauna da shi anan ɗin ma....    ______★        A bazata sallamar su Babban Yaya ta shiga kunnen AA dake bedroom ɗinsa. Sai da ya ɗan rumtse idanu kafin ya miƙe cike da ƙarfin hali daga kwancen da yake a cikin sofa dake a bedroom ɗin. Tissue ɗin daya zubar a saman lallausan carpet ɗin gaban kujerar fari tas yasa hannu ya tattare. Toilet ya nufa da su ya zuba a dusbin ɗin can, dan baya buƙatar kowa ya gani daga abinda ke jikinsu. Bayan ya wanke hannunsa da fuskarsa ya fito daga bayin, ruwa ya ɗauka yasha sannan ya daidaita yanayinsa ya fita. A bakin ƙofa suke tsaye har yanzu, sai kawai ya basu hanya suka shiga. Saman sofa ɗin ya koma ya zauna, su kuma suka zauna a bakin gadonsa duk idanunsu a kansa.      Fuska ya ɗan yamutsa, tare da shagwaɓe ta cike da son danne komai ya ce, “Wai lafiya kuke kallona?”.        Babu wasa sam a fuskar Fawzan ya ce, “Ajwaad mike damunka ne?”.      “Kamar ya? Yaya Fawzan”.   Harararsa Fawzan ɗin yayi, kafin Babban Yaya ya amshe da faɗin, “Ajwaad ka tsaya da pretending ɗin nan naka haka nan. Munzo nan ne domin tambayarka. Kuma gaskiya muke buƙatar ji. Shin akwai wani ne dake maka barazana akan lamarinka da Maanal shiyyasa ka kasa amsar aurenta duk da soyayyar da kake mata”.        Wani irin girgiza zuciyar AA tayi, amma da yake namijin duniya ne sai ya danne. Idanunsa a cikin na Babban Yaya ya ce, “Barazana kuma Babban yaya? Ni kuma wani zaima barazana kamar ƙaramin yaro. Kawai dai ku kun kasa fahimtata ne tun farko. Yarinyar nan ina mata kallo ne tamkar ɗaya daga cikinmu. Ina mata soyayya ne irin ta ƴar uwa ƙanwa ciki ɗaya, shin miyasa ku kuke fassara hakan da wani abu daban.....”      “Ƙarya kake Ajwaad, wlhy son Maanal kake soyayya irin ta aure, soyayya irin wadda baka taɓa yima wata ba a duniyar nan idan aka cire iyayenmu. Soyayya kake mata irin wadda zaka iya rasa rayuwarka ma idan babu ita a ciki. Kalleka Ajwaad, kalla yanda ka zabge a kwanakin nan.  Sannan a kwankin baya na bayyanar Maanal sosai hankalinka ya kwanta, farin cikinka ya dawo. Idan kuma ba haka bane ka rantse baka sonta, mu kuma mun maka alƙawarin barin ka, ko kuma ka fidda matar aure mana!!”.           Cikin matuƙar pretending AA ya miƙe yanama Fawzan da yay maganar fusataccen kallo. “Anƙi a rantse ɗin, shin Yaya Fawzan kai ubana ne da dole saika titsiyeni na amshi abinda kake so, kai kaje ka aurenta mana ko an hanaka ne. Nifa bana son takura!!”.     A fusace shima Fawzan ɗin ya miƙe, yaje gaban AA ya tsaya yana kallonsa cikin ido. A matuƙar kausashe ya ce, “Hummm Ajwaad kenan, ka godema ALLAH zuciyata a matsayin ƙanwa kuma masoyayyar ƙanina take kallon Maanal, amma wlhy da sai na baka mamaki a wannan gaɓar, da sai naje na auri yarinyar nan naga yanda zakai. Kuma ko a yanzu, da ace wani abu bai taɓa shiga tsakanin kai da ita ba na ƙaddara wlhy da sai na aureta ɗin, sakarai kawai mai mugun hali”.      Ya hankaɗesa ya wuce fuuu. Wani irin masifar rawa jikin AA yake yi, gaba ɗaya fuskarsa ta gama birkicewa. Cikin ɓacin rai ya kalla Babban Yaya da kamar al'ajabi ya sashi suma shi kam. Fawzan mutum ne mai matuƙar haƙuri, nuna fushinsa akan Ajwaad yau ɗin nan ya girgiza babban Yaya. Sannan abubuwan Ajwaad ɗin sun sake birkita masa tunani. Kamar AA ɗin zaiyi magana sai kuma ya fasa. Fuuu ya zagaye Babban yaya ya wuce bathroom ɗinsa. Yanda ya wani bugo ƙofar da masifar ƙarfi ya dawo da babban Yaya hayyacinsa. Ya jima yana kallon ƙofar bayin kafin ya fita jiki a sanyaye, dan shifa zuwa yanzu ya fara wani kuma tunani daban....       AA kam yana bugo ƙofar a jikinta ya manne, ya wani kalar runtse idanunsa da suka gama juyewa. A saman lips ya furta, “Kayi haƙuri Yaya Fawzan kayi haƙuri kaji”. Zuuu wani damshi ya gangaro daga hancinsa, yasan minene, dan haka bai damu da buɗe ido ya kalla ba, haka abin ya cigaba da zirara masa akan gashin gemunsa har zuwa ƙirjinsa sai da yaji jiri na neman kada shi a wajen kafin yaja ƙafa da ƙyar zuwa ƙarƙashin shower ya sakar ma kansa ruwa. Ya jima a haka kafin ya fito da ƙyar, a haka jikinsa na zubar ruwa da sumar kansa ya faɗa saman gado yaja bargo ya ƙudundune. Dan wani irin sanyi yake ji da zazzaɓi da ciwon kai.       ★Tuni Saheeba ta kaima Mamy rahotan abinda ke faruwa tsakanin Fawzan da AA. Dan haka hankalinta ya ɗan so tashi, Fawzan nada haƙuri sosai a cikin yaran, amma idan yay fushi koya ƙwafama abu sai fa yasan asalinsa da tushensa. Bata buƙatar kowa ya fahimci wacece ita a tsakanin shi da Fadeel a yanzu sai anyi auren Ajwaad, dan agaɓar take son fara shirinta na dawowarsu hannunta. Dan haka ta miƙe, bedroom ta nufa ta ɗauka waya tai kiran layin AA, sai da tana gab da tsinkewa ya ɗaga, duk da yanda taji muryarsa ya motsa zuciyarta amma sai ta dake. Maganganu masu zafin gaske da dogon gargaɗi taja masa akan ƴan uwan nasa guda biyu, batare da jiran cewarsa ba ta yanke wayar.      A karo na farko al'amarin Mamy ya saka AA sakin murmushi mai ciwo. Kowa da tashi jarabawar a rayuwa, su kuma mahaifiyarsu ce tasu jarabawar. ALLAH ya basu ikon cinyewa. Musamman ma shi da ya daɗe da sanin wacece ita a duniyarsu. Bawan ALLAH haka yasha fama cikin zazzaɓi har dare, koda Oum ta kira shi a waya sai yace mata barci yake. Data bukaci yazo yaci abinci yace a kawo masa kawai sashensa zai ɗan yi wani aiki ne. Bata kawo komai a ranta ba duk da itama dai halin da take ciki na tunani da neman mafita akan al'amarinsa da Maanal yasa bata so yazo ya ganta a yanda take. Gefe ga gargaɗin Abah na tada mata hankali. Amma babu yanda zatayi... *_JUMA'A_*          Ranar juma'a jirgin ƙarfe goma suka bi zuwa Kano. Kowa ka gani a cikinsu sam babu walwala a tare da shi. Sai ma AA ɗin ne ke ɗan nuna dakiya. Sai dai a kallo guda zaka fahimci yanda yay wata irin zabgewa ta rama a tsaye. Sai manyan idanunsa da suka sake fitowa fatarsa ta sake haske ga gashin fuskarsa ya fara taruwa fiye da yanda yake barinsa dan yaƙi yay gyaran fuska. Shi kaɗai yasan irin dogon gargaɗin da yasha akan Mamy a safiyar yau da daren jiya. Shi yanzu al'amarin mahaifiyar tasu yama daina bashi mamaki ko tsoro. Abinda kawai bata sani ba ko bata cigaba da takurashi da gargaɗin ba a shirye yake ya mata biyayya koda kuwa hakan ne zai zama ƙarshen rayuwarsa. Dan shi ya sani a wannan gaɓar babu kuma abinda ya rage masa a wannan rayuwar sai jiran mutuwar.      A gefe kuma Oum sai dama-dama take da shi. Tun daga jiya zuwa yau sai faman lallashinsa da lallaɓashi take akan batunsa da Maanal ya sanar mata ko akwai wani abu da basu san da shi ba ne. Baya son tada mata da hankali, dan haka murmushi kawai yake mata yace ta kwantar da hankalinta ALLAH na tare da kowa. Duk da bata fahimci abinda yake nufi ba ita dai lallaɓashi take yi akan in sunzo koda an tambayesa ya faɗi yana da wadda yake so. Dan ita bata ɗauki wani batun kai kuɗin Rafeeq gidan su Maanal ɗin da muhimmancin da zai hana komai ba. Kawai gargaɗin Abah ne ma ya hanata kiran Rafeeq ɗin ta masa tas, dan yaja mata dogon gargaɗi akan hakan. Shi kuma Rafeeq ɗin kamar yasan abinda ta shirya masa yaƙi komawa Abujan. Ko waya yaƙi kiranta ma.       Mahmud da Hassan ne sukaje ɗaukarsu a airport. Koda suka iso gidan Baba Sardauna sun samesa cike da dukkan ahalinsu. Dan kamar ma su kaɗaine basu kai ga isowar ba sai Gwaggo Khadi data taho daga Yola. Dan sai da sukai kamar awa ɗaya ma sannan itama ta iso da tata tawagar. Itama dai bayan Mahmud data mallakama Baba Sardauna a wancan lokacin tana da yara biyar a yanzu. Uku maza, biyu mata. Mazan biyu sunyi aure. Hamza da Lamiɗo. Sai Nuwaira da Raihana. Sune ƴammata da take damuwa da rashin yin aurensu. Sai autanta Abdullahi, shi kam da sauransa. Koda yake koshi ɗin yanzu akama auren zama zai yi da matar sumul.       Tuni an kacame da hirar zuminci a ƙaton falon gidan Baba Sardauna da dama an tanadesa domin irin wannan haɗuwar. Ƴaƴa da iyaye anata zabga hira cike da farin ciki. Akwai irin AA marasa yawan magana a cikinsu, amma idan akai irin wannan haɗuwar kakanji bakin kowa ya buɗe. Hatta shi AA ɗin yakan ɗan saki jiki kaɗan. Sai dai yau tunda aka gama gaisawa yama zame jikinsa yabar falon. Sai da Oum ta farga baya nan ta fara jajensa. Sai Modibbo ke sanar mata ai yana waje yana waya, jin haka yasa ta cigaba da hirarta, duk da rabin hankalinta na kansa, wani kuma tsagi nakan rashin ganin Rafeeq. Wasa-wasa AA bai dawo falon ba sai da za'a fara meeting. A lokacin ne kuma Rafeeq shima ya iso tare da Abbu, dama shima bai kai ga isowaba. Alhaji ƙarami da Mah-mah ne kawai sai Rufaidah. Bayan addu'a ga wanda suka rasa da kuma su da suke raye aka fara abinda ya tara kowa. Nasiha ce mai ratsa jiki Baba Sardauna ya fara sannan ya tafi kai tsaye kan abinda yasa su tara wanan taro na gaggawa. Ba komai bane face auren da suke son ƙullawa. Maganar Rafeeq itace farko, Baba yay bayanin sun riga sun kai kuɗi kuma an amsa nan da sati uku biki, dan haka zasu haɗe da sauran suma ayi a huta kawai. Amma an bama AA da Najeeb da su Nuwaira dama idan suna da wanda suke so su faɗa. Da Najeeb aka fara kasancewar uba a wajen su AA ɗin. Kansa a ƙasa yace shi baida wacce yake so, amma su ƙara bashi lokaci zai kawo. Baba Sardauna yace Sam bashi yiwuwa, babu wata dama da zasu ƙara basu, ya zaɓa a cikin ƴaƴan dangi gasu nan. Rasa abin cewa Najeeb da ransa ya gama ɓaci yayi, sai kawai yace shike nan ya basu dama kowacce suka zaɓa masa. Albarka aka shiga saka masa. Kafin aka koma kan AA. Sarai yana kallon irin kallon da Oum ke masa, hakama Mamy, hakama Yaya Fawzan da Babban Yaya. Abah ne kawai baya hangowa da ƙyau. Amma duk sai ya ture komai cike da dakiya yace shima ya basu dama duk wadda sukaga ta dace su bashi. Da ƙarfi Oum ta runtse idannunta, yayinda Fawzan kema AA wani irin kallon takaici da jin haushi. Mamy kuwa murmushi ta saki tare da sauke ajiyar zuciya a cikinta. Dan tasan dai zaɓinta data ba su Baba Sardauna zasu bashi. An koma kan su Nuwaira sukace suma sun bada zaɓi.      Sai dai me, bayan an sakama AA albarka shima buɗar bakin Baba Sardauna sai cewa yay, “To Alhamdullahi, munyi farin ciki da wannan biyya taku. Dan haka bama sai anje da nisa ba. Mun yanke shawarar haɗa auren ku ku huɗun lokaci guda, zakuma muyi amfani da ranar Rafeeq da aka tsaida dan ayi a wuce wajen. Tunda ku dukanku ba muhallin zama kuka rasa ba. Babu kuma wanda bai da abinyin da idan yau akace za'ayi nasan zaku shiga ku fito. Balle ma bama buƙatar komai daga kowanneku, ku shirya tarbar matayenku kawai. Magana ta ƙarshe akwai zaman da mukai shekaru uku da suka wuce a wannan falon game da Ajwaad na auren yarinya da aka bashi wadda ta fito daga ke ɓangarenki Kamila”. Da sauri Mamy ta kalla baba Sardauna ranta fal farin ciki amma tana ɓoyewa. Cigaba yay da faɗin, “To ban manta ba, dan haka zamu tuntuɓi iyayen nata in sha ALLAHU. Sai yarinya daga Kaduna da ƙanin mahaifinyarta da kansa ya kirani itama yazo da batunta akan tarayyar su da Ajwaad ɗin dai suka kuma bamu damar zuwa tsaida magana itama in har ya shirya zamuje ayi magana tunda shi da alama da mata biyu zai fara, ya nuna mana duk ya fimu gwarzantaka har mu dake iyayen naku”. Yanda yay maganar da ƴar raha ya saka wasu yin dariya. Yayinda mamaki ya gama lulluɓe wasu, Ajwaad ne wai da auren mata biyu lokaci ɗaya, duk wannan jin kan nashi tab ɗin. Oum kam suman zaune tayi, burinta su haɗa ido da AA amma yaƙi yarda. Haka Abah da su Babban Yaya ma. Ran Mamy kam fes. Haka dai akai addu'a taro ya tashi.........✍️ _Humm wlhy kuna bani dariya da yanda kuka matsu da al'amarin Mamy dama sauran mutanen da mukema kallon ƙalubale a wannan labarin. Shin wai mun taɓa ganin rayuwar da babu ƙalubale a cikinta ne?. Ni da ku mu koma cikin rayuwarmu mu kalla mana, itafa rayuwa gaba ɗayanta ma jarabawace, mukance ai rayuwa rayuwace, rayuwar novel kuma rayuwar novel ce kana karantawa ne dan nishaɗi da farin ciki. Eh hakane kam banyi musu ba, amma mu sani mutane da yawa na ɗaukar darasi da fahimtar tasu rayuwar a dai wannan rayuwar novels ɗin da mukema kallon nishaɗi da labarin hikayoyi kawai. Da ace labarin akan soyayyar su AA da Maanal ce kawai, ƙalubalen rabuwar ma bazai shigo ba, Sai kawai suyi rayuwar ƙurciyarsu suyi aure shike nan miya rage. To koma ita kanta soyayyar ai duk daɗinta ƙalubalen cikinta yafi yawa koda a zahirin ne. To amma ni akwai saƙon da nake son isarwa a labarin gaba ɗayansa. Idan kukai haƙuri za'akai fiye ma da inda kuke tunani. Ka aikata alkairi ma yaka ƙare balle akasinsa a wannan rayuwar. Dole ne mu yarda akwai farin ciki, akwai kuka a rayuwa. Duk yanda muke tunanin mu masu gaggawane duk gaggawarmu muna tafiya ne bisa zartarwar hukuncin UBANGIJI. Dan haka dan ALLAH ku barni na isar da sakon da nake son isarwa dan masu buƙatar hakan su amfana. Ni da nake wahalar rubutun da hana kaina barci da wasu muhimman abubuwan rayuwa nafi ku ƙagauta naga nakai gacci, dan banƙi na runtse ido naga na kammala ba. Fatan alkairi a gareku baki ɗaya🙏_ _Maanal kuma sai Uncle RK ko Abuja babu kowa ehe🤪🏃🏃🏃_ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖9️⃣5️⃣ ______________ .........Zaman wannan meeting na Kano ya matuƙar saka Mamy a farin ciki. Yayinda Oum da Babban Yaya ke cikin damuwa da zaman neman mafita. Abah da Yaya Fawzan kuwa sun mugun ƙullatar AA. Shiko tunda suka dawo Abuja yay bala'in maida kansa busy. Sam baya zaman gida, yakan fita da safe sosai, sai ya kai goma kuma bai koma gidan ba. Sam yaƙi bada wani space da Oum zatai zaman yin magana da shi balle su Babban Yaya. A kamfani ma ya toshe duk wata hanya da zata haɗa shi da Maanal. Itama kuma a nata ɓangaren haka ne. Duk hanyar da zata haɗata da AA ta toshe ta. A wannan halin aka shiga shirin bikin ƙaddamar da agogonsu. Taro na farko kuma kenan da kamfani zai yi Maanal na nan. Ita da RK normal ne, dan tuni shima ya dawo Abujan, amma ya ɗauke ƙafarsa da zuwa gidan su AA gaba ɗaya. Hasali ma tunda ya dawo babu wanda zaice ya ganshi a cikinsu. Ga Abah ya kafama Oum takunkumi akan cewa RK ɗin komai. Dan shi yana bayansa ɗari bisa ɗari.        A haka aka shiga satin bikin kamfani, wanda ke nuni da daura sati biyu kacal gagarumin bikin auren da familyn Darma ke shirin yi na ƴaƴa biyar cif. Ana cikin wannan shirye-shirye Ammie tazo Abuja tare da Daddy. Zai ɗan yi wani aiki na kwana biyu anan tace zata biyoshi dan ta ɗan huta da hayaniyar gidan su, daga nan su ɗanyi shawara da Shahidah. Sai dare Shahidah da Manaal suka je gaishesu dan da rana suna wajen aiki. Sai kawai Maanal ta maƙale anan zata kwana wajen Ammie. Dan haka su Shahidah suka wuce suka barta. Washe gari Daddy ya cema Ammie ta shirya ya kaita ta gaida Oum gaskiya. Dan bai kamata ta shigo Abuja ta fita bataje ba tunda komai ya wuce. Tayi farin ciki da hakan sosai kuwa. Bayan sallar juma'a Maanal ta taso aiki sai kawai suka tafi tunda ita ta san gidan.        Sanye take cikin Abaya fara tas da tai mata ƙyau sosai. Sai ɗan kwalliyar golden kaɗan a jikinta. Kasancewar zuwan na surprise ne sun matuƙar saka Oum a farin ciki. Nan fa ta shiga kai-kawon musu hidima. Sunfi mintuna goma da zuwa sai ga Yaya Fawzan da Babban Yaya da su Naufal sun dawo massallaci. Suma sunyi farin cikin ganin su Ammie ɗin. Cike da girmamawa suka shiga gaida Ammie, dan shi Daddy yana ajiyesu ya wuce akan sai an jima in ya dawo ɗaukarsu ya zai shigo. Gaishesu Maanal tayi itama. Fawzan ya tasata da tsokanar daya saba mata Babban ya na tare mata. Ita dai yau murmushi kawai take ta kasa maida masa. Suna cikin haka AA ya shigo shima. Yana sanye cikin mayan kaya da suka masa ƙyau. Sai dai a kallo ɗaya zaka fahimci irin ramar da yayi, ga ƙasumbar daya tara sosai yanzu baya gyarawa. Yana yin sallama idonsa akan Maanal ɗin ya fara sauka. Ɗan turus yayi kamar yanda itama tayi duru-duru, sai kuma ya janye idanun nasa cike da basarwa ya ƙarasa shigowa. Itama natan ta janye tana mai danne komai. Oum dake kallonsu ta cije lips, hakama Yaya Fawzan sai da ya taɓe baki. Ammie kam kallonsa take fuska ƙawace da murmushi. A mamakin kowa sai sukaga shima ya saki murmushin, tare da cigaba da takowa a hankali cikin nutsuwarsa ya nufi kujerar da Ammien take Oum a gefenta. Saman carpet ɗin ya zauna a gaban Ammie gab, sam ya kasa haɗa idanunsa da Ammien, wani irin kunyarta mai girma da bai taɓa ji ba a shekarun baya yake ji a yanzu duk da kuwa ko randa suka haɗu a Kaduna ma yaji hakan, amma sai yaji na yau yafi na waccan ranar girma kodan daga su sau su ne oho. Sai da ƙyar ya iya dai-daita nutsuwarsa ya shiga gaisheta. Kasare Oum da su Babban sukai suna kallonsu...         Gaisheta ya farayi cike da nutsuwa da girmamawa. Murmushi mai sanyi Ammie ta saki, cikin danne komai cike da kulawa ta amsa tare da faɗin, “Ikon ALLAH Ajwaad baka da lafiya ne? Irin wannan zabgewa haka lokaci ɗaya?”.       Idanunsa ya ɗan lumshe tare da sakin murmushi mai sanyi. Yanzun ma kansa a ƙasa ya bata amsa da, “Lafiya Lau nake Ammie. Kai kawo ne kawai na yau da kullum kin san muna shirin fitar da project ɗin mu da Maanal tai aikin sa”.         “To, to ALLAH sarki ai ban sani ba. Kasan ƴar uwar taka ta koya miskilanci yanzu ko labari bata bani ba. ALLAH ya sanya albarka yasa a fitar a sa'a”.     Da Amin duk suka amsa, yayinda AA ya ɗago ya ɗan kalla Maanal. Suna haɗa ido ta hararesa da taɓe baki ta ɗauke kanta. Karan farko ya saki wani ɗan murmushi shima ya ɗauke nasa idon, sai suka sake haɗa ido da Fawzan alamar yana kallonsu shima kenan. Harararsa shima AA ɗin yayi. Fawzan yay dariya yana ɗauke kansa da faɗin, “Gulma ajali”. A fili. Dan haka kowa ya kallesa. Ganin duk sun watso masa idanu sai ya nuna AA, ya ce, “Dafa wancan yaron nake”.      Sake harararsa AA yayi, Ammie dake murmushi ta ce, “Fawzan har yanzu dai baka canja ba ashe”.           Dariya yayi shima, ya ce, “Kai Ammie ALLAH na canja sosai, ɗanki ne dai yana nan da baƙin halinsa.” ya ɗan kashema AA ido.      “A'a Fawzan Ajwaad mutumin kirki ne. Shi dai ba mai yawan magana bane kawai”.    Murmushi sosai AA yayi saboda jin furucin Ammie, matar da yakema kallon uwa bayan iyaye biyu daya mallaka a duniya. Wato Oum da Mamy. Hakama Oum da Babban Yaya duk murmushi sukayi. Babban Yaya ya kalla Fawzan tare da faɗin, “Kasan shi Auta ɗan gatan iyayensa ne, basa taɓa yarda da laifinsa in dai Ammie ce da Oum”.     Dariya Ammie tayi da faɗin, “Kaima harda kai Fadeel. Shike nan munji ɗin”.      Haka sukaita hirarsu cikin nishaɗi gwannin sha'awa. Yayinda Maanal ta ƙirƙirarma kanta barcin ƙarya, aiko Oum tace ta tashi taje ɗaki ta kwanta. Babu yanda ta iya ta miƙe, duk da koba komai ta gujema idanun AA ai....     Bayan sallar la'asar Oum ta tafi raka Ammie sashin Mamy, a ranta tana mamakin rashin shigowar Mamy ɗin su gaisa da Ammien. Dan Saheeba da Nibras sun shigo. To ko basu faɗama Mamy ɗin bane?. Tunanin hakan yasata kauda zancen a ranta suka fice. Sun bar Maanal tana salla, itama bayan ta idar sai ta fito da nufin bin bayansu kamar yanda Ammie tace mata.. Harga ALLAH ita ba sanin sashin Mamy ɗin tayi ba tunda wancan karon da duka zo bata ma gidan. Dan haka ta fara canki canka a tsakanin sassan gidan.        “Mi kike nema?”.    Muryarsa mai sanyi ta faɗa a bayanta. Da sauri ta juyo dai-dai da shigewar ƙamshin turarensa cikin hancinta. Yitai kamar ta daburce, ta dai samu ta saita kanta, idannunta ta janye daga kallonsa tare da furta, “Sashen Mamy”.        Sashen Mamy ɗin ya ɗan kalla. Sai kuma ya janye idanun nasa ya sake maidosu a kanta. Yatsunta da taketa faman matse gefen veil ɗin abayarta ya zubama idanu kafin ya kauda yana ɗan cizar gefen lips ɗinsa.    “Idan babu damuwa ina son muyi magana”.          “Magana? Tami kuma?”. Ta faɗa a sanyaye. Idanunsa dake ƙyalli kamar ruwa na taruwa a cikinsu ya janye daga kanta. Shima cikin sanyin ya ce, “Plesse”.      “Okay ina jinka”. “Ba'a nan ba”. Ya bata amsa yana barin wajen. Bayansa tabi, sai da suka ɗan zagaya can baya ya buɗe wata ƙofa sai ta gansu a wani kyakkyawan waje, ga ƙaton swimming pool da kujerun gefen ruwa. Daga can gefe furanni ne da ƙamshinsu ya sake ni'imta wajen matuƙa. Baka jin komai a wajen sai kukan tsuntsaye masu ƙyau farare tas daketa kai-kawo. Matuƙa wajen ya ƙayatar da ita, sai faman kalle-kalle take. Wajen zama ya nuna mata a wasu rukunin fararen kujeru bayan yaja kujera ɗaya baya. Sai da ta zauna sannan shima ya zauna. Tsawon sakanni baiyi magana ba itama kanta a ƙasa, kafin a hankali ya furzar da iska ya ɗan gyara zamansa.       “Maanal!”. Ya kirayi sunanta abinda bai cika yi ba. Sai ko da taji tsigar jikinta ta tashi, amma sai ta dake ta amsa masa da, “Na'am” batare data ɗago ba.           “Kin tabbatar kina son Rafeeq?”.     Harga ALLAH sai da hanjin cikinta suka yamutsa, kanta yay mata wani irin nauyi amma dai ta dake ta jinjina masa kanta. Sai da ya lumshe idanunsa ya sake buɗesu a kanta. Yayinda maƙoshinsa keta faman kai-kawo a cikin wuyansa, sun jima shiru yana kokawa da kansa kafin yay murmushi irin na takaici mai sauti, ya ce, “Shike nan Alhamdullahi. ALLAH ya baku zaman lafiya da zuri'a masu albarka. Ki riƙe min shi amana. Rafeeq mutumin kirki ne, yanda kikaga halayen Oum shima haka yake, yana da sauƙin kai da daɗin zama. In har kika zama mai biyayya a gareshi zaki ci ribar zama da shi matuƙa. Kema na sanki da ƙyawawan halaye tuni, dan ALLAH kada ki canja, ki zama mai yin koyi da Ammie azaman haƙuri da miji. Ina miki waɗan nan nasihihin ne kasancewata yayanki, zakuma ta iya yiwuwa shine zama na ƙarshe da zan yi da ke. Dan zanyi tafiya mai nisa ne....”         Yanzu kam Maanal ta kasa riƙe hawayenta, shaaaaa haka suke zubowa suna sauka. Muryarta na rawa ta ce, “Ina zakaje?”.    Murmushi ya yi kaɗan, yana mai kauda idanunsa da suka gama kaɗewa jazur a kanta. “Zanje wani wajene mai nisa”. Ya sake faɗa a dunƙule. Batare da ya jira amsarta ba ya cigaba da faɗin, “Akwai saƙo zan bama Rafeeq zai baki daga baya, abu na ƙarshe zan damƙa amanar MAWAAD a hannunki.....”       A firgice ta ɗago tana kallonsa jikinta na tsuma ga hawaye. Harshenta har harɗewa yake wajen ambaton, “Mawaad? Kana nufin kamfani? Saboda mi?”.          Kansa ya jinjina batare daya kalleta ba. Sai kuma ya miƙe dan yakai maƙurar da bazai iya cigaba ma da mata bayanin ba, sannan baya son taga abinda ke ƙoƙarin fito masa ta hanci. Sai da ya juya mata baya yasa handkacheff ɗinsa da sauri ya tare hancinsa. Tsawon sakan biyu ya goge tsaf sannan ya juyo. Ganin kallon da take masa ya sashi sakin murmushi. “Duk kin maida kanki raguwa yanzu. Komai kuka. Shike nan na fasa yin bayanin zan ajiye miki komai a rubuce. Ina fatan dai kin gama shiryama bikin nan na gobe? Dan kin san kece tauraruwar taron”.      Hannu tasa ta share hawayenta, batare data masa magana ba ta miƙe zata bar wajen. Sai da tai taku biyu sannan ta ce, “Ni bazan zo ba”.     Da sauri yasha gabanta. Cike da kwantar da murya ya ce, “Ashe baki so nima naje kenan Besty?”.     Da matuƙar mamaki take kallon, hawaye na cika mata ido. Ya jinjina mata kansa. “Tabbas idan baki je ba nima bazanje ba”.        Wani kalar kuka ta sakar masa, sai kuma ta zagayesa da gudu ta fice a wajen gaba ɗaya. Idanunsa kawai ya lumshe ya cigaba da tsaiwa a wajen, kafin ya kai hanky ɗinsa saman hanci jin abun zai zubo.....        Banɗakin Oum Maanal ta shige tasha kukanta, gudun kada suzo su kamata ta fito ta hau gadon Oum tayi kamar mai barci. Sai ALLAH ma ya taimaketa suka jima a sashen Mamy ɗin. Dan sun tarar itama wai kanta ke ciwo ne shiyyasa bata zo sun gaisa da Ammie ba. Koda suka dawo ganinta tana barci data tashi lokacin baisa sun zargi komai ba, sai suka ɗauka barci da tayi ne.        Sai bayan sallar isha'i Daddy yazo. Nan fa suka haɗu da Abah da su Babban Yaya. AA dai baima fito ba, koda Daddy yayi jajensa sukace maybe baya gidan ne. Zuwa goma suka tafi gida suka bar Oum da kewa. Taso Maanal ta kwana anan amma taƙi, wai zataje tayi shirin taron gobe. Haka dole Oum ta barta tunda tasan taron nada muhimmanci ga Maanal ɗin kasancewar aikinta ne zai fita....      WASHE GARI.   Yau ɗin ta kasance asabar. Tako wane ɓangare masu alaƙa da Mawaad Company sun tashi da shirin babban taron ƙaddamarwa na project ɗin da aka ɗauki tsawon watanni sanyinsa. Anan cikin Companyn za'ayi taron. Yako sha gyara ɗan gaske. Ko'ina ka kalla sai ka ƙara kallo dan ƙyau. Masu himma har sun fara isowa. Irin wannan taron yakan kasance an gayyaci manyan ƴan kasuwa na ɓangarorin duniya da Mawaad ke mu'amular kasuwanci da su. Tare da na cikin ƙasa Nigeria. Sai ma'aikatan companyn da ƴan jarida. Wasu a manyan ƙasar musamman daya kasance a wannan gaɓar AA nada muƙamin gwamnati na shugaban matasa na ƙasa gaba ɗaya da shugaban ƙasa ya bashi shekara ɗaya da wasu watanni kenan. Kafin tara waje ya gama haɗuwa, dan taron za'a fara shi ne goma a tashi ƙarfe ɗaya batare da an takurama mutane ba.         A ɓangaren Maanal sai da Ammie da Shahidah sukai mata jan ido sannan ta shirya. Tayi matuƙar ƙyau kuwa kamar ka saceta ka gudu. Suna ƙoƙarin tafiya sai ga Rafeeq babu zato. Zuwan nashi yasa tsarin tafiyar ya canja. Ammie da Shahidah da mijinta da Daddy suka tafi tare. Maanal kuma tabi RK. Lokacin da suka iso wajen taron ya gama cika, dan har su Oum sun iso suma tare da uban gayya AA Darma.      Su Ammie an basu wajen zama na musamman, yayinda Maanal ta wuce inda aka tanada dominta da sauran ma'aikatansu. RK ma tare da su Oum ya zauna. Sai wani dama-dama Mamy keyi da shi, ta yanda Oum tama gagara ko yimasa kallon banza balle zazzage masa abinda ke ta faman cimata zuciya..........✍️ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖9️⃣6️⃣ ______________ 96 ........An fara gabatar da addu'oi sannan. Daga haka shugaba *_CEO Ajwaad Aliyu Abubakar Darma_* ya gabatar da bayanin sannu da zuwa ga dukkan wanda suka halarci zaman. Tare da jinjinar ban girma ga ma'aikatansa jajirtattu. Ya ɗan sauke idanunsa akan Maanal da tunda suka iso taƙi yarda su haɗa ido, janyewa yay a hankali ya sake maidawa ga mutane ya cigaba da jawabinsa. Bayan ya kammala sauran manyan ma'aikata sukayi nasu daki-daki. Kafin ya fitar da hoton ƙayataccen agogon a cikin ƙaton magijin dake a bango guda na ɗakin taron. Babu wanda bai ambaci woow da Masha ALLAH ba. Dan gaskiya agogon ya matuƙar fita da fitarsa. Kai da ka gani kasan bana ƙananun yara bane, agogo ne na masu ƙumbar susa da sarakuna. Karo na farko aka buƙaci ganin Maanal. Ta jima kafin ta miƙe, dan jitai kamar ta fasa ihu. Amma haka ta daure ta fito cike da dakiya. Fitowar tata ya saka idanu da yawa kasancewa a kanta, ita dai ta dake ta hana kanta kallon kowa harta ƙarasa in da ake buƙatar ta. Bayan sallama da gaisuwar girmamawa ta gyara tsaiwa. A karo na farko idanunta suka sauka akan RK. Murtantanin murmushin da yake mata ta mayar masa tare da janye idanun ta. Sai kuma karaf a kan na AA daya zuba mata idonu shima. Da sauri ta janye tana sake bama kanta nutsuwar dole kafin ta fara bayani mai cike da ƙayatarwa. Tasha tafi sosai, dan jawabanta sun matuƙar ƙayatarwa musamman yanda ta tsara su akan matasa da iyaye da manyan ƙasa masu mulki akan su tallafi matasa da aikin yi. Bayan jawabanta mutane da yawa sun cigaba da jawabai masu ma'ana da muhimmanci kafin a bama HALIFA SK ƊORAYI dama zuwa ya ɗan bada nishaɗi da waƙarsa mai sanyi mai taken BAZANA DAINA KUKA BA wanda shi uban gayyar ma bai san da tsarin yin hakan a wajen ba. Tunda baitin waƙar ya fara fita wajen yay wani irin tsitt, dan cike suke cike da wani irin amo mai kassara karsashi da kuzarin masoya musamman masu rauni a zuciya. Dan shi kansa AA da ba damuwa yay da jin waƙoƙin ba samun kansa yay da tsitstsinkewar jini, dan ji yake tamkar shi yake rairata. Tuni da ga shi har Maanal sun wani kalar zubama juna idanu cike da rauni da karaya gushewar tunani tare da hauhawar jinin jiki.. A bazata hawaye suka cika idanun AA, haka itama Maanal jitai kuka na taho mata, dole ta duƙar da kanta kawai waƙar na cigaba da ratsata har ya kaita ƙarshe. Tafi sosai hall ɗin ya ɗauka, manyan mutane suka fara fadar kyaututtukan da suka bashi a take a wajen. Aiko bakin Halifa ya kasa rufuwa😂 (A gayama HALIFA SK ƊORAYI Nima na bashi ƙyautar mota😂🥱 dan waƙar nan fa tayi😋😋😋🥰🥰😀).        Bayan an dawo daga break an fara bada Award na girmamawa ga waɗanda suka taimaka wannan agogo ya fito, an fara daki-daki ga duk wanda sukai hidar aikinsa har kan mai gayya mai aiki data zana wato *_Maanal Habib Giro_*. Mabanbanta mutane suka bama sauran ma'aikatan award ɗinsu, amma ita mai gayya da aiki ne zai bata da hannunsa wato AA Darma.      A hankali ta miƙe kamar ɗazun cike da nutsuwa ta tako har inda yake tsaye, yayinda shi kuma ya zuba mata kallon ƙasan ido. Sai taji duk tsigar jikinta na tashi, yayinda shima yake jin kamar bazai iya daurewa da sadaukarwarsa ba. A haka dai ya daure da ƙyar ya bata shiryayyen award ɗin da yay matuƙar ƙyau da tsaruwa dan nata yama banbanta dana sauran. An bata mic tayi godiya da jinjina ga Mawaad Company gaba ɗaya, tare da ƙara ɗorawa da wasu jawaban masu muhimmanci. Lokacin data koma wajen zamanta sai ta samu kanta da kai handky ɗinta ta share hawayen da suka cika mata ido, dan har cikin jininta waƙar ɗazun ta kekketa mata zuciyarta har yanzu, gani take kamar AA ɗin na isar da wani saƙone a gare ta kai tsaye. Shi kansa uban gayyar tunda ya bata award ɗin nan har aka tashi bai sake tashi daga inda yake zaune ba..... __________★          Alhamdullah shirye-shirye biki nata kankama. Dan ta kowane ɓangare shirin akeyi ɗan gaske. Musamman ɓangaren Darma Family masu gayya da aiki. Hakama gasu Shahidah babu zama. Itama Maanal ta ƙara dakewa ta tattara dukan hankalinta akan RK. Yanzu kam kullum ma shike kaita office yaje ya ɗakkota. Sam bata haɗuwa da AA, Dan rabonta da shi tun ranar taron kamfani. Alhamdullah a litinin data rage saura kwana goma sha uku bikin aurensu aka bata office nata na kanta matsayin Assistant ta Director Steven. Wannan muƙami ya zafi su Zaharadeen, dan a ganinsu duka yaushe ma tazo companyn. Duk da kuwa aikin da tayi a bayyane yake, dan agogon da aka ƙaddamar ya dawowa kamfani da ninkin kuɗin da aka fitar da shi fin sau ashirin a kwana ɗaya na jiya kacal. Wannan al'amari ne da bai taɓa faruwa da kamfani ba. Wasu kuwa na ganin Maanal ɗin tama cancanci fiye da hakan ai, duk da ba'ita kaɗai tayi aikin ba, hasalima ita nata zane ne kawai. Amma dai ta taka rawar gani ai. Dan da batai zanen da ƙyau ba suma masu ƙerawar da basu yi yanda ya kamata ba. To ita dai bata cema kowa komai ba, iyakaci wanda ya tayata murna tayi godiya. ALLAH sarki Yaqub da kansa ya taimaka mata ta kwashe tarkacenta zuwa sabon office ɗinta. Dan zuwa gobe ma zata fara aiki a ciki.        Aiko hakan ce ta faru, washe gari Maanal a sabon Office ɗinta ta zauna. A kuma ranar ne batun bikinta da RK ya fasu a kamfanin, tare da auren boss ɗin su da duk shima za'ai rana ɗaya. Kowa dai ya sake fahimtar kusancin Maanal da boss tunda dai RK ɗan uwansa ne na jini kowa yasan wannan. Sai ko ƙananun magana ta tashi akan shiyyasa akai saurin bata matsayi kenan. Sarai zantukan na dawo mata amma tai kunnen uwar shegu. Washe gari laraba ma ta ɗauki hutu, sai kuma bayan biki zata dawo bakin aiki. Alhamdullah duk da ɗan munafunce-munaguncen dake kai kawo haka suka taru sukai mata fatan alkairi, tare da tabbatar da zuwansu duk da shagalin ya zama biyu gana boss a gefe. To ita dai ta musu godiya da tabbatar musu tana saka idon zuwansu....         A ranar suka wuce Kaduna. Dama Shahidah nata masifa akan gyaran jikin da akema Manaal ɗin kullum yana bin iska ne saboda galauniyar da take na zuwa aiki kullum. Suna kuwa isowa Kaduna Nene ta tisa ƙeyarta zuwa gidanta. Wani irin gyaran jiki mai ban mamaki Nene ta fara mata ɗan gaske. Tunda ta shiga kuryar ɗakin Nene ko falo an haramta mata fita, hakama wayarta an kwace gyara kawai take sha ciki da waje, ita kanta abin har tsoro yake bata. Abubuwan da ake danna mata tana sha kuwa har kamar zasu sanyata amai take ji. Shiyyasa data faki ido sai ta zubar. Ga wani irin mahaukacin ƙamshi da ko yaya ta motsa sai kaji waje ya buɗe. Fatarta yayi wani irin ƙyau na tashin hankali. Sau ɗaya Nene ke bata damar yin waya da RK a rana. Shima na minti goma kawai. Duk wani abu ta bashi damar yaje su tattauna da su Aneesa, ga Najma, ga Amrah duk da ma ita Hajiya Yaya ta hanata sakewa...     _______★       Tunda fa su Hajiya Yaya suka tabbatar bikin za'ai da gaske sai kuma sabuwar hassada ta tashi. Kullum cikin habaice-habaicen suke da gugar zana. Hajiya Yayan ta saka Yazeed ɗaukar amarya Nazeefa akan dole sun tafi honeymoon. Ammie kuwa ta tattarasu ta bama banza ajiyar su. Hakama ɓangaren su Hajiya Basariyya shirin biki ake na garari da kece raini. Rashin zuwan ango sam ba damuwarsu bace. A cewarsu adai ɗaura koma minene zasuyi maganinsa ne. Itama danginta sun cika gida tab, dan wannan ne karo na farko da zata aurar.        Ranar talata aka kawo lefen Huznah, lefen da su Hajiya Basariyya aka dinga iyayi da gwalangwaso da shi har ana sakarma su Ammie habaici. Laraba akai kamu, amma na iya Huznah. Dan ita Maanal tace bata buƙata. Sai kawai akai mata feshin turare normal dai na mutanen da shike nan. Tako ci kuka a ɓoye, gashi dama dannewa kawai take yi, amma ƙirjinta gaba ɗaya a kwanakin nan jin gim yake da nauyi na tsiya. Amma tanata daurewa dan bata son kowa ya fahimci halin da take ciki har ƴan uwanta da Ammie......       ________★   A ɓangaren su Oum gasu nan ne dai, kowa ka gani babu wani karsashi ko ɗokin auren a tare da shi. An dai kwashe gaba ɗaya kayan sashen AA ana masa gyara duk da kuwa komai fes yake babu wani damuwa. Bayan an canja komai anyi sabon fenti suma sauran sassan gidan an ɗanyi gyaran. A ɓangaren Mamy kuwa cike take da farin ciki mara misaltawa duk da ita Nuratu sai wani satin za'a ɗaura nata auren kamar yanda aka tsara. Amma tun yanzu cikin shirinsu suke suma tunda za'a kawo suruka ɗaya Huznah. Tsaff Mamy ta gama shirya yanda zata tarwatsa Oum. Duk da a yanzu ma damuwar da take kallon Oum ɗin a ciki wani kalar nishaɗi da farin ciki yake sakata. Amma tanata ƙoƙarin dannewa yanda ta saba.       Ranar Laraba suka tarkata suka wuce Kano suma. Dan za'aje can a haɗe bukukuwan ne gaba ɗaya. Idan taro ya tashi lafiya sai su taho da tasu amaryar. Amma na wani satin anan Abuja za'ai komai basai sun je Kano ba, shiyyasa Mamy tafi shiryama bikin Nuratun fiye dana Huznah. Kwanaki fin biyar kenan babu wanda a cikinsu zaice yaga AA da idonsa, sai ta waya shina Oum ce ke naci kiransa. Dan yayi tafiya zuwa Lagos ta kwanaki biyar ɗin. A Kano ma zasu haɗu da shi bazai dawo tanan Abuja ba. Sunyi tunanin zuwa su sameshi a can ɗin kuwa. Amma sai suka samu bai iso ba. Suna isa da yamma ƴan kawo lefen Maanal Kaduna suka wuce. Ta mota aka tafi da kaya, su kuma suka bi jirgi bayan sallar la'asar. Dan haka Oum suna sauka ko zaman hutu batai ba ta bisu su dan tana son ganawa da Ammie. Sai Nibras data maƙale domin zuwa taci uban Huznah a cewarta. Sai uwar gulma Saheeba, tunda basuga lefen ba sanda aka taho da shi basu isa Kano ba yasa ta biyo mutane dan ganarma idonta ko lefen RK ɗin dai-dai yake da wanda suka kai na Huznah. Itama Mamyn taso zuwa Mah-mah ta janye hankalinta da wani abun acan...        To lefen dai Maanal ya iso cikin garin Kaduna, gidan Alhaji Usman Chalawa. Gida fa cike da ƴan gulma musamman ta fannin Hajiya Yaya da Hajiya Basariyyar ma tunda danginta duk suna cike fal a gidan ranar suke mothers event ɗinsu. Itako Ammie komai tace bazatayi ba sai yinin biki a wuce da amarya ɗakinta. Lokacin da aka faka dalla-dallan motoci ƴan gaske har guda biyu, ɗaya kuɗinta ya tasarma naira miliyan 90 matsayin gift wa amarya Maanal, hakama ta biyu zata iya kaiwa miliyan ashirin da biyar, ai gaba ɗaya gidan sai da ya gigice. Dan motar 90m ɗin sabuwace dal a ledarta da ba'ako kware ba, itama kuma ɗayar haka. Gashi an ƙawatasu da ribbon. Hakama akwatina jerarru na kece raini da ƴar gata kawai ake kaiwa tuni sun cike waje set-set. Ai sai kaji bakin kowa ya mutu musamman lokacin da aka sanar da cewar motar 90m fa gift ne daga Yayan Amarya AA Darma. Ɗayar itace ta kayan lefe daga ango.      (😩😩ALLAH matan novel sunji daɗi, ƙyautar motar 90mil fa, ni mai rubutawa ina nan sagadede da baki banda ko keke😭😭, dan ALLAH azo a haɗa ƙarfi da ƙarfe a saya min mota mutanena😥😥🥺)         Babbar bala'i kenan inji Hajiya Basariyya jin wai ƙyautar motar 90mil daga AA Darma wanda zai auri ƴarta. Amma ita ƴar tata kota miliyan biyu ba'a sakko mata ba dan ita babu mota. Hajiya Yaya da su kam ba ƙaramin girgiza zukatansu sukayi ba. Ita kanta Saheeba sai da zuciyarta tayi masifar girgiza. Jikinta har rawa yake ta turama Mamy text massage. Nibras ma dai sumar zaune tayi. AA ɗinta ne da ƙyautar irin wannan ƙatuwar mota haka. Oum kuwa wani irin sanyi ne ya shiga ratsa mata zuciya. A take ta kira Abah ta sanar masa dan babu wanda yasan AA zai yi wannan ƙyauta. Su kansu masu kawo lefen a hanya suka haɗu da motar. Sai da sukazo cikin Kaduna suka fahimci cikin tawagar su take saboda ganin Modibbo ne ya tuƙo ta. Bayan Oum ta yanke waya da Abah AA ta kira, sai dai ya sanar mata yana airport ne zai baro Lagos, idan ya sauka zai kirata...          Ammie ta matuƙar shiga ruɗani ita kanta da wannan ƙyauta ta AA, sai ma taji ta rasa abin faɗa dan mamaki.  Ga wannan uban lefe na girgiza hazo kamar za'a buɗe wani ƙaramin kanti. Kasancewar guri ya ƙure yamma tayi su Oum basu wani jima ba suka wuce. Duk da akwai tattaunawa sosai da Oum da Ammie ke son yi babu isasshen lokaci. Haka suka rabu akan zasu ƙarasa a waya tunda dama dai sunatayin na kullum tunda aka fara kaikawon bikin nan.......       Har su Oum suka koma Kano babu AA babu labarinsa. Dangi sai tambayarsa akeyi dan sauran anguna sunata kai-kawo amma shi babu shi babu alamarsa. Zuwa bayan isha'i dai Oum ta kasa haƙuri ta nemo su babban Yaya a waya. Shine ya tabbatar mata suma mamakin rashin isowar tashi suke. Dan ranar mazan family ɗin suke partyn su, ga shi har za'a fara shi babu shi babu alamarsa. Kuma ya ce musu zai baro Lagos suma tun ɗazun...........✍️       Jama'a kar dai Yayan su o'e ya gudu ne😲☹️.     Ashema matsoraci ne, da Uncle RK ɗinmu ne babu inda zai je😌🤣🏃🏃🏃. 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖9️⃣7️⃣ ______________ .......Sai ƙarfe kusan goma AA ya iso gidan baba Sardauna. Dan anan gaba ɗaya ake shagalin bikin. Hankalin Oum yayi mummunan tashi da ganin yanda AA yay masifar zabgewa a tsaye. Duk mai hankali yay masa kallo ɗaya yasan baida isashiyar lafiya sam. Jiki na rawa Oum ta kama hannunsa suka shige bedroom ɗinta, Dan suna a tsohon sashensu ne na gidan baba Sardauna ɗin da suka zauna a can shekarun baya.     Muryarta har rawa take wajen tambayarsa, “Ajwaad baka da lafiya ne?”.         Hannunta ya kama fuskarsa ɗauke da murmushi mai sanyi ya zaunar da ita a kusa da shi. Kafin ta kwantar da kansa a kafaɗarta. Idanunsa a lumshe hannunsa cikin nata ya ce, “Oum ki kwantar da hankalinki lafiyar Autan ki ƙalau. Zirga-zirga ce kawai taimin yawa a kwanakin nan. Tunda naje Lagos ban zauna na huta ba saboda kayan nan namu da gaske ɓata suka so yi. Amma Alhamdullah ALLAH ya kiyaye haka dan yanzu haka har sun sauka Abuja suma. Yaya hidimar bikin?”.        Hawaye ne suka zubo a fuskar Oum. Tasa hannu ta share, kafin tace, “To Alhamdullahi ALLAH ya kiyaye gaba. Amma Ajwaad har yanzu kana akan bakanka naƙin amsa kana son Maanal daren yau fa kawai ne da mu”.          A hankali ya tashi daga kan kafaɗarta, fuskarsa da wani ƙayataccen murmushi ya ce, “Oum maimaita zancen nan bashi da wani alfanu. Bara naje na ɗan watsa ruwa na kwanta na huta a gajiye nake matuƙa”.       Kai kawai ta jinjina tana ƙoƙarin haɗiye ƙwallar data cika mata ido. Har ya kai kofa zai fita ta katseshi da faɗin, “Munga mota tayi ƙyau ALLAH ya saka da alkairi yabar zuminci”.        Guntun murmushi ya ɗan saki kawai, kafin a saman laɓɓansa ya furta, “Amin”. Ya fice. Ta ƙofar baya ya fita, dan sam baya son haɗuwa da Mamy. Kai tsaye daga nan masauki ya nufa, inda duk samarin family dama masu auren kan zauna in har ana biki. A hannun Uncle Mahmud ya amshi key ɗin nasa ɗakin, dan shine da alhakin hakan dama. Shi kansa Uncle Mahmud ɗin ya tsaresa da tambayar baida lafiya ne. Amma yace masa shi ƙalau yake, yayi busy ne kwana biyu akan wasu injinansa da suka nema ɓacewa a bakin ruwa Lagos shiyyasa kawai. Badan Uncle Mahmud ya yarda ba ya ƙyalesa kawai. Shima yana samu ya shige ɗaki ya kulle kansa. Duk wanda yazo ya buga sai yace su barsa barci yake son yi ya gaji ne. Dole kowa ya ƙyalesa tunda dare yayi.       Dole sai a washe gari kowa ya iya ganinsa a ɓangaren mazan dai. Aiko suka tasashi gaba akan sai yaje an masa gyaran fuska dan ya tara uwar ƙasumba yaƙi yay gyaranta. Da farko ƙi yay, sai da Uncle Mahmud ya sashi gaba. Dan adai cikin iyayensu maza daga Abah sai Uncle Mahmud ɗin (ina fatan baku manta da ɗan gwaggo Khadijah da itama ta baiwa Baba Sardauna ba bayan Abah da Oum. To shine Uncle Mahmud).      An masa gyaran fuska mai ƙyau yana kumbure-kumbure yana jin haushi. Sai kuma gashi yayi ƙyau sosai duk da ramar da yayi ta sake bayyana kanta. Gaba ɗaya an haɗe ɗaure-ɗauren auren anan Kano ne. Dan shima Daddy tuni shi da tawagarsa sun kama hanyar Kano. Anyi haka ne domin sama ma mutane sauƙin, tunda shima dai Daddyn asalinsa bakanon ne. Danginsa duk a can suke, daga can suke zuwa Kadunar duk wani biki...       Tunda sha biyu tayi kowa yake ƙarasa shirinsa a gaggauce, musamman anguna da bakunansu suka kasa rufuwa. Sai dai banda AA da tunda suka dawo daga aski shi da Uncle Mahmud da Babban Yaya ya shige ɗaki ya kulle kansa. Ba'a farga da rashin fitowarsa ba sai da suka ɗauki hanyar tafiya massallaci. Babban Yaya ne ya ɗaga waya ya kira shi, tare da tambayarsa yana ina? Sai cewa yay gashi nan zai biyo bayansu wani abokinsa ne ya tsayar da shi. Babban Yaya bai kawo komai a ransa ba dan AA yay masifar saita kansa kafin ya ɗaga wayar. Wayar na yankewa ya kasheta gaba ɗaya yana mai kai hannu ya shafo jinin dake ziraro masa ta hanci. Murmushi ya saki tare da saurin dafe bango jin jiri na neman zubar da shi. Tun yana bin bango domin kai kansa cikin toilet harya gaza, dole ya zube a ƙofar bayin saboda wani irin nauyi da ƙirjinsa yay masa, idanunsa suka fara juyewa duhu ya fara mamaye ganinsa. Duk wani motsi ya fara nisa da kunnuwansa. Kafin cikar abinda bai wuce minti biyu ba ya nema kansa ya rasa, sai damshin ɗumin jinin dake fita masa ta hanci kawai yake iya ji a fatar jikinsa kafin a hankali komai ya koma masa ɗiffff....         _________★    A massallaci su Babban Yaya suka haɗe da Abah, koda Abah yace ina AA sukace yana nan tahowa, wani abokinsa daya iso ne ya tsaida shi. Kamar Abahn zai yi magana sai mutane suka ɗauke masa hankali. Ga shirin fara sallar juma'a anayi, dan har an fara khuɗuba. Daga can itama dai Oum hankalinta na akan AA ɗin, dan tun safe da sukai waya bata sake jinsa ba. Garama Babban Yaya dake sanar mata sun tasashi gaba sun kaisa aski shi da Uncle Mahmud har taita dariya. Duk yanda take ƙoƙarin samunsa a waya hakan ya gagara, ga mutane sai ɗaukar hankalinta suke yi, dole ya tattara wayar ta ajiye ma ta maida hankalinta garesu...       Bayan idar da sallar juma'a aka fara gabatar da ɗaure-ɗauren aure. An fara ɗaura auren Uncle Najeeb Umar Ishaq Darma da amaryarsa Raihana Kabeer Yola. Sai na Rafeeq Kasheem Kura da amaryarsa Nuwaira Kabeer Yola. A rikice Babban Yaya da Fawzan har ma da Abah suke kallon RK da su Baba Sardauna. Amma duk sai sukai murmushi kawai, Abbu ya sake bada sadaki ga Daddy matsayin na AA. Ana jira aji an ambaci sunan Huznah sai akace ga sadakin Ajwaad Aliyu Abubakar Darma, ga Maanal Habib Giro. Babu wata damuwa ko gargada ga Daddy ya amsa fuskarsa da murmushi aka ƙulla auren. Ɗaurin auren ƙarshe shine na Sageer Ahmad Isa Chalawa, da amaryarsa Huznah Usman Isa Chalawa...      Kan babbar buta, ai a rikice Abah yace, “Alhaji Usman nifa ban gane ba. Baba kun sakani a ruɗani, yaya duka aurarrakin suka canja kansu?”.       Murmushi Baba Sardauna da Baban Yola da Daddy da Abbu duk sukayi, hakama RK hankalinsa kwance sai ma murmushi yake saboda kallon da Babban Yaya da Fawzan suka zuba masa. Baba ne ya bama Abah amsa da, “Dama can a haka suke. Kai ne dai kake kallonsu ba'a haka ba. Kowa an bashi matarsa ne”. Daga haka ya juya aka ƙarasa addu'oi ga ma'auratan da fatan alkairi da zaman lafiya na har abada.      Ai sai hawaye suka shiga zuboma Yaya Fawzan. Kasa hakuri yay a take ya ɗaga waya yay kiran Oum shima kuma babban Yaya Oum ɗin yake nema. Sai ALLAH ya bama Fawzan sa'a tashi ta fara shiga. Tana ɗagawa ko sallama baiyi mata ba cikin muryar kuka ya ce, “Oum ALLAH ya mallakawa Autanki Maanal. Maanal ta zama mallakin Ajwaad Oum an ɗaura Oum an ɗaura.....” sai hawaye. Gaba ɗaya daburcewa Oum tayi, ai bama tasan tayi wani kalar tafiya jagwab ta zube a kujera wayar hannunta ta suɓuce. Hannayenta gaba ɗaya a saman fuskar ta ta fashe da kuka da ambaton sunayen ALLAH a bayyane, tare da miƙa godiya da kirari ma UBANGIJI mai hukunci bisa hukuntawarsa da rahamarsa...      Kafin kace mi mutane sun zagayeta ana tambayar lafiya-lafiya. Ta kasa cewa komai ila amfaton UBANGIJI. A haka ƴan ɗaurin aure suka fara dawowa gida. A take zancen ɗaurin aure da yanda ya kasance ya fara bayyana a cikin gidan....           Mamy na tsakiyar ƴan uwanta da suka zo wani dake matsayin kamar Yaya a wajenta na kusa kuma, dan da babansa da babansu uwa ɗaya uba ɗaya suke suka shigo domin yimata ALLAH ya sanya alkairi dan zasu wuce, daga Jigawa suka zo shiyyasa. Tanata faman washe baki bata san mike faruwa ba sai da suka gama jerama ma'auratan addu'oi sannan wanda ke kamar yaya a wajen nasu ke faɗin, “Ai ni na shiga ruɗani ma a wajen ɗaurin auren. Kuma naji mutane nata mamaki suma har wasu na tambaya”.         Cike da isa Mamy ta dubesa, dan haka take musu daman saboda akaf dangin nasu itace mai auren mai kuɗi, itace ke raba musu kayan azumi dana salla, duk da ba wani na kirki bane ba hakan bai hana su girmamata ba. Kuma su babban Yaya ne da Abah ke badawa duk shekara amma sai ta sayi ƙananun atamfa da yaduka ta manna musu. Hakama abincin bawani na kirki ba. Fuska a yamutse ta ce, “Wani abu ne ya faru a wajen ɗaurin auren?”.        “Eh to bana ce ba. Akan dai canji da mukaji ne ga ita sunan matar shi Ajwaad da kika sanar mana ne da farko.”       “Kamar ya canji Yaya Lurwanu?”.    Kafin ya bata amsa Saheeba ta iso kamar an jehota tana ƙwala kiran Mamy! Mamy!. Idanu sosai Mamy ta zuba mata, haka suma sauran mutanen dake wajen. Bata jira amsar Mamy ba ta miƙa mata waya tana faɗin, “Abah ne keta kiran wayarki, shine na ɗaga yace na kawo miki”.       Amsa tayi, dai-dai nan kiran ya ƙara shigowa. Sai kawai ta ɗaga takai kunne cike da kissa tai sallama. Cike da fara'a Abah ya ce, “Ina kuka shige haka ke da Fateema sai nemanku nake a waya babu wanda ya ɗaga min, ki sanar mata ina mata albishir da cewar an ɗaura auren Autan ta da da Autarta Maanal....”       Wani irin dimmmm Mamy taji a kunneta kawai, tamkar an ɗaga irin curarren ƙarfen nan an bugama mutum a tsakkiyar kansa babu zato babu tsammani.......      🤣🤪🏃🤐          ________★            Acan massallaci kuwa mutanene cikin ɗunbin mamaki. Musamman ma'aikatan Mawaad Company da mafi yawansu suka halarci wannan aure. Tuni musu ya kaure akan batun. Wasu suce Maanal ta kamfani wasu suce ba ita bace ba. A gefe kuma suma kansu su babban Yaya harma da Abah a rikice suke. Ga mutane, dole suka danne dan daga nan an ɗunguma ne ƙaton hall ɗin da aka shirya walimar cin abinci ga mahalarta wannan ɗaurin aure. Sai dai kuma hankali ya fara komawa akan rashin ganin AA a wajen. Dole aka fara neman layukan wayarsa, amma duk switch off. Hankali tashe Babban Yaya da Uncle Hussain suka koma can gidan dan dubawa. Sunko iso ɗakinsa a garƙame har yanzu. Tun suna bugawa da kiran sunansa har suka fara ƙoƙarin ɓalle ƙofar amma sun kasa. Ga su Abah nata kiransu a waya. Ai kafin kace mi su Aban suma dole sun iso. Nan fa aka taruma ƙofa da ƙyar aka ƙaryata.       Innalillahi wa-inna ilaihiraji'un kowa ya faɗa ganin AA yashe a ƙasa babu alamar rai a tare da shi sai uban jini dayay masa kaca-kaca, ga alamun zubarsa nan ta baki ta hancinsa. Gaba ɗaya babban Yaya ya ɗagosa jikinsa na rawa, hawaye tuni sun gama wanke masa fuska, da wani irin ƙarfi yake girgiza AA yana kiran sunansa, amma ina gaba ɗaya jikinsa ya gama saki. Babu alamar akwai sauran numfashi a tare da shi.        Wani irin baya Abah da jikinsa ke rawa ganin yanda AA ɗin yake yarab yayi, sai da aka taresa dan kaɗan ya hana ya zube ƙasa. Baba Sardauna ne ya samu ƙarfin halin faɗin a ɗaukesa zuwa asibiti. Haka kuwa akayi duk da duk wanda ya kalli AA zaice yama rasu basu fidda rai ba, Uncle Najeeb da Alhaji ƙarami suka kamosa. Daka gansa kaga gawa kawai. A haka suka fita da shi aka saka a mota, suma duk suka shiga aka wuce.....    😭😭😭🥲🥺🤐       ___________★            A Kaduna duka amare biyun sunyi ƙyau, sai dai Maanal kwance take zazzaɓi ya mata rijib, tun su Aneesa na ɗaukar abin wasa har suka fuskanci gaske take dan rawar sanyi ma take yi bana wasa ba. Da sauri Najma ta lulluɓeta da ƙaton duvet. Kafin ta fice tai kiran Amaal. Hankalin Amaal ya tashi, amma ta daure cikin hikima tayi kiran Shahidah dan bata son su ɗagama Ammie dake a tsakiyar mutane hankali. Ganin halin da Maanal ɗin ke ciki ba wasan yara bane ba Shahidah ta bada shawarar su sanarma Nene. Aikuwa haka akayi, da taimakon Nene aka bama Maanal magani, sannan ta zauna ta dinga tofa mata addu'oi. Ga ƙawayen Hajiya Basariyya sun cika gidan da kiɗa na hauka dan sifiku suka warware a harabar gidan saboda duk mazan sun wuce Kano sai mata kawai a gidan.          A dai-dai wannan lokacin kiran Oum ya shigo wayar Ammie. Kasancewar wayar tana a hannun Amaal sai kawai ta ɗaga. Ko sallamarta Oum bata amsa ba tace, “Ƴar uwata”. Muryarta na rawar kuka. Cikin faɗuwar gaba Amaal tace, “Oum ba Ammie bace nice, wayar tata na hannuna ne ai. Amma Oum mike faruwa kamar fa kina kuka?”.        “Dole ne nai kuka Amal dole ne. Yau ALLAH ya tabbatar da Maanal a matsayin matar Ajwaad”.       Suɓucewa wayar ta nema yi, sai da ƙyar Amal ta tarota, da wani irin mamaki ta ce, “Oum! Kina nufin Ajwaad aka aurama Maanal?”.        Ai da wani kalar sauri kowa dake a ɗakin ya juya yana kallon Amal. Manaal dake kwance tana faman rawar sanyi a bargo tai wani irin yakice duvet ɗin itama ta tashi zaram kamar wadda ke amfani da magic sai gata a gaban Amaal. Wayar kawai ta fige jikinta da muryarta na mazari ta ce, “Oum wace Maanal ɗin? Badai ni ba? Dan ALLAH kada kuyimin haka ni Rafeeq nake so, shi na zaɓa, da shi nake son rayuw.......”      Batare data karasa ba kawai ta sulale ƙasa yaraf wayar tai nata waje. Ai da gudu kowa yay kanta ana ƙwala mata kira....    A dai-dai lokacin da Maanal ke sulalewa acan a sume anan sashen su Hajiya Basariyya itama ƙaninta ne ya kirata cike da mamaki yake tambayarta yaya haka, yaji ɗaurin aure ya juye akan Sageer ɗan ƙanin Daddy maimakon AA Darma data sanar musu. Shi kuma AA Darma ɗin sunji an aura masa wata wai ita Maanal Habib Giro.         Gaba ɗaya Hajiya Basariyya ta saki wayar dake a kunnen nata ta faɗo ƙasa ta tarwatse. Ita kuma tai baya sai gata jaɓar a saman gado ta zube...........✍️                     ☹️☹️😥😥🥲🤐 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖9️⃣8️⃣ ______________ .......Isowar labarin halin da AA ke ciki ya saka komai tsayawa cak ta kowanne ɓangare. Cikin ƙanƙanin lokaci mafi rinjayen manyan family ɗin suna a asibitin. Yayinda tuni RK, Abbu, da wasu likitoci suna a kansa anata ƙoƙarin ganin an ceto rayuwarsa.       Sosai Oum ke kuka, kuka mai ban tausayi, dan dole Abah ya dake tashi zuciyar ya kasance da ita. Dama yaranta Babban Yaya da Fawzan suna manne da ita. Abin mamaki a farko Mamy bata asibitin, sai dai ƴan uwanta suka tausheta dan da neman birkicewa tai zata tonama kanta asiri suka janyeta zuwa ɗaki. Sun nuna mata cewar tada hankalinta fa babu abinda zai janyo sai rushewarta a wannan zuri'a, amma idan ta cigaba da dannewa komai ya lafa sai ta ribantu da cikar burinta, saboda tabbas suna zargin akwai abinda ke faruwa tunda har ɗaurin auren yay wannan juyewar, gaba ɗaya kuma laifin sun maidashi ga Oum ne, acewarsu dama itace ta tura RK jikin Maanal ɗin domin hakan ta kasance ita a yaudare ta. To dan haka saita kwantar da hankalinta amarya ta tare a kumayi bikin Nuratu wani satin daga nan sai su san matakin ɗauka. Dan ko zasuyi yawo tsirara suma sai sun bata taimako na kashe wannan aure, acewarsu Nuratu bazatai rayuwa da kishiya ba. Da ƙyar dai suka tausheta ta haƙura suka shirya suka tafi asibiti, sai kuma da suka iso suka tarar da tashin hankali yafi wanda ma suke hasashe. Domin kuwa awanni sai shuɗawa suke babu wani bayani a game da samuwar AA ɗin.       Karo na farko da hankalin Mamy ya fara tashi, zuciyarta ta dinga raya mata kadafa ace rasa Ajwaad zatayi. Kai ina bata fatan haka, dan soyayyar da takema yaron daban take akan ta sauran yaran. Sai dai kuma abinda ya ƙona mata zuciya ganin yanda Abah da Babban Yaya da Fawzan keta dama-dama da Oum. Hakama sauran manyan kowa dai hankalinsa nakan Oum, ita aketa tausa da tunatar da ita tai masa addu'a. Dan ita ko kallonta kowa baiba a matsayin wadda tasha wahalar rainon cikin Ajwaad da naƙudarsa, da gaske dai ta tabbata sun ma manta da cewar itace mahaifiyarsa tarihi ya goge hakan....       Sai da su RK suka kwashe awa ɗai-ɗai har bakwai kafin su fara fitowa. Zuwa lokacin har anyi sallar magrib. Amma sai ƙalilan ne suka samun ƙarfin zuwa yinta. Kusan gaba ɗaya akai ca akansu, ALLAH sarki Abbu ga tsufa. Kaida ka gansu kasan su kansu sun jigata. Dan tuni babbar rigar saman kayansu duk sunyi fatali da su shi da RK. Abbu ne ya sauke ajiyar zuciya bayan yace su sameshi a office. Bayan duk sun zauna a ƙaton haɗaɗɗen Office ɗin nashi cikin nutsuwarsa da Oum suka gado ya ce, “Kowa ya kwantar da hankalinsa tun awa biyu da kasancewar mu da shi aka samesa, bugun zuciyarsa ne yaƙi dai-daita tun ɗazun sai yanzu Alhamdullah. Amma duk da haka yana buƙatar addu'a, yaron nan ya jima a cikin ciwo, zuciyarsa ta kumbura a shirye take da komai ya iya faruwa. Amma Alhmdllh tunda har ankai ga wannan matakin muna fatan iyakar wahalar kenan dan gaskiya ya auna arziƙi. Yanzu za'a canja masa ɗaki domin hutawa, muna saka ran nan da awannin talatin numfashinsa zai dawo a gangar jikinsa in sha ALLAHU”.      Sosai kowa ya dinga sakin ajiyar zuciya da jerama UBANGIJI godiya. Harga ALLAH bayanin Abbu ya daki zuciyar Mamy matuƙa. Bayan kamar mintuna biyar aka fito da AA, babu wanda bai ji sabbin hawaye ba, wato ɗan adam ba'a bakin komai yake ba. Wlhy duk iskancin da muke ji a rayuwa da ciwo ƙalilan idan UBANGIJI ya so nuna ba komai bane mu a cikin sakan sai mun bayyana a ba komai ɗin ba. Cikin ƙanƙanin lokaci AA ya canja, kamar ba ɗan gayu ɗan kwalisar nan shugaban Mawaad Company ba ya arrahaman.....      ________★       A Kaduna kam ai gidan gaba ɗaya ya hargitse, kafin kace mi dangin Hajiya Basariyya sun cika sashen Ammie. Wani irin harmutsi ne na tashin hankali daban mamaki. Dan faɗi kawai suke sai sun daki Ammie. Yayinda Huznah ke ɗauke da kakkaifar wuƙa tana rantsuwa da UBANGIJI sai ta kashe Maanal. Dole aka rufe Ammie da Maanal har ma da su Amaal a ɗaki. Kafin Nene ta kira Daddy ta tabbatar masa fa akwai matsala ya dawo Kaduna. Hankalin Daddy ya tashi matuƙa da jin abinda ke faruwa, dole yay kiran CP na Kaduna yace a tura ƴan sanda gidansa. Wannan fa dabara itace ta kawo sassaucin al'amarin. Dan dole kowa ya nutsu kaf dangin Hajiya Basariyya aka korasu sashenta, saboda Daddy ya bada umarnin hakanne kawai bawai a ɗibesu zuwa station ba, sai idan sunyi gardama be. Sai a wannan gaɓar Huznah ta yanke jiki ta faɗi wai ita ta suma. Nan suka rufu a kanta Hajiya Basariyya na kukan idan har ƴarta ta mutu sai ta ɗaure Ammie. Dan sun tabbatar baƙin asiri taima AA Darma dan ya auri karuwar ɗiyarta ragowar wani...      Oho su Ammie bama su san anai ba. Dan su nasu hankalin na nan akan Maanal da aka samu ta farfaɗo a bisa taimakon likita da sukai gaggawar kira, abokin Yaya Yazeed kenan. Dole akai mata allurar barci mai ƙarfi domin samun nutsuwarta, Alhmdllh cikin ƙanƙanin lokaci barcin kuwa ya bugeta. Da wannan damar suka samu sukai zaman jimanta al'amarin, dan Ammie tayi matuƙar ƙagara Daddy ya iso, yace ya taho, saboda dole ya baro kano, ALLAH ma ya taimakesa ya samu jirgi. Suna isowa Kaduna yake samun kira daga Kanon akan halin da AA ke ciki, sai kuma hankalinsa ya ƙara tashi matuƙa. Dole yana isowa yace su Ammie su fara shirin wucewa Kano ɗin. A ɓangaren Hajiya Basariyya ma yace a shirya Huznah dan yau bazata kwanar masa gida ba a gidan mijinta zata kwana, Kanon kenan. Hajiya Basariyya ta birkice zatai masa hauka Yayanta ya wanke mata fuska da mari dan shi dama baya ɗaukar wargi. Ya kuma rantse mata idan ta sake cewa tak sai ya saka Daddy ya saketa. Wannan fa yasa dole ta nutsu, sai kukan baƙin ciki tana jin zuciyarta kamar itama zata fashe ɗin. Tana ji tana gani wasu dangin Daddy duka shirya Huznah dake kuka na fitar hankali. Tana rantsuwar bata son Sageer AA take so, itama ɗin dai Kawu Sani ɗin ne yay mata jan ido dole tai tsit. An gama shirya amarya Huznah tsaf, ashe abokan ango ana gama ɗaurin aure dama sun ɗakko hanyar Kano domin ɗaukar amaryar su. Zancen dinner ɗin da Hajiya Basariyya ta shirya anan Kaduna tasha ruwa kenan. (Sageer dai ya jima yana son Huznah tun tana ƙarama, sai dai Hajiya Basariyya na taka masa birki ganin ubansa bai kai Daddy arziƙi ba. Shi kuma sai kawai ya janye jikinsa ya barta ya cigaba da dabgarsa. Kwatsam sati uku da suka wuce Daddy ya samesa har kano ya zaunar da shi tare da masa tambayar har yanzu yana son Huznah? Sosai ya daburce a lokacin, dan harga ALLAH yana sonta har yanzu, kawai dai ya kama kansa ne dan ya fahimci uwarta da ita kanta sai a hankali. Da ƙyar ya iya jinjinama Daddy kai, aiko a take yace ya bashi ita, yaje kawai ya hau shiri biki nan da sati uku. Amma yana son yay shiru da bakinsa har sai ranar ɗaurin aure. Mamansa da Babansa ma sun sake kwakkwafarsa akan ya kame bakinsa ko a cikin dangi ba'ason kowa ya sani sai ranar. Amma zasuyi shirin biki normal sunan amarya ne kawai bazai fito ba sai ranar. Sauran ƴan uwa ma zai ce musu Daddy ne yakai kuɗin aure da kansa. Lamarin ɓoyewar ya bama Sageer mamaki, sai dai bai iya ya tambaya ba dan baya iya musu da iyayensa. Sannan yana matuƙar ganin girma da kimar Daddy a rayuwa, bazasu manta da halaccinsa ba, shine ya tsaya tsayin daka akan iliminsu da ginuwar iyayensu da dukiyarsa. Ai ko baya son Huznah akace gata zai amsa da hannu bibbiyu. Balle ma yana son abarsa).         Sai da aka fara wucewa da amarya Huznah da tawagar dangin Hajiya Basariyya da babu yanda suka iya, dan ƴaƴansu Sani yace kowa ya shirya a wuce da shi akai amarya, wanda bazasu je ba anan cikin Kaduna suke su koma gidajensu biki ya tashi anan gidan Daddy ba'a buƙatar ganin kowa. Hakan kuwa dole sukayi, aka bar Hajiya Basariyya na faman kwasar kuka, sai manya da basu wuce biyar ba aka bar mata akan su ƙarasa haɗa kayan Huznah ɗin kafin gobe a bita da su. Kayan ɗaki dai dama kai tsaye can Daddy ya tura aka shirya a gidan Sageer, na Maanal kuma aka kai Abuja gidan su AA, ita kuma Hajiya Basariyya ta saki baki Abuja na Huznah aka kai, dan ko kaɗan Daddyn bai basu wata ƙofa ta fahimtar komai akan auren ba....       A ɓangaren Ammie tana son ƙarin bayani daga Daddyn itama amma babu fuska, dan ya haɗe gabas da yamma yace su shirya kawai, zasuje can Kanon sai a ƙarasa bikin acan ya tanadar da gidan da zasu zauna. Ita mai biyayya ce akoda yaushe a gareshi, dan haka ta fara shiryawa ita da kaf ƴan uwanta. Wanda zasubi mota suka fara yin gaba. Musamman ƙwai da ƙarkwatar iyalan Nene, tunda dama dai sune dangin kawai, sai abokan arziƙi da ake gaisawa daga haka sukai addu'a suka kama gabansu. Wanda kuma zumuncin yay ƙarfi sosai suka shiga tawagar ƴan wucewa a mota.         Ƙarfe biyar Ammie, Shahidah, Amaal, Nene, sai Maanal da aka tada da ƙyar daga barci aka shiryata tana faman layi suka wuce airport dan su jirgi zasu bi, harda shi kansa Daddy ɗin. Wannan abu ya ƙona ran Hajiya Basariyya da sauran danginta. Dan haka suka bata shawara itama ta shirya gobe duk su tafi Kanon gara a ƙarasa komai akan idonta, dan sun fahimci wai Daddy na fifita agolarsa sama da ƴarsa. Haka kuwa akayi, a daren suka fara shirin komai daya dace acewarsu fitar sassafe zasuyi....      Kuce min ina uwargida ran gida Hajiya Yaya. Ai tana sashenta ita da ƴaƴanta da su Aunty Sabuwa na kwasar dariya. Dan su tun farkon faɗan daɗi yay musu. Acewarsu ai Hajiya Basariyyar ce dai-dai da Ammie. Zuwan ƴan sanda a gidan ne ya su nutsuwar dole suka cigaba da gulmar daga ciki. Koda Daddy ya dawo kuma Hajiya Yayar tazo domin bugar cikinsa sai yay mata banza, dan dama haushinta yake ji akan tura Yazeed honeymoon ɗin dole da tayi. Itama ganin yanda yay matan sai tai zuciya wai ya dizgata saboda bata da muhimmanci a garesa. Bai kulata ba taja ƴan matan ƙafafunta ta koma sashenta cikin ƴan uwanta suka sake buɗe babin zagin Ammie da Hajiya Basariyya ɗin ma. Koda za'a wuce da Huznah babu wanda yay niyyar bi a cikinsu, sai kuma Daddy yasa aka tattaro masa kaf ƴaƴan yace su shirya su bi masu tafiya Kanon. Babu yanda suka iya suna tura baki da ƙunƙuni dole sukai shirin tafiyar. Ganin haka sai Aunty Sabuwa ta zuge Hajiya Yaya akan ai ta shirya kawai suma subi ayari dan ayi komai akan idonsu. Dan Jaraba da masifa Hajiya Yaya fa bata jurar doguwar tafiyar mota saboda ƙiba amma haka ta shirya ɗin suka wuce batare da ko sanin Daddy ɗin ba......       __________★      Su dai su Ammie kasancewar tafiya ce ta jirgi sun isa cikin mintuna ne, dama kuma sai biyar na yamma suka wuce. Sunbi taxi ɗin cikin airport zuwa anguwar da Daddy ya tanadar musu gida. Da gani gidane sabo amma komai a kwai a cikinsa. Wannan ba abun mamaki bane dan sana'ar Daddyn kenan sayen gidaje da sayarwa. Maanal dai dana barci take ko'a hanya. Dole suna shiga aka nema mata wajen kwanciya ta kwanta. Su kuma suka fara ƙoƙarin gabatar da sallar magriba. Shima Daddy ta fita massallaci. Bayan an idar da sallar ne ya dawo yace suyi shirin zuwa asibiti, amma da nufin za'a bar Amaal saboda yara da kuma Maanal. Dan masu tahowa a mota ma na gab da shigowa cikin Kano. Wanda suka taho da Huznah ma su har sun iso, dan ita kai tsaye gidan nata mijin aka isa da ita ita da ƴan rakkiyarta...      Su Ammie sun iso asibiti dai-dai gama jawabin Abbu, su Oum na ƙoƙarin shiga massallacin asibitin dake da ɓangaren mata dana maza domin gabatar da salla. Dan asibitin mallaki ne ga Abbu, shine wanda ya fara ginawa bayan dawowarsu Nigeria. Kafin aima RK nashi a Abuja kamar yanda ya buƙata. Suka kuma sake yin reshe a wasu sassan jihohin a yanzu haka domin dai taimakon al'umma...........✍️ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖9️⃣9️⃣ ______________ ........Sosai Oum taji daɗin ganin Ammie, hakama su Babban Yaya dama su Baba Sardauna isowar su Ammien akan lokaci batare da sun fifita shagalin biki ba ya faranta musu rai matuƙa. Sun kuma sake jinjina martabawar Daddy. Ammie dama ƴa ce ga wannan family na Darma, dan duk an santa musamman ma su iyaye da ta ɗauka matsayin iyaye a sanda tana rayuwa tare da Oum. Cikin girmamawa ta dinga gaishesu da yima AA addu'ar fatan samun lafiya. Suma sunta amsawa cike da dattakonsu da mamakin ganin yanda ta canja kamar ba ita ba. Dan shi Baba Sardauna ma kasa haƙuri yayi sai da ya mata ɗan ƙorafi na gudarsu da tayi. Haƙuri kawai ta bada ita dai, dan tasan zaman kace nace da kare kanta kamar raini ne take musu. Hakama Shahidah sai da su Babban suka tsokaneta cikin ƙarfin hali. Itama dai murmushin kawai take saki kanta a ƙasa...        Nene ce ta bama Oum labarin halin da Maanal ke ciki. Dan tunda suka iso taketa faman tambaya. Kowa yay mata addu'ar samun lafiya itama amma banda Mamy da ahalinta. Dan su fa farko ma yi sukai kamar basuga su Ammien ba sai kuma mi suka gani oho musu suka ware dai aka gaisa. Bayan sallar isha'i su Ammien sukai musu sallama da addu'a ga AA tunda ba'a bar kowa ya ganshi ba gaskiya. Suma kuma su Oum ɗin gida ma zasu wuce Fawzan da RK da Uncle Hussain kawai za'a bari. Har mota sukai musu rakkiya, bayan sun wuce suma su Oum ɗin suka wuce...     Su Ammie sun samu ƴan tahowa a mota sun iso. Dama da abincinsu nacan Kaduna duk suka taho, dan haka sai aka samu sauƙi babu wata damuwar abinci ko ruwa balle lemuka. Sai a wannan lokacin Daddy ya samu zama da su Nene da Ammie, dan suma su Yaya Nuhu sun iso, dama suna a Kanon su ai tun daurin aure tunda Daddy ne kawai da Yaya Sani suka wuce ɗazun. Dalla-dalla Daddy yay musu bayani da tabbatar musu dama can tun kawo kuɗin aure da akayi bada sunan RK akai ba, da sunan AA su Abbu suka kai kuɗi Kaduna. Kuma sun tabbatar masa RK ne da kansa ya sakasu yin hakan, amma sun roƙesa akan dan ALLAH kada kowa yasan hakan har sai ran ɗaurin aure. Suka kuma bashi haƙuri akan al'amarin AA da Huznah bamai yiwuwa bane, dan da'a haɗa auren shi AA ɗin ya cutar da ita gara a aura masa Maanal ɗin kawai kamar yanda kowa yasan hankalinsa akanta yake. Dalilin ƙin bijirewarsa ne kawai basu sani ba kuma sun gagara ganowa. Da kuma suka binciki miyyasa shi RK ya haƙura ya sadaukar masa, sai yace musu wataran zai faɗa, yanzu dai shi buƙatarsa duk rintsi AA ya samu auren Maanal ne kawai. Shi kuma ya basu zaɓin koma wacece zai amsa da hannu biyu kuma zai riƙe amana in sha ALLAHU.       Wannan zance shine ya girgiza Daddy, yaji zuciyarsa ta karaya sosai game da son haɗa Yazeed da Maanal daya dage a baya. Bayan wucewarsu kuma washe gari ya zaunar da Yazeed yay masa nasiha sosai sannan ya gaya masa gaskiya akan yabama AA Maanal dan shine yafi cancanta. Abinda ya shiga tsakaninsu a barshi kawai a matsayin ƙaddara da babu makawa sai ta faru su basu isa hanawa ba. Yazeed mai biyayya ne a garesa, dan haka ko jayayya baiyi masa ba. Daga ƙarshe ya bama Ammie da Nene akan ɓoye musu da sukayi tun farko shi da yaran Nenen.           Murmushi kawai Ammie tayi, sai Nene ce keta faman sanya albarka da tabbatarma Daddy cewar baiyi laifin komai ba. Hakan ma da yay shine dai-dai. Dan ɓoye aure alkairi ne kodan gudun maƙiya da mahassada. Yanzu ba gashi anyi komai cikin kwanciyar hankali ba babu wani tsugunne-tsugunne. Amma da ace an bayyana ai ba'asan irin ƙurar da zata tashi ba sam. Hakan kuwa hankalin kowa kwance. Shi kuma Ajwaad ALLAH ya bashi lafiya da ita kanta ma Maanal ɗin. Itama Huznah suka sanya ma nata auren albarka sosai tare da roƙar Daddyn a lallaɓata dan ALLAH harta haƙura. Dan an mata laifi sosai.      Murmushi kawai Daddy yayi. Ya kuma basu labarin yanda ya ƙulla shima auren na Huznah bayan wucewar ƴan Kano da yay nazari. Ya kuma shawarci Yazeed suka yanke hukuncin hakan dan a samu masalaha, itama a taimaketa da zaman gidan tana kara tsofewa.....       WASHE GARI            Zuwa washe gari duka ɓangarorin uku sai muce Alhamdullah. Idan ka cire AA dake kwance a gadon asibiti har yanzu bai farka ba. Amma dai ana saran daidaituwar al'amura da yawa a tare da shi. Maanal ma ta tashi jikinta da sauƙi, sai rashin ƙarfi da rashin walwalar fuska. Dan ko abinci sai da Nene ta zaunar da ita ta bata da kanta a baki cike da kulawa, tana kuma mata nasiha cikin hikima. Zuwa tashin hantsi Daddy da Ammie da manyan gaba ɗaya suka je asibiti suka duba jikin AA, har yanzu dai ba'a bari a shiga inda yake. Dan sun tarar da su Oum duk a waje, suma kuma basu jima da zuwa ba, tare kuma suka baro asibitin da su, saboda manyan family ɗin na Darma sun yanke a cigaba da bikin kawai, dinner ce da aka shirya gaba ɗaya sai walima, sai suka soke dinner ɗin za'ai walima kawai. A jiya ya kamata a kawo amare ayi dinner da daddare da safe ai walima da buɗar kai kowa ya ɗauki matarsa. Da kuma abin ya juye sai ya zam yau za'a kawo amaren ayi walimar zuwa gobe kowa ya kama gabansa.         Wannan yasa shi kansa AA ɗin farkawarsa kawai ake jira dan za'a wuce da shi can KK HOSPITAL na Abuja ne. Idan kuma an samu yanda ake so ma falillahil hamdu..... ________★     A ɓangaren su Hajiya Basariyya kam dole ta sauka a gidan ƴan uwarta, su kuma can dangi suna gidan amarya wasu kuma a gidan iyayen angon musamman dangin su Daddyn, ita kuma dangin Hajiya Basariyya ɗin aka barsu a gidan Huznah amarya da har safiyar yau kuka ya gagara tsaya mata. A hakan ma dan Maman Yaseerah na tsaye a kanta da tabbatar mata ta kwantar da hankalinta auren nan sai sun kashesa ta auri AA ta fidda Maanal. Dan haka ita da wata ƙanwar Hajiya Basariyyan itama hatsabibiyar kanta sune zagaye da Huznah ɗin suna ta ɗorata akan mugayen abubuwa da zata dinga tafkawa mijin dama iyayensa duk da kuwa ƙanin ubantane uban nasa uwa ɗaya uba ɗaya. Itako tsaf take ɗauke komai harma tana ƙara nata a cikin zuciya. Oho sudai dangin Daddy ko'a kwalar rigarsu, shahalin bikinsu sukeyi cike da farin ciki, Hajiya Yaya kuwa ta shige cikinsu tayi kane-kane danta ƙona ran Hajiya Basariyya, dan su basu san su Ammie suma suna nan Kanon ba sam, tunda sai da suka taho sannan Daddy ya taho da su Ammie, kuma sunji ance ango babu lafiya a tunaninsu ai biki ya tsaya tunda anata kai waketa kaya, shiyyasa taga gwara ta maida hankali tayi maganin Hajiya Basariyyar kafin ta koma kan Ammie, duk da ma dai case ɗinta da Ammien yanzu kaɗanne ALLAH ya raba ɗanta da ƙarfen kafa, sai dai hassadar wanda yarinyar ta samu a matsayin miji ne ya kasa wuce musu a ƙahon zuciya daga ita har ƙanwarta Sabuwa...        Duk abinda Hajiya yayan keyi yana komawa kunnen Hajiya Basariyya, tayi niyyar shiryawa kuma itama ta koma can cikin dangin mijin nasu da ƙyar ƴan uwanta suka dinga tausarta akan tabar komai a gama bikin lafiya idan suka koma gida ayita. Amma yanzu kam ta shanye kodan su san ta yanda zasu raba wannan aure na Huznah..... ________★         Hajiya Mamy kam duk mai hankali yay mata kallo ɗaya zai san a harmutse take, sai dai da yake za'a iya danganta yanayin nata da halin da AA ke a ciki kai tsaye, tunda an san duk kawaicin da zata nuna dole hankalinta ya tashi. Amma a ɓangaren Hajiya Majdiya wata kalmar data fita daga bakin Mamy karaf ta shige a kunnenta batare da su sun farga da ita ba, sai dai kafin Mamy ta cigaba da surutunta yan uwanta na tausarta Maman Saheeba ta lura da Hajiya Majdiya ɗin, shine tai saurin ƙwaɓar Mamy da fargar da sauran kasancewar Hajiya Majdiya ɗin a wajen ta hanyar ambaton sunanta. Ita dai Hajiya Majdiya ta fita tana juya kalmar Mamy ɗin da tace, _“Nifa bana jin zan iya cigaba da wannan kauda kan, gara ayita kawai ta ƙare tunda basu da wuta basu da aljanna”._        Hajiya Majdiya ta wuni da waɗan nan kalamai na Mamy, sai kuma abinda ya faru a Kaduna na hararar da Mamy tai ma Ammie ya shiga dawo mata. Ta auna da yanda Rafeeq ya tsara kasancewar auren batare da ko su kansa dake ƴan uwansa ciki ɗaya sun san manufarsa ba. Kai hatta Mah-mah bata san da wannan shirin ba. Daga shi sai baba Sardauna sai Abbu da Alhaji ƙarami da Baban Yola. Kai itafa magana ta ALLAH zuciyarta ta fara mata rawa akan Mamy. Daga ƙarshe ta kasa haƙuri tai kiran RK a waya tace tana son magana da shi, dan ita irin mutanen nan ne mara iya riƙe abu a rai yayta damunsu, tafi son sha yanzu magani yanzu dan ma karta shiga haƙƙin mutum.      Babu wani jimawa kuwa RK ɗin yazo tunda dama suna a kusa da gidan ne. Gefe suka koma yana tsokanarta da faɗin, “Aunty wai ko kuɗin zaki ƙara min ne, dan dama a talauce nake wlhy babu daɗi ango ya kasance babu kuɗi a jikinsa”.       Dariya tayi da faɗin, “Kai dai son kuɗinka yayi yawa Rafeeq. Sai kace kayi wata tsiya a bikin ne kuda akaima auren gata. Ni yanzu ma da zaka saka min ƴar miliyan biyu zan so hakan ina son shiga kasuwa kafin na bar kanon”.         “Ni da ke ba'a san wanda yafi wani son kuɗi ba ai, ina ma laifin kice dubu ɗari biyar”.     “Ko ita na samu ɗin na gode”. “To wannan kam zaki samu ɗin”. “Aiko na gode ALLAH ya saka da alkairi angon Nuwaira”.          Murmushi yayi da ɗan taɓe baki, itama sai ta murmusa ɗin kawai. Sai kuma ta kallesa da ƙyau. “Wai nikan Rafeeq na tambayeka mana”.      “Ina jinki Aunty miya faru?”.    “Ya akai al'amarin aurarrakin nan ya canja haka wai, tun jiya kowa abu ke cinsa a rai halin da Ajwaad ke ciki ya danne komai.”          “Kai aunty dan ALLAH ku bar wannan zancen kawai, mu ɗauka haka ALLAH ya tsara dama tun farko, ni banga wani abun kace nace ba....”    “Ba kace nace bane ba Rafeeq, wani abu ne ya ban mamaki yanzu, Aunty Babba da Umma sun sakani kira musu Aunty Kamila zasuyi magana sai na samesu cikin wani yanayi ita da ƴan uwanta, yayinda wani furuci nata ya daki zuwciyata, _wai ita bata jin zata iya cigaba da wannan kauda kan, gara ayita kawai ta ƙare tunda basu da wuta basu da aljanna._ To su waye? Kauda kan mi kuma ta daɗe tanayi har take jin bazata jureba a yanzu? Dan inda zaka gane maganar nada muhimmanci Maman Saheeba na ganina tai saurin fargar da su kasancewata, sannan a jiya sai bayan mun wuce asibiti da fin awa guda sannan ta zo ita da ƴan uwanta. Bazan ɓoye maka ba ranar bikin Yazeed a Kaduna da suka je wlhy wani mugun kallo naga tanama Hajiya Asiya, sai dai ban yarda hakan bane ba tunda ni dai ban san akwai wata matsala tsakaninsu ba a labarin rayuwar zamansu da naji ta baya, naso ɗan tuntuɓar Aunty Babba to amma kasan halinta akan Aunty Kamila”.         Sosai RK ke kallon Hajiya Majdiya har takai ƙarshen zancenta, kafin ya ɗan yi jimm na wani lokaci. “Tab ɗin inji mata, to ai nima dai bayanan naki sun sakani a ruɗani, mizai saka Aunty Kamila tai wancan furucin? Kuma miya haɗata da Ammien su Maanal da zata mata kallon banza?”.       “Ai shine, nima dai abin da ban wani ɗaukesa da muhimmanci ba, sai dai furucin nata na yau ya girgizani tare da dawo min abinda ya shuɗe. Shiyyasa nace bari na tuntuɓeka kodai akwai abinda kake ɓoye mana dan kowa yana mamakin haƙurewarka akan sadaukarma Ajwaad yarinyar nan, musamman ma ni dana san kana sonta sosai”.          Fuskarsa da ɗan murmushi ya ce,............✍️ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖1️⃣0️⃣0️⃣ ______________ .......“Aunty wannan maganar sai mun zauna kawai zan fahimtar dake komai. Amma maganar Aunty Kamila kamar ya kamata muɗan saka mata ido mu nazarceta dan karmu yanke hukunci kai tsaye akan abinda ba haka yake ba. Amma bazan ɓoye miki ba nima zuwanta Kano akwanaki game da auren Ajwaad ya tsaya min a rai na kuma jima abin bai bar zuciyata ba gaskiya, musamman dana san yaran data kawo akan ya aura shi hankalinsa baya akansu, sannan basu da nagartar da zaka zaɓesu a matan aure nagartattu ma ɗan daka haifa. Dan haka harna kasa haƙuri na tambayi Mah-mah akan Fadeel da Fawzan sune suka zaɓi matansu na aure ne? Bayan rikicin daya hana wancan auren na farko? Amma sai ta bani amsa da cewar ta manta gaskiya, amma kamar Aunty Kamila ce ta bada shawarar shi Fadeel ya aura ita Saheeba ɗiyar ƴar uwarta a lokacin, Fawzan kuma shine ya kawo matarsa da kansa, daga baya suka fahimci akwai alaƙa tsakanin Maman yarinyar da Aunty Kamila, amma hakan ai ba komai bane tunda Fawzan ɗin ne da kansa yace yana so”.        “Tofa, kaji wata kuma sabuwa.”     Shi dai RK baki kawai ya ɗan taɓe da faɗin, “To koma dai miye su suka sani. Yanzu yaya ake ciki? Yau za'a kawo amaren ne?”.     Harararsa Hajiya Majdiya tayi, shi kuma ya sanya dariya yana susar kai... Tattaunawar da Hajiya Majdiya tayi da Rafeeq ta sake sakata aune-aunen abubuwa, amma dai sai ta ajiye komai kamar yanda suka ajiye magana akan zasu nutsu su sake tattaunawa bayan biki... ________★          Ana yin sallar la'asar iyaye suka sanya Maanal a tsakkiya, nasiha akai mata mai ratsa jiki tana kwasar kuka. Ji take ita da zasu tausaya mata da sun barta. Dan tunda taji ana faɗar yau za'a kaita hankalinta ya sake tashi ta ƙara langarewa ita a dole bata da lafiya. Amma su Nene sun nuna idan taje can ta warware gara ta matsa tai jiyyar mijinta dake cikin halin ciwo. Duk da tun a jiya taji AA ɗin baida lafiya sai taji zuciyarta na ƙara shiga tashin hankali a yanzu. Amma dai ta danne. Kafin magrib an gama shiryata tsaf cikin lafaya ƴar ubansu mai ƙyau da tsadar gaske da Ammie ta tanada domin wannan ranar kawai ga autar ta, dan lokacin su Amal ma haka tayi. Aka kuma kawo alƙyabba data amsa sunanta alƙyabba aka ɗora mata akan lafayar, sannan aka baɗeta da ƙamshi na musamman.       Ana idar da sallar Magrib jerarrun motoci daga zuri'ar Darma suka iso domin ɗaukar amaryar su. Anan fa ne sabon kuka ya tashi. Maanal ta ƙanƙame Ammie da su Shahidah tace babu inda zataje. Babu wanda kukanta bai bama tausayi ba, dan ita kanta Ammie kukan take sosai balle su Amaal, duk da tasan inda Maanal ɗin zataje baida maraba da gabanta, zama ta iya samun kulawar da ƙila bazata samu a gabanta ba, dan Oum ba akan Manaal ba ita kanta uwace a gareta kuma babbar Yaya da kake jin alfahari da samunta a gareka. To a haka dai da ƙyar aka raba Maanal da su Ammie.      Yaya Fawzan da kansa zai ɗauki amarya, wannan alƙawarine da yay ma kansa dama shine zai kaima Auta Maanal a duk randa aka ɗaura musu aure. To Alhamdullah alƙawarin ALLAH kuwa ya cika. Kasancewar ba wani yawa ne da su ba ƴan kai amaryar tunda dangin Ammie ne kawai sai wasu a dangin Daddy da yay musu magana tun ɗazu suka baro  can gidan bikin Huznah suka dawo nan a wadace suka shiga motocin, a kuma nutse babu hayaniya babu hargowa. Su Aneesa ƙawayen amarya na tare da ita.       Sauran amare biyu dama sun iso suma tun ɗazun daga gidan Baban Yola, dan jiya da suka iso daga Yola a gidan baban Yola suka sauke turuga ba'a ƙaraso da su nan gidan Baba Sardauna ba da za'a amshi amaren gaba ɗaya sai yau. To su tun bayan sallar la'asar aka ɗakkosu, dan haka yanzu hankalin kowa ya koma kan isowar amaryar AA ɗin wato Maanal.         Lokacin da suka iso bayan Oum ta gabatar da sujudar shukur ta fita da kanta har harabar gidan inda motar amarya kawai ta shigo ta fiddo Maanal da kanta daga mota. Aiko Maanal najin maganar Oum sai ta sake ƙanƙameta ta fashe mata da kuka. Itama Oum ɗin sai kawai ta fara hawaye da murmushi a lokaci guda. Nan ko wayoyi suka fara aikinsu na hotuna da video, a gefe dama Yaya Fawzan ya tanadi mai ɗauka dama na musamman da zai ɗauki komai na bikin nan dan AA idan ya samu lafiya yaga komai yanda ya kasance. Tunda ALLAH ya ƙaddara za'ai bikin yana a halin ciwo.       An shiga da amarya Maanal har ɗakin Umma inda sauran amaren biyu suke, su Nene kuma aka basu masauki mai ƙyau dan Hajiya Majdiya ce tsaye akan komai. To da yake ma basu zo da shirin daɗewa ba sai suka wuce da wuri akan zuwa gobe zasu zo wajen walima in sha ALLAHU. Sai dai su ƙawayen amarya na tare da ita. Aiko sun haɗe da ƙawayen sauran amaren nan ko suka dunƙule anata kwasar hira. Maanal dai bata kula kowa ba, hasalima a kwance take zazzaɓi yay mata rijif. Suko sauran amaren Nuwaira da Raihana nata dama-dama da ita. Suma dai ƙyawawa kuma yarane kamar dai Maanal ɗin, garama Raihana ta girme musu dan itace yayar Nuwaira. Daka gansu suma kaga jinin Darma Family, dan kamaninsu da su Oum a bayyane suke sosai. Sun san Maanal a zamanin ƙuruciya, musamman Nuwaira da Maanal ɗin tasha jibgarta idan suka zo Kano a wancan lokacin. Sai wancan lokacin yayta dawo musu a rai suka amshi Maanal ɗin hannu bibbiyu, to dama dai baka gayama jinin Darma wulaƙanci, dattakonsu da mutuntawarsu ga kowa a bayyane take yaransu da manya. Sai dai su kuma basa ɗaukar wulaƙanci da raini ga kowa....   _________★       Zuwa washe gari hankalin su RK ya fara tashi akan rashin farkowar AA. Dole suka fara kaikawo a kansa da gwada dabaru. Amma dai babu alamar hakan, cigaban kawai da aka samu shine daidaituwar bugun zuciyarsa. Normal zuciyarsa ta koma dai-dai tana aiki, sai dai bayan ita babu wani ɓangare na jikinsa dake motsawa balle akai ga batun numfashi. Gashi dai nan kwance samɓal abinsa zagaye da na'urorin a ƙirjinsa da hancinsa har ma da baki. RK ne da yay wani tunani ya bama su Abbu shawarar ko a kawo Maanal asibitin ta gwada kira musu sunansa a cikin kunne.         Babu wani ja inja su Abbu suka amince da hakan, dan irin wannan abubuwan duk dabarune na likitoci. Babu ɓata lokaci kuwa RK yay kiran Oum ya mata bayani. Dama shirin zuwa asibitin suke yi sai kawai aka saka Maanal ta shirya itama. Dama dai tayi wankanta kamar sauran amaren tun safe. Tana sanye da atamfa data mata ƙyau sosai. Sai farin mayafi daya sake ƙawata ƙyawunta da ɗaurin da Najma ta mata akan dole harda ƴar kwalliya. Sam fuskarta babu walwala sosai, dan kanta ciwo yake mata har yanzu. Ga kukan data sha a kwana biyun nan idanunta duk a kumbure. Koda suka taho ma tana kwance a jikin Oum ne. Bata wani yi mamakin ganinsu a asibiti ba tunda an sanar mata dama AA na asibiti, sai dai wani abu daya ɗan zunguri zuciyarta bayan sun fito a mota suma su Mamy dake a cikin wata motar sun fito, risinawa tai ga gaishesu, kanta a ƙasa shiyyasa bata banbance wanda ya amsa mata da wanda bai amsa ba. Sai da ta ɗago saboda kama hannunta da Oum tai zasu shiga cikin asibitin sai idonta ya sauka akan Mamy, wani mugun kallo ta samu idon Mamyn na mata akai-akaice, harga ALLAH sai da gabanta ya faɗi, amma kuma Mamyn tai saurin janye idonta dan dama a yanda take mata kallon bai zama lallai kowa ya lura ba gaskiya, da alama itama ta kamata ne a bazata. Sai dai kuma komai ya faru ne a idon Hajiya Majdiya, dan haka itama zuciyar tata sai da ta girgiza...       Sun dai shiga ciki, inda suka samu su Babban yaya da su Abah su Baba Sardauna, Baban Yola da su Abbu duk acan, kusan ma duk mazan family ɗin na'a asibitin ne. Hakan ya ƙara saka Manaal a cikin matsanancin kunya, ta ƙara jan mayafinta ya rufe mata rabin fuska kanta kuma a ƙasa. Cike da girmamawa taje har gaban su Baba Sardauna ta durƙusa tana gaishesu kasancewar su iyayen duk suna a waje ɗaya ne zaune. Dukansu babu wanda fuskarsa bata kasance a cikin fara'a ba. Suka shiga amsa mata da kulawa da sanya albarka shi Baba Sardauna ma harda tsokanarta irin wasa na jika da kaka. Ita dai kanta a ƙasa fuskarta a rufe babu wanda zaice ga'a yanda take. Hakan sai ya ƙara saka musu ƙaunarta da jin gamsuwa da ita, dama kuma a binciken da sukai basu samu wani aibu a tare da ita ba kamar yanda suka sami akan Huznah, balle ma sun san ƙuruciyarta kaf ɗinsu musamman ma shi Baba Sardauna da Baban Yola da Abah. Abbu ne kawai sai tsintsa-tsinta saboda lokacin ba'a ƙasar suke ba.       RK ne ya jagoranceta zuwa ɗakin da AA yake, karon farko kuma kenan da wani zai shiga ya ganshi idan ka cire likitoci da kullum ke kai-kawo a kansa. Wani bala'in girgiza zuciyar Maanal tayi da ganin yanda AA ɗin yake zagaye da na'urori tun kan su shiga, sai jikinta ya fara rawa. RK ya riga yasan tata matsalar itama, dan haka da sauri kuma cike da lallashi ya ce, “Please Maanal relax, ba wata babbar matsala Ajwaad yake a ciki ba, numfashinsa ne yay nisa da tun a daren jiya muke saka ran dawowarsa amma shiru, amma in sha ALLAHU idan yanzu kikai juriya ringa kiran sunansa a cikin kunne muna fatan nasarar dawowar tasa dan bugun zuciyarsa ya dawo normal. Dan haka ki kwantar da hankalinki nutsuwarki muke buƙata. Sannan zaki kira shi da sunan Besty ne ba sunansa ba.....”       Da sauri Maanal ta kalla RK a karo na farko. Kansa ya jinjina mata. “Hakan shine mafita Maanal, dan wannan halin da yake ciki yana da alaƙa da tsoron rasaki da ya shiga, idan kuma ya jiki a kusa da shi a yanzu in sha ALLAHU muna fatan nasara.”      Sosai ta zubama RK ɗin idanu saboda kalamansa, da alama jin cewar a kanta ya shiga halin ya girgizata. Shima RK ɗin ya fahimci hakan, dan haka yay murmushi da faɗin, “Maanal wasu abubuwan ba kai tsaye muke fahimtarsu a rayuwa ba sai dalili ya ratsa. Shiyyasa barin wasu al'amuran a dunƙule yafi alkairi sama da buɗesu ma duniya ko mu mu sansu. Yanzu dai kece hope ɗinmu na ƙarshe akan Ajwaad, dan haka bismillah”.        Gaba ɗaya jikin Maanal ya gama mutuwa, hawayen da take ta faman riƙewa suka shiga zubowa, dole ta saka gefen mayafinta ta share sannan suka ƙarasa shiga cikin ɗakin. Sun sami likitoci biyu sai Abbu a tare da AA ɗin, dan haka kai tsaye gaban gadon da AA ɗin yake kwance aka kaita, tare da nuna mata kujerar dake gab da gadon ajiye. Sai da ta zauna sannan ɗaya daga cikin likitocin ya matso ta ɗayan ɓangaren AA ɗin hannunsa riƙe da file, umarnin riƙe hannun AA ɗin ya bata, dan haka tai diri-diri na jin kunya tana satar kallon inda Abbu yake. Murmushi Abbu yay a karo na farko, tare da ƙarasowa gaban gadon cike da lallashi ya ce, “My dear karki damu kinji, ki saka a ranki ceton rai zakiyi dan Ajwaad na a gaɓar rayuwa ko mutuwa ne a yanzu, in har zuciyarsa ta tsaya daga aiki to shike nan dan itace kawai ke nuna mana yana a raye a halin yanzun. Ke kuma mun tabbatar kina a cikin wannan zuciyar tasa, wannan abun da zakiyi shine zai motsata da ƙarfin ikon ALLAH ƙarfin bugunta ya gauraye raunin gaggangar jikinsa dukkan hanyoyin numfashinsa su buɗe”.        Kanta dake a ƙasa ta jinjinama Abbu, kafin a hankali ta kai hannunta dake zane da baƙin lalle da ja saman nashi dake ajiye a kan shafaffen cikinsa. Jitai wani irin shock ya shigeta, ta ɗan ja hannun baya tana rumtse idanu, fin sakan biyu kafin ta sake kaiwa saboda maganar da Doctor ya sake mata. Gently ta sarƙe tafukan hannunsu cikin juna, sai ta samu kanta da matsesu, wata rarrauniyar ajiyar zuciya na suɓuce mata. Sanyin tafin hannun nasa ratsata yake har cikin ƙwaƙwalwa, yayinda nata dake da ɗumi na tasiri a daskararriyar gangar jikinsa. Sai da ta sake matsar da kujerar sosai gaban gadon kafin ta samu damar rankwafar da fuskantar a saitin kunnensa nunfashinta dake fita a sarƙe na sauka a ciki. Bugun zuciyar ta na ƙaruwa saboda yanda tasirin ƙamshinsa da ya gama kama masa jiki ke shiga cikin ƙofifin hancinta. Idannunta a lumshe, lips ɗinta na rawa, muryarta da wani irin rauni da sanyi kamar mai raɗa ta furta, “Besty! Besty! Besty ka tashi gani a tare da kai, Maanal ɗinka ce, Bestyn ka, ƙanwarka daka raina da hannayenka,  ka buɗe idonka dan ALLAH ka ganni kaji Besty, muci abinci tare, muyi wanki tare, muyi hira tare, ka kaini kitso ina maka kuka kana lallashina. Na takalo faɗa ka tare min koda su Didi ne.” sai hawaye sharrr suka shiga sakko mata daga idanu suna sauka akan jikinsa. Sosai kuka ya sarƙeta harta kife fuskarta a jikinsa ta sake shi mai ƙarfin gaske a cikin kunnen nasa..........✍️ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖1️⃣0️⃣1️⃣ ______________ ........Babu wanda ya dakatar da ita a cikin likitocin, saboda hakan su ya musu dai-dai ne, dan RK ma gefe ya maida kansa yana murmushi. Hakama Abbu tausayin yaran ne ya wani sake mamayesa. Al'amarin kamar wani film sai ga yatsan ƙafarsa babbar ya motsa. Ai wata irin zaburar farin ciki likitocin da dama idanunsu tsaye suke kyam akan duka gaɓɓan AA ɗin sukai. Ita dai Maanal da gaske kuka yaci ƙarfinta ta yanda tama manta da ba ita kaɗai mace ba a ɗakin. Sai da hannun AA dake cikin nata yay wani irin nasifar matse nata, shi kuma yay wata irin yunƙurawar zabura har sai da gadon yay girgiza wasu a cikin igiyiyin na'urorin dake jikinsa suka fincike kansu da kansu. Da wani kalar sauri ta ɗago itama, yayinda su RK suka zagayeshi suna ambaton Alhamdullahi a tare. Sosai riƙon da AA yayma hannun Maanal ke azabtar da ita, dan riƙo ne na mazan gaske, amma ta daure dan anyi-anyi a raba hannun nasu hakan ya ta gagara, sai Abbu yace a barshi kawai a hankan. Haka yana riƙe da hannunta a gaban idonta suketa ƙoƙarin dai-daita numfashinsa da zaburar da yake yi. Fin mintuna talatin kafin komai ya daidaita ya koma dan kansa ya nutsu, yayinda numfashin nasa ke fita a hankali a hankali...       Ƙasa-ƙasa Abbu dake kallon Maanal ya ce, “Sake kiransa”. Kanta ta jinjina, a hankali ta sake ɗan matsawa gab da gadon ta ce, “Besty!!”. Hannunsa dake riƙe da nata ya ɗan motsa, sai kuma ya ɗan ƙara damƙe natan ta yanda har sai da ta ɗan yamutsa fuska dan zafi. A hakan ta cigaba da kiran sunan nasa. A yanzu kam idanunsa dake rufe ya ɗan fara motsawa, sannu a hankali dogayen eyelashes ɗinsa dake baƙaƙe siɗik kwance suka fara rawa suma, sai kuma ya fara ɗaga su kaɗan-kaɗan tsagar idanunsa suka sake bayyana. Nuni Abbu yake mata da hannu alamar ta cigaba da kiransa dai. Ita kuma tanata maimaitawar batare da gajiyawa ba, har ALLAH ya bama AA damar buɗe gaba ɗaya juyayyun idanunsa dake a kumbure kuma jazur. Lumshesu ya sake ƙoƙrin yi irin luuuu ɗin nan, sai dai kafin su gama rufewa ya sake ɗagasu suka buɗe saboda tasirin da muryar Maanal ke cigaba da yi masa a cikin kunne. A buɗewa ta biyun kam sosai ya buɗesu, ya kuma tsaidasu a kanta, yanda ya zuba mata su cikin tsakkiyar nata idanun kamar ɗan maye yasa tsigar jikinta tashi. Dole bakinta ya kasa cigaba da motsawa ta daina kiransa, haka su Abbu ma sunyi tsittt kamar ruwa ya cinyesu a ɗakin. Fin minti biyu yana mata wannan kallon kafin ya sake ƙoƙarin jan idanun zai rufe Abbu ya kira sunansa shima..        “Ajwaad!!”.     Luuuu ya sake ƙoƙarin buɗe idanun ya saukesu akan Abbu. Murmushi yay masa, sai kuma ya nuna masa Maanal. “Kasan wannan?”.       Idanun nasa ya juya a hankali ya sake maida su kan Maanal da Abbu ya nuna. Ɗan sake kafeta yay da kallon kafin ya maido idanun kan Abbu ya jinjina masa kansa alamar ya santa. Murmushi Abbu yay da jinjina kansa ya ce, “Alhamdullahi minene sunanta?”.         Idanunsa ya ɗan rufe kamar yanda ɗabi'arsa take musamman a lokacin da bai son yin magana, kafin ya buɗe a karo na farko ya motsa pink lips ɗinsa da suka tattare waje ɗaya suka bushe kaɗan ya furta, “Besty”. Babu wanda yaji sautin muryar amma sun fahimci abinda ya faɗa daga motsin laɓɓansa. Cike da gamsuwa fuskar Abbu da murmushi ya nuna kansa shima ya ce, “Nifa?”. Nan ma lips ɗin ya motsa kawai ya ce, “Abbu!”. Nan ma Abbu ya jinjina kai ya juya ya nuna masa RK ya ce, “Wannan fa?”.       A mamakinsu sai ya kauda kai yaƙi magana. Abbu ya sake maimaita masa, batare da ya juya ya kalla RK ɗin ba ya ɗan jujjuya kansa alamar bai sanshi ba. Kasa haƙuri RK yay ya fashe da dariya. Abbu ma dai murmushi yake sosai. Su dai sauran likitocin basu fahimci abinda ke faruwa ba sukam, amma sunyi mamaki da yace bai sanshi ba. Maanal da abin ya bama mamaki itama ta ce, “Rafeeq ɗin ne baka sani ba?”.        Idanunsa ya ɗaga a hankali ya zuba mata, itama kallonsa take fuskanta da mamaki har yanzu. Cikin dariya RK yace, “Barsa daughter, zan fasa tariyar taki ne har sai randa ya fara ganeni ɗan rainin hankali”.       Barin wajen Abbu yay yana dariya da girgiza kai, yayinda AA ya ɗan juya ido alamar don hararar RK yake son yi amma idanun sun masa nauyi, sai ya sake jimƙe hannun Maanal da ƙarfi har sai da ta saki ɗan ƙara dan dama a takure take dama, hannun ya mata tsami sosai. Karo na farko AA ɗin ya kalli abinda ke cikin hannun nashi, da mamaki ya zubama hannun nata mai zane da lalle raɗam idanunsa kumburarru. Fuskarsa na nuna mamaki ya juya ya kalleta, fuska ta ɓata sosai da tura baki gaba. Idanunsa kawai ya rufe, dan a karo na farko sai ya fara jin kamar mafarkin daya saba ne. (Wai ya akai ma ta kasance a kusa da shi, hannunta kuma cikin nashi? Ya rabba) Ya ayyana a zuciyarsa yana sake buɗe idon dai a kan hannayen nasu dan ya yarda kawai mafarki ne.            Cike da shaƙiyanci RK ya duƙo saitin kunnensa ya raɗa masa, _“Kada ka wani firgita kanka yanzu kam HALAL ce. Besty ta zama mallakin Besty yarona”. Da sauri AA ya juya yana kallonsa. RK ya kashe masa ido ɗaya”. Harga ALLAH daburcewa AA yayi, sai numfashinsa ya nema fara wani irin fisga. Dai-dai nan Abbu da yaje yayma su Oum albishir ɗin farfaɗowar AA ɗin ya sake shigowa. Da sauri ya ƙaraso gaban gadon yana faɗin, “Subahannallahi mi kuma ya faru?”.       Kallon da sauran doctors ɗin kema RK yasa Abbu kallonsa shima. “Miya faru Rafeeq?”.         “Relax Abbu babu komai fa. Kawai na masa albishir ne”.    Baki buɗe Abbu ya ce, “Amma kasan zaka iya maida shi cikin suma wane irin likita ne kai?”.       Dariya RK yay. Ya ce, “Ai karka wani damu Abbu koya suma sai ya sake farfaɗowa. Ɗan rainin wayon bani yace bai sani ba”.     Da sauri Abbu ya jawo abu alamar zai daki RK, aiko ya fita da gudu yana dariya.....     _____________★          Sai muce Alhamdullah, zuwa bayan sallar la'asar AA da aka saka barcin awoyi dan brain ɗinsa da zuciyarsa su zama fresh ya sake farkawa. Zuwa yanzu dai kam anata shiga duba shi, dan har an canja masa ɗaki ma. Maanal dai tun da ya fara barci suka wuce gida ran Oum fes, dan anayin azhar aka fara gudanar da walima. Bayan an idar da la'asar akai buɗar kai, a kuma lokacin ne AA ya farka acan asibiti su Abah zagaye da shi. Dan duk mazan ne dai yanzu matan duk suna gida wajen walima. Duk da dai hankalin Oum da Maanal duk yana asibitin amma suna daurewa ne kawai na dole. Hakama Mamy da gaba ɗaya take a jagule dan ko wajan walimar bata zauna ba, sai ma ƙirƙirar barin gidan da sukayi ana fara walimar zuwa can gidan babbar yayarsu. Acan suka samu damar baje zantukan bakinsu yanda ya kamata. Da tsare-tsaren yanda zasu cimma Maanal da Oum, dan yanzu kam dai yaƙin ya zame musu biyu. Sai batun Nuratu da suke tunanin Darma Family ɗin da zasu iya cewa bazai yiwu a wannan satin ba saboda halin da AA ɗin ke ciki. Dan haka hankalinsu a tashe yake tannan ɓangaren shiyyasa suketa faman tausar Mamyn akan son birkicewar da take neman yi....          Shida na yamma aka kammala komai da komai, aka shirya amare domin musu rakkiya. Nuwaira gidan Abbu za'a kaita ɓangaren RK daya sha gyara, sai daga baya zai ɗauka abarsa su wuce Abuja tunda can rayuwarsa take shi. Sai Raihana haɗaɗɗen gidan Uncle Najeeb dake kusa dana Baban Yola shima dai, hakama su Modibbo duk kusa da kusa suke. Wannan kusan aƙidar Darma family ce, da wahala kaga yaransu sunyi nesa da su.. Maanal dai tana nan gidan Baba Sardauna su sai zuwa gobe in sha ALLAHU zasu wuce Abuja. Danginta dai da ƙawayenta da suka zo wajen walima duk a ranar suka tattare a can gidan da suka sauka. Suma dai zuwa gobe in sha ALLAHU zasu wuce Kaduna. Su Didi wayo sukaima Maanal akan zasu dawo gobe suka gudu, dan haka ta sakankance da hakan. Ga kuma Najma na ɗebe mata kewa ga Oum. Dan yanzu tana a ɗakin Oum ɗinne. Zuwa bayan isha'i gidan Baba Sardauna ya rage mutane sosai, dan wasu zasu kwana a gidan Baban Yola da gidan Abbu ne da sauran gidajen ƴan uwa. Zuwa safiya kowa ya kama gabansa, dama dai danginsu ne na Yola sukafi yawa. Sai dangin mahaifin su Nuwaira da ƴan kura dangin Abbu.         Kusan takwas da rabi Oum ta saka Maanal shiryawa dan zasuje asibiti sake duba AA, duk da Fawzan ya kira Oum yana sanar mata Autan nata ya saka bore shi sai an sallamesa sai da Abah yay masa jan ido da Abbu sannan. Amma yace shi gobe babu wani asibiti da zai wuce gida zaije, tunda an sanar masa gobe zasu wuce Abuja. Ji Maanal tai kamar ta langare tace bata da lafiya. Dan dama ɗazun allurar da akai masa ce ga ceceta suka gudo. Amma babu yanda ta iya dole ta shirya ɗin suka wuce. Sauƙin ma basu kaɗai bane. Harda Umma, Hajiya Majdiya, Mamy, da wasu sauran dangi da suka rage manya. Sai ita sai Najma a yara da su Saheeba. Sun iso asibitin abin mamaki suka sami ƴan uwan Mamy harda Nuratu da basu san sanda ta zo Kanon ba. Dan tunda aka fara bikin nan babu ita. Tunda Mamy taga Nuratu take ta faman murmushi, yayinda Nuratun babu kunya ta wani rungume Mamy. Su Mamanta kuma suna gaisuwa da su Oum.          Sai da aka gama gaishe-gaishen sannan suka shiga, dan suma su Nuratun isowarsu kenan ashe. Oum dake riƙe da hannun Maanal ce a gaba, sai Umma sannan Mamy da Hajiya Majdiya dake a jere. Bayansu su Nuratun ne da su Shaheeda. Zaune yake kam yanzu an ɗan ɗago gadon ta saitin kansa sosai sama sai ya zam ya jingina. RK na tsaye a gefensa yana cire masa drip, babban yaya a kujera, Fawzan a gadon kusa da ƙafafunsa da kofi a hannu, sai Uncle Mahmud da Uncle Hussain nata ɗayan gefen zaune a kujeru suma. Yanda fuskokinsu ke wasai zai baka tabbacin hira suke cike da nishaɗi. Yayinda AA ke ɓata fuska yana kallon kofin shayin hannun Yaya Fawzan da alamu suka nuna shi zai ba mawa. Sannu da zuwa gwarazen mazajen kema iyayen nasu, suka kuma shiga tashi domin basu kujerun. Yayinda AA ya zubama Maanal idanunsa shanyayyu har yanzu. Ita ko tunda dai masa kallo ɗaya ta janye abinta kanta ma a ƙasa take gaida su babban Yaya. Cike da neman magana Ya Fawzan ya ce, “Kai Alhmdllh gara ma dai da kuka zo. Lilly zo kiji da mijinki dama daru yake ma mutane yaƙi cin abinci”.        Ji Maanal tayi kamar ƙasa ta tsage ta shige. Ta sake riƙe hannun Oum sosai cikin nata tana matsawa jikinta. Murmushi Oum tayi da faɗin, “Kace kana nan kana takura min shi da takurarka”.          “Oh Oum hakama zakice. Shikenan wlhy Lilly zauna ku ƙarata tunda babarsa ma maimakon ta gode min kinji mitake faɗa.”      “Eh anji ɗin”. Cewar Oum tana zaunar da Maanal a inda Fawzan ɗin ya tashi kusa da AA kenan a gadon jiyyarsa. Ta kuma amshi tea ɗin ta miƙa mata. Kuka kawai ya rage Maanal ta saki dan kunya. Dan yanda ta kalla Oum kamar zata fasa ihu. Amma sai Oum ɗin tayi kamar bata gani ba ta damƙa mata kofin a hannu. Dariya su Umma daketa tsokanar Maanal irin wasan kaka da jika tun jiya take musu. Ta zauna a kujerar da Babban yaya ya tashi yana gyara mata tana faɗin, “Ɗan nema, ni zaka kalla ba ita ba ai, kasan dai da tsohuwar zuma ake magani”.        Dariya su Oum sukayi, AA daya shagala a kallon Maanal tun ɗazun ya janye idanunsa a hankali yana ɗan murmushi saboda zancen Umma. Dama shi bai iya maida wasa sai Fawzan da Babban Yaya. Kosu kakanni sukai masa iyakarsa murmushi ne. Umma ta riga ta san hali dan haka bata damu ba ta maida kallonta akan Maanal da tunda Oum ta damƙa mata kofin shayi ta kasa motsi. “Maanal matsa ki bashi kada ya huce kinji, idan ma dan nice bazanyi kishi ba, zan daure na haɗiye ko iya na yau ne tunda amarya kike. Amarya kuma ance kota buzuzu ce daɗin suna ne da ita”.      Dariya su Fawzan suka sanya. Hakama su Oum.........✍️ 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖1️⃣0️⃣2️⃣ ______________ ........Babu yanda Maanal ta iya ganin hankalin su Oum ya koma a gaishe-gaishe da su Uncle Mahmud dole ta matsa kaɗan zuciyarta na wani irin bugawa, jikinta na gogar ƙafafunsa musamman ta wajen gwiwa zuwa cinyiyinsa kaɗan saboda yanayin zaman nasa. Batare data kallesa ba ta miƙa kofin shayin kusa da bakinsa.         Idanu ya ɗan zubama kofin kafin a hankali ta yanda ita sai wanda ke kusa da su gab suka ji ya furta, “Idan da zafi kuma fa, baki sha kinji ba sai ya ƙona ni?”.      Idanunta da suke ɗan tara ruwa na kunya ta ɗago ta ɗan kallesa, sai ya wani sake narke nasa dake kallonta ƙasa-ƙasa yaɗan matse fuska. Da sauri taja numfashi tare da jan hannunta baya, kamar zatai kuka ta ce, “Babu fa wani zafi”.        “Ban yarda ba kisha na gani ”.    Ya faɗa kamar mai raɗa. Kaɗan ta hararesa sannan takai kofin kusa da bakinta a kunyace ta ɗan sha. Shi ko ya wani zuba mata ido kamar ya manta da basu kaɗai bane ba fa. Sai da ta sake maido kofin kusa da bakin nasa tana ɗan tura baki sannan ya janye idanun lips ɗinsa suka motsa kaɗan kamar zai yi murmushi. Maimakon ya amsa a haka sai ya ɗaura hannunsa a hankali saman nata dake riƙe da kofin a haka ya kai bakin nasa. Lumshe idanunta tayi tsigar jikinta na tashi....       Duk da wannan abu dake faruwa akan idon Mamy da Nuratu, Nibras, Saheeba da Mamansu da yayar Mamy ne. Dan su amaimakon gaisuwa da hirar da akeyi a ɗakin hankalinsu na kan AA da Maanal ne. Suko su Oum hirarsu suke cike da dattako sun basar kamar basa ganin komai. Yayinda Hajiya Majdiya ke karance yanayin su Mamy ɗin tsaf tanama RK nuni da idanu. Shi dai murmushi kawai yayi dan abun nasu Mamy ma dariya ya bashi. Dan duk da Mamy ɗin na ƙawata fuskarta da murmushin dannewa mai hankalin daya saka mata ido zai fahimci ranta a dagule yake. Nibras kam tuni ƙwalla sun cika mata ido, dama kwana biyun nan hankalinta a tashe yake, ko bikin bata so zuwa ba amma ta rasa ta hanyar da zata zame tunda tasan Mamanta bazata barta ba, ace ana bikin gidansu da family ɗin mijinta gaba ɗaya babu ita zai zama abin magana. Wata kalar tsanar Maanal take ji mai tsannanin gaske. Hakama Nuratu ta kumbura tayi fam kamar ta shaƙe Maanal take ji. Dan har ƴar zabura tayi kamar zataje kansu Mamy ta damƙe mata hannu a kaikaice. Saheeba kam nata faman taɓe baki.       Oho su masoyan ma basu san anai ba. Musamman Maanal ma data juya musu baya. AA kam ta shan shayinsa yake ko gaishe shi da sukai kowa bai kallaba a cikinsu dan baima san waye da waye ba, babu wani daɗewa sai gashi ya shanye tas, a take zufa ta shiga tsatstsafo masa a goshi. Aiko sai Fawzan da RK suka samu na tasashi a gaba da tsokana. Wai gulmamme ashe yana jin yunwar yaketa basu wahala tun ɗazun da yake su ya raina su. Yanzu da yake Bestyn sa ce ta bashi gashi ya shanye babu ko gargada. Harararsu kawai yay ya ɗauke kansa, sai Oum ce ke tare masa su Umma da su Uncle Mahmud na dariya. Mamy dai ta ɗauke kai ita adole bata san anai ba. Tsabar neman magana irin na Hajiya Majdiya sai ta ciri tissue dake a bed side drawer ta miƙama Maanal tana faɗin, “Daughter share masa wannan gumin goshin kinji. Son ko zaka ƙara da wani abun? Kaga farfesu nan Oum ɗin ka ta maka da kanta yanama ina?”. Ta shiga waige-waige. Miƙo mata Najma dake kusa da Yaya Fawzan tayi, dan itama fa a bikin nan ita da Yaya Fawzan wani al'amari ne mai girma ke neman shiga. A mamakin kowa babu musu AA yace zai ci. Aiko Maanal ta tura baki gaba tana kai tissue ɗin da Hajiya Majdiya ɗin ta bata saman goshin nasa. Yanzu ma hannun nata ya riƙe a haka aka goge gumin tana jin kamar ta fasa ihu dan kunya.      Tsaf Hajiya Majdiya ta zuba farfesun a ƙyaƙyƙyawan glass bowl ƙarami ta miƙama Maanal. Cikin marairaicewa Maanal ta ce, “Ummy zaifa iya ci da kansa”.     Daƙuwa Hajiya Majdiya ta mata da faɗin, “Ungo nan, ashe inada sauran tsalle sai na zauna na sake miki sabon karatu kuwa, dan in kinji ana uwar zamani nice nan, maza bashi bawan ALLAH yaci daga ciyarwarki ya godema ALLAH wannan ramar duk ta ɓace yayi angwancinsa kamar sauran baby muke so da wuri in sha ALLAHU nan da wata goma muna nan a Kano kamar haka taron sunan ƴaƴa da jikoki”.       Abu Oum ta ɗauka ta kaima Hajiya Majdiya kamar zata daketa ta ce, “Kedai Majdiya anyi uwar banza wlhy”. Da sauri ta kauce tana dariya. Hakama su Umma da su Babban Yaya kai kawai suka kauda gefe suna dariya. Yayinda takaici ya turniƙe su Mamy har wuya. Maanal kam jitai kamar ta zura da gudu daga Kano har Kaduna a ƙafa. Da yatsa AA da kansa ke a ƙasa yana wani munafukin ɓoyayyen murmushi ya ɗan takali hannun Maanal cike da tsokana. Ƙin kulashi tayi, sai da taga ya cigaba ta ɗan kalla gefe da gefe da ido taga kamar babu mai kallonsu takai hannu ta mintsini hannun nashi...        “Ouch!! Oum kingata ko”. Ya faɗa a hankali yana ɓata fuska.    Juyowa Oum tayi, yayinda Maanal ta daburce mamakin AA ɗin na neman halakata. Ganin yanda Maanal ɗin tai tsuru-tsuru da ƙyar ya danne dariyar dake neman suɓuce masa, cikin wayancewa ya ce, “Yunwa nake ji Oum ki amsa ni to bani tunda ita bazata ban ba”.         Cike da lallashi Oum ta ce, “Kwantar da hankalinka zata baka. Babyna kinga bashi kada ya huce. Kinga magani zai sha.”       Kai Manaal ta iya jinjina ma Oum kawai, ta ɗiba naman takai bakinsa, ido ɗaya ya kashe mata tare da ɗan dallo halshensa kaɗan alamar gwalo. Itama cike da haushi da shagwaɓa ta ce, “Oum kinga yana mun gwalo”.              Da sauri AA ya waro idanu waje yana nuna kansa. Yayinda Oum ta kai masa ɗan rankwashi tana faɗin, “Auta ka kiyayen ALLAH bar ganin baka da lafiya. Dama ka samu take baka”.       Duk wanda yasan rayuwarsu yasan wannan ba komai bane. Dan haka Fawzan karaf yace, “Aifa yanzu munga takanmu. O'e tsokanar faɗa, o'e kai ƙara”.        “Kai kuma sa ido ba”.    Cewar AA yana hararrasa. Babban Yaya ya ce, “Sana'ar banza kuwa nan yafi afki”.      “Oh haɗin kan zai dawo kenan?, ALLAH yaso nima yanzu ina da magoya baya. Ga Naufal, Anum, Saheeba ga Nibras”. Fawzan ya faɗa yana kallonsu a ɗage.        Sosai abun ya bama su Umma dariya ya kuma birgesu. RK ya ce, “Nima kuwa ina bayanka Son. Suje suyita haɗin kan mana ganinsu a rana ba wuya zai yi ba”.      “Aniyarka ta bika, ai dama halinka ya kwaso kwabo da kwabo”. AA ya faɗa yana jifan RK da spoon ɗin cikin farfesun hannun Maanal. Cafe cokalin RK yayi, ya ce, “Eh lallai ai nagama Safa da marwar jawoka a bakin rami kamin fitsara fa. To bari kaji bar ganin ka samu, yanzu nan saina maidaka doguwar suma da allura”.          Dariya Uncle Mahmud harda da Uncle Hussain harda hawaye, duk da wannan irin drama ɗin tsakanin AA da RK abune a bayyane a tsakaninsu kowa ya sani. Amma yau ɗin daya haɗa da tasu Fawzan sai ta saka kowa nishaɗi. Yayinda sashen su Mamy ke jin kamar zasu mutu. Ƙarshe dai Umma ce ta kira RK akan ya tafi wajen amaryarsa da aka kai tun ɗazun dare nayi. Suma su Uncle Hussain duk sai suka musu sallama. Ganin haka su Maman Saheeba da takaici ke neman kashewa suma sukace zasu wuce dare nayi. Sai Nuratu da muryarta ke faman rawa alamar danne kuka tace ita zata zauna a wajen Mamy ta kwana. Amma sai mamanta tace a'a tazo su wuce, dan su mamy gobe zasu wuce Abuja da safe. Haka babu yanda ta iya ta bisu, suna fita ta rushe da kuka kuwa dan yanda ko kallonta AA baiyi ba ya zafeta matuƙa. Dan kasa jan motar data tuƙosu sanda zasu zo tayi, sai Maman tata ce ta amsa. Nibras ma dai kukan take a kaikaice. Bata taɓa jin tsanar family ɗin Fawzan ba irin yau a rayuwarta. Dan duk yanda ake bata labari da misalta mata yanda suka shaƙu da su Maanal bata san abin yakai har irin haka ba gaskiya. Duk rashin magana irin ta babban Yaya kaga yau yana biyema wannan iskancin nasu ai kasan abin babba ne. Shi kansa AA da kowa yasan baƙin halinsa jiba yanda yake ma yarinyar nan ko kunyar su Oum babu..       Oho AA dai yama maida hankali akan amsar naman da Maanal ke bashi cike da jin nauyi, gashi dan wulaƙanci da son bata kunya sai ya wani riƙe hannun nata a duk sanda zata kai masa a baki. Kallon kuwa da ya ke binta da shi gaba ɗaya tayar mata da tsigar jiki yake yi. Shi ko da alama ta lura ko'a jikinsa. Kamar kuwa ta sani ko'a jikin nasa, duk da adukan abinda yake yana cijewa ne kawai saboda Mamy, dan sam yaƙi yarda ya kalleta tunda suka shigo. Har cikin rai kuma yana tsoron keɓewarsu da ita duk da yasan itama tasan yayi biyayya ga umarninta, saboda har yanzu ji yake al'amarin kamar mafarki wai Maanal matarsa ce. Tunda ya farka da yamma su babban Yaya dake tare da shi da su Uncle Hussain sun sanar da shi komai. Shi kansa a yanzu baima san irin ƙaunar da yake ma RK ba. Duk kuwa dama can a kaf dangin nasu ƙaunar da yakema Rafeeq daban ce a rayuwa. Duk da basu rayu tare ba tun ƙuruciya, kusan ma sai bayan faruwar abinda ya faru tsakaninsa da Maanal a jiyyar da yayi ce shaƙuwar tasu ta fara da Rafeeq ɗin. Amma tabbas har yanzu jinsa yake kamar barci yake komai a mafarki ne zai farka yaga Rafeeq ya auri Maanal, shi kuma an aura masa zaɓin Mamy...        Har sha biyu Mamy, Umma, Oum, Hajiya Majdiya da su Babban Yaya, Saheeba Nibras sai Maanal suna asibitin. Sai da baba Sardauna ya kira waya yace su taho haka nan Doctor nason yima AA allurar da zai samu isasshen barci sunje sun tsare su kuma suna jin kunyar yin magana sai da ɗaya daga cikinsu ya kira Baba Sardauna ɗin a waya sannan. Haka badan sun so ba suka hau shirin tafiya. Dan hira ake mai daɗi. Amma Maanal gaba ɗaya a takure dama take jin kanta da rayuwarta. Dan ma inda ALLAH ya taimaketa bayan ta gama bashi farfesun sai romon ya ɗan zubar mata a jiki shine ta shiga zuwa toilet ɗin ɗakin wankewa kamar yanda Umma ta umarceta, data dawo sai ta canja wajen zama. Duk da kallon da AA ke mata ƙasa-ƙasa da mata alama ta dawo da ido taƙi kulashi, tama maida hankalinta ga Najma suma hirarsu ƙasa-ƙasa duk da Najma ɗin ce ke tsiyaya surutun ita nata murmushi. Sai Fawzan dake kusa da su dake saka musu baki jefi-jefi. Hakan da Maanal tayi ba ƙaramin birge Umma tayi ba. Dan ta sake yarda da tarbiyyar yarinyar ɗari bisa ɗari, hakan na nuna musu koda aka rabu mahaifiyarsu batai sakacin cigaba da inganta tarbiyyar su ba kenan. Ana cewa za'a tafi itace gaba-gaba a fita kuwa. AA ya bita da kallo yana jin kamar ya jawota ya hanata tafiyar yace anan zata kwana. Sai dai babu yanda ya iya. Suna haɗa ido da Fawzan ya wani ɗage masa gira cike da tsokana, kafin ƙasa-ƙasa yanda kowa bazai ji ba ya ce, “Kota dawo ne Auta? Kaga sai ai amarcin a gadon asibiti kawai”.          Kunnen Fawzan Babban Yaya da yaji komai ya kama, a haka ya jashi yana faɗin, “Kai dai bakin nan naka ko”.      Dafe hannunsa Fawzan yay yana kiran Oum, yayinda AA ke murmushi da faɗin, “Babban Yaya dan ALLAH ka cire kunnen duka”.     Oum ce ta ƙwaci Fawzan a hannun Babban Yaya tana faɗin, “Haba Babban Yaya cire min kunnen yaro zakai. Kai kayi Auta yayi kun saka min shi tsakkiya”.        “To Oum ALLAH yaron nan ne Inaga sanda kikai wankan jegonsa baki gasa masa shi ba da ƙyau”. Ya harari Fawzan ɗin ya fice. Murmushi Oum tai ta kama Hannun Fawzan dake harrar AA dake masa murmushi da gwalo suka fice.........✍️           ALLAH ka bani aron rayuwa da damar gina Family ɗina like wannan zuri'a. ALLAH suna kasheni da ƙyaƙyƙyawar rayuwarsu🥰🥰🥰😘😀🥱. 09032345899 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_* *_Typing📲_* *_💞AJIYA A DUHU....💞_* *_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_* *_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_* _Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._ *_My TikTok account 👇_* https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1 *_Instagram👇🏻_* https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv *_Arewabooks_* Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30 *_WhatsApp channel_* https://whatsapp.com/channel/0029Vb1UKNuGk1FwLVPMgu2R _Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_ 🅿️➖1️⃣0️⃣3️⃣ ______________ ......Alhamdullah washe gari safiyar Lahadi kowa yay himmar kama gabansa. Duk da jikin AA baya gama yin ƙarfi bane dole Doctors ɗin suka sallamesa dan ya matsa. Ya kuma dage ko sun koma Abuja bazai cigaba da kwanciya a KK HOSPITAL ba kamar yanda suka so. Zama na musamman Baba Sardauna yay da su da Baban Yola. Sukai musu nasiha irin ta iyaye. Sun nuna musu su riƙe junansu da amana da haƙuri, kar su ɗauka wannan soyayyar da suke ma juna saɓani bazai shiga ba watarana. Ita rayuwar aure zomu zauna zo mu saɓa sunanta. Sannan ibada ce tana da banbanci da soyayyar waje. A karo na farko kuma AA ya bama iyayen nasa haƙuri. Ya kuma tabbatar musu zai riƙeta amana iya iyawarsa. Zai kuma basu mamaki in sha ALLAHU. Haka kuma ya roƙa gafarar Abah da Mamy da Oum harma da su Babban Yaya, amma bai fito ya faɗi dalilinsa na waccan dagiyar ba. Ya dai ce su yafe masa akan kuskurensa.       A take duk sukace sun yafe masa ai komai ya wuce. Sai dai Mamy dai ta ciki na ciki, dan ba ƙaramin a ƙule take da shi ba da wannan kauce-kaucen da yake na hana kansa koda haɗa idanu da ita da yake yi. Amma dai kamar yanda ta saba ta fuske abinta. Sai dai shi da kansa yasan ita ɗin BALBELA ce, wajenta fari cikinta baƙi. Ya kuma san ba lallai ta yarda babu haɗin bakinsa akan wannan aure ba, amma kuma ya ɗauri aniyar tunda fa ALLAH ya bashi to fa mutuwa kawai zata raba, sai dai Mamy ta yafe masa kuma. Dan ya tabbatar a yanzu mataki na biyu da zata bijiro masa da shi shine ya saki Maanal. Shi kuma magana ta ALLAH abunda ko a cikin ciwon hauka yake bazai iya ba kenan, da dai ba'a aura masan ba zai gwammaci yay biyayar ya rasa ransa kamar yanda yay ƙudiri a baya.      Bayan dai doguwar nasiha da addu'a sukai shirin wucewa airport. Masu aikinsu tuni sun kama hanyar Abuja a motoci kamar yanda suka zo. Su dai jirgi zasu bi. Hankalin Maanal ya fara tashi ganin har suna niyyar wucewa su Didi basu zo ba kamar yanda sukai mata alƙawari. Dan haka ta kasa dannewa ta tambayi Oum. Murmushi kawai Oum tai mata da tabbatar mata ai zuwa yanzu ma su Ammie suna cikin Kaduna. Dan tafiyar sassafe sukayi ma su sun bar Kano. Aiko sai Manaal ta sanya ma Oum kuka. Lallashinta Oum ɗin ta dinga yi, amma ina hawayenta sun kasa tsayawa. Ita gani take miyasa zasuyi mata haka, kenan haka za'a wuce da ita Abujan babu danginta ko ɗaya da nufin rakkiya kamar wata mara gata. Salon ma AA ɗin ya samu na wulaƙantata da jin ya sameta a banza kamar yanda ya tsara, dan ita fa har yanzu bata yarda dama RK da AA shiri sukai ba, tunda da bakinsa ya tabbatar mata kota halin ƙaƙa sai ta sameta. Sai kawai dan rainin wayo ranar ɗaurin aure ace mata RK ya sadaukar da ita ga AA kamar wata wayar salula ko motar hawansu...       To haka dai taketa wannan mita a ranta har suka fito domin tafiya. Tsabar son ƙular da AA sai tai wuff ta shige motar da Mamy ta shiga. Aiko Fawzan ya dinga kwasar dariya dan a idonsa AA ya wani waro ido na mamaki yana kallon Maanal ɗin. Daƙuwa Abah da shima abin ya bashi dariya yay ma Fawzan, shi kansa Baba Sardauna sai da ya murmusa. Haka kawai shi dai yake matuƙar jin ƙaunar yarinyar, sannan yin auren nan sai yake jin kamar an sauke masa wasu kaya ne da suka jima a saman kansa, sau kusan huɗu yana zuwa har saudia yana addu'a akan alaƙar AA da Maanal kawai, tare da fatan bayyanarsu garesu a duk inda suke. Dan a ganinsa bai kamata jininsu ya lalata yarinyar su kasa mutunta rayuwarta a ƙarƙashin inuwar aurensa ba. Shi kansa Abah ji yake ko yanzu yabar wannan duniya burinsa ya gama cika, fatansa ALLAH ya basu zuri'a masu albarka su da su Fawzan.       Da suka fa iso airport ne duk kauce-kaucen Maanal dole a waje ɗaya suka zauna da AA. Sai dai inda ALLAH ya taimaketa akwai Naufal a tare da su, sai kawai ta canjama yaron sit ya koma tsakkiyarsu. Kallonta kawai AA keyi ta gefen ido, amma bai tanka ba. Data zauna ma sai ta ƙirƙiri barcin ƙarya tabarsa da surutun Naufal ɗin. Sun sauka garin Abuja a mintoci. Inda Alhmdllh suka samu drivern Abah da su AS na jiransu domin tarba. Dan abin sha'awa motocine reras har goma ciff idan ka cire drivern Abah da Uncle Sadeeq mijin Didi Shahidah sauran duk staff ɗin Mawaad Company ne. Har cikin rai Maanal taji sanyi da zuwan Uncle Sadeeq ɗin. Dan ya dai kankaro mata mutunci itama. Aiko Oum itama sai tai yakana ta saka Maanal ɗin a motarsa, itama ta shiga. Sauran kuma suka shiga sauran motocin harda AA daba haka yaso ba.             Har ƙaton harabar gidan duka motocin suka shiga. A mamakin AA da Maanal Oum ta shige sashenta. Shi kuma akan barsa da ma'aikatansa dake ta masa yaya jiki da addu'oin samun lafiya mai ɗorewa. Sai da komai ya lafa suka wuce har Uncle Sadeeq sannan Fawzan ya taimaka masa zuwa upstairs dan jikinsa babu wani ƙarfi har yanzu ƙarfin hali ne kawai...... __________★         A ɓangaren su Hajiya Basariyya suma yau dai suka koma Kaduna. Dan tazararsu da su Ammie kaɗan ne. Sai dai kuma Daddy ya kafa ya tsare yace Hajiya Basariyya bazata shigar masa gida ba ita da Hajiya Yaya tunda bai san da zuwansu Kano ba. Aiki rigima ta kaure shi kuma yasa aka rufe masa gate ɗinsa. Dole Hajiya Yaya tai kiran Babbanta a waya. Ganin haka sai itama Hajiya Basariyyar tai kiran yayanta tana masa kuka. Kamar haɗin baki duk basu sauraresu ba sukace sai sunji ta bakin Daddy, dan haka su kamo hanya su taho gidan da yace. Hankulansu ya sake tashi amma sun san dole suyi hakan tunda iyayen nasu suka basu umarni......      A cikin gida kuma su Shahidah na sashen Ammie suna ƙoƙarin kimtsawa ita tana sashen Daddy suna tafka rigima tana masa kuka akan ya saka maigadi ya buɗema su Hajiya Basariyya gate. Shi ko yay mata banza, data damesa ya buɗe mata wuta akan babu ruwanta. Ita kuma cikin fushi tace bazata zauna ba itama tafiya zatai. Randa ya shirya su dawo sai su dawo gaba ɗaya. Shi kuma cikin ɓacin rai ya rantse mata in har ta fita sai ya bata mamaki tunda tsoron su Hajiya Basariyyar take.          Sosai ranta ya ƙara ɓaci, ta wuce sashenta tana kuka. Ta ce su Shahidah su shirya su wuce gidajensu. Kamar Daddyn ya sani sai gashi a sashen. Yace bata isa ba babu inda zasu sai sun gama abinda suke yi. Kai koda ma yau ɗin sukai niyyar tafiya shi ya hana hakan. Suma hankalinsu ya tashi da ganin abinda basu taɓa gani ba tsakanin Daddyn da Ammie. Kai ko mahaifinsu a sanda yake wulaƙantata bata yarda ta nuna musu. Hankali tashe Shahidah tai kiran Nene da suma suka wuce nasu gida ita da zuri'arta ta sanar mata. Tashi sosai hankalin Nene yayi ta kira Ammie a waya. Itace ta mata faɗa da nasiha ta kwantar mata da hankali, tare da gargaɗinta fita a abinda babu ruwanta. Can tsakaninsa ne da matansa ta saka musu ido. Wannan faɗa na Nene ya saka Ammie haƙurin dole..... ______★         A can kuma Kano dangin Nuratu sun gama shirinsu na tahowa Abuja suma, dan suna akan bakansu na aure a sati mai zuwa babu fashi babu canji kamar yanda Mamy ta ɗorasu...........✍️     _Hummm tofa tirƙa-tirƙa kenan. Masu karatu Amin afuwa, Amin afuwa zan dakata anan. Duk da naso gama book ɗin nan gaba ɗaya amma na fahimci yin haka zai tarwatsa ginin labarin tun farko ƙarshen yazo bai gamsar da ku ba. Ni kuma ba haka nake buƙata ba. Ni kaina ban san zai yi tsawon haka ba labarin nan. Amma tarihinsu ya wawurar mana kaso mai yawan gaske wlhy🥺. To wannan fa shine kana naka ALLAH na nashi. Dan haka ina sake neman afuwarku muyi hakuri sai zuwa bayan salla idan muna da sauran rayuwar kaiwa, muna ma fatan kaiwar in sha ALLAHU 😥🙏. Nafi son labarin ya gamsar damu yanda ya kamata kamar yanda ya faro kansa ne shiyyasa._ Kar ku manta shi kansa part 2 ɗin ɗauke yake da tirƙa-tirƙa tasa ta kansa.   Yaya zaman AA da Maanal zai kasance. Zai yi maganin ƙudirinta da wuri kodan lagon soyayyar da take masa duk da yana basarwa da dannewa😆🥰? Yaya batun aurensa da Nuratu, zai yiwu kuwa? Kun dai san mamy bata wasa bace😆🥺😩. Yaya Mamy zata haƙura ta amshi Maanal kokuwa itama zata fiddo mata da ainahin halinta ne kamar yanda AA ya sani? Idan ta fito ɗin yaya zasu kwashe da Maanal? Kun san fa ance ko Giwa ta faɗi tafi ƙarfin wawason karnuka. Da alama AA na shirin farfaɗo mana da Maanal ɗin data mutu a baya mai tsiwa da rashin ragowa. Dan haka tsakaninta da Saheeba da Nibras fa akwai zazzafan wasa dan za'a zuba facalanci ne fa zazzafa, saboda kowa da nasa ƙudirin akan Maanal tsakanin Saheeba da Nibras. Humm gidan Ambassador Aliyu Darma fa zai koma ƙarƙashin jam'iyu guda biyu ne. Itama Oum ta samu mai tayata faɗa a yanzu wato Maanal, kunga kuwa dole a buga zazzafan wasa dan Mamy zata shigo da sabon salon da dole ne Maanal ta shiga wasan....🤣👍 A ɓangaren dangin su Maanal ya zasu ɗauki wannan aure da basu san anyi ba. Dan kar ku manta Senator Bukar fa ya basu lokaci, tare da kuɗi kuma kun san sai sun ci kuɗin nan. Shi ko bai gaji asara ba dole ai masa aman kayansa...🤣👍 Ɓangaren Babu kun dai san alƙalamin Bilynku baya yafiya, dole kowa ya girbi abinda ya shuka. To dole fa Babu sai ya biya bashi shi da Gwaggo walle😌😆🏃 Hummm mai kankat, rayuwar Maawad Company, yaya zata kasance tsakanin waɗan nan masoya biyu a yanzu, idan kuma Mamy tasan AA ya jima da raba Company biyu rabi nasa rabi na Maanal har anyi komai a rubuce tasa hannu ya saka yaya kuke gani🤣😌👍?. Yaya soyayyar Najma da Fawzan zata kasance? Mi kuma kuke tunani idan aure ya ƙullu? Oum nada Maanal da Najma kenan a jam'iyyar ta. Mamy nada Saheeba da Nibras ga Nuratu idan ta shigo🤪🤣👍. Sai amarya Huznah a gidan Man Sageer. Auren can zai rabu kuwa? Zata haƙura da AA ko kuwa alkawarin da uwarta tai mata da ƙawarta zai cika🥱?. Ɓangaren Hajiya Yaya, itama fa akwai zazzafan wasa tsakaninta da tata surukar idan sun gama shan honeymoon sun dawo. Hakama tsakanin uban Nazeefa da Daddy akwai zazzafan wasa. Shi kansa Yazeed ɗin fa. Hummmm zai bama kowa mamaki💃💃💃🤣👍 Kudai karna cikaku da surutu, muyi fatan ALLAH ya kaimu bayan salla da rai da lafiya. Ya rabbi kasa muyi ibada karɓaɓɓiya. Ya rabbi kasa mu kasance a cikin ƴan tattaun bayi a wannan wata mai albarka. ALLAH kasa mu zama jajirtattu a wajen ibada🙏. Dan ALLAH ina barar addu'ar ku dukkan masoyana koda a ranar farko ce ta azumin. Har ƴan bati a min dan ALLAH 😌 tare da al'ummar Musulmai baki ɗaya 🙏. Ina ƙara dai neman afuwarku Please Please nasan wasu zasuce ba haka sukaso ba. To ayi hakuri, ayi hakuri kamar yau ne zamu dawo in sha ALLAHU.🙏🙏🙏 San so, ƙaunar ƙauna Zafafa ke muku baki ɗayanmu kamar yanda kuke mana❤️🥰🥰🥰🥰🥰🥰🙏             Bilyn Abdull ce😘               Kumuje zuwa book 2 🏃🏃🏃             09032345899     *_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*